Follow us on social media
Showing 12001 words to 15000 words out of 147042 words
Chapter 5 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
ne, saboda lambar ba suna, kuma ni na san sai dare ko asuba yake kiran Amma, in da na san shi ne ai ba zan ɗauka ba, ni da lokacin da maganar aurena da Habib ya taso ya kira Amma a waya yana faɗa wai ya za su biye mini na ƙi karatu na ce aure zan yi ina yarinya da ni ban san komai ba? Da shi da Hamma Kabiru da yake shima irin halin su ɗaya ya zo yana ma Baffa kumfar bakin cewa na yi ƙankanta da aure."
Baɗɗo ta kalli Ummu ganin har ta fara hawaye.
"Ni yaushe na ce aure na ke so? Ni dai ba na ce ba ne a ƙyale ni bana son cigaba da karatu abin da na san kawai na ce kenan."
Sai kawai Ummu ta fashe kuka Baɗɗo da ya ke ta san hali sai ta dafa kafaɗanta tana faɗin" To ke ma ban da abin ki duk wanda ya ji ba ki son karatu ai zai fassara ki da cewa aure kike so ne SisNa"
Kafaɗan Baɗɗo ta kai ma duka ita kuma sai ta goje tana dariya .
"In kowa bai fahimci halin da na ke ciki ai ke na san za ki fahimce ni. Karatu na daga cikin abin da ke wahalar da ni, tun da ya ke ba ni wahala na yi kuma iya yina na riƙa ganewa na kasa ba gwara na hakura ba, domin ina tsoron na shiga jami'a domin faranta ma su Hamma Kabiru rai kafin na yi nisa a kore ni."
Baɗɗo ta kwashe da dariya Ummi na ta ya ta da guntun hawayenta.
"Hamma Saddam ya ce sai ya ga wanda zai aure ni ina low class ban ji turanci mai zurfi, sai ko ga shi ya sha mamaki. Ya ga Noori na, wanda kyau dai na fuska da zati bai isa ya nuna masa ba."
"Bai isa ba."
Baɗɗo ta faɗa tana dariya.
"Bestie ta ce tana roƙon Allah ya ba ta miji kamar Habib. Ya so ta kamar yadda yake sona."
"Amin."
Baɗɗo ta amsa kafin ta ce" Ai Habib miji goma ne, kin gama dacewa SisNa muma Allah ya sa mu da ce irin na ki."
"In sha Allahu za ku samu fiye da wanda ya fi Habib ma."
"Allah ya sa hakan."
Baɗɗo ta sake amsa mata, sannan suka cigaba da hiran su, ana haka sai ga Shamsiya ta kira wayar Ummu sai ta saka ta speaker suna fara mgana Baɗɗo ta kira sunanta.
"Bestien SisNa."
Tana jin haka ta san Baɗɗo ce domin haka take kiran ta, ita kuma sai ta ce mata Sisna Bestie na.
"Wayau kika yi mini Sisna bestie na? Kika taho duba Bestie ba tare da ni ba?
Shamsiya ta faɗa daga cikin wayar, Baɗɗo ta ce mata itama fa ta kwana biyu ban leƙo ta ba sai yau fa kin san saboda makaranta mun kusa fara jarabawa.
Shamsiya ta ce suma sun kusa farawa shi ya sa amfani da wayar ma sai a hankali.
Shamsiya irin yaran nan ne masu ƙoƙari da nacin karatu, kaf gidansu yan boko ne sai kin gama jami'a ko kin kusa gamawa kike da damar fidda mijin aure, ko ba ka son karatu su a gidan su wajibi ne sun ɗauki boko kamar wani zunubi ne in ba ka yi ba. Ita kanta Shamsiyar ɗaliba ce a jami'ar Modibbo Adama University Yola a garin girai can ta ke zama a hostel sai sun samu hutu take zuwa ganin gida.
Sun daɗe suna waya suna ta hira, har sai da dawowar Habib ya katse su. Baɗɗo sai da ta kauda idanuwanta, saboda rumgumar da ta gudana tsakanin Habib da Ummu in da a ce ana sabo da tuni ta saba da ganin haka tun bayan auran Ummun da Habib.
"Baɗɗon mu."
