Follow us on social media
Showing 66001 words to 69000 words out of 147042 words
Chapter 23 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
shi.
"Ya sa ke ni..."
Ta faɗa tana sarƙewa cikin matsanancin kuka.
Sai da Baffa ya miƙe da sauri kansa ya sara, idanuwansa suka ciko da ƙwalla hannunsa na rawa haka ƙafafuwansa shuru ya yi yana kiran sunan Allah a cikin zuciyarsa domin ya samu ya tattaro natsuwarsa.
Ammah ta biyo shi a tsayen tana tambayan shi jin ya yi shuru sannan ba su yanke wayar ba, ta san waye Baffa shurun sa na nufin damuwa mai yawa ko a fuskarsa ma ya bayyana haka.
Tana so ta yi magana amma sai ta kasa ta dai tsura masa ido kawai tana bin shi da kallo.
"Baffa Habib ya sake ni, ya sake ni jiya da daddare."
Ummu Salma ta sake faɗa cikin kuka jin Baffa ya yi shuru, bai ce komai ba.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un."
Baffa ya samu bakin shi da furtawa cikin wata murya mai cike da tausayin Ummu.
"Allahumma ajirni fimusibatihi. Daga gare ka muke Allah kuma a gare ka za mu koma."
Baffa ya sake faɗa cikin yaƙinin da cewa akwai Allah da sanin sa komai ya faru kuma shi zai kawo sauƙin lamarin cikin gaggawa.
Ummu kuka kawai take rusawa kamar ranta zai fita Baffa ya kasa jure jin kukan ta kawai sai ya kashe wayar, ya ma kasa kallon Ammah wacce ke bin shi da kallo, kansa ya juyar kawai ya koma ya zauna a gefen gado ya dukar da kansa lokaci ɗaya ya saka hannayensa duka biyu ya dafe kansa yana sake maimaita salati da muryansa cikin rauni da tausayi.
"Allah ya ba ki ikon cinye wannan jarabar mai zafi da raɗaɗi Ummu Salma."
Muryansa ta karye da man Baffa akwai rauni ko ciwo mutun yake yi sai ya yi kuka lokacin da Ammah ke haihuwa haka zai yi ta kuka asibiti in tana naguda, ganin yanayin shi kawai ya ba ta tabbacin wani abu ya faru mara daɗi amma ba ta tambaya ba, sai ta bishi ta zauna a gefen shi ta ɗora hannayenta saman kafaɗan shi tana ɗan matsawa alamun lallashi duk da itama ƙarfin hali take yi amma zuciyarta ta yi rauni ba ta so ta nuna ne.
Shuru na wani lokaci kafin Baffa ya fesar da numfashi cikin hikima ya share ƙwallar da ta ɗan siraro masa ta gefen idanuwansa saboda kar Ammah ta gani abin da bai sani ba, ta riga ta gan shi, kukan sa kawai ya sake ba ta tabbacin Ummu ta fsɗa cikin kaddaran aure, kaddaran da take ta yi mata fatan kar Allah ya sa ta faɗa a cikinsa, domin ba ko wacce mace ba ce jaruma, ba ko wacce mace ba ce take iya tsallake wannan jarabawar sai jaruma sai sadaukiya amma Ummu ba za ta iya ba zuciyarta karama ce tana da rauni ba lalle ne ta fuskanci girman jarabawan da ya faɗa mata ba.
Baffa ya ɗago kanshi suka haɗa ido da Ammaj sai kawai ta yi masa mirmishi, ita wai a dole ta nuna masa ba ta damu ba, fillanci na cin ta amma duk wanda ya kalleta ya san a cikin zuciyarta tsoro ne da fargaba ba ta tambaye shi ba shima sai ya kasa faɗa mata, illah hannayenta da ya jimƙe cikin nashi yana kallon ta amma ya kasa mgana a cikin zuciyarsa salati kawai yake yi da kiran sunan Allah.
Itama sai ta jimƙe hannayen na shi cikin nata cikin karfin hali ta kira sunan shi.
"Baffa."
Bai amsa ba amma yana ta kallon ta.
Sai kuma ta yi shuru ta kasa mgana tana so ne ta tambaye shi amma ta kasa, shi kuma ya san halinta ba za ta sake tambaya ba saboda kawaicin ta sai kawai ya yi kumdulan fada mata ita uwa ce ya kamata ta sani ko domin su yi tunanin mafita.
