Follow us on social media
Showing 75001 words to 78000 words out of 147042 words
Chapter 26 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
shi. Ta sha kuka tana faɗin ita har abada ba ta da alaqa da waɗanan mutanen Baffa ya nuna mata ita ko ke da alaqa da su, tunda akwai jininsu a tare da ita. Da ta yi bore Ammah ta ce ba ruwanta tunda daman tuntuni ta ce ta bar mata ɗan, jin haka yasa ta cire bakin ta akan Lamiɗo da man kuma ba saka bakin take yi ba.
Rayuwa ta gangara har Lamiɗo ya gama karatun shi na degree da Master akan Nautical Sceinces a jami'ar Akademi laut Malaysia. Ya samu ƙwarewa da horo kan tuƙin jirgin ruwa kuma lokacin ne Fulanin Daura ta buƙaci Jikan da ta juya ma baya tun a farko. Saboda duka ƴa'yan sarakunan da ta aura ma Maimartaba ba su ba ta jika namiji ba sai mata ita kuma tana so zuru'an ta su ƙare a zamowa sarakuna ne shi ya sa ta ɓullo da maganar nemo Fatima da abin da ta haifa shi kuma da man Maimartaba yana neman dama ne sai ga Fulanin Daura har falon Ammah tare da manyan ƴa'ƴanta mata
ta duka tana ba ma su Baffa haƙuri, Baffa ya ce shi ya daɗe da yafewa Fatima za ta roƙa gafara. Mami kuwa ta ƙi yafe musu har sai da Fulanin Daura ta je har falonta a gidan mijinta dake garin Kaduna. Dalilin mijinta Alhaji isa ya sa ta yafe ma Fulani da ɗanta amma game da Lamiɗo ta ce ba ruwanta a ciki ta nemi Baffa da Ammah sune iyayen Lamido. To shima dai Lamiɗon ya yi taurin kai duk da daman ya san ba Baffa da Ammah ba ne suka haife shi ba. Maimartaba na zuwa Jimeta a ɓoye Baffa ya kai masa Lamiɗo ya gansa sannan da yana Malaysia yana zuwa ganinsa tare da Hajiya Zaliha(Mahma)
A haka ne sabo ya shiga tsakanin su kuma Maimartaba da kansa ya zaunar da Lamiɗo ya bashi labarin duk abin da ya faru shi ya sa ya fi jin haushin Fulanin Daura.
Bai amince da komawa Daura ba sai da Ammah ta saka baki sannan ya koma Daura da zama a cikin Masaurata. Gari ya ɗauka domin waɗanda suka san da auran aminttun sarkin a wancan zamanin duk sun rasu sai mutum ɗaya ne ya rage a lokacin shi ne ya ba da shaidan Lamiɗo ɗan Masaurata ne balle ma kamanninsa da kowa ya gani ba sai ya yi magana ba, kamar Maimartaba yana tashen ƙuruciyarsa.
Bai daɗe da komawa Daura ba ya kama aiki gadan gadan da kamfanin Nigerian Port Authority a matsayin matuƙin jirginsu Captain bayan ya karɓi licence ɗinsa a matsayin pilot matuƙin jirgin ruwa By Nigerian Maritime Administration and Safety Agency (NIMASA)
Sai ya zamana baya samun zama sosai amma duk salla a Daura yake yin ta saboda za a gudanar da hawan salla tare da shi, kuma uwa uba yana da wasu yan'uwan da suke uba ɗaya duk da ba su tashi a gida ɗaya ba amma dai yana son su tunda su ɗin jininsa ne.
Sai da ya auri ƴar Sarkin Kano sannan aka na ɗa shi Yariman Daura mai jiran gado duk da abubuwan sarauta ba su dame shi ba amma Muhammad Lamiɗo mutum ne nagari mai kirki kamar mahaifinsa. In dai ya na Daura talakawa da matasa na cikin alheri yana da alheri sannan ga ƙokarin samo ma matasa ayyukan yi.
