Follow us on social media

Showing 60001 words to 63000 words out of 147042 words

Chapter 21 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar

su ya gaishe da matan mahaifin shi sannan ya shiga ɗakin da mahaifin shi ke jinya ya zauna.

Hatsari ya yi shekaru goma da suka wuce, ya bugu a kansa har ya shafi ƙwaƙwalwarsa sannan ƙugunsa ya samu matsala baya iya zama daga kwanciya sai kwanciya sannan baya mgana sai dai ya yi ta kallo ka kawai da idanuwana sannan kan ma da sauƙi.

Har kusa da shi ya ƙarisa ya riƙe hannun shi yana gaishe shi yana ta dai kallon shi. Gwaggo ta shigo ita ce babba a matan gidan kuma ita ce ta riƙe Habibu, sai dai a gidan shi ne kaɗai ke da ɗan rufin asiri shi ne Namiji babba sauran duk mata ne suna gidan mazajen su shi ya sa duk ɗawainiyar gidansu tana wuyan sa, da laluran mahaifinsa na shekaru goma ana ta fama, a dangin mahaifin na shi ban da Alhaji Sheriff to kowa ma nema yake yi lamarin dai sai godiya.

Gwaggo ta tambayi Ummu da ina tafisu, ya ce tana gida ta ce a gaishe su ya yi ƙarya. Itama ganin ta kwana biyu ba ta zo ba ne ya sa ta tambaya. Tare da Gwaggo suka yi ta hira a ɗakin Mahaifin na shi suna cikin hiran ne Alhaji Sheriff ya kira shi a waya yana tambayan sa ko ya dawo? Sai ya ce ma ga shi a gida kawai sai ya ce su haɗu a gidan bayan an yi issha'i shima zai zo gidan.

Habib ya sha mamakin ganin har da Baba Usman ma ya zo, ya ɗauka ya zo duba ɗan'uwansa ne tunda yana zuwa amma sai ya ji yana tambayan shi ko sun yi waya da Alhaji Sheriff?
Sai ya ce masa sun yi ya ce zai zo bayan sallan isha'i. Jin da ya yi Baba Usman ya ce to bari su yi sallan su jira zuwan shi ya sa sha jinin jikin shi.

Tare da Baba Usman suka yi salla a masallacin kusa da gidan su suna idarwa suka dawo gidan sai suka iske Alhaji Sheriff ya iso da yake shi a anguwansu sukan riga nan anguwan yin sallan su, tun da Habib ya ga Gwaggo bayan sun gaisa da Alhaji Sheriff ta miƙe za ta fita ya ce ta dawo ta zauna maganar ta shafe ta daga nan ya san lamarin ya yi ƙamarin da ya wuce na shi lissafin.

Ƙansa na ƙasa ya ji Alhaji Sheriff na jero maganganu Gwaggo na salati ya kwashe yadda abin ya faro tun daga farko har zuwan Mahaifin Ummu Salma wajen shi da yadda suka tattauna.

"Habibu ba ka kyauta ba sam."

Gwaggo ta faɗa tana kallon shi cikin mamaki shi dai kansa na ƙasa amma ransa ya ɓaci.

"Ya ci amanar aure, abin na shi har ya kai ya fara yi ma iyalan na shi horan yunwa? Ga juna biyu in wani abu ya same ta iyayenta suka yi ƙaran shi a kotu ba? Yana da kalaman da zai iya kare kanshi da su ne?

Baba Usman ya faɗa yana kallon Habibu da ya ji duk ya muzanta. Ga shi a gaban mahaifin shi suna ta maimaita maganar, duk da ba ya magana amma yana jin duk abin da ke faruwa a ɗakin.

"To kun ji dai halin da ake ciki, tun da har na yi masa faɗa bai ji ba shi ya sa na ce mu taru anan ga mahaifin shi tare da ke mariƙiyarsa domin kun san halin da ake ciki. Mahaifinta ya ba ni saƙo na ba shi, ya ce in har ba ya son yar sa to ya dawo masa da ita shi bai gaji da ciyar da ita ba."

"Yana da gaskiya."

