Follow us on social media
Showing 18001 words to 21000 words out of 147042 words
Chapter 7 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
ce in ta haifi namiji sunan yaro Muhammad Lamiɗo in mace ce kuma Ummu-Kursum shi ya sa lokacin da ta iso Jimeta ta ce ma Baffa ya yi ma jaririn huɗuba da Muhammad Lamiɗo, ko ba ya raye za ta saka masa da ƙaunar da ya nuna mata wajen cika wasiyyarsa.
Ita ce za ta ba da labarin mutuwa mai tonon asiri domin mutuwa ce ta yi sanadiyar tonuwar asirinta, ta yi sillar gurbata rayuwar farincikinta zuwa baƙin ciki, ta wani bangaren kuma hakan ya yi sillar sauya rayuwarta daga wannan Fatimar yar mubi bafullatan ƙauye mara ilimi zuwa wata Fatima ta dabam da ta samu cigaban rayuwa ta ƙo'ina. Tabbas ta wannan bangaren za ta gode musu domin sun ma yar da rayuwarta yadda ba taɓa tunanin komawa ba.
Kimtsa kanta ta yi, gilashinta ta fiddo a cikin jaka ta saka saboda kauda idanuwan mutane a kanta bayan ta duba madubin motar ta ga idanuwanta sun yi jajir, sannan ta ɗau jakarta ta fito daga cikin motar ta yi amfani da key ɗin ta rufe motar. Tana fara takawa zuwa office ɗin ta daliɓan da take ɗauka yan level 1 suna ta gaishe ta ita kuma tana amsawa cikin sakewa daliɓai suna son ta saboda tana da sauƙin kai da taimako har malaman ma sun san Dr Fatima Baba wajen karamci da kyautatama duk wanda take tare da shi.
****
Su Ammah sai da suka yi kwana goma sha ɗaya sannan suka dawo, washegari Ummu-Salma ta je yi mata sannu da dawowa. Ta iske kayan biki niƙi-niƙi ga su nan a ɗakin Ammah har da bag da aka raba mai ƙaton hoton Amarya a ciki ake saka atamfa mai kyau da mayafi har da turaruka, ga kayan su fulawa tun da ta zo Ammah ke ba ta labarin abin da ya faru a wajen bikin nan, Hamma Sadam ma ba a bar shi a baya ba shima yana ɗorawa da na shi, su Ammah fa kaya suka dawo da shi niƙi niƙi ita da Ummin ikki, bayan kala ukun da aka yi musu Fulani ta ba su turame goma da dubu 200k Maimartaba Sarki ya ba su naira dubu 500k tukwaici Gimbiya Shahida ma da turamen zannuwa 20 da kuɗi har shaddodi aka ba da aka wo ma Baffa sun je ɗaurin auran amma tare da Hamma Abdullahi, Hamma Abdulrahaman bai samu zuwa ba, shi kan shi Hamma Sadam shaddoji sun fi kala biyar sabbi gezner masu tsada da takalma haɗe da hulana da ya dawo da su, cikin jin daɗi suke ba da labarin zuwan su Daura da man haka ne in dai Ammah ta je to haka za a rako ta da kayan arziƙi niƙi-niki Ammah kuma ta shiga rabo gidajen yan'uwa da Dangi, har can Mubi saƙon na iske musu. Ta ciccire ma su Umma Balki na su kason, da matan su Baffa Umaru.
Duk da ba ta samu zuwa ba tare da na Umma Salamatu da Umman A'i, Hamma Sadam ne zai je ya kai musu gobe, jibi zai koma makaranta.
Sannan ta ɗibar ma matan su Hamma Abdullahi, ita dai Adda Nauwara an ba ta na ta acan, amma na su Hamma Kabiru da Mustapha Amma ta ajiye musu abin biki, ita kanta Ummu da ta je an ba ta jaka da kayan fulawa sai turare. Sannan ta karɓan ma Baɗɗo itama.
"Amma na Bestie fa?
Amma ta ce za ta ijiye mata in ta zo da kanta sai ta ba ta.
Ummu tura baki ta yi kafin ta ce" Amma ni zan ci ne? Zan ajiye mata ne tana can makaranta sun kusa farawa jarabawa."
