Follow us on social media

Showing 30001 words to 33000 words out of 147042 words

Chapter 11 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar

alheri ne.

Ba ta bari ya lura da ita ba bakin ta alaikum ta koma ɗakinta ta faɗa kan gado ta na mai fashewa da kuka matsananci, kuka take yi kamar ranta zai fita ta yi ta tunanin mene ne dalilin Habib na aikata haka? Sai wata zuciyar ta bata amsa da cikin jikin ki, tabbas ko ta amince ko kar ta amince cikin jikin ta ne Habib ya yi alwashin sai ya fidda shi ko ta ƙarfin tsiya.
Ita kuma yanzu ta ji ma tana sake ƙaunar cikin ta, ta yi alƙawarin komai zai same ta sai ta kare shi ta zame masa garkuwan yadda Habib bai isa ya matso kusa da shi ba.

washegari Habib na fita ta je ta kwarara wannan zoɓon a tiolet ta zuba masa ruwa ya wuce. In da ta sake tabbatar da zargin ta a daran da ya dawo har ɗakin sai da ya leƙa ta ya ɗauka zai gan ta a galabai ce wata ƙila cikin ya zube amma bai fahimci komai ba a fusace ya buga mata ƙofa ya fice ya bar Ummu da hawaye a fili tana tambayan kanta.

"Me ya sa Habib? Me ya sa haka?

Tana mai ƙara kecewa da kuka da ƙarfi har yana fidda Sauti a cikin zuciyarta ta ke jin wani zafi da radaɗi, gani ta ke yi kamar ba rayuwarta ba ce, ita fa ce Ummu-Salma wacce Habib ya nuna duk duniya ba shi da kamarta amma kalle ta a cikin gidansa kashi ma ya fita daraja, duk da ya ce bai shirya zama uba ba, sannan ba ya son ta shi ya sa ba zai iya haɗa zuru'a da ita ba. Ita tana son shi har kuma gobe ba ta ji ta cikin nadaman auren shi ba wallahi tana son Habib kuma za ta yi komai domin ta ga ta tsira da mijinta da auran ta.

**

*3:45am*

Habib ne a cikin ɗakin sa ya kasa zaune ya kasa tsaye,  kansa har sara masa yake yi saboda damuwa da tunanin mafita? Wani amsa zai ba ma Masoyiyar shi in ta tambaye shi labarin cikin da ke jikin Umma-Salma? Ya faɗa mata cikin na nan bai zube ba, ya saɓa alƙawari domin ba haka suka yi ba, shi kuma duk wata hanya da zai bi domin Ummu ta saduda ya bi amma taurin kanta ya wuce tunanin shi, ya ɗauka matakin da ya fara ɗauka akanta zai yi tasirin da za ta neme shi ta bashi hakuri, salim alim a zubar da cikin nan ya gama more sadakin sa sannan ya kaɗa ta amma ta nuna masa ita ɗin mai taurin kai ne, saboda rasa mafita ya sa ya je ya siyo mganin barci sleeping pills ya saka mata da yawa a cikin zoɓon da ya san tana so sosai amma ya fahimci kamar ko ta sha bai yi mata komai ba. Sannan ya duba bai ga roban zoɓan ba in da a ce tasha yana da tabbacin ba a gida zai gan ta  ba sai dai a kira shi a ce tana asibiti amma yanayin da ya ganta ya ba shi tabbacin wannan karon bai samu mafita ba.

Hannun shi guda ɗaya ya buga a ɗayan, lokaci ɗaya yana mai dafe kan shi cikin matsanancin damuwa na rashin mafita,  me ya sa Ummu-Salma ta kasa gane wa ne?  Ita duk maganganun da ya faɗa mata ba ta yarda ba ya son ta ba? Ba ta yarda ba ita ce zaɓin sa ba, ko kuwa sai ya zauna ya yi mata gwari-gwari ne sannan za ta  gane manufar auran shi da ita, yana cikin wannan tunanin wayarsa dake yashe saman gado ta fara vibration yana kai idanuwan shi wajen sai da gaban shi ya faɗi.