Gwaggo ta faɗa tana mai hararan Habib

"Habibu me ya same ka! Kai fa da kanka ka zo ka ce kana son yarinyar nan aka je aka nema maka auranta, auren ko shekara bai yi ba amma an fara samun matsala, kana ɗan musulmi bafillace ka ce sai an zubar da ciki? An ya kana so ka yi albarka kuwa ba ka san ya'ya rahama ba ne! Ka san wanda zai ji ƙan ka anan gaba ne?

Gwaggo ta faɗa tana kallon shi, ya ma kasa mgana jujjuya saƙon da aka ce mahaifin Ummu ya bar masa yake yi a cikin zuciyarsa. Lalle ko zai dawo masa da ƴarsa gida tunda  haka ya buƙata.

"Kuma yana da tabbacin in ya zubar da cikin ubangiji zai sake ba shi wani damar a gaba ne? Yana da ilimin shi amma Habibu na neman ya yi ma kansa sakarci."

Baba Usman ya faɗa yana zaune kusa da Alhaji Sheriff, amma har lokacin Habib bai tanka ba, ya sunkunyar da kansa kawai yana wani tunani. Ba zai ce komai da zai ɓata musu rai ba saboda nan gaba za su yi masa amfani.

"Ni dai na gama iya ƙoƙarina na zare hannuna akan duk abin da ya shafi Habibu tun da ba ya jin magana. Ya je ya yi duk abin da zai yi amma ya sani in har ya gaji da zama da yarinyar mutane ne gwara ya sake ta zai fi alheri akan ya zauna yana azabtar da ita"

Alhaji Sheriff ya faɗa yana nuna Habibu kafin ya cigaba da faɗin" Shi ya sa na tara ku gwara kun san abin da ke faruwa. Ke Aina'u ki yi masa mgana wataƙila ya saurare ki, ni dai na gama nawa"
Yana gama faɗin haka ya tashi zai fita Gwaggo da Baba Usman suna ta ba shi haƙuri.

"Ka yi hakuri Alhaji na ka ne fa ba yadda za ka yi. Don Allah ka dawo ka zauna zai ji maganar ka in sha Allahu."

Gwaggo ta faɗa cikin tausasawa Baba Usman na ta ya ta.

"Sai hakuri Alhaji, kai Habibu ka yi magana ka ba shi hakuri tunda ba ka da gaskiya."

Habib ya tura hulan kansa baya yana shafa gaban goshin shi yadda yake jin zuciyarsa a lokacin kamar ya buɗe idanuwana ya ga Ummu Salma ya fara ƙwallo da ita ko zai wuce takaicin shi.

"Ka yi haƙuri Abba ba zan ƙara ba."

Ya faɗa yana ƙasa-ƙasa da kansa kamar na gari.
Da ƙyar ya dawo ya zauna yana faɗin" Ni da na ce na cire hannuna ya je can ya yi duk abin da ya ga zai iya ai ya girma zai iya tafiyar da rayuwarsa yadda yake so."
"Ka yi hakuri Alhaji. Habibu duƙa ka ba ma baban ka hakuri."
Gwaggo ta faɗa tana kallon Habib, ko ba ta ce ba dole zai rankwafa ya ba shi haƙuri saboda kar nan gaba ya ce ba zai shige masa gaba wajen auren masoyiyarsa ba.

"Ka yi hakuri Abba kuskure ne hakan ba zai sake faruwa ba"

Habib ya faɗa yana sauke kansa ƙasa sai da ya yi ta ban haƙuri sannan Alhaji Sheriff  ya sassauto yana faɗin" Duk fa wannan  faɗan da ka ga muna yi maka Habibu don muna son ka ne, muna son rayuwarka ta zama abin sha'awa da ƙwatan ce"

"Sosai. Kuma wanda ba shi da na gaba ai shi ke da kaico."

Baba Usman ya faɗa shima. Shi dai Habib yana ta basu haƙuri kansa a ƙasa.

"Ya rage na ka Habibu. Sai ka shirya ko gobe ne ka je gidan surukan naka ka ba su hakuri sannan kar mu sake jin wata magana ta sake tasowa. In hakan ya faru Habibu zan cire hannuna akan ka wannan karon."