Duk da shi miskili ne mara sakewa amma kuma mutanen garin Daura suna son shi saboda yana da kyautawa. In dai ya zo Daura to tare da shi ake zaman Fada a dole sai an koya masa abubuwan da suka shafi sarauta, abin da ba su sani ba shi bai taɓa sha'awar Sarauta duk da ko bai faɗa ba mutane da dama in suka gan shi da yanayin shi sai sun ce yana da jinin sarauta a jikin shi. Sannan in dai ya zauna da Maimartaba to ba su da hira sai hiran sarauta da tarihin masaurata da sarakunan da suka gabata. Haka ma Hajiya Zaliha ko da wani lokaci suka haɗu girman matsayin shi take nuna masa, da lissafinta na cewa wata rana shi ne a kan ƙaragan da mahaifinsa ke zaune yanzu. Shi sai dai ya ji su kawai kwata-kwata baya son mulki kuma ba zai taɓa sha'awa ba, saboda mulki hayaniya ne da damuwa tare da nauyi shi kuma ba ya so.
Hajiya Zaliha(Mahma) tana son Lamiɗo sosai saboda ba ta taɓa haihuwa ba shima yana son ta ko domin yadda take ji da shi ya sakata cikin jerin mata masu muhimmanci a rayuwarsa.
Fulanin Daura da ta tsufa yanzu ba ta da abin so kamar Lamiɗo tana ji da shi kamar tsoka ɗaya a miya. Shi ko ba ya wani ta kanta amma dai yana zuwa wajenta ya zauna na wani lokaci in dai ya zo garin.
Itama in ya je wajenta haka za ta zaunar da shi tana ta yi masa hira da labarin Masarautar Daura har ya gaji da ji ya haddace. Da yana jin haushin ta akan abin da ya faru amma daga baya ya daina tun da ita kanta Mami ta na can tana wata sabuwar rayuwar da shi da Ahalin na shi duk ba sa gabanta shi ya sa ya bar komai ya wuce ya kuma rumgumi ahalinsa. Ba a sauya ma tuwo suna duk a je a dawo abin faharin shi da asalin shi garin Daura ne.
Dalilin abin da Fulani Daura ta aikata ne daga baya Fargar Jaji ya kamata ta yi nadama. Saboda haka ya sa duk wani abu da zai faru a Masarautan Daura za a sanar ma da Ammah da Baffa saboda Lamiɗo zumunci mai karfi ne a tsakanin Ammah da Gimbiya Shahida uwar gidan Maimartaba da man duka sauran matan na shi.
Sannan Fulanin Daura yadda ta dauki Lamiɗo da muhimmanci haka ta dauƙi Ammah da Baffa. Mami ce tun da ta ce ba ta da alaqa da su haka ɗin take ba ta ma nuna ma ita ta haifi Lamiɗo ballanta wani abu ya sa a sako ta a ciki. Shima kuma ba ya taɓa nuna Mami a matsayin mahaifiyarsa Ammah ce uwar sa har gaban abada.
Lamiɗo kawai suka sani da marikan shi da suke tamkar iyayen shi, shima Lamiɗon ba ya ɗaukan kowa a matsayin iyayen shi sai Ammah da Baffa Mami dai kawai sunan ta uwa ne amma babu shaƙuwar ɗa da uwa a tsakanin su. Dalilin Lamiɗo har Hajji Masarauta ta kai Ammah da Baffa suka je suka sauke farali.
***
Ummu Salma ta kasance a wajen Ammah da Baffa a matsayin yar Auta. Ta taso cikin zaratan yayyen ta maza bakwai ko na ce takwas ga Lamiɗo sannan ita mace, shi ya sa in dai ana maganar gata sai dai a yi kwataance da Ummu Salma.
