Follow us on social media
Showing 36001 words to 39000 words out of 147042 words
Chapter 13 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
na rasa komai a duniya"
Ummu ta faɗa muryanta ma ba ta fita saboda dishewar da ta yi.
Baɗɗo ta sake share hawayen ta kafin ta ce" Kina da yadda za ki yi ko Ummu, kuma ke ce kike da kowa. Wannan mganar ba shuru za ki yi ba dole ne su Baffa sun san abin da ke faruwa"
Da sauri Ummu ta waro jajayen idanuwanta tana kallon Baɗɗo jin ta ambaci su Baffa in mgana ta kai wajen su Baffa ai shike nan kuma.
"E dole su sani saboda mgana ce da ta wuce tsakanin ku. Neman fa cikar burin sa ya ke yi saboda haka zai iya yin komai saboda haka. A dalilin haka ma zai iya yi miki illa Ummu."
Kai Ummu ta ke girgizawa lokaci ɗaya tana faɗin" Habib ba zai iya cutar da ni ba. Ba zai iya ba."
Baɗɗo ta yi kasaƙe tana kallon ta kafin ta ce" Nima na yi tunanin haka a baya. Amma yanzu kam ban yarda da shi ba. Ke da kan ki kika ce ya saka miki mganin da zai lalata cikin jikin ki har sau biyu a lemu bai yi nasara ba, na ƙarshen ma kin ce da karfin tsiya ya so ya yi miki ɗure, kina da tabbacin maganin ba zai yi miki lahani ba ke a karan kanki bayan cikin dake jikin ki? Ko kina da tabbacin ke ɗin za ki tsira?
Sai jikin Ummu ya yi sanyi ta koma ta yi lakwas tana tsiyayan hawaye.
"To kin gani dole iyaye su shiga ciki Sisna, in sha Allahu komai zai daidai ta."
Ta faɗa tana mai share mata hawaye da hannayenta duka biyu.
"Ina tsoro, ina tsoron kar su Baffa su ji wannan abun su raba ni da Habib."
Ummu ta sake faɗa da har sai da Baɗdo ta ji kamar ta sake fashewa da kuka saboda tausayin Ummu, wata kila ya yi kusa zuciyarta ta aminta da cewa Habib ba masoyin ƙwarai ba ne a gare ta, ba yanzu za ta tantance girman yaudaran da ya yi mata ba wataƙila sai anan gaba.
"Ba raba ki da shi za su yi ba. A matsayin su na iyaye za su shiga su gyara ta in da aka samu ɓaraka ne"
Ummu ta jinjina kai kafin ta ce" Ba yanzu zan sanar da su ba Baɗɗo "
"To sai yaushe?
Ta tambaaye ta cikin mamaki."
"Mu sake ba ma Habib lokaci. Wataƙila wasa ya ke yi, wataƙila yana gwada ni ne ya gani."
Kallon ba ki da hankali Baɗɗo ke yi mata ta ma kasa mgana saboda mamaki, mutumin da a cikin idanuwan ki ya ce ba ya son ki ba domin ki haihu ya aure ki ba, sannan ya yi ƙokarin lalata cikin jikin ki da karfin tsiya amma har a yanzu kare shi Ummu ke yi! Tana tunanin wai wasa Habib ya ke yi?
"Kin ga kar mu yi gaggawan sanar ma gida, in ya zo muka daidaita fa ?
Baɗɗo ta kasa mgana saboda ta rasa ma abin cewa saboda tausayin Ummu da mamakin ta.
"Kin ji? Mu sake ba shi lokaci na yi miki alƙawarin in bai sauya ba da kaina zan je gida na faɗa ma Baffa duk abin da ke faruwa."
Baɗɗo ba ta da cewa tun da Ummu na ta mata magiyan kar ta faɗa ma kowa, ita da kanta za ta je ta faɗa ma su Baffa in har Habib bai sauka daga kan gudirin shi ba.
"Na ji ba zan faɗa ma kowa ba. Sai dai ina tunanin yadda za ki cigaba da rayuwa a haka da shi, ina tsoron kar ya sake yunƙurin cimma burin sa ya yi miki lahani wata rana."