"Jamila."
Tunda ta ji wannan sunan a bakin Baffa ta san maganar da zai faɗa mata mai girma ne.
"Habibu ne ya saki Auta jiya da daddare."
Ya faɗa yana kallonta hannayenta na cikin na shi yana matsawa, shuru na wani lokaci yana kallon ta duk da ta tsammaci haka amma ai zato ne ba gaskiya ba yanzu da ta samu tabbacin sai ta ji zuciyarta ta yi duhu wani abu kamar ya sare daga kirjinta kwata-ƙwacin abin da ta ji a lokacin da Fatima ta zo gare su da tsohon dare ɗauke da jaririn da ko jinin haihuwa ba a wanke masa ba, a lokacin da ta ba ma Baffa takardan saki, abin da ta ji a lokacin a wannan lokacin ma shi ta sake ji.
"Ta kira ni tana ta kuka Jamila. Gwanin ban tausayi "
Ya sake faɗa muryansa har tana sauyawa, Ammah ta yi ajiyar zuciya kafin ta tattaro kalaman bakinta ta furta." Allah ya sa hakan ya zame mana alheri gabadaya "
"Amin "
Ya amsa yana kallon ta.
Shuru na wani lokaci kafin Amma ta yi ƙarfin halin cewa" Baffa wa zai je ya taho da Ummu?
Ta faɗa tana kallon shi, sai yanzu ya tuna ya kamata wani ya je ya ɗauko ta zuwa gida a yanayin da ta ke ciki tana bukatar wani a kusa da ita.
"Bari na yi ma Saddam magana ya tuka ni muje mu taho da ita."
Baffa ys faɗa yana miƙewa da sauri Amma ta mike ta riko shi ganin duk ya daburce kallon ta ya yi yana cigaba da faɗin" tana ta kuka gwara na je da kaina "
Ya faɗa yana laluban aljihun jikinsa
"Ammah ina key ɗin mota ta?
Ya faɗa yana waige-waige Baffa fa ba ya cikin natsuwarsa shi ya sa ta sake riko shi tana kiran sunan shi.
"Baffa."
Sai kawai ya tsaya yana kallonta
"Jamila Auta tana can tana kuka ba ki ji muryan ta ba."
Ya faɗa cikin karyewan sauti, kawai sai ta faɗa jikin shi, domin itama in ta cigaba da jin sautin Baffa cikin rauni za ta iya fashewa da kuka ba ta sani ba, jin ta a jikinsa ya sa ya yi shuru kawai yana sauke ajiyar zuciya, bayansa take ɗan tapping da hannunta alamun lallashi, kuma ta yi nasara domin sai ya ɗan samu natsuwar zuciya.
"Ba kai za ka je ba Baffa."
Ya ji Ammah ta faɗa da sauri ya dago ta kafin ya yi magana ta yi saurin cewa" ka kira Abdullahi ka sanar da shi abin da ke faruwa ka ce ya ɗau mota ya je ya ɗauko Aminiya zan kira ta yanzu na sanar da ita abin da ke faruwa, ita in suka je za ta shiga ciki ta taho da Ummu gida."
Tabbas ya aminta da shawaran ta, gwara mace ta je zai fi akan namiji.
"Hakan ya yi, amma ko na kira Abdulrrahman ne?
"Aa gwara dai Abdullahi ka san halin Abdulrrahman fusattace ne."
Shi saboda tashin hankali duk ya manta da halin ƴa'yan na shi, wayarsa ya fara laluba Ammah ta ɗauko masa ita a gefen gado ta mika masa lokaci ɗaya tana faɗin" Ka kira shi yanzu, bari na je na kira Aminiya"
Tana gama faɗin haka ta wuce ta fita daga ɗakin, falon ta yana sakaye ne ta tura ta shiga wayarta a chaji ta sakata tun daran jiya hannanunta na rawa kamar yadda zuciyarta ke bugawa.
Tana duba wayar sai ta ga ma Ummu ta kirata sau uku a lokacin da ta kira Baffa kenan, lambar Ummin ikki ta nemo wacce ta yi ma saving da Aminiya, duk da Ammah ba ta yi karatun boko ba amma sun yi yaki da jahilci shi ya sa ta iya karanta hausa, wani lokacin ma da fillanci take yi saving din lambobin wayarta.