Habib ya faɗa yana yi mata murmishi bayan sun gama oyoyon shi da Ummu.
"Noorin mu."
Dariya ya yi, domin Habib akwai harka ko yau kuka taɓa haɗuwa da shi sai ka ji kamar ka yi shekara da sanin shi, yana da magana da harka sosai.
"Na sa ka ki jirana ko?
Bari na yi wanka mu ci abinci sai mu je mu kai Baɗɗon mu gida ko Baby?
Ummu ta gyaɗa masa kanta lokaci ɗaya tana mai saukar da kanta a saman kafaɗan sa.
A falo suka bar Baɗɗo suka shiga ciki mintina talatin sai ga su sun fito Habib ya yi wanka ya sanya kaya zuwa jallabiya baƙa a dinning suka zauna Ummu ta yi serving ɗin su jalop rice mai salat, sai zoɓo sauran na jiya ne da ta saka a frizer suna ci jefi-jefi suna hira, hiran kuma tsakanin Habib da Baɗɗo ne yawanci kuma akan karatun ta ne.
Sai can ne Ummu ta kan sako musu baki ko kuma in ya juya ya sako ta a ciki.
Sai wajen tara na dare Habib da Ummu suka tafi kai Baɗɗo gida, da suka isa ƙofar gidan Habib ya ce su shiga ciki su gaisa da Ummu ikki, Ummu ta ce aa suna shiga za ta yi musu faɗa ne.
"Mu shiga Baby, ba fa Ammah ba ce."
Ya faɗa yana dariya Ummu ta girgiza kai kafin ta ce" Ba ka san su ba ne, daga ita har Amma halin su ɗaya."
Ya dage sai da suka shiga cikin gida, matan baban su Baɗɗo Biyu Ummin ikki ce uwargida sai Anty Saratu, suna tsakar gida ne suna hira lokacin da suka shigo Baɗɗo da Ummu Habib kuma ya tsaya a sauro kafin su yi masa iso.
"Ke yanzu Ummu kin kyauta ma kan ki kenan?
Da tsohon daren nan?
Ummin ikki ta fara faɗan ta, itama kamar Amma ne ba su gani su ƙyale.
"Ummi Baɗɗo ce ta yi dare Habib ya ce ta jira mu kawo ta gida."
"Habib ya ce ko ku kuka ce?
Umma ikki ta faɗa tana hararan su, Baɗdo ta kwaso rantsuwa tana faɗin" Wallahi Ummi shi ya ce na jira shi."
Wata uwar harara ta maka musu, atare Ummu da Baɗɗo suka saka dariya suna kumshe bakin su.
"Ja'iran yara kawai, to ina shi Habibun? Waje ku ka baro shi?
Jin haka yasa Ummu ta miƙe tana faɗin" Bari na ce ya shigo."
Ummin Ikki ta yi ƙaramin tsaki kafin ta ce" Ba ni hijabi na"
Hijabin Baɗɗo ta ɗauko mata a cikin ɗaki ta saka ita kuma Anty Saratu da man ta shiga ciki tun bayan da suka gaisa da Ummu da farko.
Habib har ƙasa ya duka ya gaishe da Ummin ikki kamar yadda ya saba ta amsa mishi cikin sakewa, ba su daɗe ba suka yi musu Baɗɗo ta raka su har bakin gida nan suka ci karo da Baban su Baɗɗo ya dawo shima faɗan ya fara yi da ya gan su.
"Kai Habibu ba za ka daina biye ma shirmanmun yaran nan kuna yawan dare ba ko?
Ya faɗa ba wasa a muryan shi Habib a ka bari da kare su Ummu.
"To ku yi sauri ku isa gida garin da kamar hadari. Allah ya yi muku albarka."
Suka amsa da Amin ya shiga gida, su kuma suka shige motar Habib ta kamfanin Toyata, Baɗɗo na ɗaga musu hannu har suka ɓace daga layin.
*****
Ammah da tawagarta ranar litini da safe jirginsu ya ɗaga zuwa katsina. Ummu ma ba ta san tafiyarsu ba sai da ta ga Hamma Sadam na posting ɗin hotunan shi a status a cikin jirgi a first class, shi ne ta tambaye shi ya ce tun safe suna Daura.
