Follow us on social media
Showing 135001 words to 138000 words out of 147042 words
Chapter 46 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
ta yi, ba ta so.
"Kin san abin da kika yi."
Numfashi ya ja kafin ya dire.
"Ya saka Ammah Suma."
Ya dire maganarsa abin na sukan zuciyansa. Yana tuna lokacin da Ammah ta zube a kasa a bakin emergency, ya ji tsoro ya kuma ji fargaban in wani abu ya same ta ya zai yi??
"Kina so ki kashe mini uwa ne.?
Ya faɗa ya ɗan ɗaga murya.
Wai uwa, itama ai mahaifiyarta ce.
Tuni har ta fara kuka har yana sauti
"In kin shirya mutuwa saboda wani rubbish, "
Ya dakata yana ɗan sauke numfashi domin ya fara harzuƙa in ma ya tuna dalilin da yarinyar nan ta nemi kashe kanta
"To ki mutu, amma kar ki bari sanadin haka ya taɓa Ammah ko Baffa."
Ummu ta fashe da kuka sai ga ta duke ganin ta ƙasa durƙusawan zai yi mata wahala sai kawai ta baje a zaune tana kuka har da gunji. Mami na makewayi sai faman Uhm uhm take yi amma Lamiɗo bai saurare ta ba, bai ma nuna yaji ba.
"Hamma ka yi.."
"Will you keep your mouth shut."
Lamiɗo ya faɗa cikin murya mai amo da ta yi sanadiyar shigowar su Ammah ɗakin cikin mamaki, kafin ka ji muryan Lamiɗo a sama ahaka ana daɗewa sai in ranshi ya ɓaci ganin Ummu durkushe tana kuka ya ba su amsar tambayar su.
"Ai gwara kai ma ka yi mata faɗa yarinya kamar wacce ba ta yi makaranta ba? Har gobe in na tuna da abin da ta yi sai na ji kamar na mutu saboda bakin ciki. Baffa da Mami sun yi tsaye sun hana a yi mata faɗa."
Hamma Abdulrrahaman ya faɗa cikin jin haushi, shi ya ji daɗi domin har gobe bai huce ba tunda ba a bari ya yi mata duka ba.
"Me ya sa kike kuka?
Ya cigaba da mgana cikin kaushin muryasa.
"Me ya sa lokacin da za ki aikata ba ki tuna da komai ba.?
Ummu dai ta daina kuka ta haɗiye shi, tun tsawar da ya yi mata da farko.
"Tunda ya ce ba ya sonki ya sake ki."
"Dole ne."
"Za ki yi pushing kanki in to a relatioship ɗin da ba ki da amfani ne a wajen ne?
Are you Stupid? Ko ke ba ki da wata daraja matsayinki ta ƴ'a mace ne?
Ya gama faɗa a jere yana haki cikin ɓacin rai.
"Faɗa ma ta dai Lamiɗo "
Ammah ta faɗa cikin bacin rai, ba ta ma son tuna abin saboda ɓacin ran da ta ke shiga
"Ki sani kina da komai ba ki kuma rasa komai va saboda haka ki sani wannan abin da kika yi is a stupidity, kuma kar ki sake."
Ya faɗa har yana ɗaga murya.
"Domin in kika sake ba mgana zan tsaya ina yi dake ba. I will deal with you. "
Ya faɗa yana ɗan jinjina kansa.
Ummu kuka har da majina.
"Ku yi haƙuri."
Take faɗa, tana kuka Hamma Abdulrrahman ya cigaba da faɗa yana masifa.
Daidai lokacin Mami ta fito daga tiolet, cikinta ne ya karta tun ɗazu take Allah Allah ta fito, saboda ta ga an yi ma Auta taron dangi.
"A'a Lauya bari, shi ya yi na shi ya gama kai kuma sai ka ɗora naka! Wallahi ku fita daga idanuwana na rufe."
Mami ta fada tana isa gaban Ummu ta duka tana fadin" is ok ya isa yi shurun ki"
Hawaye take share mata da hannayenta.
"Fatima ki bari a yi mata faɗa don Allah."
Ammah ta faɗa da ya sa Mami ta tashi a fusace tana fadin" To duk ba an yi mata ba, kuma ta yi nadama don Allah ku ko kukan da take yi bai ba ku tausayi ba?
"Wani tausayi? Mu ma ai haka ta ɗaga mana hankali."