Sai dai tana kiran wayar sai ta ji a kashe, har sau biyu ba ta shiga ba sai kawai ta laluɓo lambar wayar Aisha(Baɗɗo). Tana kiranta ita sai ta shiga.
Baɗɗo na kwance a ɗakin su bayan ta idar da sallar asuba gajiya ne a jikinta jiya wajen takwas na dare ta iso gida daga Mubi, tana idar da salla sai ta ɗan kishigiɗa barcin ya ɗan ɗauke ta kenan ta ji ringing ɗin wayarta dake gefen filon data ke kwance da barci-barci ma a idanuwanta ta zaro wayar sai dai ta wattsake ganin sunan Ammah tana kiranta, ido ta waro tana sake duban sunan mai kiran da gaske dai Ammah ce.
"Wa ke kira hala ?
Adda Kaltume ke tambaya ganin yadda Baɗɗon ta zaro ido kamar ta ga wani abun tsoro.
"Ammah ce fa."
Ta faɗa tana kallon ƙaramin agogon bangon dake ɗakin barcin na su, ƙarfe 6:32am na safe to ba lafiya.
"Topha, ɗaga mu ji Allah ya sa dai lafiya"
Adda Kaltume ta faɗa, daidai lokacin da Baɗɗo ta ɗaga kiran Ammah bayan ta sake kiran ta a karo na biyu.
"Ammah ina kwana."
Daga can bangaren Ammah ba ta tsaya amsa gaisuwar Baɗɗo ba da sauri ta ce" Aisha ina Aminiya?
"Tana ɗakin ta "
"Kai mata wayar zan yi magana da ita."
Amma ta faɗa muryanta cunkushe, Baɗɗo ta mike tana amsawa da to Adda Kaltume tana ta mata tambaya me ya faru da hannu, ita kuma Baɗɗo tana ɗaga mata hannu alamun ba ta sani ba.
Ummin ikki na cikin ɗakinta, itama da carbi a hannunta tana ja ne barci ya ɗan sace ta tana zaune tana ta gyangaɗi sai ta ji Baɗɗo a saman kanta tana faɗa mata ga Amma na son magana da ita.
"To Allah ya sa lafiya "
Ta faɗa tana leken waje ganin har lokacin gari bai ida sa wayewa ba.
Tana karɓan wayan ta saka a kunnenta lokaci ɗaya tana faɗin" Aminiya Allah ya sa lafiya."
Ummi ikki ta faɗa cikin fargaba kira da sassafe haka ba na lafiya ba ne.
"Wayarki a kashe Aminiya ?
Ammah ta faɗa, da sauri Ummin ikki ta ce" Tun jiya ban ga wayar ba, waya sani ma ko ta mace ba chaji ne."
Amma tace" To ƙila."
"Lafiya Aminiya? Na ji muryan ki wani iri ne"
Amma ta yi ajiyar zuciya kafin ta ce" Ki shirya ga Abdullahi nan zai zo ya ɗauke ki zuwa gidan Ummu"
"Me ya faru da Ummun?
Ummin ikki ta tambaya har tana waro ido, Baɗɗo na gefe tun da taji an ambaci sunan Ummu ta matso kusa da sauri tana son jin abin da ya faru.
"Ya sake ta ne."
Ammah ta faɗa tana runtse ido, kafafunta sun fara rawa da ya sa dole ta lalubi gefen kujeran dake gefenta ta zauna tana ƙoƙarin daidaita yanayin ta.
"Ya sake ta fa ta kika ce Aminiya! Shi Habibun ne ya saki Ummu Salma?
Ummin ikki ta faɗa da karfi da ya sa Baɗɗo ta yi zaman yan bori a gaban Ummin tana faɗin" Habib ya saki Ummu?
Ta sake maimaitawa hannunta a saman ka cikin tashin hankali.
"Ya sake ta Aminiya, Abdullahi na hanya za ku je ku taho da ita "
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un amma dai Habibu ya cuce mu Allah ya isa tsakanin mu da shi."
Ummin ikki ta fada sai ga hawaye Ammah kashe wayarta kawai ta yi ta bar Ummin tana ta salati da tsine ma Habibu.
Baɗɗo ta fashe da kuka tana faɗin" Innalillahi Ummi Habib ne ya saki Ummun? Ummun tawa?