Alhaji Sheriff ya jaddada  masa, ya kuma amsa masa da cewa zai yi abin da ya ce sun daɗe suna yi masa faɗa da nasihu, ya yi kamar yana ji nan ko a kasan zuciyarsa shi kaɗai ya san abin da yake saƙawa an kawo gabar da ba zai iya kauda kai ba tunda ya ce in gaji da ƴarsa to ya dawo masa da ita, ai ko zai dawo masa da ita, da man duk ya nuna alamun haka sune ba su gane ba. Sai goma saura ya bar gidan duk da tun yana can ake ta kiran wayarsa da turo saƙo bai duba ba sai da ya fito daga gidan ya ɗau hanya sannan ne ne ya duba wayarsa.

Da man ya san ita ce saboda sun yi da ita yau zai je wajenta amma bai samu zuwa ba, Ummu Salma ta ɓata masa kyakyawan daran sa, amma hakan ma ya yi yau zai yada ƙwallon mangwaro ya huta da ƙuda.

"Habib wani abu ya faru ne?

Saƙon da ya buɗe kenan bayan tarin kiran da ta yi masa bai amsa ba yana gaban su Abba.

"Za ki iya aurena nan da wata biyar ?

Haka ya rubuta ya tura, ba daɗewa ko sai ga shi an turo masa da amsa.

"Me zai hana? Ni da man kai nake jira ni nawa matsalan mai sauki ne Habib."

Mirmishi ya yi shi kaɗai kafin ya sake yin rubutu ya tura.
Saboda haka har gefen titi ya gangara ya yi parking ɗin motar shi.

"To ki shirya kin kusa zamo wa Amaryan Habib in sha Allahu."

Yana gama turawa sai ya saka wayarsa a Aeroplane mode saboda ba ya so ta dame shi da tambayoyi abin da ya sani ɗaya ne a wannan daran zai yakice Ummu Salma daga rayuwarsa da ita da cikin jikinta har gaban abada ba ya fatan a sake danganta shi da su, zai fara sabuwar rayuwar da ya tsara ma kansa nan da wattani biyar.

Tabbas kaddara ta riga fata. Da man zanen kaddaran su in ya fara tare to Ubangiji bai yi hukuncin labarin na su zai kamallah a tare da juna ba.
Ummu Salma da Habib za su rabu a wannan  duniya amma kuma za su sake haɗewa a wata sabuwar duniyar.


*littafin Fargar Jaji na kuɗi ne a manhajar Telegram akan #1k. Tura Kuɗin karatun ku ta wannan acct ɗin 9069067488 JAMILA UMAR OPAY sannan sai ku tura shaidar biya ta waɗannan lambobin kamar haka.*

09069067488.
08032773332.

*Yan kasuwa masu buƙatar a tallata muku hajojinku a cikin wannan kayattacen labarin za ku iya tuntuɓata kai tsaye ta wannan lambar 09069067488 Na gode.*




*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t

*10*

*10:12pm*

Ƙarfe goma da mintina sha biyu Habib ya shiga falon gidan shi, da ƙishin ruwa ya dawo shi ya sa yana shigowa falon bayan ya kunna hasken wuta.

Da yake Ummu ta kashe komai kafin ta kwanta Kitchen ya zarce yana neman ruwa a firiza amma babu ruwa sai wani guda ɗaya pure water da ya gani a saman kantan kitchen ya ɗauka sha, ya manta bai bar komai a gidan ba, ruwan bai ishe shi ba amma haka nan ya haƙura har zai fita sai ya leƙa store bai yi mamakin ganin kayan abinci ba, daman dalilin da ya sa ta nace ta ƙi tafiya saboda iyayenta sun kawo mata kayan abinci ne tunda daman ta ji daɗin kai shi ƙara wajen iyayenta.