"Allah ba zai ba shi sa'a ba"
Tunda ta ce Allah sai jikin Baɗɗo ya yi sanyi amma jikinta da zuciyarta suna cike da tausayin Ummu ne, ganin yadda ta koma duk ta lalace sannan daga ganin ta, tana bukatar ma ganin likita. Ummu ta faɗa mata magungunar da aka rubuta mata a asibiti Habib bai siya ba sannan ga yanayin da take kwana tana ta shi a ciki.
"Gaskiya ya kama ta mu je asibiti."
Baɗɗo ta faɗa lokaci ɗaya tana miƙewa. Ummu ta kalle ta a sanyaye kafin ta ce" Nima ina son na je asibiti ba ni da lafiya sosai."
"Yanzu za ki tashi mu je."
Ummu ta sake kallonta kafin ta ce" Habib bai sani ba."
Baɗɗo ta ji kamar ta rufe Ummu da duka saboda baƙin ciki da takaici.
"Kina ganin in na fita bai sani ba, ba matsala.?
Ta sake tambayan ta a sanyaye.
Sai da Baɗɗo ta ya fa mayafin ta sannan ta kalli Ummu tana faɗin" Yana gidan kike fama da ciwo amma bai damu da ke ba, kin ga kenan in kin fita domin neman lafiyarki hakan ba matsala ba ne."
Ummu ta girgiza kai kafin ta ce" A'a bari dai na kira shi na sanar da shi."
Kasa ma mgana Baɗɗo ta yi sai ma ta koma ta zauna tana kallo Ummu ta tashi tana dafe dafen bango ta koma bedroom ɗin ta sai ga shi ta fito da wayarta a hannu tana ta kiran wayar Habib amma sai a saka kiran na ta a forwording.
"Ba na samun shi."
Ta faɗa a sanyaye
Baɗɗo ta yi kamar ba ta ji ta ba haushi duk ya ishe ta.
"Ya zan yi yanzu?
"Ki zauna sai lokacin da kika same shi a waya, in ya ce ma kar ki je ki zauna ki mutu"
Ta faɗa cikin haushi jin haka
Ya sa jikin Ummu ya sake yin sanyi ta zauna kusa da Baɗɗo tana mai marairaicewa.
"Ya zan yi to? Na rasa tunanin da zan yi?
Ta faɗa hawaye suna taruwa a ƙwarmin idanuwanta.
"Ki ta shi na raka ki asibiti a duba lafiyarki Ummu-Salma."
Baɗɗo ta faɗa tana mai sake miƙewa tsaye wannan karon har tana rataya jakar da ta zo da ita ba yadda Ummu ta iya haka ta ɗauko hijabi ta da ƙaramar jakarta da Atm ɗin ta ke ciki ba ta da kuɗi a hannunta, kulle ɗakin suka yi suka fita zuwa bakin titi sannan suka hau Keke Napep zuwa asibitin da Ummu ta ke da fayel, boshon clinic da taimakon Baɗɗo dake riƙe da ita. Suna zuwa suka ga likita da ya ke ta je da katin ta, likitan na ta faɗa cewa babu wadattacen ruwa a jikinta sannan akwai maleria mai zafi a tare da ita.
Riƙe ta suka yi bayan sun saka mata drip sun yi mata allurai har da na barci ta samu barci sannan likita ya ce Ummu ba ta cin abinci sannan ga jinin ta ya ɗan hau shi ya sa za su rike ta zuwa yamma su gani. Baɗɗo ce ta zauna da ita a asibiti nan tun kafin azahar sai gabda mangariba kuma ba ta kira kowa ba, Ummin ikki dai ta kira ta ganin duhu ya shiga ba ta dawo ba sai ta ce mata ta samu Ummu na fama da zazzaɓi ta ɗan taya ta ayyuka ne amma in dare ya yi sosai ba ta dawo ba to za ta kwana tare da ita, ta yi ma Ummin ƙaryan cewa Habib ba ya nan ya yi tafiya.
