Follow us on social media

Showing 108001 words to 111000 words out of 147042 words

Chapter 37 - FARGAR JAJI Soyayya Ta Koma Cin Amana by Jamila Umar

Suwaiba ta gani a ɗakin tana zaune tana ba ma ƙaramar yarinyar ta Mimi mama.

"Adda an yi salla ne?
"Tun ɗazu. Biyar ma ta kusa."
Ta bata amsa.
Sai ta miƙe da sauri tana faɗin.
"Shi ne ba wanda ya tashe ni?

"Ummi ta ce a kyale ki likita ya ce ki huta sosai."
Ba ta sake magana ba ta shiga tiolet ta yo alwala ta zo ta yi salla. An riga an shigo mata da abincinta ta ja ta zuba tuwo ɗaya a filet ta fara ci, miyar ma daɗinta na musamman ne saboda zuwan Hamma Lamiɗo.
Tana jiyo muryan Hamma Abdullahi da na Hamma Abdulrrahman, har da na Ammah da Baffa amma ba ta jiyo na Hamma Lamiɗo ba.
Sai ta yi tunanin ko har sun karisa gidan na su ne?

"Adda su Hamma Lamiɗo sun tafi gidan su ne?

"Aa ba su tafi ba, ga shi can shi a falo suna hira da su Baban Mimi a falo, har da Baffa ma."

Ummu ta yi shuru ba ta sake magana ba.

"Balkisun kuma tana ɗakin Ammah tare da hadiman ta da suka zo tare."
Ummu ta ɗan gyaɗa kai, da man in dai za ta zo, tana tare da hadimanta.

Nan Adda Suwaiba ta fita ta barta bayan ta gama cin abinci tana son shan ruwa amma ba za ta iya fita falo ba tana jin kunya.
Sai kawai ta yi zaman ta.
Har fa mangariba duka suna gidan ba su tafi ba. Ummin ikki ce kawai ta tafi gida.
Bayan mazan duk sun fita sallan magariba itama ta idar kenan Ammah ta leƙo ta ganta saman darduma tana lazimi.

"Ke kam ba ki ji zuwan yayanki tun ɗazu ba ne? Ko da yake kina ta barci."

Kafin Ummu ta yi magana Ammah ta riga ta da cewa.
"To taso ki gaishe da matar yayan naki, kafin su dawo daga masallaci."
Ba ta isa ta zille ba domin Ammah ba a yi mata wasa.
Dole ta miƙe ta bi bayanta zuwa ɗakin Ammah in da ta iske Balkisu da ya'yanta tare da Sabuwa da Anitha
Da ta gaisheta ta amsa tana kallonta.

"Ba ki da lafiya ne?
Ta faɗa cikin yanayin maganarta.
Ta kasa mgana, domin ba ta san me za ta ce ba.
"Uhm ba ta da lafiya ai tana ma gida ne sun rabu da mijin"
Balkisu ta yi salati cikin yanayinta ta ce. "Subhanallahi."
Nan fa Ammah ta gyara zama ta shiga ba ta labarin abin da ya faru.

Ummu ta kasa zama ganin har Sabuwa na yi mata wani kallo, Anitha ma ta kafe ta da kallo kamar ta san me ake faɗa. Sai kawai ta tashi za ta fita Beena ta biyo ta a baya tana magana ba ma ta jin me take faɗa, ba shaƙuwa da yaran ta yi ba ko a baya suka zo gidan ba ta ta kan su.

Tana fitowa daidai su Hamma Abdulrahaman suna shigowa falon Ammah.
Sun riga sun ganta ba ta da yadda za ta yi, ga Beena ta rike mata gefen hijabi tana fadin egg za ta ci.
Kanta na ƙasa ta ma kasa ɗagowa tsabar kunya da nauyi.

"Ummu kin ta shi? Na leƙo ɗazu aka ce kina barci. Sannu ya jikin?
Hamma Abdullahi ya faɗa
"Ba ta da lafiya ne?
Hamma Abdulrrahaman ya faɗa yana kallon ta.

"E sai da suka je asibiti da Ummin ikki."