Amma ta ce Allah ya sa a yi cikin sa'a amma ba za ta ba yar ba.
"To na Noori na Ammah."
Ummu ta faɗa, Amma ta yi mata wani kallo kafin ta ce" Waye kuma haka?
Ummu na dariya ta ce" Kai Amma Habib ɗin ne ba ki san sunan shi Noori ba?
Ammah ta aika mata da daƙuwa kafin ta ce" ƙaniyar ki Ummu Salma."
Sai ta fara dariya ƙarshen ta dai sai da Amma ta ba da nashi shima tana cewa" Ya kira ni ina can ya gaishe ni, ya cancanci ya samu tsaraban Daura."
Saboda tana so ta tsokani Ammah ya sa ta sake cewa " Amma to ina na Mami na? Na ga ba ki cire mata ba ne"
Wannan karon sai da aka wurgeta da mafici sannan aka ce" Mamiyo, in tana son tsaraban me ya hana ta je da kanta? Uwar nan taki zuciyarta ba ta da kyau ko a waya ba ta kira ni ba, nima ko na ce ba zan kira ta ba ina nan za ta zo ta same ni."
Ummu ta gyara zama tana faɗin" Ammah to suma sauran da kika ba su ai ba su je ba."
Ta gama faɗa tana tura baki.
Amma ta miƙe ta fice tana faɗin" Ba zan ba yar ba, na ƙarfi ne ki ƙwatan mata mai uwa."
Ta fita ta bar Ummu na dariya da man ta san ba za ta ajiye mata ba amma ta yi son kai za ta aika da shi Mubi, ita Mami ko oho.
Ummu har dare tana gidan, labari kam sai da ta gaji da shi, Hamma Lamiɗo dai bai zo ba wai yana cikin aiki, matar shi ce dai ta samu zuwa da yaran shi itama Ammah ta ce ana gama biki daga Abuja ta hau jirgi ta koma Lagos saboda aikinta.
Da man Baffa baya nan ko da Ammah ta dawo ya je kwatano
Habib ya zo ya ɗauki Ummu da yamma, daga nan suka ƙarisa gidan iyayen shi dake anguwar Doubeli, Baban Habib ya tsufa yana zaune ma ba ya iya tafiya mahaifiyar Habib ce ta rasu, amma akwai sauran mata uku a cikin gida. Suna da yawa wasu duk sun yi aure mata da mazan wasu kuma yanzu suke tasowa. Da ya ke lokacin da aka yi ma Ummu buɗar kai(Fansa) akwai sunan da suka sanya mata bisa al'ada Tafisu da shi duka ahalin Habib suke kiranta da shi, shi ya sa in dai ta shiga cikin su ba sunan ta Ummu Salma ba, sunan ta Tafisu nan suka yi dare sai wajen tara na dare suka koma gida.
Duk kuma gajiyar nan da Ummu Salma ta kwaso bai saka Habib ya ɗaga mata ƙafa ba, har mamakin shi take yi ba ya gajiya, in har Habib bai kusanceta ba sai dai in tana jinin haila ne, shima ɗin saboda ba shi da yadda zai yi ne ammaa kafin ta samu tsarki duka gabban jikinta sai sun koma suna raɗaɗi saboda yadda suke shan yamutsa ba ya barin ta sukuni ko kaɗan shi ya sa har yau ta saka kumarin nan na masu aure ga shi sun kwarari wattani takwas da yin aure, ko lokacin da ta samu ciki da ga samanta ne kawai ta yi kiɓa amma ban da jikinta, irin yadda Habib ke matsa mata lamba ba lalle ta yi kumari ba, abu kamar cin tuwo ba ya gajiya.
Kuma har lokacin tana jin wannan sauye-sauyen a jikinta amma tun da ta yi gwaji ta ga ba haka ba ne sai ba ta saka ma kanta tunanin komai ba.
Ta fi danganta hakan da rashin hutun da Habib ba ya bari gangar jikinta ya samu shi ne dalili.
Abin da ba ta sani ba shi ne tana da shigar ciki. Dalilin wannan cikin rayuwarta za ta juye daga farinciki zuwa aƙasin hakan.