An sallami Ummu tare da magunguna da dokokin likita bayan ta sha leda uku na ruwa sai kuma ta ji daɗin jikinta ta daina jin jirin nan da ciwon kai, ya ce ta samu hutu sosai ma'ana sun ba ta bedrest sannan ta riƙa cin abincin domin inganta jaririn dake cikin ta. Ba su suka shigo gida ba sai ana kiran sallar isha'i kuma har a lokacin Habib bai dawo ba, Ummu wanka ta yi ta shiga rama salollin da ke kanta ita kuma Baɗɗo bayan ta yi sallar isha'i ta zage tana gyara gidan duk ya yi ƙura tun da Ummu tana ta kanta ba ta gyaran gida ba, har fashasshen kwalban da ke saman dinning Baɗɗo ce ta kwashe shi ta gyara wajen lemun da Habib ya saka ma mganin ita ta kwarara shi a tiolet ta saka kwalayen exotic ɗin a dusbin
sannan ta yi ma Ummu faten wake ta so ta saka allayahu amma babu, kuma in da ake siyarwa sai kasuwa.
An ci sa'a kuma Ummu ta ci faten waken bai dawo mata ba sai ta ɗora da ruwan lipton mai zafi ya samu ya warware mata ciki sannan Baɗɗo ta ba ta magungunar ta tasha, ta ji daɗi da Baɗɗon ta ce mata sai gobe da safe za ta tafi in ta ga jikin na ta da sauƙi. Suna zaune a falo Ummu na kwance kanta na saman cinyar Baɗɗo suna kallo gefe ɗaya kuma suna hira sama sama sai aka kira Baɗɗo a waya wata class mate ɗin ta ce, ganin suna mgana ne ya sa Ummu ta shiga tunani mai zurfi tsoron ta in mganar nan ta je kunnen Baffa har yayyenta suka ji labari sai Habib ya gane ba shi da wayau sannan tana da tabbacin sai sun raba auran nan da nan a cikin su akwai waɗanda ba su so auren nata ba, ba wai don ba su son Habib ba, a cewar su karatu ya kamata ta cigaba da yi ba aure ba ita kuma ba saboda haɗuwarta da Habib ba. Tun tana ƙarama da ta fahimci ba ta da ƙwaƙwalwar karatu ta ce ita daga sakandiri ba ta son ta cigaba da karatu.
A lokacin ba tasa aure a lissafin ta ba domin ba ta ɗauka za ta haɗu da Habib a gabar ba, shi ya sa son auren ma baya cikin lissafin ta, ba ta taɓa tunanin za ta haɗu da Habib a lokacin ba ballanta har aure ya shiga tsakanin su ba. Abu ne da ya faru lokaci kaɗan haɗuwarsu da auren su wattani biyar ne a wancan lokacin Hamma Kabiru ya yi ta faɗa da cewa an yi gaggawa ya kamata a ɗan sake jira, shi kuma Baffa ya ce tunda dai Ummu tana so kuma shima Habib ɗin ya shirya bai ga amfanin ɓata lokaci ba. Tsoron ta ɗaya in suka ji mganar ba ta san yadda lamarin zai ƙare ba, wataƙila ya yi lalacewar da kafin lamarin ya gyaru za a ɗau lokaci.
Ta yi nisa cikin tunaninta ba ta san shigowar Habib ba, sai da ta ji ƙamshin turaran shi sannan ta farga, tana ɗagowa suka haɗa ido huɗu da shi yana tsaye yana kallon su. Da sauri ta miƙe zaune tana kallon shi, jikinta har rawa ya ke yi saboda ganin Habib ba ta san ta yi kewarsa ba sai da ta gan shi, ta ji wani irin sanyi a cikin ranta.
"Sannu da zuwa Noori."
Ta faɗa lokacin da take miƙewa tsaye. Baɗɗo na zaune tana ganin ikon Allah. Sai da ta ga Habib sannan ta san a ɗazu ba haushin shi take ji ba, yanzu ne ta ke jin kamar ta rufe shi da duka da ta gan shi. Barin ma yadda yake bin Ummu da wani kallon banza ita ko baiwar Allah hannu ta miƙa za ta karɓi jakar hannunsa da sauri ya kauce ya kuma raɓa ta zai wuce ciki Baɗɗo ta ga ba za ta iya jurewa ta miƙe a fusace.