"Allah ya sauwake. Sannu "
Shima ya faɗa yana kallonta.
"Papa."
Beena ta faɗa ganin babanta sai kuma ta saki Ummu ta nufe sa ta faɗa jikinsa.
Kamar tsautsayi Ummu ta ɗago kanta karaf sai a idanuwan Hamma Lamiɗo da yake zaune saman kujeran zaman mutum biyu da ke falon Ammah.




*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L6zUax648eTERbvw8Bqyie?mode=gi_t

*17*

Sanye yake da wani baƙin yadi mara kauri domin in ka ƙura ido sosai za ka iya hango farar vest ɗin dake jikin shi ta ciki.
Ɗinkin zamani ne amma rigar ta kai har wajen gwiwan ƙafafunsa, kansa da hula amma saboda ya tara suma sai hulan ta samu matsugguni a saman gashin kan nashi, sannan gefe da gefen fuskar shi sumar ta ɗan bayyana.

Ummu ta yi saurin kauda kanta, shi da man bai nuna ma ya ganta ba, Beena ce ke yi masa raɗa a kunne yana sauraranta.
Ummu ta so ta yi sauri ta koma ɗakinta ne amma ina ta juya za ta shige kenan kawai ta ji Hamma Abdullahi ya kira ta.

"Ummu"
Ta juyo tana kallon shi.

"Ba ki ga Lamiɗo ba ne? Na ji ba ki gaishe shi ba ne"

Ummu ta runtse ido tana cije baki Hamma Abdullahi ya kwafsa mata, ita fa ba ta so ma ya ganta ba, ballatana ma har gaisuwa ya haɗa su ita a fatan ta ma har su gama zaman garin su koma ma ba za su haɗu ba sai ga shi tun a ranar farko Allah bai cika mata wannan manufar ba

"Sannu da zuwa Hamma, in yini?

Ta faɗa daga in da take tsaye.
Amma Hamma Lamiɗo ya yi kamar bai ji ta ba.
Da man halinsa ne ko a baya sai ka yi ta gaishe shi yana ji ya yi kamar bai ji ba in kuma ya amsa to a gajarce ne.

"Anan kuma! Ƙariso ciki wataƙila bai ma ji ki ba."
Hamma Abdullahi ya sake faɗa. Kamar Ummu ta fashe da kuka har hawaye sun kawo mata cikin kwarmin idanuwanta.
Haka nan jikinta a sanyaye ta ƙariso tsakiyar falon ta ɗan rankwafa daga gefe jikin kujera

"Ina yini Hamma".
Ta faɗa cikin rawan murya.

"Fatan an zo lafiya?

Ta sake faɗa kanta na ƙasa.
Nan ma shuru ya yi kamar bai ji ba sai da Hamma Abdullahi ya ce ana gaishe shi sannan ya ɗago yana kallon shi, Ummu ya nuna masa yana faɗin" Autar Ammah ke gaishe ka."
Kanta na ƙasa ba ta ɗago ba, saboda haka ba ta san ko ya kalleta ba ta ji dai ya amsa da lafiya da muryansa nan na shi a ginshiƙe kamar ba zai yi magana ba.
Zumbur ta miƙe ta bar falon har tana harɗewa da hijabin jikinta sai da ta ɗan laɓe daga can korido tana so ta ji ko zai tambaya me ya sa ya ganta a gida? Duk da ta san ba zai taɓa tambaya ba. Bai yi magana ba suma su Hamma Abdullahi ba su yi masa maganar ba sai ma suka shiga wata hirar ta dabam hakimin yana zaune yana sauraransu yana amsa musu ɗaya bayan ɗaya a ginshike cike da kasaita. Ita dai tunda ta shige ɗakinta ba ta sake fitowa ba, ana yin sallar isha'i ta tashi ta yi Adda Suwaiba ta ɗauko mata ruwa ta sha magungunnan ta, ƙila akwai na barci ne a ciki nan da nan barci ya ɗauketa. Cikin barci sama-sama ta ji Baffa ya shigo duba ta, ba ma za ta iya tuna me ta ce masa ba, shi dai ta tuna yana ce mata Auta ya jikin naki? Daga nan sai asuba ta iya farkawa shima wasu masallatan sun sallame salla.
Gidan shuru ashe tun jiya da daddare da baƙin da suka zo da yan gidan duk sun tafi gidajen su.