"M.S..!

Ita ce ke kira, a kuma yanzu ba shi da amsar da zai ba ta, ya na ta falling ɗin ta yana ta gazawa. Me ya sa ya yi wannan wawancin tun farko bai kai Ummu Salma an cire mata cikin nan ba tare da ta sani ba? Ba ya bukatar barin wani abu na shi a rayuwar Ummu Salma, bukatar shi in ya gama biyan buƙatar shi da ita ya sake ta shike nan babu wani sauran alaqa, sannan ba haka suka yi da Masoyiyar shi ba ya riga ya yi mata alƙawarin ba wata macen da za ta fara haifa masa zuru'a sai ita, kuma ba ya son saɓa wannan alƙawarin a matsayin shi na namiji, kwata-kwata ya rasa mafita duk yadda ya ɗau lamarin kamar wasa ba wasa ba ne, lamarin na bukatar ya yi aiki tukari akan haka in ba haka ba daga baya zai zo ya yi fargar jaji alhalin lokaci ya riga ya ƙure masa.

Ganin ba za'a daina kiran ba ne, ya san halin mai kiran da saka damuwa , kuma so ta ke ta ji yadda labarin cikin jikin Umma ya tsaya shi kuma ba shi da wata amsa mai daɗin da zai iya sanar da ita.
Kiran na ƙarshe da ya katse ba a sake kira ba sai can ba daɗewa sai ya ji ƙaran shigowan saƙo hannunsa na rawa ya jawo wayar ya buɗe saƙon

"Habib ko ka ɗaga kirana ko gobe na zo gidan ka, koma me zai faru sai da ya faru. Ka amsa kirana."

Haka aka rubuta a jikin saƙon, jikinsa na rawa yana ƙokarin kiran lambar sai ga shi an sake kira a sanyaye ya ɗaga amma bai yi mgana ba.

"Habib me ya faru ne?

Aka tambaye shi, daga can cikin sanyin murya kuma muryan ta mace ce.

Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce"  Ina tunanin cikin yana nan"
Ya faɗa lokaci ɗaya yana mai shafa kansa cikin damuwa.

"Kana ma tunani ne ba ka da tabbaci Habib?

Aka sake faɗa wannan karon cikin ɗaga murya.

"Walahi na saka mata kamar yadda na faɗa miki. Sai dai..."

"Sai dai me?

Ta katse shi a fusace.

"Ina tunanin ba ta sha ba."

Wani ɗan ihu aka saki acikin wayar daga can bangaren.

"Ki yi hakuri zan samo wata mafitar."

"Wata mafitar! Ai ka daɗe da rasa damar ka Habib. Tun farko kai ka jawo mana wannan matsalan tun farkon auran ku na ce ka sa a yi mata planning yadda wanzuwar ciki a jikinta ba zai ba mu matsala ba, ba ka aminta da shawarana ba ka zauna a tunanin shekara ɗaya ya yi kaɗan ɗin da za ta samu ciki, ka manta da yanzu aure ma ba a shekara ake haihuwa, cikin ta na farko ba domin Allah ya yi zubewar shi da shi ma ya bamu matsala wannan ma Habib ka kasa yin wani tunani? Sai da na ce maka kar ka sanar da ita komai ka ɗauke ta ka kai ta asibiti a zubar da cikin ka kuma sake ta daga can amma ka ce ba haka ba na ka tsarin za a bi yanzu ga in da na ka tsarin ya kai mu. Haba Habib ina jin kamar na haukace in na tuna jakar yarinyar ce ta riga ni aje ƙwan haihuwarka a mahaifarta ji na ke yi kamar zan suma saboda baƙin ciki."

Ta karishe faɗa cikin ƙaraji, jikinsa har rawa yake yi wajen zayyano mata kalaman ban haƙuri da rarrashi.