"Habib."
Ta kira sunan shi a kausashe, sai ya tsaya kafin ya juyo fuskar nan kamar bai taɓa dariya ba. Yadda ya yi ma kamar bai taɓa ganin Baɗɗo ba.
"Ina son mgana da kai."
Tana kallon cikin idanuwansa ta faɗi haka.
"SisNa kar ki ce masa komai don Allah."
Ummu ta faɗa tana mai rike hannun Baɗɗo cikin magiya.
"Bar ta ta faɗi abin da ke bakin ta, in tana tunanin za ta iya sauya tunanina ne akan mganar da za ta yi Bismillah."
Ya ba ta amsa har yana wani ɗaga hannu, Baɗɗo ta kalle shi cikin wani yanayi shima kai tsayen yake kallon ta.
"Na san ta faɗa miki abin da ke faruwa, in har ke yar'uwata ce da gaske gwara ki ba ta shawaran ta bi umarnina in tana so ta tsira da sauran abin da ya rage mata."
Ya faɗa cikin gadara sannan yana nuna Ummu kamar ya ga abin ƙyama.
"Domin ba ta da wani sauran wani abin da ya rage a tsakanin mu yanzu."
Ba Ummu ba, hatta Baɗɗo sai da ta ji ta muzanta idanuwanta suka kawo ruwa sai ta yi saurin shanyewa.
"Habib Allah ya fika."
Haka kawai Baɗɗo ta faɗa ta ja hannun Ummu suka raɓa ta gefen shi, Ummu tirjiya take yi amma Baɗɗo ba ta sake ta ba sai da suka shiga cikin bedroom ɗinta ta kuma ma yar da kofa ta rufe, suna jiyo dariyan Habib na tura haushi.
"Ki bar ni na je na ba shi haƙuri."
Ummu ta faɗa tana nufar ƙofar Bedroom ɗin da ƙarfi Baɗɗo ta ce" Wallahi in kika fita daga ɗaki nan, sai na kira Baffa na faɗa masa duk abin da ke faruwa."
Kalaman Baɗɗo suka sarƙe ta, ta kasa gaba ballanta baya, kuma yadda Baɗɗo ta ɗau alwashi ba za ta fasa abin da ta ce ba shi ya sa ta koma kawai ta kwanta a saman gado ta fashe da kuka.
"Ina son Habib. Ina so na bashi hakuri mu dawo kamar baya."
Dole Baɗɗo ta sauko ta fara lallashin Ummu domin ta fahimci tana son Habib kuma tana son cikin ta, ba ta da wata mafita ne a yanzu. Sun daɗe ba su yi barci ba Baɗdo na sake ba ta baki sai dai ta ba ta tabbaacin in har Habib bai daina yunƙurin zubar mata da ciki ba to ta koma gida kar ta sake zama yana wulakanta ta alhalin tana da gata.
Ita ko Ummu a zuciyarta addu'a take yi Allah ya sassauta zuciyar Habib in ya rabu da ita ina za ta saka kanta tana ji gwara su cigaba da zama a haka ta tsira da shi, sannan ta tsira da cikin jikinta da auran ta gabaɗaya tunani take yi zuwa nan gaba kaɗan Habib zai yi nadama zai dawo ya ba ta haƙuri su gyara rayuwan auren su, in shi ba ya son ta ita tana son shi sannan za ta iya jure komai saboda ta tsira da auran shi, shi ya sa ba ta kaunar mganar ta je kunnen Baffa, in ya ji kamar duka yayyenta sun ji, in kuma akwai waɗanda za su yi shuru to akwai fusatattu irin su Hamma Kabiru da Hamma Abdulrahaman da ba su da wasa ko kaɗan tana da tabbacin ko za ta mutu sai sun raba auren ta da Habib, ita kuma tana son shi tana fatan ta rayu da shi har karshen rayuwarta.
