Follow us on social media

Showing 51001 words to 54000 words out of 147042 words

Chapter 18 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar

yi sallama har ƙofar gida su Baffa suka raka su, Alhaji Sheriff ya shiga motarsa shi ya fara tafiya sannan su daga baya, har sun shiga mota Baffa ya ƙwanƙwasa ma Habib gilashin mota ta bangaren sa, bayan ya zuge gilashin Baffa ya kalle shi lokaci ɗaya yana kallon Ummu kafin ya kira sunan shi.

"Habibu"

Ya amsa ƙansa na ƙasa amma a cikin zuciyarsa faɗi ya ke yi an fa dame ni

"Kai ne da kanka ka zo ka ce kana son Auta na kuma ba ka ita cikin yaƙinin cewa za ka iya riƙe mini ita amana. Ko ba haka ba?

"Haka ne"

"To ina so ka sani amanarta da na baka tun ranar da ta tashi a ƙarƙashin ikona na ke so ka sake tunawa. Habibu kar ka saka na ji na sare bisa yaƙinina akan ka, don Allah ka riƙe mini Ummu bisa amana da gaskiya."

Baffa ya ƙarishe faɗa cikin magiya, Habib ya kalle shi yana masa mirmishin yaudara da bai kai zucci ba kafin ya ce" In sha Allahu Baffa"
Baffa ya ji daɗi har ya miƙa masa hannu suka sake musabaha yana ɗaga musu hannu suka bar ƙofar gidan  Baffa Umaru yana gefe kamar an kira shi a waya ne yana ta mgana.

Suna fita daga kwanar anguwan Habib ya kalli Ummu kafin ya ce" Me ya sa kika ɓoye ma iyayenki gaskiyan manufata a kan aurana da ke?
Ummu ta ɗago tana kallon shi cikin mamaki murna take yi na ganin komai ya daidai ta tsakanin ta da Habib amma kalamsa sai suka ruguza murnan ta da saka ranta.

"Me ya sa ba ki faɗa musu cewa bana son ki ba sannan kin rufe musu ba auran soyayya na yi da ke ba, auren shaa'awa ne. Me ya sa ba ki sanar da su gaskiyan mganar ba?

Ya sake jefo mata tambayoyi, kanta na ƙasa tana wasa da gefen hijabinta ta ce" Saboda ina tunanin ba gaskiya ka faɗa ba, kana dai fadin haka ne saboda na ƙi bi umarnin ka na zubar da cikin jikina."
Habib ya kece da wata dariya kafin ya ce," Har yanzu ke a tunanin ki wasa na ke yi dake Ummu Salma?
Lalle ko ba ki da hankali na kuma yadda ke ɗin shashasha ce."

Ya fada har yana buga sitiyarin mota, Ummu ta kalle shi idanuwanta da hawaye kafin ta ce" Ka kirani da kowani suna ban damu ba. In dai har zan cigaba da zama a ƙarkashin ka, sannan zan tsira da cikin jikina na yarda ka kirani da kowa ni suna har wanda ma ya fi shashasha"

Kallon ba ki da hankali yake yi mata ita kuma kawai sai ta kece masa da kuka.

"Habib ka san ina son ka? Kai ma kana sona me ya ka sauya! Ni ce fa Ummu salman ka?

Ta ƙarishe faɗa cikin kuka, sai ya sake yin dariya kafin ya ce" Lalle ba ki da hankali."
Haka kawai ya ke faɗa lokaci ɗaya yana kallonta kuma yana dariyan haushi da takaici.

"Na ji ba ni da hankali in dai akan ka ne Habib. Na ji ka ma ce na haukace duk na yarda da haka amma don Allah ka saurara mini haka nan na azabatu don Allah Noori."

Yadda take marairaicewa ne ya sake tunzura shi, a fusace ya daka mata tsawa.
"Wallahi bana son ki, bana sha'awan sake wani sauran zama a tsakanina da ke."
ƙasaƙe Ummu ta yi tana kallon shi hawaye na kece mata wasu na zuba wasu na sake tunkuɗowa.
Gefen titi Habib ya gangara ya kashe motan ya gyara zama yana sake kallon Ummu tana kuka kamar ran ta zai fita.