"My love kin ga kwantar da hankalin ki, ni na yi miki alƙawarin bayan ke babu wata macen da ita isa ta fara haɗa zuru'a da ni. Ki kwantar da hankalin ki dole cikin nan ya zube a goben nan in sha Allahu."

Ya faɗa cikin sigan lallashi, daƙyar har yana ɗan ɗaga hannu kamar tana ganin shi.
Shuru na wani lokaci daga can bangaren kafin ta sauke numfashi ta ce" Habib ka san ina son ka shi ya sa na ba ka damar yin abin da kake so ko?

"Na sani."

"To kar ka ba ni kunya. Kar ka saka na cire yaƙini na a kan ka."

"In sha Allahu, gobe zan ɗauke ta mu je asibiti a cire cikin nan ko tana so ba ta so."

Dariya aka yi daga can bangaren kafin ta ce" Habib kar ma ka fara, in ka yi haka za ka yi nadama. Yadda Ummu ta san manufarka akan cikin jikinta ko Saudiya ne ba za ta sake aminta da kai ba balle har ta haɗa tafiya da kai. Ka samo wata mafitar dai."

Sai da ta faɗa kuma ya fahimci haka yadda ya bayyana munafarsa ba lalle Ummu ta sake aminta da shi ba amma duk da haka ba zai sare ba zai sake jaraba sa'ar shi sun daɗe suna waya yana faɗa mata kalaman soyayya cikin lallashi har sai da ya tabbatar da hankalinta ya kwanta sun rabu da cewa duk yadda zai yi zai yi na ganin cikin nan ya zube a gobe in sha Allahu.

Su sun gama na su tsarin, abin da kuma ba su sani ba Ubangiji shi ya riga ya gama nashi. A cikin zanen kaddaran su Ubangiji ya rubuta cewa Habib da Ummu za su samar da gudan jini, daga gudan jini zuwa rai.

***

Wani abu ya ba ma Ummu mamaki da ya sa kuma ta fara shakku, lamarin Habib yanzu ya zama abin tsoro da taka tsan-tsan a wajen ta.
Shigowa fa ɗakin ta ya yi da safe kafin ya wuce wajen aiki yana tambayan ta ya jikin ta yana fatan ba ta da wata matsala.
Tsabar mamaki sai ta kasa mgana, tana kallon shi yana yi mata mirmishi, mirmishin da har cikin zuciyarta ba ta yarda da shi ba.

"Sannu, Baby zan tafi wajen aiki, amma ina so ki yi mini girki da kwalliya yau in na dawo za mu yi mgana."

Har ya fice daga ɗakin tana bin shi da kallo bakin ta sake ta kasa mgana wata zuciyar na faɗa mata Ko dai ya saduda ne, wata ƙila ya gane kuskuren shi ne zai ba ta haƙuri, da ya ke tana son Habib ta kuma aminta dashi shi ya sa wata zuciyarta ta rinjaye ta da cewa hakuri zai ba ta, ayayin da wata zuciyar a can gefe tana ɗan ɗari-ɗari alamun ba ta aminta da saukowan Habib lokaci ɗaya ba. Sai dai duk da haka ba ta fasa yin abin da ya ce ba, yamma na yi ba ta ko jin daɗin jikinta ta miƙe ta fara aiki Baɗɗo ma ta kira ta a waya ta ce tana tunanin za ta shigo sai ta ce mata ta bari sai gobe, acikin ranta tana murna da farinciki na daidatawar ta da Habib ko da Baɗɗo za ta zo gobe ba za ta fahimci komai ba.

Farar shinkafa ta dafa da miya sai salat. Har da kunun aya ta yi duk da tana yi tana faman hutawa domin sai ta ke jin numfashin ta na yin sama sama kamar zai ɗauke. Ko kafin mangariba ta gama komai sai da ta idar da salla sannan ta rarrafa ta yi wanka tana jin jikinta ya yi zafi zazzaɓin jikinta ya dawo, ammma haka nan ta yi masa kwalliya cikin wata doguwar riga baka mai kwalliyan ja a jikinta shi ya sa ma mayafin rigar ja ne, ta yi kyau duk da ba kwalliya ta yi ba amma fuskarta ta yi mata fayau kamar wacce ta shekara tana jinya.

