Follow us on social media
Showing 132001 words to 135000 words out of 147042 words
Chapter 45 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar
yar shaƙuwa.
"Daman ba Hamma Kabiru ba ne ya ba ni jininsa ba?
"A daran ta ina Hamma Kabiru zai taho? Yau ne ma ya samu zuwa ba daɗewa. Hamma Lamiɗo ne ya ba ki jininsa Sisna, ni kaina lamarin ya ba ni mamaki ban taba tunanin yana da tausayi haka ba"
Ummu Salma ta haɗiye wani miyau a maƙwagaronta.
Jikinta take kallo tana jinjina kai wai akwai jinin Hamma Lamiɗo a jikinta yanzu haka.
"Kin ga farar shaddar jikinsa duk ta ɓaci da jinin ki, Baffa ya yi ta cewa ya je gida ya sauya bai tafi ba saboda faɗuwar da Ammah ta yi shi ya zauna da ita har asuba aka sallameta sai ya ɗauketa zuwa gida ni da Baffa kuma muka kwana dake sai da safe ne Ummi ta zo sannan ya koma gida."
Ummu ta share hawayenta da gefen hannunta na hagu, hannunta na dama take kallo dake dauke da bandage ya kumbura
"Ɗinki aka yi miki. Likitan ya ce Allah yasa yankar bai yi zurfi ba."
Ummu dai sai sharan kwalla ba magana.
"Kin faɗa musu abin da ya faru ne?
Ta tambaya tana kallon Baɗɗo
"Na faɗa musu, kawarki Shamsiya ce ta za ta auri Habib shi ne kika yi yinkurin kashe kanki."
Ummu ta runtse idanuwanta tana jin kalmar kashe kanta ita ta aikata amma nadamar take yi, tsanar kalmar take yi.
"Hamma Abdullahi da Hamma Abdulrahaman sun yi ta faɗa, Baffa na fama da kansa bai ma yi musu magana ba zuwan Mami ne ma da ta yi musu mgana suka ɗan yi sauki da faɗan na su, amma kaf din su sun shiga damuwa ana kiransu a safiyar jiya suka cika asibitin nan tare da matan su, Mami ma ajiyan ta iso da rana. Hamma Jibo ne kaɗai bai zo ba saboda aiki Hamma Sadam na makaranta bana ma tunanin ya san abin da ya faru."
Ummu ta yi shuru kafin ta ce" Baɗdo na yi nadamar sanin Habib na yi nadamar sanin Shamsiya a rayuwata."
"Ki bar su da Allah, yau ne daurin auran an ma ɗaura tun dazu ta je ga ta ga Habib ɗin shima ga shi ga Shamsiyan in dai don sun tozarta ki ne suka samu damar auran juna. To da ikon Allah suma sai Allah ya tozarta su."
"Allah ya isa, ba zan taɓa yafe musu ba, sun lalata mini rayuwata. Me na yi musu?
Ummu ta sake fada tana kuka.
"Ba ki yi musu komai ba, ki dauka a haka a matsayin kaddaran ki. Ki bar masa faɗan shi zai saka miki "
Ummu ta cije lebenta na kasa tana jin wani irin turiri a zuciyanta. Ta tsani Habib ta tsani maza ma gabaɗaya dalilin shi yau take kwance akan gadon asibiti ta gode ma Allah da ya sake ba ta wata damar da yanzu ta mutu shikenan ta mutu a kafira ta yi asaran rayuwanta saboda Habib da Shamsiya da man burinsu kenan. In dai haka ne ba za ta sake ba su wannan damar ba, za ta cire su daga duniyarta har abada amma ba lalle ne abin da suka yi mata ya bace daga zuciyarta ba, har abada sun riga sun dasa masa ciwo mai wuyar warkewa a zuciyanta.
"Ki yi hakuri, ki yi hakuri amma don Allsh kar ki sake tunanin kashe kanki Ummu Salma."
Baɗdo ta faɗa cikin karaya.
"Ba zan kara ba, in sha Allahu ba zan kara ba."
Ta faɗa cikin kuka da hawaye shaɓe-shaɓe.
Suka rumgume juna Ummu na kuka da shessheƙa Baɗɗo na hawayen tausayin Ummu.