Tun tasowar Ummu ta tsani karatun boko, domin kanta gaskiya ba ya ja, kusan na kusa da na ƙarshe take ɗaukowa a makaranta. Duk gori da zagin da su Hamma Kabiru ke yi mata bai sa ta gyara ba. Kuma makaranta mai tsada take yi ta Ahmadu Ribaɗo Collage a garin Yola. Amma sai a saran kuɗi ake yi kwaƙwalwar Ummi ba ta fahimtar komai har gwara ma bangaren islamiya shi ba laifi amma na bokon nan ne sai a hankali. Ita kawai karatun boko na wahalar da ita ne, duk ko yadda ba ta iya shan inuwa ɗaya da su Hamma Kabiru a cewar su daƙikiya ce ita kar Hamma Lamiɗo ya ji labari ita tun zaman shi a gidan su jininsu bai taɓa haɗuwa ba, wata maganar arziƙi ba ta taɓa haɗa su ba shi ba ya magana ma. In ka gan shi yana mgana to da Ammah ne ko Hamma Kabiru, tun tana yarinya ta san shi ba ɗan Ammah da Baffa ba ne saboda su suna kama da juna amma shi kamininsa na dabam ne, duk da ba ta son shi amma kuma akwai shakuwa a tsakaninta da mahaifiyar shi Mami, wacce ita ta yi renon ta bayan Ammah ta haifeta kafin auranta sannan bayan ta yi aure tana yawan zuwa Kaduna gidan Mami ta yi hutu, Mami mace ce mai fara'a sannan ita da mijinta suna ji da ita in suka je kasashen waje haka Mami za ta ciko mata jaka cike da kayan sawa na alfarma sai wanda ya gani. Ta sha zama ta yi ta mamakin yadda Mami ta iya haihuwan Hamma Lamiɗo ita ba ta ga ta in da ma suka haɗu ba, shi dabam ita dabam ita mai fara'a ce mai kirki da son Jama'a saɓanin Lamiɗo da ba shi da fara'a ba shi da son mutane sannan ba shi da kyakyawan mu'amala.
Ummu Salma ta taso ta ga Aminci tsakanin Amma da Ummin ikki shi ya sa itama Aminta ya haɗa ta da Aisha(Baɗɗo) a yayin da makaranta ya haɗa ta da Shamsiya(Bestie) su suna da son karatu kuma suna ganewa ba kamar ita ba tun da kuma ta fahimci ba ta gane karatu ta ce ba za ta ci a karatun boko ba, daga lokacin ta saka ma kanta tunanin daga sakandiri ba za ta cigaba da karatu ba.
Kuma haka aka yi ba yadda ba a yi ba amma Ummu Salma ta ce ta gama Baffa kuma da Ammah suka goya mata baya. Abu ɗaya Ummu ta fi mayar da hankali shi ne girken-girken zamani, ta bakin Hamma Kabiru ya ce shi kaɗai take ganewa.
Bayan ta gama sakandiri ta je Kaduna ta yi wattani huɗu a wajen Mami saboda tsangwaman su Hamma Kabiru akan sai ta cigaba da makaranta tun ballanta ganin kawayenta Baɗɗo da Shamsiya sun cigaba.
A can kaduna ta yi ta shiga catering School tana samun ƙwarewa bayan ta dawo Jimeta ma ba ta zauna ba yayyenta sun gaji da magana sun ƙyale ta tun da Baffa yace boko ba dole ba ne, shi bai yi ba Ammah ma ba ta yi ba amma ba su mutu ba sun rayu saboda haka a bar Auta ta sarara. Kadunan ma da ta gudo saboda Mami ta fara zaunar da ita tana kwatance a kanta na amfanin karatu tunda ta ji haka tace za ta koma gida saboda Mami za ta iya jan Ra'ayin ta in kuma hakan ya faru ko ta shiga ba za ta iya ba gwara maganin ayi kar a fara.
Sai da ta yi zaman shekaru uku a gida ba makaranta ba ta da aiki sai girke girken zamani a gida duk abin da ta koya sai ta gwada shi tun ballantana abubuwan da take gani a waya tunda Mami ta siya mata waya Samsumg babba ta zamani, ko da yaushe tana cikin kwabin fulawa ita ce Cake ita ce donot wani abun ta yi ya yi daɗi wani kuma ya lalace Amma ta yi ta masifa Baffa ne mai supporting ɗin ta.