"To ta ji, ku fita kawai."
Mami ta katse Hamma Abdulrraahman tana nuna musu hanyar fita, Lamiɗo ya juya zai fita Mami ta jawo hannunshi tana fadin" Kai ne ka fara ko? Kai ba ka san na saka dokar kar wanda ya yi ma Auta mgana ba? Kalli yadda ka sanya ta kuka juna biyu gare ta ba fa"
Mamaki ya kama shi sai kawai ya tsaya yana kallon Mami bai yi magana ba.
"Ammah ja zugan yayanki ku je falo. Ganin su ma firgita mini yarinya yake yi "
Ta faɗa tana sakin hannun Lamido ta juya ga Ummu.
Ya daɗe yana kallon hannun shi da ta rike, kafin ya juya ya bar ɗakin.
Ammah ta ce su fita kawai.
"Ke ma dai Fatima ki zama mai gaskiya "
"Gaskiyan kenan Ammah."
Ta faɗa bayan sun fice.
Nan suka bar Mami da zaman lallashi, Ummu ta yi ta kuka tana ce ma Mami ta yi nadama ba za ta kara ba..
Haka Mami ta yi ta masifa, da hamma Abdulrahaman shi dai Lamiɗo ya gudu Hamma Abdullahi ya tafi kai shi filin jirgi.
"Wai ina ganin Basamuden ɗan Ammah da ba ya magana, shi ne zai zo ya tasa ya'ta yana yi mata faɗa, wallahi da ina kusa bai isa ba."
"Kar ku manta dai ya ba ta jininsa, ba domin shi ba da yanzu kina zaman makoki.,"
Ammah ta faɗa tana dariya.
"To sai me! Ai don Allah ya yi kuma ba a saka shi ba, da sai ya bari a saka mata na siya "
Ammah na ta dariyan Mamin ganin ta da karfin hali.
"Shima ɗana taimako ya yi, kuma fadan da ya yi mata na ta so kanta ne."
"To ina ruwan shi? Sai da ta warke ne zai zo da wani tsawonsa kamar falla waya yana yi ma mutane faɗa "
Mami ta sake faɗa cikin kufululewa.
Ammah ta yi wucewarta ɗakin Baffa domin ta gyara tana ce ma Mami.
"Ku kuka sani dai Fatima."
Mami ita kaɗai ma faɗanta ta dinga yi.
Hamma Abdulrrahaman ya sulale ya gudu shima Abdullahi daga filin jirgi bai dawo gidan ba.
Faɗan da Mami ta yi ranar har dare, sai da Ummun ta koma ba ta hakuri.
"Gwara na tattaraki mu tafi can su daina ganinki, tunda Ammah ta daure musu kugu, Baffa kuma ba zaman gidan yake yi ba, balle ya tsaya miki "
Haka da Baffa ya dawo ta tare shi da cewa Ammah ta yi gayyar yayanta sun saka Auta kuka.
"Baffa har da wannan ɗan nata kamar basamude, shi ya fara zuwa ya yi mata kerere a gaba yana ta masifa, ashe karyan miskilanci yake yi tunda yana faɗa, Ammah na gefe da sauran yayanta suna cewa ya yi daidai."
"Ba su kyauta ba "
Baffa ya faɗa yana danne dariyansa.
"Ammah ce fa ba ta tsawarta musu ba."
"Ammah ma ba ta kyauta ba."
Ya sake faɗa yana dariya.
Ammah ta shigo ɗakin kawo ma Baffa abinci ta ce" An zo an kawo ƙarana kenan?
"E wai har da basamuden danki kika kira ya zo ya yi ma Auta faɗa."
Ammah ta kwashe da dariya Baffa na ta yata.
"Allah ya shirye ki Fatima."
Ammah ta faɗa tana ficewa daga dakin.
"Gwara ki dauki yarki ku koma Kaduna sai kun shekara ba su ganta ba, ina ce va shike nan ba, sai na ga wanda ya'yan Ammah za su yi ma faɗan"
"Ai Baffa ka bar su da ni, boko ce suke gwada mana, nima yar bokon ce sai dai mu buga ta."
Baffa na dariya sosai ya ce" A gaida Fatima Baba, Fatin Gwaggo. Yau da ma suna raye su ga yadda Ubangiji ya mayar da Fatin su."