"Eyye Baffa ne ya biya muku kuɗin jirgin?
"Wani Baffa, ai wani kaya sai amale Hamma Lamiɗo ne, na ke faɗa miki a rukunin masu kuɗi muka je katsina. A VIP muka kame, muna sauka kuma ga motocin masarauta da dogarai da yan sanda suna jiran saukan mu, suka kwashe mu da jerin convoy motoci hadaɗɗu, sai ga mu dai a cikin Masarautan Daura."
Duk Hamma Saddam ne ya zayyano mata wannan labarin, da man shi nan ya fi ƙwarewa.
"Ba shakka. To ina su Ammah yanzu?
"Suna can cikin gida ni ina bangaren Hamma Lamiɗo ne nan ake sauke ni, Ummu kin ga masarautar Daura? Kin ga shashen Hamma Lamiɗo? Na rantse da girman Allah ban taɓa ganin tsaruwa da kyau na masarauta kamar yadda na ga tsaruwa irin ta masarautar Daura ba"
"Uhm. Na gani."
Ta tura masa ganin yana neman ya manta itama fa ta je ta ga komai ba sai ya sake zayyana mata ba.
"Yanzu muna tare da Saleem ne ƙanin Hamma Lamiɗo, anjuma za mu je gaida Mai mairtaba Sarki"
Ba ta tambaye shi ba amma sai zuba mata labarai yake yi, gajiya ta yi ta katse shi da cewa." kai ma har can Abuja za ka je?
Ya dawo mata da amsa da cewa sosai ma a gobe za su tafi tare da tawagar matayen Sarki amarya da tawaganta suna can tun shekaranjiya.
"Allah ya ba da sa'a."
Ta rubuta mai daga nan ta kashe data, amma bayan awa ɗaya da ta sake kunnawa sai da ta ga saƙon sa
"Kin san Mai martaba Sarki na da wani ƙaton gida a garin Abuja acan za mu sauka. Har sai an gama shagulgula sai ranar ɗaurin daure da safe za mu koma Daura."
Emojin mirmishi kawai Ummu ta tura masa, ita fa shi yasa ba ta yi mamaki da ta ga Hamma Saddam ya je Jamia yana karantar aikin jarida daman ya fi dacewa da shi, shi fa duk in da ya je sai kowa ya sani posting ne kan posting har da karin bayanai, ranar ya saka status sun fi goma na ƙarshe shi ne wanda ya ɗauka tare da Mai martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Nasiru Muhammad Daura a cikin fadar shi yana zaune kan ƙaraga idanuwansa ne kawai ake iya gani saboda yana cikin naɗi. Caption ɗin da ya saka ne ya sa Ummu kwashewa da dariya.
"Allah ya ja zamanin ka ubanmu uban ƙasa, Allah ya ƙara maka lafiya Mai mairtaba Sarkin Daura."
Hamma Saddam na da abin ban mamaki, sawa yake yi har bargar dawakai da ya shiga sai da ya yi hoto ya saka, Ummu ta tabbatar da ba za ta yi missing komai na shagalin bikin nan ba, tun da dai Hamma Saddam ya na can ai kamar suna can ne suma.
Sai ranar Jumma'a Habib ya sauke ta gida da safe kafin ya tafi wajen aiki, duk da Ammah ba ta nan amma Baffa na gida bai je ko'ina ba tare suka yi ta hira sai da ya fita zuwa sallar jumma'a, yana fita ba daɗewa matar Hamma Abdurrahaman ta zo ita da yara, Adda Ummu Sulain tare suka yini a gidan har dare, Ummu ta yi ma Baffa tuwo miyar yauƙi, da man da Amma ba ta nan daga gidajen su Hamma Abdullahi ake kawo masa abinci sai misalin tara na dare Habib ya zo ya ɗauki Ummu suka koma gida bayan ta yi guzirin tuwo saboda ɗumamen safe.
Lalle ko an sha shagali a garin Abuja, ashe su Ammah duk uwar Amarya ta yi musu anko da man shi ya sa take ta tambayan mutanen da za su zo daga bangaren Ammah. An yi mothers Day su Amma an sha kamfala da mayafi ita da Ummin ikki, Hamma Saddam ya ɗora su a status a ƙasa ya saka
"Hamma Lamiɗo mai uwaye biyu."