"Ko zuwa gidanku da kike ganin na yi kina jin daɗin watakila na sauka daga kan kudiri na ne, to gwara ki daina murna ki dawo cikin hayyacin ki, sannan ki sake buɗe kunnuwan ki da kyau ki saurare ni."

Ya faɗa yana karkaɗa kunnunsa guda ɗaya sannan ya cigaba da faɗin" Na bi umarnin Abba ne saboda shima nan gaba zai yi mini wani amfani saboda ke kuma ba zan ɓata gobe na ba, amma wallahi tallahi ban sauka daga kan kudirina ba. Bana son ki sannan ba na son cikin dake jikin ki, sai dai ina so ki sani daga yau ba zan sake matsa miki akan zubar da ciki ba da kanki za ki yi nadamar taurin kan da kika yi mini. Ke ba ki ga komai ba yanzu ne za a fara wasan Ummu Salama."

Ya ƙarishe faɗa yana yi mata wani irin kallo har yana kashe mata ido ɗaya.

"Ka san da haka me ya sa ka amsa ma  Baffa da cewa za ka riƙe ni bisa Amanar da ya ba ka?

Ta tambaye shi cikin kuka, ƴar dariya ya yi kafin ya ce" Ummu in kin koma gida ya kamata ki koma makaranta ki yi karatu mai zurfi wataƙila zuwa lokacin za ki fahimci komai."
Kallon ban gane maka ba ta yi masa sai ya girgiza kai lokaci ɗaya ya ta da motar suka fara tafiya.

"Har sai na faɗa miki maganganun babanki da na yayansa ne ma ko ƙaninsa duk sun shiga ne sun fita? Sai na faɗa miki ni da man ban karɓi amanarki tun farko ba, abin da ya sa na aure ki jikin ki, kuma sadaki na biya sannan more komai, ai amanar kenan bayan na gama amfana dake zan mayar masa dake gidansa."

Ummu ta yi ƙuru tana kallon Habib, hawaye suna kwaranya a saman kumatun ta.

"Don Allah kar ka rabu da ni Habib.'

Ta faɗa cikin matsanancin kuka.

"Kar ki damu da sauran lokaci ai ba ki gama yin nadama ba. Sai na tabbatar da kin yi nadaman taurin kan da kika yi mini sannan zan ba ki sakamakonki ki ƙara gaba. Wataƙila a lokacin za ki ji kin tsane ni har ki fahimci da gaske na ke yi wannan manufar tawa da gaske na ke yi a kan ki."

"Habib kar ka lalata mini rayuwata don Allah"

Ummu Salma ta faɗa tana ji kamar ranta zai fita daga gangan jikin ta.

"Ni kuma in ban yi haka ba tawa rayuwarce za ta lalace ki gane mana. Ni tawa rayuwar ban ma fara ba ke kuma tunda kin fara taki ki bari kawai na ƙarisa lalatata gabaɗaya kowa ma ya huta."

Ya ƙarishe faɗa har yana shafa kumatun ta, kuka kawai Ummu Salma take yi kamar za ta shiɗe mai fitar da sauti. Habib na ta dariyan nishaɗi daga ƙarshe ma sai ya ƙure wakar Auta waziri na Autar mata ba ya son jin kukan ta, tana damun shi har suka isa gida ba ta daina kuka ba ta ɗauka yana ajiye ta sai juya amma ina tana saka ƙafa a bedroom ɗin ta yana shigowa tun da ta ga ya tura ƙofa yana nufota ta san manufarsa.

"Tunda ka ce ba ka sona to jikina ya haramta a gare ka Habib."

Ta faɗa lokaci ɗaya tana kuka samnan ta ƙamƙame jikinta da hannayen ta.