Da safen ma Ammah ta yi abin ƙari Hamma Abdullahi ya zo ya ɗauka bayan shi ma Adda Ummu Sulaim ta yo, sannan haka ma Adda Suwaiba ta kawo duka ya haɗa ya tafi da shi gidan Hamma Lamiɗo dake Jambutu haske.

**

*Jambtutu Haske*

Gidan Hamma Lamiɗo babban gida ne, mai ɗauke bangare biyu manya manya. Ɗayan bangaren an gyara shi amma babu kayan amfanin yau da kullum yana ma rufe ne ɗayan bangaren ne suke sauka in har sun zo garin. Kayattacen gida ne mai kyau wanda ya dace da zamani
Ko da Hamma Abdullahi ya kai musu abin ƙari ya daɗe yana knooking ɗin gidan ba a zo an ɓude ba. Kuma ya yi ta kiran wayar Lamiɗo tana shiga amma ba a ɗagawa.
Har ya yi niyyar juyawa sai ga Sabuwa ta zo ta buɗe gidan ganin shi ne yasa ta rankwafa tana gaishe shi ya amsa lokaci ɗaya yana miƙa mata kwandunan dake hannunsa masu ɗauke da abincin ta karɓa tana yi masa godiya.

"Uwardakina da Ranka shi daɗe ba su tashi ba."

Ta faɗa tana kallon Hamma Abdullahi
Agogon fatan dake tsitsiyan hannun shi na hagu ya kalla ƙarfe 9:50am  da man ya yi tunanin haka su ai yan Lagos ne ba sa buƙatar tashi da wuri ba irin su da sukan fita ƙwadago da sassafe ba.

"Ba matsala in sun tashi ga saƙo nan daga Ammah."

"Allah ya saka da alheri. Madalla mun gode."
Sabuwa ta faɗa sannan suka yi sallama ya wuce zuwa motarsa ita kuma ta rufe gidan ta koma cikin gidan
Duk wanda ya san matar Lamiɗo ya san ta da amintattaciyar hadimanta Sabuwa tunda duk in da ta saka kafa nan itama take sakawa shi ya sa kowa ya san ta a bangaren Ammah itama tas tasan kowa, haka ma Anitha mai kula da su Sultan duk in tafiya ta kama Balkisu ko na kwana ɗaya ne in dai tare da yara za ta yi tafiyar Anitha na tare da ita saboda kula da yaran shi ya sa itama ta san kowa kamar yadda kowa ma in ya ganta ya san amfaninta ba sai ya yi magana ko tambaya ba
Hidiya da Debora kaɗai da su James ake bari a gida.
Hidiya ana tafiya da ita amma sai in Bilkisu za ta je kano haka ganin gida ko kuma in za su je Daura amma yawan cin tafiye-tafiyenta ta fi yin su tare da Sabuwa da Anitha.

Kitchen Sabuwa ta kai kwandunan abincin tunda masu gidan ba su tashi ba sai sha biyu na rana su da ƴaƴan su. Sai da suka yi wanka suka shirya sannan Sabuwa ta jera musu abin karin a saman dinning
Akwai ruwan zafi da kayan tea sannan akwai kunin ɠyaɗa da soyayyen fanke wannan na Ammah ne, sai soyayyan ƙwai da daffaffe, sai soyayyar indomie, na gidan Hamma Abdullahi kenan na gidan Hamma Abdulrrahaman kuma soyyayar doya ce da ƙwai da plantain sai ruwan zafi, Bilkisu ta ba da umarnin Sabuwa ta ɗibar musu ita da Anitha tunda abincin ya yi musu yawa.

Ita dai tea ta sha da soyayyan doya yaran kuma sun ci ƙwai da plantain Lamiɗo kuma kunun ɠyadan shi ya sha da fanke, har wani jin daɗi yake yi domin ya yi kewar abincinka Ammah na'u'i masu daɗi, ta san yana so shi ya sa ta yi masa, shi fa har gobe yana faɗa babu wacce ta san shi dari bisa ɗari irin Ammah, ko bai yi magana ba ta san abin da ya fi so da wanda ba ya so.