Washegari ma Baɗɗo ta yi ma Ummu abin da za ta karya kunin gyaɗa ta dama mata sai ta yi musu fanke. Habib da Baɗɗo sun haɗu lokacin da ta fito daga kitchen shi kuma ya yi shirin fita zai bar gida kowa ya yi kamar bai ga kowa ba
Baɗɗo ta kitchen ta ke leƙen Habib har ya bar falon lalle Duniya juyi juyi na gaba ya koma baya yau wai ita ce Habib zai gani ya yi kamar bai gan ta ba, ita fa mamaki ta ke yi yadda lamarin nan ya sauya. A baya ganin irin dacen da Ummu ta yi sai ta ke mafarkin ta samu miji kamar sa, amma yanzu ta ji auren da namijin ma gabaɗaya sun fita kanta, ba su da tabbas ba su da garanti ka aminta da su su ha'in ce ka, ka ba su Amana su ci, sun san salon yaudara kala kala, su kuma ga su ba tukwane ba ne ballanta ka fara ƙwanƙwasa wa kafin ka ɗauka, ba ka isa ka gane manufar su ba sai ka shiga da ga ciki, tana aiki tana hawaye Habib ya cutar da zuciyar Ummu, sannan ya cutar da kuruciyarta suma na tare da ita ya cutar da zukatan su. Damuwarta ɗaya tunanin halin da Ummu za ta shiga matuƙar Habib ya sake ta ko in iyaye suka shiga mganar ba a samu masalaha ba, tana tsoron kar damuwa da zafin zuciya su yi ma Ummu illa. Sai da ta gama shan kukanta ta share hawayenta saboda kar Ummu ta fahimci ta yi kuka itama ta fara ta samu ta yi shuru ta daina kukan da ta kwana tana yi.
Su na gama karyawa Baɗɗo ta wanke abubuwan da suka ɓata ta ɗan gyara mata gidan ta yi wanka ta yi shirin tafiya Ummu ta fara hawaye ita mai idanuwan kuka da cewa Baɗɗo ta ƙara kwana.
"Aa ba zan sa ke kwana ba, kar mijin ki ya zo ya sake ganina, karon mu ba zai yi daɗi ba."
Ummu ta na ji tana gani Baɗɗo ta yi mata sallama ta tafi ta bar ta, bayan ta jadadda mata ta kula da kanta ta riƙa samun hutu domin kiyaye dokar likita. Sannan in ta ga wata matsala kar ta zauna ta kira gida in tahowar ba zai yuyu ba Ummu ta amsa da to za ta kiyaye. Baɗɗo na tafiya ta koma ta kwanta tana ta kuka, kukan da ya fara zame mata jiki a acikin kwanaki nan.
Bayan tafiyar Baɗɗo maimakon lamarin Habib ya gyaru sai ma ya sake lalacewa. Ba ya ma nuna cewa akwai wata hallita a gidan, in sau goma Ummu za ta yi masa mgana ba zai amsa ta ba, a cewarsa in ta ga ya dawo yana kula ta sai in har ta bi umarnin sa, umarnin da Ummu ta gwammace su zauna a haka da ta amince da buƙatar sa na zubar da cikin, cikin da duk duniya yanzu ba ta da wanda take so sama da shi. Ba ta san dare nawa ta ɓata tana kuka ba, ba ta san sau nawa ta duka a gaban Habib tana kuka akan cewa ya yi hakuri ya yafe mata. Amma bai kalle ta ba yana nan akan bakan sa, ko ta zubar da ciki ko kuma su cigaba da zama a haka kafin ya yanke hukunci a kanta.
Baya cin abincin ta, ba ya neman ta bai damu da ita ba ko za ta mutu bai damu ba, ba shi da asara sai ya raba dare yake dawowa sannan ya zauna a falo ya yi ta waya cikin harshen turanci. Ummu ta yi kuka, kuka har ya zame mata jiki saboda halin da ta ke ciki. Wato ga ta jahila wacce ba ta jin turanci shi ya sa in zai yi waya sai ya sauya