Hoton ya yi kyau, sai da Ummi ta ɗauka itama ta yi status, da wanda aka yi ma Ammah ita kaɗai ta yi shar da ita, ita da ta tashi saka hoton sai ta yi zolaya.
"Amman Baffa"
Ta saka emojin love da rawa.
Baffa kuma ya gani dariya kawai ya yi bai yi mgana ba.
Da man Hamman Saddam ya faɗa ma Ummu Amma na ta masa faɗan wai ya yi ya tura ma tsohon ta hotunan ta. Ummu ta yi dariya sosai rayuwar auran Ammah da Baffa rayuwa ce abar burgewa da tsari, ita tana da zafi shi kuma Baffa mai sanyi ne da haƙuri shi ya sa aka zauna lafiya.
An yi Dinner na gani na faɗa abu ne masu mulki da sarauta, matan sarakuna sun zo ma uwar Amarya biki, a matsayinta na uwargidan Mai mairtaba Sarkin Daura Gimbiya Shahida, itama ɗiya take ga tsohon wazirin na garin Daura. Sai ga su Ammah a tawagan uwar Amarya suna jera kafaɗa da matan gwamnoni da sarakuna da matan ƴ'an majilisu har da matar mataimakin shugaban ƙasa, ga matar Gwamnan Jihar Katsina sannan ga bangaren uwar ango itama da na ta tawagan, matan ministoci da masu faɗa aji a fadar gwammatin tarayya.
Ammah sun yi hotuna da uwar Amarya sannan ta yi da Amaryan da ango sai kuma wanda ta yi ita da matar Hamma Lamiɗo Dr. Balkisu Usman Bayero"
Su Hamma Saddam an saje cikin ƴaƴan sarakuna da ƴaƴan ministoci shima cikin ɗanyar gezner irin ta masu bikin, sai da Ummu ta yi da gaske ta iya ma gane shi, lalle su Hamma Saddam an samu duniya.
Matar Hamma Lamiɗo Ummu ta shagala da kallo, matar nan akwai gayu, yar gayu ce ta bugawa a jarida ga kyau ga ilimi ga gayu, ƴa'ƴan su Biyu mai sunan Maimartaba Nasiru(Sultan) sai mai sunan Amma, Jamila(Beena) wani arnen leshi ne a jikinta da ga gan shi ka ga kuɗi, ankon Dinner ɗin ne amma na ta kalan peach ne na su Amma kuma maroon ne kalan ya yi kyau sannan da mayafin su kalan head ɗin su, Amma da Ummin ikki fa har da makeup aka sha irin light ɗin nan sun fa ba za kafacity.
Baɗɗo ta saka su a status ta rubuta.
"Capacity iya capacity Amma da Ummin ikki."
Babu wanda bai saka su a status ba, har Hamma Jibo, Hamma Kabiru ne ya saka hoton Amma ita kaɗai ya yi caption da cewa.
"Ammah uwar Amini Lamiɗo"
Ummu na gani sai da ta taɓe baki, duk wannan bidirin da ake yi shi gogan bai san ma ana yi ba.
Ba ta da lambarsa , yadda bai taɓa nuna damuwarsa akan rayuwarta ba, itama ba ta damu dashi ba duk da ko uwa ɗaya ce ta yi musu tarbiya.
Har Adda Nauwara matar Hamma Jibo ta je Dinner ɗin ita da su Saudat, tun da suna garin suma sun yi kyau da ya ke Hamma Jibo shima ba daga nan ba ɗan gayu ne sosai, matarsa ma yar gayu ce haka ma ƴaƴan su. In suka zo hutu Jimeta ba sa yin hausa wa junan su yaran su yi ta turanci wata rana da Saudat ta yi ma Ammah mgana da turanci yini ta yi faɗa tana cewa ita za a nuna ma iskanci to ko uban ta nan ya girma ita da Baffa hausa da fillanci suka koya masa ba ta son tsirfa da iyayi, kar a sake yi mata turanci a gida gargaɗi aka yi ma Hamma Jibo da Adda Nauwara, da cewa ba su ko ya ma yara fillanci ba sai wani turanci yaren da ba na su ba. Ammah fa Ƴa'ƴan Hamma Lamiɗo ba su jin hausa daga uwar har uban da turanci suke yi musu mgana gwara ma Hamma Lamiɗo shi yana yi musu hausa da fillanci wani lokacin amma uwar sai turanci amma har yau ba a ji Amma ta yi faɗa akan haka ba tun da Hamma Lamiɗo ne, shi kuma Hamma Lamiɗo shalele ne a wajen Ammaj ba ya laifi.