Sai da suka gama karyawa sannan suka koma cikin ɗakin barcin su, yaran kuma Anitha ta ja su falo ta kunna musu tibi suna kallon cartoon aka bar Sabuwa da gyara in da suka ci abincin.
Tunda suka koma cikin ɗakin barcin su, magana ko ta fatar baki ba ta sake shiga tsakanin miji da matan ba, shi yana zaune a wata kujera kwara ɗaya dake cikin bedroom ɗin ita kuma tana kishiɠide a gefen gado tana duba wayarta shi ma ɗin ya duba wayar tasa har ya ga Abdullahi ya yi ta kiran shi amma bai bi bayan kiran ba.
Kansa kawai ya ɗan jinginar a jikin kujeran ya ɗan yi balance kafafunsa na lumshe a cikin tattausan cafet ɗin da ke cikin dakin barcin.

Idanuwansa na lumshe kamar mai barci sai dai ba barcin yake yi ba, a halin shi ko awa uku zai iya yi a haka ba tare da ya gaji ba shi dai kawai yana son shuru fiye da komai a rayuwarsa.
Sanye yake da riga da wando bakake, rigar mai gajerun hannu ne tana da ɗan taushi sai wandon iyakarsa gwiwan kafarsa, gargasan da ke kafafun nashi duk sun bayyana a waje.
Kansa ba hula sumar kan ta kwanta haka gemunsa da sajensa, Balkisu ta ajiye wayarta kawai tana kallon mijinta tana mai jin wani alfahari.

Da farko ta ɗauka tara gemu da saje ba na manyan mutane ba ne ta ɗauka na talakawa ne irin uztazan nan sai da ta haɗu da Lamiɗo ta san tara gemu ma baiwa ne da ƙasaita saboda shi ya sa take son gemu da saje. Kuma itama ta fahimci yana so, wai a haka ma yana ragewa in yana wajen aiki in suka yi video call gashi duk ya cika masa fuska sai ta ce ranka ya daɗe ya kamata a yi aski kai kawai yake ɗaga mata baya magana, tana so ta riƙa rage masa amma baya barin ta, sau ɗaya ya taɓa bari ta rage masa shima ita ce ta matsa daga ranar kuma ko ta ce za ta ce za ta yi masa sai ya ce a'a. Ita da ta so har private part ɗin sa ta dinga masa sheving amma ina ta san ba zai taɓa aminta ba.

Ko fa kaya ta saka in dai jikinta ya bayyana ba ya son kallonta sai ya dinga wani kauda kai in ta matsa kuma sai ya runtse ido yana faɗin
Ki je ki sauya kayan jikin ki mana"
Yau ma wata riga ce a jikinta mai santsi tana da yar ciki da jaket. Da za su fita beakfast sai ta saka jaket din suna dawowa ɗaki ta cire ta zauna daga ita sai ta cikin mara hannu ta ɗan kamata amma tana da ɗan tsawo tunda ta kai wajen gwiwan kafafunta, kanta kuma da man mayafi ne ta saka ta yi rolling shima tuni ta cire, ta bar suman kan nata da ya sha gyara sai ƙamshi yake yi yana ƙyalli.

Mirmishi take yi ita kaɗai tana tuna daran jiya. Ba ta ɗauka zai kula ta ba, ganin sun yini gidan Ammah kuma ga gajiyan tafiya amma suna yin shirin barci ta shige jikinsa ta lafe masa tana sauke numfashi ya birkice mata, in ta tuna irin yadda ya yi mata rawan jiki sai ta ji wani irin daɗi ya kamata. A baya kafin ta fahimce shi sai ta yi ta kuka tana tunanin ko ita mijinta baya jin daɗin ta ne ? Mata da yawa ƙawayenta ƴaƴan sarakuna da abokan karatunta masu aure suna irin hiran yadda ko gyara suka yi irin yadda mazajensu ke ruɗewa har da waɗanda ake yi ma kuka da ihu, amma ita mijinta bai taɓa mata ko sambatu ba, kuma in zai dawo haka za ta yi ta shiri ta gyara ciki da waje, daga can Kano Umma me aiko mata da kayan gyara da yawa ta yi ta sha ammah in ya dawo suka kaɗaice ba ta ganin wani canji. Sai da ta ga wani rubutun wani likitan kan maza yana bayani kan kashe kashe da rukunin maza da ta bi rubutun sa anan ne ta gano mijinta a cikin rukunin maza.