Da gangan ya kwashe kayan abincin shi ya kai gidan su, a tunanin shi ai ba za ta zauna ta mutu da yunwa ba, in ta ga babu komai za ta koma gida ta sanar ma da iyayenta halin da ta ke ciki, su kuma kafin ma su kira shi zai aika mata da takardan sakinta, amma saboda maita da rashin zuciya ba ta tafi ba sai ma aka kawo mata kayan abincin saboda dole ne sai ta zauna a gidan shi, to ya gaji shima zai sauwaƙe ma kan shi ne, gida da man na haya ne kuma shekara ɗaya ne kuɗin hayar kuma na shekaran ya kama gidan saboda biyan buƙatan shi ya kuma samu biyan buƙatan shi to ba zai damu domin ya bar musu ragowan kuɗin hayar ba. A gidan kansa  zai gina wata sabuwar rayuwar da ya tanada shi da abar ƙaunarsa.

A fusace ya fito daga kitchen ɗin ya shiga ɗakin da ya ke kwana ya nemo takarda da biro, yana fitowa ƙofar ɗakin da Ummu ke ciki ya shiga bugawa cikin sauri sannan da ƙarfi kamar zai ɓalla ƙofar sannan lokaci ɗaya yana kiran sunan ta.

"Ummu Salma."

"Ke Ummu Salma."

Ya ke faɗa da muryansa a sama lokaci ɗaya yana cigaba da buga ƙofar da karfi.

Kamar a mafarki ta ji bugun ƙofar domin har ta fara barci kanta ke ciwo saboda kukan da ta sha, sai ta sha pracetamol tana idar da sallar isha'i ta kwanta cikin ikon Allah barci ya kwashe ta da man wani lokacin tana samun yin barci a farkon dare amma in ta farka ne yake da matukar wahala ta samu nasaran komawa, wata rana ta tashi ta yi salla wata rana kuma ta yi karatun Qur'ani wata rana kuma ta yi kuka. Yau ma da wuri ta samu barcin amma bugun ƙofar da Habib yake yi ya katse mata barcin nata kuma a daidai lokacin daman mafarkin Habib ɗin take yi wai ya kira ta yana yi mata mgana ita kuma ta ɗuka har ƙasa tana bashi haƙuri har ya tashi zai tafi ta riƙo kafarsa amma ya juya ya ture ta a cikinta ta faɗi, sai ga jini na bin ƙafarta shi ya sa bugun ƙofar da mafarkin da ta yi suka samar mata da tashi a firgice tare da fargaba mai tsanani.

"Ba za ki buɗe ba! Ke Ummu Salma."

Ta ji muryan Habib yana magana, ta sake figicewa cikin gigita ta sauko daga kan gadon da take kwance, ta ma manta da hulan kanta da ya saɓule bayan ta kwanta sai da ta nufi ƙofar sannan ta shafa kanta ta ji ba ɗankwali ga shi kan ya yi datti goron kitso har ya ɓace saboda daɗewa, saboda ba ta kitso take yi ba.

"Wai ba za ki buɗe ba? Na san fa kina jina."

Habib ya sake faɗa kuma yana cigaba da buga ƙofar, yadda jikinta ke rawa haka zuciyarta ke rawa domin ba ta san da abin da Habib ya zo a daran nan ba amma dai tafi tunanin abin da ke kawo shi wajenta ya zo nema jikinta, in shi ne kuma ya zo ga shi nan har sai ya gaji.
Saboda saurin ta buɗe kofar har tana neman faɗuwa rigar jikinta ce ta harɗeta ta kusa kaiwa ƙasa sai da ta riƙe gefen wardrope ɗin dake ɗakin. Hannnunta na rawa ta murza key ɗin dake jikin ƙofar ta buɗe ɗakin, Habib ya tsaya yana kallon ta cikin bacin rai.

"Ni za ki mayar ɗan iska kina ji ina kiran ki kina yi mini shuru?

Kanta na ƙasa ta ce" Ka yi haƙuri ban ji ba ne"
Ta ɗauka abin da ya saba kawo shi yau ma shi ya kawo shi ya sa tana gama bashi haƙuri ta juya za ta koma ciki.

"Ki same ni a falo."