"Allah? To ai saboda jikin na ki na aure ki, kin ga kenan ba ki isa ki hana ni more abin da na biya sadaki saboda shi ba."

Yana gama faɗin haka ya tura ta , ta faɗa saman gado ya bi ta ya danne da ƙarfin tsiya yake so ya haye mata ta fara mutsu mutsun hana shi cimma burin shi a zafafe ya kifa mata maruka biyu a saman fuskarta.

"Saboda jikin ki na aure ki, saboda haka in kika kuskura kika sake saka mini hannu sai na yi miki illah."

Ummu-Salma ta ji kamar duniyar ta tsaya mata cak, tana mai kallon Habib da idanuwanta masu zubar da ƙwalla, ko motsin kirki ba ta ƙara yi ba har Habib ya raba ta da kayan jikinta ya biya buƙatan shi son ran shi ya tashi ya bar ta nan, hawaye ne masu zafi suke zubo mata ta gefe da gefen fuskarta. A cikin zuciyarta take jin wani irin zafi zafin da ba ta taɓa jin irin shi ba tun da Amma ta kawo ta duniya, ta yi kuka ta yi kuka kukan nadama da baƙin ciki sannan a karon farko ta ji ta fara tsanar Habib, tunda har ya iya kai hannun shi jikinta sannan ya haiƙe mata ba da son ran ta ba, ta daina faɗa da shi ne domin a yadda ya zuciya zai iya yi mata illa ita da abin da ke cikin ta, ta fi awa biyu tana kwance tana kuka ta kasa tashi sai da ta ji ana ta sallar azahar a masallatan kusa sannan ta iya jan kafafunta zuwa tiolet ta tsarkake jikinta sannan ta yo wanka da alwala azaune ta iya yin salla har kuma ta gama ba ta daina hawaye ba. Fuskarta ta yi jajir in da Habib ya mare ta har da tashin hannayensa zuciyarta ta yi duhu tana mata suya haka ta yini a cikin wannan halin bai kuma hana Habib dawowa gare ta da daddare ba, ba ta sake ƙoƙarin hana shi ba ta bar shi ya yi duk abin da ya ga dama da ita ya tsallake ta ya barta tana fama da suyan zuciya da hawayen bakin ciki da tausayin kanta. Domin ba ta isa ta hana shi abin da ya aura sabo da shi ba.

Tun daga ranar zaman su ya sake juya teburi. Hatta kayan abinci kaf Habib ya kwashe su a gidan nan ma'ana ta dinga ci da kanta, store ɗin ta bai bar ko ƙwayan abinci ba sai abin da ba a rasa ba da kuma ta gani ba ta yi mgana ba domin ita ta riga ta gama aminta da duka kalaman Habib, da gaske ba ya son ta sannan saboda jikinta ya aure ta kuma tana bashi yana cigaba da mora. Duk lokacin da ya ji bukatarta zai zo gare ta ita kuma za ta kwanta ta buɗe masa har ya yi ya gama abin da zai yi ya tashi ba zai yi mata mgana ba itama ba za ta yi masa ba, tun in yana yi tana kuka har ta samu nauyin zuciya ta daina kuka sai dai idanuwanta na kallon rufin sama tana mai jin suya a cikin zuciyarta. Ta ɓoye ma kowa halin da ta ke ciki har Baffa Umaru sai da ya kirata ta ce masa komai ya daidai ta, ta riga ta gama sarewa da rayuwarta, gwara ta zauna a duk wani tsanani daga Habib kar ta yadda ya sake ta saboda in ya sake ta a yanzu ya gama cutar da ita. Duk wani abu da mace za ta yi taƙama da shi Habib ya ɗauke da ga wajen ta, ba ta da komai sai rai kawai sannan ba za ta koma gida ta bar ma su Baffa abin faɗe a anguwa da dangi ba gwara ta cigaba da zama a yadda Ubangiji ya zaɓa mata rayuwa. Za ta zauna da Habib ta ba shi abin da yake so matukar zai barta ta cigaba da zama da auran shi a kanta