Namijin da ba ya iya bayyana ƙololuwar jin daɗinsa ko da daɗin zai kashe shi ne, amma zai yi rawan jiki sannan zuciyarsa za ta tsananta bugu sannan zai ta yin zufa amma ba wai ya yi kuka ko sambatu ko wata alama ba, daga lokacin ta samu salama tunda ta fahimci duk yana yin haka kawai dai sambatu ne da ihu ba ya yi, jiya ma da ta tafiyar da ragamar ya yi ta mata nishi kamar numfashinsa zai kwace daga ƙirjinsa. Shi dai in har wajen zai yi duhu to zai iya sakin jiki a yi komai sai bayan sun natsa ne in haske ya gauraye ɗakin ya yi kamar ba shi ba, kai tana son Lamiɗo domin ta san ta yi ma sauran mata zarra samun namiji  mai kama da maza ɗari a waje ɗaya.

Tana so su dinga zama suna hira duk da itama ba ta da surutu amma tana so ta ga tana yi masa hira ko ba zai yi magana ba ya yi ta kallonta da yanayin kallon shi mai narkan mata da zuciya.
Amma matsalan itama ba ta iya hiran ba, da ta fara sai ta rasa me za ta ce, in dai ba hiran can Daura ba shima sama sama, har gwara ma in tana yi masa hiran Ammah har mirmishi za ta ga yana yi mata sannan in ta yi tambaya yana bata amsa jefi-jefi. Ta daɗe da shaida cewa Lamiɗo na kaunar Ammah ninki da yadda yake son mahaifiyarsa Mami ita kuma kowa ya shaida yadda take ƙaunarsa, shi ya sa itama kamar ta lasheta saboda ita ɗin Matar Lamiɗo ce, tana gani in ta je matan su Hamma Abdulrrahaman Ammah ba ta yi ta kan su, amma ita da yaranta da jikinta da komai take yi musu wahala. Da farkon auren su ba ta san dawan garin ba duk da ta san a hannun Uncle ɗin sa ya taso yayan mahaifiyarsa. Ta ɗauka mahaifiyarsa na da tasiri a rayuwarsa sai daga baya ta fahimci komai domin lamarin ma a bayyane yake. Mami da Lamiɗo in suka haɗu ban da gaisuwa ba abinda ke sake haɗa su, a waya ko sai su yi sama da wata ba su yi magana ba in ba wani abu ba ne ya taso ya kirata ba. Musamman ma dai ya fi kiranta ya gaisheta in su Islam na gida ya ce a ba su wayar shi dai yana da son yara duk da baya son hayaniya. Wayar ma da yake yi mata Ammah ce ta ce ya riƙa kiranta yana gaisheta mahaifiyarsa ce, amma mijinta Alhaji Isa akwai girmamawa mai girma a tsakanin shi da Lamiɗo shi har ya fi Mami ma jawo shi a jiki amma ita kamar ba ɗan ta ba, ko da yake da man ta ce ba ɗanta ba ne ɗan Ammah ne.

Da fari har ita tana kira ta gaisheta lokaci bayan lokaci ranar dai Mami ta faɗa mata gaskiya da cewa in za ta yi kamun kafa ne ta je ta kama kafar Ammah ita  uwar Lamido ce kawai a haihuwa amma nan duniya ba shi da iyayen da suka wuce masa Ammah da Baffa kuma ta ga haka, domin a wajensa shima ba shi da iyayen da suka fisu, akwai wani zuwan da suka yi Daura ta tambayi Fulani Daura ita ta zaunar da ita ta bata labarin mafarin komai ta kuma shaida mata Mami ta yanke alaqa da duk wanda ya danganci Lamiɗo da su Ammah kawai suke zumunci, kuma ta ga hakan in za su haɗu sau nawa bayan gaisuwa ba ta taɓa ganin sun yi wata magana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login