A haka Mami ta dawo ta same su, sai ta fara faɗan ya haka kuma? Ita Baɗɗo da za ta yi lallashi sai ta bige da kuka nan take tace su bari ba ta so.
Dole suka share hawayen su, sai dai ajiyar zuciya.
Sai mangariba likita ya dawo suka sake ɗaura ma Ummu karin ruwa sannan suka yi mata allura.
Mami ta koma gida da Hamma Abdullahi ya kawo Baffa ya duba Ummu ya sameta idanuwanta biyu tana kuka ta rirriƙe hannayen Baffa tana cewa ya yi hakuri.
"Bakomai Auta, na yi ma Allah godiya da kika kuɓuta ina sake masa godiya."
Da yakee an yi mata allura ashe akwai na barci ba daɗewa sai barci ya kwashe ta.
Baɗɗo ne da Mami suka kwana da ita, can dare Mami ta dawo da abinci da kayan da aka samu aka sauyawa Ummu.
Sai a daran Ummu Salma ta sha tea cikin ta ya warware sannan ta ɗan ci abincin kaɗan.
Washegari ma yan'uwa suna ta zuwa duba ta, don ma nurses ɗin suna hanawa, sai a ranar aka ɗan rike Ummu zuwa tiolet ɗin Mami ta ɗan yi mata wanka amma ba a bari ya taba hannun ba.
Bayan sun fito Baɗɗo ta kama mata suka sanya mata wata doguwar riga mai bubu, ta samu ta rarrafa ta yi rama sallolin da suka suɓuce mata daga zaune.
Wasa wasa sai da Ummu ta yi sati a asibiti sai da ta yi ras suka tabbatar da ba wata matsala sannan suka ba su sallama bayan an cire bandejin hannun ɗinkin ya fara shigewa ciki ya ɗan yi baƙi wajen sun ce ta samu hutu saboda jininta ya hau da kuma lafiyan jaririn jikinta.
Har aka sallameta Mami ne da Baɗdo ke jinyarta
Ammah ta zo ta duba ta sau daya itama haka ta riƙeta tana kuka tana cewa ta yafe mata Ammah ta ce ba komai amma ta sani in ta kashe kanta saboda Habib ko Shamsiya ta sani ba za ta taɓa yafe mata ba.
Yan'uwan Ammah duk sun zo har su Umma Salamatu.
Bangaren su Baffa Umaru dai Baffa bai faɗa musu ba yace kar a tayar musu da hankali.
Hamma Kabiru da Hamma Mustapha sun koma wajen aikinsu tun kafin a sallami Ummu ganin ta samu sauki sosai.
Ummu tana so ta tambayi Hamma Lamiɗo domin ba ta ganin shi ba tun bayan da ta farka amma ba ta samu hali ba, sai a daran da suka koma gida ta ji Ammah na faɗa ma Hamma Jibo a waya da cewa komai na asibitin nan shi ya biya. Ashe baya nan tun washegarin ranar da abin ya faru ya koma Lagos, amma yana kiran Ammah da Baffa yana jin yanayin da ake ciki.
Ummu Salma kunya take ji in aka ba ta waya za a gaisheta sai ta yi ta tunanin shike nan yanzu kowa ya ji labarin ta kusa kashe kanta. Har matar Hamma Lamiɗo ta kira a wayar Ammah an ba ta sun gaisa, haka ma Hamma Jibo da Adda Nauwara amma ba a fasa zahirin abin da ya faru ga kowa ba.
Hamma Saddam da Hamma Abdulrahim ba a gaya musu ba. Saboda suna nesa ba amfanin yayata maganar tunda lamarin ba mai daɗi ba ne.
Ummu ta yi nadama ko da yaushe kuka take yi tana neman gafaran Allah tun ballanta da Baffa ya kirata ya zaunar da ita ya sake tunasar da ita abin da ta manta.
Ya horar da ita hakuri da imani, Ammah kuma faɗa ta yi ta yi, domin daman ta ce tun lokacin da ta ji Shamsiya na wannan maganar ta ɗora mata ayar tambaya.