****
Jalingo street.
Tun jiya da daddare take fama da tashin zuciya amma ba ta damu ba, ta fi danganta hakan da soyayyen ƙwan da ta ci da safiyar ranar ne, can kuma da rana da ta sha zoɓo sai tashin zuciyar ya kwanta har dare da Habib ya dawo ba ta sake ji ba, da safe kuma da tashi sai kasala duk ya rufeta miyau na taruwa a bakinta sannan da zafin jiki ta kwana, Habib bai sani ba kuma bai hana da asuban ya sake nemanta ba, wani abu ke ba ta mamaki a group ɗin makarantan su na sakandiri mai suna Ahmadu ribaɗu Collage wanda suka buɗe na mata zalla akwai matan aure kuma tana gani suna hira, wata Aisha Iro ta taɓa tambayan cewa mijinta sai su yi kwana biyu bai neme ta ba, hakan ba matsala ba ce, nan fa aka yi ma tambayar caa, kowa na faɗin albarkacin bakinsa.
Mafi rinjaye sun ce ba wani abu ba ne, domin rayuwar aure ba domin saduwa ba ne, zamantakewar aure ibada ne. Wasu ma suna ta cewa sai su yi sati kuma ana zaune lafiya, sai dai a yi romance kawai a kwanta tun lokacin da ta ga maganganun su abin ya tsaya mata arai, ba ta taɓa tattauna wannan matsalan da kowa ba sai Baɗɗo ita kuma ba aure ta yi ba sai ta nuna mata wataƙila Habib na cikin maza mabuƙata, ko Bestie ba su taɓa maganar da ita ba amma lamarin na damun ta, ba ta nemi komai ta rasa ba, ba abin da Habib ba ya yi mata matsalanta da shi kawai wannan bangaren ne, kamar wata machine haka ya ɗauke ta kwata-kwata ba ya barin ta samu hutu, tana haɗa musu abin karyawa tana ta tunane-tunane a cikin ranta, ta taɓa yi masa mgana tun farkon auren su ya ce ta shirya mijinta mai yawan buƙata ne amma ita a ganin ta buƙatar ta shi ta yi yawa ne.
Indomie da ƙwai ta dafa ma Habib ba ta jin daɗin jikinta shi yasa ba ta yi dogon breakfast ɗin da zai ba ta wahala ba, sai ruwan tea da ta dafa masa sai da ta jera komai saman dinning sannan ta koma ciki ta tashe shi, wajen taimaka masa ya yi wanka ma sai da ya maimaita a tiolet, in Ummu ba ta furta ta gaji a baki ba gangar jikinta ya nuna gajiya da jarabar Habib, shi ya fara tsarkake jikinsa ya fito ya bar ta a cikin tiolet tana jin kirjinta da kanta sun yi mata nauyi.
Ko da ta fito har ya shirya kan shi cikin suit, ko yadda ya ganta ta yi wani suku-suku ba fara'a bai damu da ya tambayi dalili ba, faɗa mata yake yi ta yi sauri kar ya makara.
Wata riga mai gajeren hannu doguwa ta saka sai hula ta rufe gashin kanta dake jiƙe sai ta sallame shi ko za ta dawo ta busar da shi.
Tun da suka zauna saman Dinning karnin Dafaffen ƙwan nan ya dame ta, ba ta ma saka ma kanta shi ba, indomie ɗin kawai ta zuba wacce ta dafa tare da su carrot da greenbeans, tana kai cokali na ɗaya biyu, na ukun ne ya gagare ta haɗiyewa tuni ta ji kayan cikinta sun fara yamutsawa da gudu ta tashi ta faɗa tiolet kafin Habib ya samu damar mgana ya ji Ummu na ta sheƙa amai kamar za ta amayar da kayan cikinta.
Da sauri ya tashi daga zaman karyan da yake yi cikin mamaki ya bita tiolet ɗin amma daga baƙin kofa ya tsaya.
"Baby me ke faruwa? Wani abu kika ci?
Ya faɗa cikin bayyana damuwa a muryansa. Kuma damuwar har ya bayyana a saman fuskar shi.