Ta ji ya faɗa ta juya cikin mamaki shi kuma tuni ya bar wajen, zuciyar ta amsa na rashin sanin dalilin kiran Habib amma ba ta yi ƙasa a gwiwa ba ta bi bayan shi zuwa falon, jikinta ya yi wani irin sanyi ne lokacin da ta ga Habib zaune kan kujera mai zaman mutum biyu ya harɗe kafafunsa kamar wani basarake ga littafi da takarda a hannun shi har da biron rubutu.

Kasa ƙarisowa ta yi ta tsaya cak daga nesa tana kallon shi cikin bugawar zuciya, me Habib zai yi da takarda da biro? Allah ya sa ba abin da zuciyarta ke saƙa mata ba ne, in ko haka ne da ta ce ita yau Ummu Salma ta shiga uku ta lalace rayuwarta ta faɗa cikin mawuyacin garari, gararin da har abada ba za ta iya fita daga cikin sa ba.

"Malama ki ƙariso kin tsaya mini a saman kaina "

Salau-salau haka ta ƙarisa gaban shi, ta zauna a kasan cafet tana mai ƙura ma kwalliyan cafet ɗin idanuwanta, amma hankalinta ba ya wajen in da zai lura ma kafafunta da hannayenta ma rawa suke yi tsabar firgici.

"Kin gama na ki aikin saura nawa aikin kuma Ummu Salma."

Sai ta ɗago tana kallon shi amma ba ta yi magana ba.

"Kin je kin haɗa ni da iyayena, kin yi ƙoƙarin ɓata mini gobe na sai dai burin ki bai cika ba."

Ya sake fada yana mai kallon ta fuskar nan ba fara'a kamar bai taɓa dariya ba.

"Me kuma na yi?

Ummu ta faɗa muryanta na karyewa kamar ta fashe da kuka.

"Ni kike tambaya abin da kika yi! Kin manta kin sake kai ƙarana wajen iyayen ki? Ke a tunanin ki za su iya sauya komai ne?

Ta ma kasa mgana bakinta na rawa, shi ya sa kawai ta yi shuru amma har hawaye sun kece mata maganarsa ya ba ta tabbacin Baffa ya ji labarin halin da take ciki, magana ta kai kunnen iyayen Habib.

"Ummu Salma ba ke kaɗai ne ba ki da tunani ba har da iyayenki ma."

Da sauri ta ɗago ta kalle shi cikin mamakin kalaman shi, iyayenta ne marasa tunani?  Yau ita Habib ke faɗa ma iyayenta ne ba su da tunani?

"E haka na ce ba su da tunani, in har suna da tunani ai ya ci ace zuwa yanzu sun fahimci bana ra'ayin ki, na nuna bana son ki a aikace duk domin su fahimta su sauƙaƙa mini aiki amma sun kasa fahimta ban sani ba ko a wajen su ne kika gado wannan kidahumancin na ki ba"

Habib ya gama faɗa har yana nuna kanta cikin izgili.

Ummu Salma ta yi ma Habib ƙuru da ido ta kasa mgana, domin sai ta ji kamar an zare mata duka lakkan jikinta.
Yau iyayenta ne kidahumai a bakin Habib? Iyayenta fa? In ita ya zageta ta shanye, to ai bai kama ta ya taɓo bangaren iyayenta ba, domin ya san duk ɗa na gari ba zai zura ido ana cikin zarafin iyayenshi kuma ya yi shuru ba.

"Na gaji da ke, na gaji da auren ki wallahi, ke kika fara cutar da iyayen ki tun da kika ɓoye musu gaskiyan manufata akan ki, su kuma rashin tunanin su da lissafin su yasa suke tunanin ina son ki, sannan iyayena suna da ikon sarrafa rayuwata ne? Ina, rayuwata ce ni ke da ikon zaɓa ma kaina yau n da gobe na ba wani ba, ba kuma wanda ya isa ya saka ni na zauna da abin da bana so, a farko ni ne na yi ra'ayin zama dake saboda ina son cimma burina, yanzu kuma na gama amfana dake, na cimma burina akan ki me kuma ya yi saura a tsakanina da ke?

Ya faɗa yana zare mata ido.
Ummu na hawaye har da majina, ta ce" Iyayena ba su yi maka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login