Ta kuma ce in Ummu Salma ta haifu to ta manta da Habib ballanta Shamiya har a gaban Ka'aba ta yi ma Allah kirari da kukan cewa Allah ya saka musu, yadda Habib ya wulakanta su shima Allah ya mayar masa da abin da ya yi musu.
Ita dai Ummu sai kuka ta yi nadama sanadin Habib ta goga ma kanta taɓo, yankan hannunta ko da ya fara warkewa har abada za ta koma ga Allah da wannan tabon a hannunta in ta kalli hannunta sai ta tuna da wannan bakar ranar.
Baɗɗo ta cika ƙawa kuma yar'uwa domin bayan ta yi jinyarta a asibiti da suka dawo gida kullum sai ta zo, makaranta ma daina zuwa ta yi a cewarta karatu kawai suke yi wacce suke tare ke saka mata attendence in za a yi test kuma tana yi mata, Ummu ta riƙe alherin Baɗɗo a cikin zuciyanta, tana fatan nan gaba kafin ta mutu Allah ya ba ta ikon da za ta iya saka ma Baɗɗo da tarin alherukan da ta yi mata.
Ba Baɗɗo ba hatta Ummin ikki ba ta zauna ba ita ke zaune da Ammah a gida lokacin Ummu tana asibiti. Ita da zuru'anta ba aminta ba sun zame ma Ammah ahali ita da ya'yanta da ƴan'uwanta gabaɗaya.
Mami dai wannan karon ta ce kafarta kafar Ummu Salma. Za ta ɗauke ta gabadaya daga Jimeta ta koma Kaduna a can kuma za ta haihu. Baffa ma wannan karon bai yi gaddama ba, shima zai so Auta ta ɗan yi nesa da wannan garin na wani dogon lokaci duka yayyenta ma sun amince da haka domin sauya muhalli da jama'a da yanayin iskar gari na kawo kwanciyar hankali. Ummun ma ta aminta daman ko Mamin ba ta ce kafarta kafarta ba ita za ta ce za ta bita domin ta gaji da Jimeta ji take yi gabadaya tana kuntace ne da zaman garin, da Umma Balki ce ta ce za ta tafi da Ummun Mubi Mami ta ce Kaduna za ta tafi da ita har sai da ta ji haushi wai a cewarta ita kanta Mamin yarinya ce ba za ta iya kula da Ummun ba sannan biye mata za ta yi ba za ta yi mata faɗa in ta yi ba daidai ba. Baffa ya yi ta dariya ya na ce ma Umma Balki mai ɗa kamar Lamiɗo ne yarinya? Ta ce E mana ai auran wuri ta yi ta haife shi Lamiɗo ai ɗan yarinya ne. Baffa kamar cikinsa zai kulle Mami dai tana jin ta ba ta saka baki da man tun tana gida kafin ta yi aure a Kaduna in dai Umma Balki ta zo gidan sai sun yi tsiya ba ta gani ta ƙyale.
Baffa ya raba gaddama ya ce Auta ta zabi in da za ta je ita kuma ta ce Kaduna. Umma Balki ta ce Allah ya kiyaye hanya amma ba haka taso ba. Hamma Abdulrahaman ya ce itama dai Umma Balki da rigima nauyi kawai Ummu za ta kara mata, gwara dai Mamin ta tafi da ita can Kaduna zai fi. Haka ko aka yi tuni suka fara shirin tafiya Kaduna kayan Ummu masu dan kyau kaɗan Mami ta ce za ta tafi da shi sauran har na wajen Habib ta ce duk Ammah ta aika da su Mubi a kyautar da su in suka je can Kaduna za ta yi mata sabbin ɗinkuna. Alhaji Isa ne zai zo da yara ranar asabar in suka kwana lahadi sai su koma gabaɗaya tare da Ummun da Mami.
Shi ya sa ranar jumma'a da safe Mami ta ɗauketa suka je can asibitin da take awo Hamma Abdullahi ya kai su ta yi musu bayanin za ta tafi da Ummu tana son report na bayananta saboda in sun koma can in za ta fara zuwa sabon asibiti sai ta nuna musu. Abu na kuɗi ba daɗewa suka rubuta duka bayanan suka ba ta, wajen sha ɗaya suka dawo gidan nan Ammah ke faɗa musu Hamma Lamiɗo ya zo bayan fitan su ba daɗewa sun fita tare da Hamma Abdulrrahman.