Ba ta ma san yana yi ba, tana duƙe tana sheka amai sai da ta amayar da duk abin da ke cikinta sannan ta samu sukuni, ruwa ta buɗe a famfon sink ɗin ta wanke bakinta sannan ta kora Aman ta ɗago tana haki ta nufo hanyar fitowa jiri ya ɗebe ta za ta faɗi Habib ya yi saurin riƙo ta.
"Baby me ke damun ki ne?
Are you sick?
Ummu da saurin kuka tuni ta lafe a jikin shi ta fashe masa da kuka.
"Ni ma ban sani ba Noori amma ina jin jikina duk ba daɗi."
Ta faɗa cikin shagwaɓa, tarairayota ya yi suka dawo falo ya zaunar da ita akan kujera ya zauna a gefenta yana mai ƙura mata ido.
Gabansa ya faɗi kar dai a ce Ummu Salma wani cikin ta samu? Da ko ya shiga uku.
Da sauri ya tallabo fuskarta da duka tafukan hannayensa kafin ya ce" Baby yaushe rabon ki da ganin al'adan ki?
"Tun bayan ɓarin da na yi sau ɗaya na yi Noori."
Ta faɗa tana wani lumshe idanuwa har ga Allah jikinta ba ya yi mata daɗi so take yi ta kwanta.
"Ummu-Salma ko ciki ne da ke?
Ya faɗa cikin wata murya mai cike da fargaba.
"Ban sani ba, nima kwanaki na yi tunanin haka sai da na siyo PT na yi gwaji sai na ga babu komai."
Ta faɗa cikin sanyin murya tana mai ɗora kanta a saman kafaɗanta.
Duk da haka bai gamsu ba, sake ɗagota ya yi yana sake ƙare mata kallo.
"Noori ka bar ni na kwanta jiri nake gani."
Ta faɗa cikin shagwaɓa shi ba ma ta ita yake yi ba kirjinta yake kallo sai a lokacin ya lura kirjinta sun tasa bai taɓa lura da hakan ba.
"Wani yanayi kika ce kina ji a jikin ki?
Ya tambaya agaggauce.
Ita ko Ummu Salma ta ɗauka duk murna ce ya sa cikin sanyin murya ta amsa shin
"Noori ina ji fa ba ciki ba ne, na faɗa maka na gwada ba komai."
"Ki amsa mini tambaya ta."
Ya katse ta da sauri, numfashi ta fesar kafin ta shiga faɗa masa yanayin da take ciki ai tun kafin ta ƙarisa ya miƙe da sauri ya koma cikin bedroom ɗin su, da mamaki ta bi shi da kallo ganin ya fito da Hijabin ta a hannun shi da key ɗin motarsa lokaci ɗaya yana faɗin.
"Tashi mu je asibiti a yi gwaji."
Cikin mamaki take bin sa da kallo ba ta samu damar mgana ba har ya zura mata hijabi ya koma ciki ya ɗauko mata takalmi jikinsa sai rawa yake yi kamar mazari.
Tausayin shi ya kamata lokacin da ya duka yana zura mata takalmi kansa ta shafa lokaci ɗaya tana faɗin" Ka kwantar da hankalin ka Noori."
Miƙewa ya yi lokaci ɗaya yana kama hannunta ta miƙe tsaye ba tare da ya amsa mganar ta ba.
"Ka ji ?
Ta sake faɗa bayan ta riƙo hannunsa guda ɗaya kallonta ya yi duk ya firgice a cikin ƙanƙanin lokaci.
"Hankalina ba zai kwanta ba sai an yi gwajin nan."
Ya faɗa da sauri lokaci ɗaya ya ja jakarsa dake gefenta ya rataya, riƙe da key ɗin mota a ɗayan hannun na shi, ɗayan kuma ya jawo hannunta. Ita ce ma ta ce ya tsaya ta kashe kayan wuta sannan ta ɗauko key ɗin gidan suka fita tare ta rufe suka rankaya motarsa ƙirar Benz har suka ɗauki hanya bai sake yi mata mgana ba hankalinsa duk ya tashi sai faman gudu yake yi a titi
Ganin haka ya sa Ummu ta kama hannun shi dake saman sintari sai ya juyo yana mai kallon ta.