Sai kuma suka koma tuna rayuwarsu ta baya tare da yi ma iyayensu addu'a daga karshe ma tare suke cin abincin Ammah ta sake dawowa ganin suna cin abinci ya sa ta rike baki tana fadin" Fatima kin zo kin ƙwace mini Baffa, miye nufin ki?
"Jibi za mu bar muku gidan."
"Umma ta gaida Aisha."
Baffa dariya kawai ya yi yana girgiza kansa.
Ammah itama zama ta yi suna cin abincin su uku daga faranti ɗaya, in ya kalle su sai ya tuna a shekarun baya shikenan raba faɗa a tsakanin Mami da Ammah, amma shaƙuwa ce mai tsanani a tsakaninsu, wacce ma alƙalami ba zai iya rubutawa ba.
*1k on Telegram
09069067488.
*Janafty*
*FARGAR JAJI.*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*
"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"
https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC
*21*
Washegari asabar Alhaji isa ya iso Jimeta tare da Islam da Faruk. Mami da kanta tare da Hamma Abdullahi suka je filin jirgi suka ɗauko su zuwa gida.
A shashen mazan gidan daman ya kan sauka in ya zo duk da in kwana ya kama shi hotel yake tafiya yau ɗin ma a bangaren su Hamma Saddam Mami ta sauke shi sai bayan ya ci abinci ya natsa sannan ya shigo cikin gida suka gaisa shi da Amma, Baffa ba ya nan ya je cikin garin Jalingo sai can yamma ya dawo tare suka yi sallar mangariba da Alhaji isa har isha'in ma daman abokan kasuwanci ne tun a baya sannan megida ne da yaronsa. Yanzu kuma har da surukanta da ya haɗa su dalilin auran Mami, duk da hakan zumumcin da ya haɗa su bai yanke ba yau ɗin ma bayan sun dawo daga masallaci a tsakar gida Ammah ta yi musu shimfiɗa ta kuma haɗe musu abinci waje ɗaya suka zauna suna ci suna hira, irin ta su ta masu kasuwancin ƙarafa da siya da siyarwan motoci daga jin yadda suke magana a tsakaninsu za ka fahimci akwai kyakyawam alaqa a tsakanin su.
Mami kuma da Ammah suna falo suna kallo tare da Faruk jefi-jefi suna taɓa hira a tsakanin su, Ummu kuma tana cikin ɗakin ta tare da Islam sarkin surutu tunda suka iso tana makale da ita tana yi mata zence, ta sha labarai kala-kala har sai da ta gaji, tamboyoyi har ta gaji da amsa mata su. Tun a can Kaduna Babansu ya sanar da su Ya Ummu za ta koma gidan su da zama to fa suna sauka ɗakinta ta fara zuwa tambayanta na farko shi ne.
"Ya Ummu wai da gaske gidanmu za ki koma da zama?
Ummu Salma na mirmishi ta ce.
"In sha Allahu Islam."
Nan fa ta fara murna da tsalle, Islam yarinya ce mai shiga rai, tana da son mutane da mgana kamar Mami yar kimanin shekara sha biyu 12, Faruk kuma ɗan shekaru bakwai ne 8, shi bai da surutu sai dai rigima ce da shi sosai kamar yaron goye.
To duk bayan mintina sai ta zagayo ta ce"Ya Ummu da gaske za ki bi mu gidanmu?
In ta amsa mata da E bai hana anjuma ta sake dawowa da irin wannan tambayan har sai da ta gaji da amsa mata. Mami ma cewa ta yi ta kore ta daga ɗakin ta ce a ƙyaleta, ganin ta da surutunta na sanyata nishaɗi, kuma ta tabbata ko can ta je islam da Faruk ba za su barta ta yi kewa ba, domin samun yara a gida yana haskaka gida tare da samar da walwala ga mazauna gidan gabaɗaya.
A can tsakar gida kuwa bayan su Baffa sun gama cin abinci sun wanke hannuwansu a roban wanke hannun da Ammah ta ajiye musu, suka ɗan shiga hiran yadda kasuwancin siyar da tsoffin karafan motoci ya yi kasa yanzu ba kamar a baya ba, Baffa na mganar kasuwancin motocin da sabbin ƙarafan ma sun fi tafiya a yanzu shi kuma Alhaji Isa na sake kora masa jawaban, tun da shi dila ne kamfani guda gare shi na siyar da motoci wani lokacim ma su Baffa kan siya motoci a wajen su in hakan ta kama.