Gaban Ummu sai da ya faɗi saboda jin sunan Lamiɗo, in ta tuna da shi sai ta tuna da cewa jininsa na yawo a cikin jinin jikinta sai ta ji wani iri a acikin zuciyanta.
Ita dai ciki ta shige ta ɗan cigaba da kimtsa kayanta, ta ɗauko tsohuwar wayarta bayan ta cire layin ta karya ta ba ma Ammah tace ta kyautar. Ta sake komawa ciki tana cikin har aka yi azahar Mami na falo suna ta hira da Ammah.
Ta idar da salla kenan ta ji shigowar su gidan ba ta ji dai muryansa ba amma ta san da shi tunda ta ji Ammah na kiran sunan shi
Ba ta aikin komai yanzu tunda dai ba ta fara amfani da hannunta na hagu ba, duk da dai ɗinkin ya shige kuma wajen yana warkewa.
Saboda Hamma Lamiɗo ta ki fitowa ga shi tana jin yunwa ta so ta je ko kitchen ne ta samu abincin tunda Ammah ta gama shinkafa da miya tun ɗazu, amma ba ta son kallon Hamma Lamiɗo kunya take ki shi ya sa ta kasa fita, ta aikata abu yanzu kuma daga baya tana jin matsanacin kunya idan aka danganta ta da abin da ta aikata. Allah ya sa ma ba a yayata lamarin ba iya na gida ne da na jiki jiki na kusa suka san meke faruwa ko can su Baffa Umaru da suka ce sun ji cewa Auta ba lafiya sai Baffa ya ce kawai rashin lafiya ne ta yi, to babu amfanin faɗin komai tunda dai ba abin daɗi ba ne.
Haka ta naɗe yunwarta a cikin ɗaki ba wanda ya tuna da ita tana jin hiransu a falo da alama ma abinci suke ci domin tana jin Hamma Abdullahi na cika baki da abinci yana magana yau daga Ammah har Mami sun manta da ita, to ai gwara Mami yau watakila ta sha'afa ne Ammah kuma yau tunda Lamiɗo ya zo ko Baffa sai ta manta da shi ba ma ita ba.
Tana cikin halin yunwar nan Mami ta shigo yin salla ita ce ta taimake ta, bayan ta idar ta ce mata yunwa take ji sai ta fita da sauri ta je ta zubo mata abinci ta kawo mata sannan ta fita falo ta ɗauko mata ruwan gora da ake ajiyewa saman frizan saboda Ummu ba ta shan ruwa mai sanyi ba duka ake sanyawa a firizan ba.
Tana jin Hamma Abdulrrahman na ce ma Mami wai tana shagwaɓa ta, ta kai mata abinci har ɗaki ruwan ma da shi za ta bita.
"Kafafunta ne ke ciwo? Haba Mami."
Amsar da Mami ta bashi ne yasa tana cin abinci sai da ta yi dariya sai da ta kusa ƙwarewa.
"Ina ruwan ka? Nan kuma Ammah ke rawan jiki da ku ban yi magana ba, ta manta da mai juna biyu, nima shine na miƙe na ke kula da ya'ta."
"Ah Mami ki ce dai kawai kishi kike yi da mu kawai."
Hamma Abdullahi ya faɗa yana dariya.
"Ku dai kuke kishi da Auta, ku ana kula da ku, tun shigowarku Ammah ta ba ku abinci ita mai yaron ciki ta manta da ita."
Ammah na dariya ta ce" To ba kin fanshe ni ba, ina nan ina ji da mazan ke kiji da macen ba shike nan ba."
Mami ta yi wucewarta ta bar suna mata dariya.
Lamido na zaune a gefe ko tak bai ce ba, dukkansu shigar fararen kaya suka yi. A saman cafet din Ammah suka baje suna cin abincin Lamiɗo salat kawai ya ke ci da miyan shinkafan kaɗan yake ɗibaa, duk hiran da ake yi ba kasafai yake saka musu baki ba.
Ko Mami sun gaisa irin gaisuwan da suka saba, ya tambayi su Islam tace ai za su haɗu gobe za su taho tare da babansu, ya kasa ce mata shi yau zai koma Lagos, sai kawai ya yi mata shuru.