Take faɗa tana kuka, Ummin ikki ta ce" Wannan yaron ya gama cutar mu Allah sarki Ummu."
Da man kuma Ammah ta sanar da ita zaman da aka yi na farko ta dinga zagin shi tana cewa mara albarka, to amma daga baya Ammah ta ce mata an daidaita ashe bai hakura ba sai da ya mayar da ƙaramar yarinya bazawara.
Kukan Baɗɗo da hargagin Ummi ya fiddo da duka yaran gidan har mahaifin su Baɗɗo duk wanda ya tambaya aka faɗa masa abin da ya faru sai ya girgiza.
"Subhanallah lamarin bai yi daɗi ba me ya faru ne?
Baban su Baɗɗo na tambaya Ummi ba ma tsaya masa bayani ba ta miƙe tana faɗin Abdullahi na hanya zai zo ya dauketa za ta je ta taho da Ummu zuwa gida Baɗɗo na jin haka ta ce itama za ta je Ummi ta ce ba za ta je ba.
"Ummi ki je da ita in Ummu ta gan ta za ta ji daɗi "
Adda Kaltume ta faɗa cikin damuwa ta girgiza da jin wai Habib ya saki Ummu Salma, duk wanda ke gidan nan ya san waye Habib domin zuwa goma in Ummu za ta yi shi zai kawo ta ya kuma zo ya ɗauke ta kuma duk zuwa sai ya shigo ya gaida Ummi da Baba, tun kafin auren su ma bayan auren ma sai ya zama ɗan gida nan zai zo ɗaukan Ummu su zauna a falon Ummi da shi da Baɗɗo da Ummun suna ta hira suna dariya.
Kowa sai jinjina lamarin yake yi, abin mamaki abin tausayi ga rayuwar Ummu, da wayar da Ammah ta yi da Ummin ikki ko minti talatin ba a yi ba sai ga Hamma Abdullahi bakwai saura mintina ya iso gidan yadda ya shigo kawai za ka san shima labarin ya dake shi, jallabiya ce a jikinshi a baibai ya sako ta ma domin yana barcin nan na bayan asuba ya samu wayar Baffa labarin da ya faɗa masa ne ya sa ya diro daga kan gado bai shirya ba, ya razana da jin wai mijin Ummu ya sake ta! Har ya kariso gidan Ummin ikki yana tunanin to me ya sa zai sake ta? To ta yi masa wani abu ne?
Daga Ummin har Baɗɗo da hijaban jikinsu suka bi Abdullahi takalma kawai suka saka, suna tafe a mota Ummin ikki na sake kwashe ma Habib albarka Baɗɗo na daga baya tana ta sharan ƙwalla tausayin halin da Ummu take ciki a daidai wannan lokacin.
"Ummi to wai me ya sa zai sake ta? Ko ta yi masa wani abu ne?
Abdullahi ya tambaya jin yadda Ummin ke mgana da alamu ta san wani abu.
"Ba ka san abin da ya faru kwanaki ba ne Abdullahi?
"Ban sani ba Ummi, Baffa bai faɗa mini ba, haka ma Ammah."
Nan fa ta warware masa komai mamaki ya kama shi sai ma ya kasa mgana wato shi ya sa kenan ya ga Baffa Umaru ya zo har da mijin Ummu da ita kanta ashe lokacin duk matsalan ne ya ta so.
"Wai ba ya son ciki ka ji fa, sai ka ce shi uwarsa ba cikin ta yi ta haife shi ba wataƙila daga sama ya faɗo"
Ummin ikki ta faɗa cikin takaici da haushi.
"Allah ya kyauta."
Kawai Abdullahi ya ce amma maganganu na yawo a cikin ranshi, ta ya ya mutum zai auri macen da yake so kuma ya ce ba ya son ciki? Cikin kuma na shi ne, daga karshe hadda saki? Kai gaskiya yana tamtama an ya mijin nan na Ummu Salma yana son ta kuwa? Domin wanda ke son ka ba zai yi maka wannan tozarcin ba.