A cikin hiran ne Baffa ya kalli Alhaji isa cikin nisawa kafin ya ce" Alhaji ina son mgana da kai, duk da na san kun gama mgana da Fatima amma amatsayina na wakilin Fatima, uban Ummu Salma ya kamata na yi magana da kai."
"Ina jin ka ina fatan ba kan maganar zaman Ummu a wajen mu ba ne ko Baffa?
Tunda shima Baffa yake kiran shi tun ma kafin aure su da Fatima, abokan kasuwancin Baffa duk da wannan sunan suke kiran shi.
"Akan maganar ne."
Baffa ya amsa masa cikin ɗan sanyin magana.
"Haba Baffa, ai ina ce mun wuce haka a tsakaninmu. Ko ban auri Fatima ba ni mai riƙe Ummu Salma ne, ballantana ina auren Fatima. Ba ka da sauran haufi ko tsoro. Ummu Salma za ta samu sauyin rayuwa tare damu na ba ka tabbacin yadda zan yi ma Islam da Faruku haka zan yi ma Ummu Salma. Sannan haka itama Fatima saboda haka ka kwantar da hankalinka ba abinda zai sake faruwa da yardan Allah."
Yana mgana Baffa na ta gyaɗa kansa cikin gamsuwa.
Yana direwa ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce.
"Na gode sosai, Ubangiji ya yi ma arziƙin ka albarka. Da man tsoro na ke ji, kar Auta ta sake tunanin kashe kanta a karo na biyu"
"Hakan ba zai sake faruwa ba in sha Allahu."
Alhaji Isa ya sake ba shi tabbacin sa.
"Allah ya sa haka. Ubangiji ya sa tafiyarta ya zama mabuɗin alherin rayuwarta."
Suka amsa da Amin a tare, tare da su Ammah daga cikin ɗaki domin sun rage ƙaran talabijin ɗin Faruk ne ma ya matsa sai da aka mayar masa da tashar carttoon, shi ya sa hankulansu ya ɗan karkata kan mganganun Baffa da Alhaji Isa.
Wajen goman na dare Alhaji Isa ya tafi makwanci ya kwanta daman jirginsu karfe sha ɗaya na safe zai ta shi zuwa Kaduna.
Shi ya sa sai wajen goma ya zo gidan abin karyawa ma tun a waya ya ce ma Mami kar ta wahalar da kanta, ya riga da ya yi breakfast a hotel ɗin da ya kwana.
Ko da ya zo gida cike da yan sallama.
Ummin ikki da Baɗɗo, tare da matan su Hamma Abdullahi da yayan su, Hamma Abdullahin ma yana nan tunda shi zai kai su filin jirgi, Hamma Abdulrrahaman ne matarsa ta ce ya yi sammakon fita yana da wata sharia da yake jagoranta.
Ko da garin Allah ya waye daman Ummu Salma ta ji kamar ta buɗe idanuwanta ta ga ta yi nesa da garin Jimeta gabaɗaaya garin ya fita da ga zuciyanta a baya ba ta taɓa tunanin wata kaddara za ta iya raba ta da mahaifarta ba sai ga shi kaddaran Habibu ta sa za ta yi nesa da iyayenta da duka yan'uwanta domin tsira da salamar zuciyarta, ta tsani garin Jimeta da duk wani farincikin da ta samu a cikin ta dalilin Habib..
Sai ga shi suna sallama da Baɗɗo tana hawaye itama tana hawaye.
"Zan yi kewar ki Sisna. In sha Allahu in muka samu hutu zan dinga zuwa ina ganin ki."
Baɗɗo ta faɗa tana sharan ƙwallah.
"Na gode Aisha. Ba zan taɓa mantawa da alherinki ga zumuncin mu ba, nima Allah ya ba ni iko da tsawon rayuwa domin na samu damar saka miki."
Ummu Salma ta faɗa cikin kuka sannan suka sake rumgume juna.
Dakyar suka saki juna, Ummin ikki ma ta rike hannuwanta tana fadin" Ki je can ki sake sabuwar rayuwa. Kar ki dawo mini sai da sabon suruki kin ji ko Ummu?
Ta faɗa cikin mirmishi a zuciyan Ummu Salma faɗi take yi wa zai sake sona a haka Ummin ikki? Amma a fili mirmishi ta yi lokaci ɗaya tana gyaɗa kanta cikin fitan hawaye.
