ENGLISH DESCRIPTION
The narrative centers on a family gathering where the children present their school results to their father, Malan. While Faisal and Fatima (children of the first wife, Inne) excel, the children of the second wife, Mama, perform poorly. To deflect blame, Farida (Mama’s daughter) attempts to forge her grades, leading to a violent confrontation where Malan beats her for lying.
The plot thickens as Mama employs a calculated "divide and conquer" strategy. She manipulates Malan into believing that Inne (the estranged first wife) is using "asiri" (black magic) to ruin the intelligence of her children while boosting her own. By playing the victim and feigning concern, Mama successfully turns Malan against his own high-achieving children, Faisal and Fatima. The script vividly portrays the physical and emotional abuse the stepchildren endure, including a climactic physical altercation where Faisal, pushed to his breaking point, accidentally strikes Mama while trying to defend himself, leading to a brutal retaliatory beating by his half-brothers.
HAUSA DESCRIPTION
Labarin ya ta’allaka ne akan wani taron iyali inda yara suke nuna sakamakon jarabawarsu ta makaranta (result) ga mahaifinsu, Malan. Yayin da Faisal da Fatima (’ya’yan matar fari, Inne) suka nuna kokari sosai, su kuwa ’ya’yan matar gida, Mama, ba su yi abin kirki ba. Don kauce wa laifi, Farida (’yar Mama) ta yi kokarin karya lamba a jikin takardarta, wanda hakan ya kai ga barkewar rikici inda Malan ya dake ta saboda yin karya.
Al'amura sun kara rudarwa yayin da Mama ta bi wani salo na neman raba kan iyalin. Ta yi amfani da makirci wajen gamsar da Malan cewa Inne (matar fari wacce aka kora) tana amfani da asiri ne domin ta bata kwakwalwar ’ya’yanta (yaran Mama) yayin da take karawa nata ’ya’yan kokari. Ta hanyar nuna kanta a matsayin wacce aka zalunta da nuna damuwar karya, Mama ta yi nasarar juya hankalin Malan akan kwararrun ’ya’yansa, Faisal da Fatima. Wannan rubutu ya fito da irin cin zarafi na fili da na zuciya da yaran kishiya suke fuskanta, har zuwa lokacin da Faisal ya kai bango, ya buge Mama ba tare da son ransa ba yayin da yake kokarin kare kansa, wanda hakan ya sa ’yan’uwansa maza suka yi masa dukan tsiya.