Bai sake magana ba har suka isa gidan, a bakin flat ɗin Ummu suka yi parking ɗin motar, dukkansu kuma suka firfito, abin mamaki ƙofar falon Ummu ma a buɗe take har ga labule nan a waje shi ya sa kawai suka faɗa, Baɗɗo ce ta shige gaba da sauri Ummi a bayanta Abdullahi kuma sai ya tsaya daga waje bai shiga ba, a tunanin shi ko Habib ɗin na gidan abin da ba su sani ba tun wajen shidda da rabi ya tattara kayan shi kaf ya bar gidan a motar shi baya son ma wani cikin yanuwan Ummu su gan shi tun da abin da ya haɗa su ya raba baya fata ko son sake haɗuwa da duk wani abu da ya shafi Ummu Salma. Tunda ya ce ya gama da ita, to har abada ya gama da shafin ta.
Yadda Baɗɗo ta ga Ummu Salma ya sake tsinke mata zuciya tana zaune a in da ta yi salla kanta jingine da wardrope, ta yi kuri kawai ba ta magana ba ta kuma kuka amma fuskarta da idanuwanta sun kunbura babu kyan gani.
Rumgumeta ta yi ta fashe da kuka tana faɗin" Allah ya saka miki Ummu, da ikon Allah Habib sai ya ga sakamakon shi."
Ummu ba ta mgana tana dai kallon Baɗɗo kawai, Ummin ikki ta kasa mgana saboda tausayin Ummu har tana ƙwalla.
"Baɗɗo kamata ta tashi, ki kaita falo ki zo ki ɗan haɗa mata kayan sawan ta."
Da to Baɗɗo ta amsa, ta taimaka ta miƙar da Ummu tsaye ta riƙe ta zuwa falo, ta zaunar da ita a saman kujera ta zauna kawai tana kallon ta, bakin ma ya ɗinke ba mgana sai dai kawai ido.
Baɗɗo na kuka ta juya ta koma ciki tare da Ummin ikki suka cika akwatin Ummu huɗu da kayan sawan ta, Ummin ikki ta ce duk a cire zannuwan gadon kar su yi ƙura a tusa su cikin wardrope kafin a ga abin da Ubangiji zai yi, Baɗɗo ce ta yaye zanin gado sai ga takarda ta faɗo ta ɗauka ta buɗe ta karanta.
"Ummi."
Ta faɗa cikin ƙaraji lokacin da ta gama karanta takardan sakin Ummu Salma.
"Mene ne ya faru?
Ummin ikki ta faɗa cikin tashin hankali tana kallon Baɗɗo..
"Ummi saki uku fa Habib ya yi ma Ummu."
Ta faɗa tana nuna mata takardan hannunta
"Innalillahi wa'inna alaihirraju'un."
Ummin ikki ta faɗa kanta har yana sarawa.
"Wannan wani irin sakin wulakanci ne da tozarci?
Ta faɗa tana hawaye, Baɗɗo ba saki ukun take yi ma kuka ba illa maganganun da Habib ya rubuta masu alamu da tozarci da wulakanci bayan sakin
Karɓan takardan Ummin ikki ta yi ta ce bari ta kai ma Abdullahi bayan ta umarci Baɗɗo da ta yi sauri ta naɗe zanin gado ta kuma jawo akwatunan Ummu zuwa falo.
Abdullahi na tsaye jikin motar shi yana waya da Hamma Jibo.
Jiya sai wajen goma na dare suka isa, yana shirin zuwa wajen aiki ne Abdullahi ya kira shi yana sanar da shi mugun labari, shi ne suke tattaunawa yana ba shi labarin halin da ya je gidan Ummu ya same ta a ciki har zuwan da suka yi shi da Baffa gidan waliyin Habibun ashe duk bai ji ba shi ne ya yi mata sakin wulakanci, sai a lokacin Abdullahi ya tuna wato ranar da ya ga Baffa da Hamma Jibo sun tafi ashe can suka je.
"Ni fa Hamma duk ban san abin da ke faruwa ba, kwanaki dai na ganta a gida duk ta rame to ni ban kawo cewa mata matsala ba ce."
Abdullahi ya faɗa yana nusar da hannunsa a cikin sumar kansa.
"An ɗauka za a iya gyara lamarin ne ashe bai zai gyaru ba."
Hamma Jibo ya faɗa daga can bangaren cikin damuwa da tausayin ƙanwar tasu.
Kafin Hamma Abdullahi ya sake magana Ummin ikki ta fito wajensa tana mika masa takardan hannun ta.
"Abdullahi ka ji tozarcin