Ummu Salma Bata taɓa tunanin za ta haɗu da Habib ba sai ga shi Allah ya haɗa su, wata rana ta dawo daga gidan su Baɗɗo ya biyo ta. Duk da a ganin farko ta ji ya yi mata ba ta ɗauka soyayyar da ya nema a wajenta zai kai su ga aure ba sai ga shi komai ya faru cikin lokaci. Ummu Salma da Habib sun yi soyayya kamar su lashe juna kafin aure ya nuna mata duk duniya bai so wata mace sama da ita ba, yayyenta suka yi ta mganganun cewa bai kamata a yi mata aure a lokacin ba, amma Baffa ya ce tunda ta samu miji kuma ya bincika yaron nagari ne zai aurar da Ummu sun yi adawa sosai amma kuma sun haƙura daga karshe. Cikin wattani biyar aka yi auran Ummu Salma da Habib auran ya zama abin kwatance kowa na ganin Ummu ta gama yin dace, ko bayan auran Habib ya nuna ma Duniya Ummu Salma ce duniyarsa, zaman lafiya da soyayya da ƙauna shi ya rike su a cikin wattani takwas ɗin da suka yi da aure. Duk masu adawan auren ta sun haƙura ganin tana zaune lafiya da mijinta.
Ummu Salma ta ɗauka ta gama dacewa. Ta ɗauka bayan ita da wahala a samu mace irin ta a cikin tsara. Sai ga shi cikin wattani uku Habib ya yi ma rayuwarta juyin waina daga sama ta koma kasa. Cikin wattani tara zuwa goma da auran su ya yi ma rayuwarta katon taɓon da har ta koma ga Allah ba za ta manta ba.
*littafin Fargar Jaji na kuɗi ne a manhajar Telegram akan #1k. Tura Kuɗin karatun ku ta wannan acct ɗin 9069067488 JAMILA UMAR OPAY sannan sai ku tura shaidar biya ta waɗanan lambobin kamar haka.*
09069067488.
08032773332.
*Yan kasuwa masu buƙatar a tallata muku hajojinku a cikin wannan kayattacen labarin za ku iya tuntuɓata kai tsaye ta wannan lambar 09069067488 Na gode.*
*Janafty*
*FARGAR JAJI.*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*
"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"
https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t
*12*
Hamma Abdullahi ya ɗauko Ummin ikki a mazaunin gaba na motarsa sai Baɗɗo da Ummu dake zaune a gidan baya akan hanyar su ta zuwa gidan Baffa. Baɗɗo ne ke ta kuka saboda in ta kalli Ummu sai ta ji rauni ya dabaibaye ta, ita ma Ummin ikki hawayen take yi tana sake rantsuwan ba za su yafe ba sai Allah ya yi ma Ummu sakayya akan tozarcin da Habib ya yi mata.
Hamma Abdullahi ko baya magana tuƙinsa kawai yake yi amma in da za a tona zuciyarsa da wataƙila an fahimci halin baƙincikin da yake ciki, takardan sakin tana cikin aljihun jallabiyan jikinsa har wani ɗaci yake ji a ran shi na tozarcin kalaman Habib yanzu ya ya Baffa da Amma za su ji? Ummu ma ba a maganar ta, tana zaune kawai ta ƙura ma gabanta idanuwana sai ta daɗe ba ta kyafta idanuwana ba kamar wacce ta zama gunki ba ta kuka ba ta motsi sannan babu hawaye sai dai ido kawai yana kallonta, ta cikin madubin motarsa na gaba gabaɗaya jikinsa ya yi sanyi kamar an masa wanka da ruwan sanyi, addu'a kawai yake yi mata Allah ya ba ta ikon cin wannan jarabawan domin jarabawan mai zafi ne sai wanda ubangiji ya so zai iya tsallakewa.
Har suka isa gidan Baffa dake Zone 3 suna cikin wannan yanayin har cikin haraba Hamma Abdullahi ya shiga da motar Baɗɗo ta kama Ummu ita da Ummin ikki suka shiga da ita cikin gida yayin da Hamma Abdullahi ya buɗe boot ya kwaso akwatin Ummun guda huɗu ya bi bayan su da shi. Amma na zaune a falonta tun bayan fitowarta daga wajen Baffa ba ta koma ba, ba ta so ya fahimci tana cikin gigita shima kamar ya sani sai ya bata lokaci tunda suka gama waya da Aminiya take zaune cikin mutuwar jiki da na zuciya na tsawon lokaci kafin ta ji sallama a tsakar gida zumbur ta miƙe jikinta ba in da ba ya rawa ɗago labulen da aka yi ne yasa Amma ta yi saurin komawa ta zauna tana ɗan daidaita yanayin ta.