Ko da yaushe Ammah za ta kirata tana tambayanta yadda take sai ta ce suna lafiya haka ma Baffa, har Hamma Abdulrrahman sai da ya kirata yana mata jan ido da cewa Baffa ya faɗa masa an samu masalaha yana ta jan ta mganar cewa in Habib bai daina maganar zubar da ciki ba kar ta ɓoye masa ta faɗa masa shi zai tsaya mata, amma ta ce komai lafiya bayan sum gama waya ta yi ta kuka, da ma a ce za ta iya da ta faɗa masa komai amma ba za ta iya ba suna zaman su lafiya ba za ta zama silan matsala da damuwa ga iyayenta da ƴanuwanta ba. Tun tana jin Habib a ranta har ta daina jin sa kwata-kwata ya tozarta ta ya ci mutumcin ta, ta koma sai ta fita ta siyo dan abin da za ta ci kuɗaɗe ne a hannunta sama da dubu ɗari amma sai da suka ƙare a wajen ciyar da kanta da zuwa asibiti, tunda ta sake komawa cikin ta har ya shiga wattani uku sannan ga shi likita ya ce jininta ya yi ƙasa tana ɓukatar cin ganyayyaki saboda inganta lafiyanta da abin da ke cikin ta, ba saboda kanta ba saboda gudun jinin dake tare da ita, shi take so domin duk halin da ta faɗa saboda kare shi da ta yi ne shi ya sa nan duniya babu abin da take so da ƙoƙarin karewa sai cikin jikinta. Kuma a haka dare na yi Habib zai zo ya biya buƙatar shi da ita ko a jikinsa. Tabbas saboda jikinta ya aure ta, kuma yana moran abin shi son ran shi, Ummu ta gama sakawa a ranta jikin ta ne kuma da man Habib ya kusa kai sa zuwa ga expearing date ɗin shi, gwara ta bar masa komai ya ƙarisa shi tundaa shi ya fara.

Baɗɗo ba ta nan ta tafi gidan kakanin ta a Mubi, Shamsiya kuma ta kwana biyu ba ta ji ta ba, ba ta kiran kowa wanda ya kira ta kuma ta yi masa ƙaryan tana lafiya. Mami ma ta kirata tana ba ta haƙurin cewa ba za su samu zuwa jimeta ba za su je Paris ita da megidanta da yara sai dai in sun dawo ko ita kaɗai za ta zo ta duba su. Sai ta ji daɗin haka domin ba za ta so wani na ta ya zo ya ganta a cikin wannan halin ba, kuma ta tabbata in Mami da diro Jimeta sai ta zo gidan ta kamar yadda ta saba abu ɗaya take yi da ke saka ta farinciki kallon girke-girke a wayanta sai ko salla da karatun Qur'ani amma Allah kaɗai ya san girman nauyin da ke cikin zuciyarta ita kaɗai ta san abin da ke muƙurƙusanta a cikin zuciyarta ƙarfin imani ne kawai ke riƙe da ita.

****

Shafewar sama da kwanaki arba'in Ummu Salma na cikin wannan halin rayuwan Ammah ta kira ta a waya ta shaida mata zuwan Hamma Jibo tare da matarsa da yara. Sai ta yi saurin ce ma Amma za ta zo ta gaishe su, a lokacin ma ba ta da ko sisi ballanta ta yi kuɗin abin hawa, duk kuɗaɗen dake cikin acct ɗin ta ta gama kashe su a hidimar kanta.
jiya ma waken da take dafawa ta haɗa da allaiyahu ya ƙare, kuma tun jiyan ba ta ci komai ba sai ruwan zafi kawai take sha cikinta na ɗagowa. Farkon cikin ne take laulayi ba ta iya cin abinci yanzu kuma da ta ɗan samu sauƙi tana ci ko da za ta yi amai haka likita ya ce saboda abin da ke cikin ta. Ba ta da kuɗi ta kuma rasa yadda za ta yi Allah ya dube ta a washegari Hamma Mustapha ya tura mata 10k kamar ya saka ta a aljannah haka ta ji ta kira shi tana yi masa godiya kamar za ta yi masa sujjuda.