Baffa kuma ba ya nan ma ba a masallaci ɗaya suka yi sallar Jumma'a da shi ba, da wuri ya tafi yace akwai wanda zai gani ne.
Ita dai Ummu sai da ta gama cin abincin ta sha ruwa sannan ta ji ta ta dawo daidai, sai cikinta ya sake yin ƙasa saboda ta ci Abinci kwanciya ta yi ta gefe tana ɗan sauke numfashi ta kasa zama saboda tana jin cikinta ya cika.
Mami ne ta sake shigowa ta shiga tiolet tana yi ma Ummu sannu ta amsa dakyar.
Shigan ta ba daɗewa Ammah ta leƙo ganin Ummun kwance ya sa ta ce" ke kuma daga ci sai kwanciya."
Ummu ta yunkura ta tashi zaune kafafunta a kasan cafet duk sun kumbura.
"Ammah na kasa zama ne."
"Da dai kin daure."
Ta faɗa tana ɗan kallonta ganin tana ɗan cije baki.
"Sannu."
Ammah ta ce cikin tausayawa tana kallonta.
"Ga Lamiɗo nan zai wuce ya ce zai shigo ya sake duba ki.'
Sai Ummu ta fara kifta idanuwana saboda mamaki.
Hamma Lamiɗo ne zai ce zai shigo ya duba ta, abin da ba ta taba zato ba. Ta tuna wani lokaci a baya can tun ba ta yi aure ba, ta taɓa wani irin ciwo kamar za ta mutu na typiod , kowa ya yi mata sannu ya duba ta amma ban da shi, ita tana jin ma sannu na ciwo bai taɓa shiga tsakanin su ba.
Kafin ma ta yi wani yunkuri Ammah ta fita, ta miƙe dakyar domin ta nemi hijabi ta saka sai ga Ammah ta dawo bayanta kuma Hamma Lamiɗo ne ya sawo kai cikin ƙwarjininsa.
"Gata nan ai hannu ya ɗauko warkewa."
Ammah ta faɗa tana nuna masa Ummu Salma da ta sandare a tsaye ga ciki a gaba kanta ba ɗan kwalli wani tujajjan kitso ne da ba ta san ma daɗewar shi ba, tun dawowarta gida tana jin sau ɗaya ta taba yin kitso shima Baɗɗo ce ta ga kan ya tsufa ta tsefe ta ɗan yi mata duka baya guda goma kitson bai wani kamu ba, shi ya sa duk ya zare da wuri.
Ummu kunyar duniya duk ya kamata sai kawai ta dukar da kanta ta koma tana wasa da zaren adon rigan jikinta doguwa mai kalan purple.
"Auta ba ki gaishe da yayan na ki ba, jininsa ya cece ki daga mutuwa don kaniyarki"
Ammah ta faɗa cikin ɗan zolaya.
"Ina yini Ha. Hamma."
Ta faɗa cikin ɗan rawan murya.
"Lafiya."
Ya amsa a saman leɓensa.
Hamma Abdullahi ne ya kira Ammah daga falo sai ta fita ta bar Ummu da Lamiɗo a ɗakin. Tuni ta ji jikinta ya fara rawa, haɗa inuwa ɗaya da Hamma Lamiɗo ma tashin hankali ne zuciyanta taji tana tsinkewa kamar kasa ta tsage ta shige.
Shuru na mintina biyar ta ma ɗauka ya bar ɗakin ne tana ɗagowa suka haɗa ido, ya kafeta da kaifaffun idanuwansa hannayensa duka zube a cikin aljihun wandon farar shaddar jikinsa. Kafarsa akwai safa amma bai ɓoye zarazarab yatsun kafafunsa ba.
Da sauri ta sake sadda kanta ƙasa jikinta na sake ɗaukan bari, har ɗan cikinta sai da ya motsa.
"Ashe ba ki da wayau."
Ya faɗa cikin muryansa cike da ƙasaita
"Ban sani ba "
Ya dire maganarsa yana mai kafe ta da idanuwansa.
Ummu ta kifta ido ta buɗe sai hawaye sharr suka kece mata ba ta son ana tuna mata shirmen da