Ranar da aka yi Dinner sai wajen ɗaya na dare Ummu ta kwanta Habib ya gaji da jiranta ya kwanta ta kafa ta tsare tana kallon abin da ke kwana a garin Abuja a wani ƙayattacen hall, an sha Dinner sai wanda ya je ya gani su ɗin ma dake gida sun gamsu da Dinner ɗin ta masu mulki da sarauta ne. Maƙawan arewa sun hallarta kowanne mawaƙi ya baje na shi kolin, irin su Ali jita, Naziru sarkin waƙa, Nazifi Asnanic, Auta MgBoy, Auta waziri, Salim smart, Ɗan musa da sauran su ko wanne da irin karin waƙar shi ga amarya da ango sun kuma sha kuɗi, domin miliyoyi ne ke tashi da dollars, wannan daren dai Dinner ɗin ce ta dinga trending a kafafen sada zumunta ita dai ko alama bata nuna ma tana da alaqa da masu bikin ba.
Sai washegarin ranar asabar aka ɗaura aure a masarautar Daura, Hamma Kabiru ya saka hoton Hamma Lamiɗo.
Sai da Ummu ta kau da wayar daga fuskarta saboda tsoratar da ta yi, sanye yake da uniform ɗin su na matuƙan jirgin ruwa
Farar riga da baƙin wando fuskar shi ce ta ba ta tsoro, ta yi gargasa gemunsa ya yi kamu uku, kansa gashi ya cika ya yi yawa babu kyan gani.
"Amini a bakin aiki."
Haka Hamma Kabiru ya saka, sai da ta je hoton gaba sai ta ga ya saka wanda ya yi gyaran fuska ya rage gashin fuskar da na sumar kan amma ba sosai ba.
"Amini ya yi gyaran fuska."
Wataƙila Hamma Kabiru ne ke wahalar posting ɗin Hamma lamiɗo, shi ko ba ta da tabbacin yana saka shi, duk dai kowa ya shaida akwai aminci a tsakaninsu fiye da kowa ma, Hamma Lamiɗo mutum ne da bai cika bayyana ƙarfin alaqar sa da ko ma waye a zahiri ba, fuskar shi ba ta fallasa sirrin zuciyarsa.
Kullum a ginshiƙe za ka gan shi, fuskar nan kamar yana cikin wani damuwa a kame in ma ka samu ganin shi kenan, mutumin da a shekara bai wuce sau ɗaya
yake zuwa ganin gida ba. Duk da yana da tamƙamemen gida anan garin Jimeta, sai ya yi rabin shekara a rufe wani lokacin a shekara sau ɗaya yake zuwa in an yi wani abu ne sau biyu sai dai yana yin sama da wata a Jimeta in ya samu hutun karshen shekara wani lokacin shi kaɗai ya ke tahowa matar tashi sai aiki ya yi mata sauƙi sai ta biyo shi ita da yara, daga nan ne suka wucewa Daura can ma wani alkarya guda ne da sunan bangaren Hamma Lamiɗo.
Aikin su na yana da tsauri, Captain ne shi ma'ana matuƙin jirgin ruwa ne. CAPTAIN M.N. MUHAMMAD.
Yana aiki da kamfanin Nigerian port Authority jiragen dake jigilan mutane da kayan masarufi shi ya sa suke daɗewa a saman ruwa
Babu ƙasar da ba sa zuwa ta kogi sai su yi wattani sama da shidda a saman ruwa ba su shigo gari ba, sun fi ma saurin dawowa gida in sun ɗauko kayan masarufi.
Shi ya sa suma kan cika fuskar shi wani lokacin sai sun zo bakin gabar wani garin ne suke samun damar yin wani abu, hutu ko bai wuce na awanni