Da wuri Habib ya dawo tun kafin ma a kira sallar isha'i ya shigo  gidan da niƙi-niƙin ledoji ya siyo balangu da su lemon exotic. Yana ganin ta ya buɗe mata hannuwana ya ce ta taho ita dai ba ta saki jiki ba, ta tafi gare shi ya rumgume ta yana wani shinshina wuyanta cikin sanyaya murya ya ce.

"Na yi kewar ki Baby."

Hawaye suka kece ma Ummu, amma Habib bai bar ta haka ba sai da ya ɗago ta ya saka harshen shi yana lashe mata hawayen fuskarta, daga nan ya fara yamutsa ta, duk da zuciyarta na son ta hana shi amma ta kasa cewa ta ke yi Habib ne, Habib ne fa mijinta masoyinta. Tun a falo ya raba ta da rigan jikinta sanyi take ji shi ya sa duk tsigan jikinta ya tashi ga shi jikin na ta ya ɗau zafi amma Habib bai lura da wannan ba. Haka ya iza ta zuwa cikin bedroom ɗin su ya mora jikin Ummu fiye da yadda ya saba mora tana ji ana ta sallar isha'i a masallatan kusa da su amma Habib bai saurara mata ba, ta gaji ba za ta iya ba amma bai fahimta ba, lamarin na shi babu tausayi da ya kawo kamar zai sauka sai ya koma tun Ummu na kuka a ɓoye har ta dawo tana yi a sarari babu in da jikinta ba ya rawa, sai ta ji kamar ba Habib ba sai ta ji yau ba ta ji daɗin abin ba kwata kwata ta ji wani haushi na sukan zuciyarta amma bai saurara mata ba sai da ya gaji domin kan shi ya kuma tsallake ta ya shiga tiolet domin tsarkake kan shi.

Kanta ta tusa cikin bargo tana kuka amma  ta rufe bakin ta kar ya yi sauti, tana jin shi ya fito yana ce mata ta tashi ta yi wanka su ci abinci yana jin yunwa, ko tsayawa bi ta kanta bai yi ba ya fice ya bar ta nan kwance tana kuka. Da kyar ta iya rarrafawa ta shiga tiolet mene ne ya sa Habib ya yi mata haka! Ko yana so da karfin tsiya sai ya yi ajalin cikin jikin ta ne, Allah ya fi shi domin tun da ta gano manufarsa ta ke saka shi cikin addu'o'in ta na Allah ya tsare ta ita da cikin ta daga sharrin Habib, amma me ya sa har yanzu ba ta daina jin ta daina son Habib ba, tana son shi tana son cikin jikinta sannan tana son auransu shi ya sa yau ɗin ma ta kasa yi masa gaddama.

Jikinta zazzaɓi ne rau haka ta rarrafa ta fito ta sauya kaya ga shi kanta ya jike kuma ciwo yake yi mata ba ta ko samu damar busar da shi ba Habib ya zo ya dame ta da cewa yana jin yunwa haka ta fita daga ita sai wata riga doguwa ta wani yadin material ita ce a farkon wardrope shi ya sa ta saka ta. saman dinning suka zauna ta yi serving ɗin shi ganin ita ba ta saka ma kanta ba ya sa ya tambayeta a sanyaye ta ce ba ta ci ko ta ci sai ta yi amai.
Sai ya ɗauko mata balangun da ya siyo ya ce ta ci ko kaɗan ne.

"Ba zan iya ci ba."

Ta faɗa a sanyaye ajiye spoon ɗin hannun shi ya yi yana kallon ta hannunta guda ɗaya ya kama yana faɗin" Sannu Sorry ki ci ko kaɗan ne sai ki sha wannan lemun in sha Allahu ba zaki yi Amai ba"
Tana cewa ba za ta ci ba yana ɗaukowa ya nufi bakinta da shi tana kauda kai amma sai da ya saka mata shi a cikin bakin ta da ta tauna sai ta ji daɗin shi, shi ya sa sai ta sake ɗauka ta kai bakinta tana taunawa lokaci ɗaya tana kallon shi.