"Noori."
Da sauri ya katse ta da faɗin.
"Boshon clinic za mu je ko?
Sai ta gyaɗa masa kai kafin ta ce" E. Ai can na ke da fayel."
Daga nan bai sake magana ba hankalinsa na wajen tuƙi amma daga ganin shi ba ya cikin natsuwarsa.
"Noori ka kwantar da hankalin ka, in ba cikin ba ne ma in sha Allahu na kusa samu."
Wani irin kallo ya yi mata kallon da ba ta taɓa ganin ya yi mata irin shi ba za ta sake mgana ya ɗaga murya yana faɗin.
"Ki bar ni, ba ki ga ina driving ba ne."
Sai da ta kalle shi cikin mamaki shi kuma ba ya ma cikin natsuwarsa ballanta ya ji ba daɗi kan ɗaga mata muryan da ya yi.
Idanuwanta suka cika da kwalla, tausayin Habib ya kamata yanzu in suka je asibitin suka ce ba ciki ba ne fa? Wani hali zai shiga sai ta koma addu'an Allah ya sa ciki gare ta, ko domin hankalin Habib ya kwanta daga gani ya ƙwallafa rai akan samun cikin ta.
Abin da ba ta sani ba, tunanin da ke zuciyar Habib kishiyar tunanin da ke zuciyarta ne.
****
BOSHON CLINIC.
Suna isa asibitin sai da suka sake siyan kati saboda sauri sun manta da shi a gida. Bayan Ummu ta ga likita ta yi mishi bayanin duk abubuwan da ta ke ji a jikinta nan take ya saka aka ɗibi jininta zuwa lap, ya ce su ɗan jira sakamakon ya fita.
Da yake asbitin na kuɗi ne ba wani ɓata lokaci, suna waiting area suna jira Habib ya kasa zaune ya kasa tsaye, tana shirin ta ce masa ko zai bar ta ne ya tafi wajen aiki in ta karɓi result ɗin sai ta nemi Napep ɗin da zai kaita gida kafin ma ta yi mgana ta ji yana waya yana cewa ba zai shigo office da wuri ba shi ya sa sai ta yi shuru da bakinta.
Ita dai tana zaune saboda ba za ta iya tsayuwa ba, Habib kuma ko ya zauna sai ya tashi ya kasa zama a waje ɗaya tuni farar fuskan shi ta bayyana halin damuwar da yake ciki. Ummu na zaune tana bin shi da kallo tausayin shi take ji ta cikin hijabin ta, tana ta shafa cikinta a cikin zuciyarta take faɗin.
"Allah ya tabbatar da cikin nan."
Da ace Ummu-Salma ta san gaibu, da ace ta san fargan jajin da ke jiranta da ba ta yi ma kanta wannan addu'ar ba, da ta yi addu'an in ma cikin ne Allah ya sa ya bi rariya.
Zaman jiran mintina arba'in suka karɓi sakamakon gwajin. Bakin Ummu ya ƙi rufuwa tun bayan da likita ya ce tana da ciki na wata ɗaya da kwanaki, an rubuta mata magungunar karin jini da cin abinci, sai vitamin e, amma murnanta sai ya koma ciki na ganin fuskar Habib ta yi baƙiƙirin kamar an faɗa masa saƙon mutuwa, ita da ta yi tunanin yana jin tabbacin tana da ciki sai ya ɗaga ta sama ya yi juyi da ita, amma sai ta ga saɓanin tunanin ta, amma sai ta ƙarfafi kanta da cewa haka ya yi a cikin ta na farko lokacin da ya ji labari bai nuna murnansa ba amma lokacin da ya tabbatar da ta yi ɓarin shi ya fi kowa damuwa, ya yi jinyar ta har sai da ta warke da jikinsa da aljihunsa tunda ta kwanta asibiti wajen kwana uku aka ƙara mata jini, tun a lokacin likitan ya ce ta rasa jini da yawa. A lokacin ma jinin Hamma Kabiru aka saka mata tunda sun gwada na su Hamma Abdullahi bai yi mata ba, ita