Ammah ce kawai ba ta yi kuka ba, ita da ba a ganin raunin ta.
"Ammah zan tafi, ki yafe mini."
Ummu ta faɗa bayan ta duka a gaban Ammah tana zubar ƙwalla."
"Ba ki yi mini komai ba, ki je na yafe miki duka laifukan ki da wanda na sani da wanda ban sani ba. Ina so ki tuna da cewa rabuwa da Habibu ba shi ne ƙarewar rayuwarki ba Auta, ki sani Allah na tare dake in kika mika masa lamuran ki, shi zai kawo miki agaji, don Allah ki cire komai a zuciyarki ki yi rayuwarki cikin farimciki."
"Zan yi haka Ammah."
Ta sake faɗa tana ta kuka kamar ranta zai fita.
Baffa ne ya ɗagota yana share mata hawaye.
"Bar kuka Auta, can ma Kaduna ai duk gida ne, kuma duk lokacin da kika ji kina son dawowa ai za ki dawo gida kin ji ko?
Sai ta gyaɗa masa kanta tana mai sake zubar da ƙwallah.
"Baffa ka yafe mini."
"Ban taɓa rike ki ba Auta. Ki tuna da Ubangiji a dukkan sakannin numfashinki, shi kuma ba zai barki ba, in sha Allahu."
Kanta ta gyaɗa tana sake sakin kuka har da jan majina.
"Allah ya tsare ku, ki yi ma Fatima Biyayya, ki riƙe Alhaji a matsayin Uba a gareki, domin yanzu alhakin komai na rayuwarki yana hannunsa ne."
"To Baffa.'
Ta faɗa tana sharan ƙwallah
"Fatima kama hannun ɗiyarki ku je. Allah ya sada mu da alherinsa."
Baffa ya faɗa idanuwansa na kawo ƙwalla sai ya bar ɗakin bayan ya danƙama Mami Hannun Ummun Salma, Ammah kuma ba ta ga tafiyar su ba ɗaki ta shige tana sharan ƙwalla a zuciyanta tana yi ma Ummu Salma fatan samun kwanciyar hankali da salama a in da zama zai sake cilla ta.
Masu rako har ƙofar gida akwatina biyu na kaya Ummu ta tafi da su sai kayan haihuwa sauran Mami ta ce ta bar su in suka isa can za a siya mata wasu.
Har da Baɗɗo aka tafi filin jirgi rako. Karfe sha ɗaya daidai jirginsu ya ɗaga zuwa garin Kaduna.
A first class suka zauna hatta da Faruƙu da Islam da kujerunsu, Mami da Alhaji suna waje ɗaya tare da Faruƙu ita kuma
Ummu Salma a bangaren window, Islam na gefenta yaran nan ko a jikinsu daga gani sun saba shiga jirgi, ita ko da ba ta saba ba sai da cikinta ya karta sau ɗaya ta taɓa shiga jirgi lokacin da suka je Daura naɗin Sarautan Hamma Lamiɗo shi ya turo musu kuɗin jirgi ita da Ammah suka tafi shi ne na farko sai wannan na biyu
Lokacin da ta fara ganin gajimare, jirgin ya daidaita a sama ya fara tafiya. Hawaye suka sake kece mata, tana jin shuuuu alamun jirgi na tafiya sai take jin komai na rayuwarta kamar yana gogewa, tabbas haɗuwarta da Habibu a baya tana kallon shi a wani nasara ne amma a yanzu tana cikin fargan jajin shigowarsaa rayuwanta. Saboda shi ya sa ta tsani duk wani ɗa namiji, tana ganin duk halinsu ɗaya saboda Shamsiya ya sa ta ƙara tsorata da lamuran mutane da ƙawaye, sun yi dalilin da ta gudu ta bar in da aka haifeta sun yi sanadiyar haifar mata da ciwon da har abada ba zai taɓa warkewa daga zuciyanta ba.
Amma ta yi ma kanta alƙawarin manta da duka rayuwanta a garin Jimeta. Za ta koma Kaduna a wata sabuwar Hallita. Za ta manta da Habibu da duk abin da ya dangance shi cikin jikinta kuma za ta haife shi, tana son shi amma baƙin cikinta ɗaya in ta tuna akwai jinin Habibu a jikin abin