Kuɗin sun zo mata a lokacin da take cikin matukar buƙatar su shi ya sa gari na wayewa ta shirya ta tafi kasuwa. Sai ta kwana uku ba ta sa Habib a idanuwanta ba wata rana ma ba ya kwana a gidan sai ranar da yake da buƙarar ta to tana ganin shi, shi ya sa game da fita neman abin da za ta ci da lafiyanta, in za ta fita za ta ce Allah kana gani na fita da izinin ka domin lafiyata da abin da ke cikina, sai ta saka kafarta ta fita to haka ta yi ranar ta je kasuwa ta kaso dubu takwas sauran ta dawo dasu domin ta yi na abun hawa zuwa gida gobe. Abin da ba ta sani ba tana fita ba daɗewa motar Hamma Jibo ɗauke da Matarsa Nauwara da yara suka shiga haraban gidan su, suka iske ƙofar bangarenta a rufe kuma Hamman na ta kiran wayan ta, tana ringing amma ba ta ɗagawa.

Megadi ya tambaya shi ya ba su tabbacin ta fita amma yana tunanin ba za ta daɗe ba sai Nauwara ta ce su zauna a mota su jira ta. Haka ko aka yi suna cikin mota suna hira Ummu Salma ta shigo gidan tana tafiya kamar za ta faɗi hijabi ne a jikinta amma duk wanda ya santa in dai ya ganta sai ya firgita da raman da ta yi sannan ta ɗan yi duhu hasken ta ya ragu, hannunta ɗauke da ledojin da ta auno shinkafa da fulawa sai wake da manja sai kayan ganye tun da yanzu ta daina cin mangyaɗa saboda ta fahimci in dai ta ci abincin mangyaɗa to ba za ta kwana lafiya ba bayan amai ta yi ta fama da tashin zuciya.

Ko kaɗan ba ta ma lura da motar dake bakin bangarenta ba, har ta nufi ƙofarta ta sauke kayan hannunta tana neman maƙulli a cikin jakar ta sai ji ta yi an kira ta kuma da sunan da aka kirata yan gidan su ne kawai ke kiranta da sunan sannan kuma ta jiyo murya kamar ta Hamma Mustapha.

"Auta."

Da sauri ta juya ba Hamma Mustapha ba ne, Hamma Jibo ne mamaki ya kamata sai da daburce.

"Hamma."

Ta faɗa cikin sauri nan da nan idanuwanta suka kawo ruwa da ta gan shi sai ta ji kamar ta warke da duka matsalolinta. Hamma Jibo ya kalli Nauwara itama ta kalle shi amma ba su yi mgana ba ya fara takawa zuwa ga Ummu sai ya ga ta kwaso gudu zuwa gare shi, ko da take gida in ya zo tana murna da ganinsa har ta zo ta riƙe mishi hannu amma ba ta taɓa faɗawa jikinsa irin na yau ba sannan lokaci ɗaya ta kece masa da kukan da ya ɗaga masa hankali.

"Hamma."

Ummu-Salma take faɗa cikin muryan kuka rike ta ya yi a zuciyarsa yana jin wani iri, me ya samu Ummu ne duk ta rame ta lalace haka?

Ɗago kanta ya yi lokaci ɗaya yana share mata hawaye da tafukan hannayen sa

"Ya isa haka Auta. Ya isa haka."

Ya ke faɗa yana sake share mata wasu hawayen da suka kwaranyo.
Nauwara na gefe ita da su Saudat duk jikinta ya yi sanyi yaran ma sun raɓe a jikinta suna kallon Babansu da Annin su, duk da yara ne amma suma sun ji wani iri fuskar su ta yi ɗif alamun damuwa.

"Me ya same ki Auta? Ko kin yi ciwo ne?

Ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login