Lokacin da suka shigo da Ummu a riƙe kallo ɗaya Amma ta yi mata ta ji ta sare, kafafunta sun yi mata nauyi da ta kasa ma miƙewa Ummu ce ta koma haka! Idanuwa sun kumbura fuskarta ta yi wani irin jajir, tana zaune kawai tana kallon su, suka zaunar da ita a saman kujera Baɗɗo ta zauna a gefenta ta jawo ta a gefen kafaɗanta tana ɗan tapping bayanta alamun lallashi, duk in da aka bi da ita can take bi kamar wata doluwa ko yarinya ƙarama.
Ummin ikki ta ƙarisa kusa da Amma ta zauna tana faɗin" Aminiya yau mun tashi cikin jarabawar Ubangiji."
Amma ta kalleta kafin ta ɗan motsa bakinta a hankali tana faɗin" Allah ya sa hakan ya zame mana alheri gabaɗaya"
Ummu ikki ta amsa da Amin kafin ta fara goge ƙwalla tana cigaba da faɗin" Wannan yaro ya cuce mu. Da ikon Allah sai Allah ya saka mana."
Ta faɗa tana kallon Ummu har a lokacin kawai waje ɗaya take kallo ko kiftawa babu, kafin ta sake cewa wani abu Hamma Abdullahi ya yi sallama ya shigo cikin gida sun amsa sannan ya shigo falon Ammah, sanda suka taho da su Ummin ikki Hamma Jibo ne ya kira wayarsa shi ya sa ya ɗan dakata suka yi magana ya sanar da shi ya kawo su gida yanzu. Akwatin hannunsa ya jera anan tsakiyar falon Ammah ko zama bai yi ba ya kalli Ummu na wani lokaci kafin ya ɗan girgiza kansa.
"Ina kwana Ammah."
Ya faɗa cikin sanyin murya.
"Lafiya lau Baba ya iyalan naka?
Ta amsa masa amma ba ta kalle shi ba kanta na ƙasa ba ta so shima ya fahimci halin da take ciki, ko ba ta fito ta nuna ba ko ta ɓoye Ammah fa uwa ce ga Ummu Salma yadda lamarin nan zai daki kowa barin ita ne.
"Suna lafiya."
Ya faɗa sai kuma ya yi shuru, Ummin ikki na ta sharan ƙwalla Baɗɗo ko hawaye ne wasu na zuba wasu na sake tunkuɗowa.
"Ba komai in sha Allah zai wuce."
Hamma Abdullahi ya faɗa domin a lokacin shima ya rasa kalaman da zai faɗi falon ya yi shuru kamar mutuwa ta gifta tun ballanta shessheƙan kukan Baɗɗo da na Ummin ikki. Ummu dai ba ta kuka da man an ce wani baƙin ciki in ka yi kukan daga baya in kukan ya ɗauke shike nan sai dai zuciya ta dinga ƙuna da raɗaɗi to hakan ce take faruwa da Ummu tunani take yi kamar ba gaskiya ba ne abin da ke faruwa gani take yi kamar komai a mafarki ne in ta farka za ta ganta a cikin ɗakin auren ta, tare da Habib amma ina duk lokacin da ta kifta idanuwanta a falon Ammah take sake ganin ta.
"Ammah Baffa fa?
Ya faɗa ganin Ammah ta yi shuru kanta na kallon ƙasa.
"Yana cikin ɗakin sa."
Ammah ta amsa masa cikin ajiyar zuciya.
Ya kama hanyar barin falon ne sai ga Baffa ya shigo da sallama daidai lokacin da Hamma Abdullahi ya ɗaga labulen falon Ammah sai ya koma da baya ya ba ma Baffa waje domin ya shigo.
Baffa ya shigo har falon Ammah ya yi tsaye kawai yana kallon Ummu Salma sanye yake da manyan kaya