"Kin gani, ba za ki yi amai ba"

Ya faɗa yana yi mata mirmishi, yake ta yi masa ba ta yi mgana ba, abin da ya ba ta mamaki da ya sa ta sake jin a ran ta cewa Habib ba shi da gaskiya, lemun exotic guda biyu ya siyo da zai tsiyaya mata na ta dabam ne, na shi ma na dabam sai ta fara tunanin tunda sha za su yi me ya sa sai ya buɗe har guda biyu, kawai sai ta ji ba ta aminta da cewa Habib ba yana wannan abin don Allah ba ne. Yana yi ne ba domin komai ba sai domin cimma manufar da ya so ta biye mishi ya aiwatar. Ita kuma ta shirya masa da sanin ta ba za ta taɓa bari ya yi galaba akan ta ba.

Guda huɗu ta ci balangun sai ta cire hannunta da sauri ya kalle ta." Kin ƙoshi kenan?
Sai ta jinjina masa kai, da sauri ya miƙo mata lemun da ya saka kofin tangaran yana faɗin" Sha wannan sai naman ya kwanta miki yadda ba za ki yi amai ba."

Kallon shi ta ke yi kafin ta ce ta ƙoshi.

"Sha mana."

Ya sake faɗa yana tura mata kofin a bakinta da sauri ta kauda kai, maimakon Habib ya bar ta haka sai ga shi har yana miƙewa ƙoƙarin sa ya tura mata wannan lemun na dole sai ta sha ganin haka kawai ya ba ta tabbacin koma mene ne yana cikin wannan lemun na hannun Habib.

Ganin ta yi Habib na neman yi mata ɗure, tunda ya tashi daga zaune ya matso kusa da ita, ya rike kanta yana tura mata kofin zuwa bakin ta yana faɗin ta sha.

"Ki sha mana."

Ya faɗa yana kallonta.

"Na ƙoshi, zan yi amai in na sha."

Ran shi ya fara ɓaci ko ta fahimci akwai wani abu a cikin lemun ne

" Ki sha na ce miki ba za ki yi Amai ba."

"Ba na so na sha."

Ummu ta faɗa lokaci ɗaya tana ƙokarin miƙewa zaune shi kuma bai sani ba ya kawo hannun shi sai ta kaɓe kofin da lemun suka tarwatse a saman dinning ɗin.
Jikin Ummu na rawa take kallon shi, shi kuma lemun da fashasshan kofin ya ke bi da kallo ran shi na ɓaci.

"Ka yi haƙuri."

Bai ce mata komai ba ya wuce kitchen ya sake ɗauko wani kofin ya zuba mata yana faɗin" Wannan ki sha, ki sha na ce Ummu Salma kafin ki ɓata mini rai."
Ai kafin ya nufota ta bar wajen Dinning ɗin zuwa falo sai ya yi tsaye da lemu a hannun shi yana kallon ta.

"Ke me ye haka?

Ya faɗa ganin Ummu ta nufi bakin ƙofa ta tsaya.

"Dawo nan malama."

Ya faɗa yana takowa tsakiyar falon.
Ummu ta sake matsawa jikin kofa ta saka hannu ta murza key ɗin ta buɗe ƙofar lokaci ɗaya tana faɗin" Na ce ba zan sha ba dole ne."
"Dole ne, dole ki sha wannan lemun domin cikin jikin ki ya zube."
Ya faɗa cikin tsawa har yana zare mata idanuwansa

Da man ta san za a rina hawaye suka kece mata cikin rauni ta ce" Me ya sa Habib? Wai me ya sa kake son raba ni da gudun jinina ne?
"Saboda bana so ki haihu. Ban shirya hakan tare da ke ba."
"To me ya sa?
Ummu ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login