Showing 3001 words to 6000 words out of 124573 words
Chapter 2 - Sangartacce Book Complete Pdf by Maman AbdulShakur.pdf
ta tsugunna a makwarara tai alwala
sanan ta shigo dakinsu, salla taga Mama dasu Raiyana nayi hakan yasa ta zauna akan kujera
tana kokarin kunna fitila, kunnawa tayi ta ijiye daidai lokacin sun sallame Layla ce tafara tasowa
Raiyana tabiyo ta abaya duk suka zauna kusa da ita Layla tace "me kika kawo mana daga
school Anty Baby?" murmushi tayi ta bude jakarta gwaiba taciro da topi ta basu duk suka karba
cikeda jin dadi Mama ta ballamata harara tace "aikin kenan" dariya tayi ta tashi tasaka hijabi tai
sallan magriba tana idarwa ta daura kanta akan cinyar Mama ahankali tace "yunwa nakeji
Mama sosai" mika hannu Mama tayi ta dauko kular tuwo dake gefenta tace "gashi nan zuba
muku kuci keda kaninki to" tashi tayi ta dauko faranti ta zuba tuwon tasa miya asama ta kalli su
Raiyana tace "ku sakko muci" sakkowa sukayi zasu sa hannu Mama ta harareta tace "bazaki je
kicire kayan makaranta bawai" kaman zatai kuka ta tashi tawuce uwar daka tacire kayan ta fito
daure da zani akirji ta zauna tana turo baki sanan suka saka hannu duka suka faraci.
Dr ne akan wani magidancin da akalla zaikai 75 years sa'an Baba buharií ˝í¸‚ acikin wani
katafaran falo sai sumbatu yake yana "Dr Ayaan dina zaka kawomin, Ayaan" shiru yayi sabida
alluran da likitan yamai daidai lokacin wani security dake sanye cikin uniform ya tsaya agaban
falon yana sallama, izini matar dake falon cikin shiga ta alfarma tamai, hakan yasa ya shigo
hanunshi rike da wata ipad, Karasowa yayi gefen Baba Sule wanda shine kanin magidancin
dabaida lpy, cike da girmamawa yace "Alhaji wanan shine CCTV footage din natun ranan da
Ayaan yafara rashin lpy abangaren shi, da lokacin daya fita daga gidan" ya kalli matar datai
tagumi tana kallon fuskar mara lpy yace "Hajiya akwai bukatar kema kizo ki kalla dan wata da
kayan yan aikin gidan nan ne tafara kawomai abinci lokacin yana garden tace kece kika aikota
takawo mai, to ayanda dai CCTV footage din yanuna yanacin abincin yafara rashin lafiya
saikuma..." yadanyi shiru cikeda damuwa yace "zodai ki kalla dakanki wata kila ki gane yarinyar
dan munemo ta dole zatasan wani abu kan batar shi" tashi matar da aka kira da Hajiya tayi ta
dawo gefen Baba sulen ta zauna jiki asanyaye tana kallo, tunda tafara kallo ta dafe zuciyar ta
tana buga salati saikuma tafashe da kuka sosai ta kalli Baba Sule tace "Baba Sule ina dana
yayi? Yanzu adai yanda yafitar nan a ina zamu ganshi, innalillahi wa innalillahi raji'un wanan
wace irin musib.." shiru tayi ganin mara lafiyan yakara farkawa yarike hanun Dr dake kanshi
yace "ina Ayaan dina? Eh Ina ka kaimin shi?".
[7/15, 12:17 PM] Ummi Tandama: ♦♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦♦
Maman Abd Shakur
5...
Free page
Iska da kiraye kirayen sallan magrib ne yashiga kunnenta yana ratsa har brain dinta, ahankali
take bude ido ganin inda take yasa ta mike tsaye a firgice tana karanto ayatul kursiyu ko ina na
jikinta na rawa, karan buga abu dataji shiya kara firgita ta hakan yasa mahaukacin kara juyowa
ya kalleta, baya tafara komawa jikinshi ko ina rawa yake, juyar dakai mahaukacin yayi yacigaba
da bubbuga kular nata abango yana dariya kafin yakamo bakin rigar shi ya cusa abaki yana ci,
hannu tasa tarufe bakinta tacigaba da komawa baya sadaf sadaf, haushin kare taji abayan ta
yasa ta buga wani irin mugun ihu ta shiga cikin gidan da gudun bala'i dan ta tsani kare, karan
yazo ya tsaya ta bakin kofan yanata haushi, zuciyar ta kiris ne yarage bai fitoba, mahaukacin ya
dena buga kular dayake yajuyo dakai yana kallonta, yanda ta makale jikin bango tana kuka
kaman zata suma, rigar shi yakara turawa abaki yana kallonta yana wani irin lankwasar dakai
yana taune rigar hakan yasa ta tsugunna awurin tareda runtse ido da karfi tana cigaba da
karanta ayatul kursiyu, wani irin mugun kuka da haushi karen yasake yi "wu wu!" hakan yasa
mahaukacin ya juyo daga dena buga kulan abango ya kalli karen, zare rigar yayi daga bakinshi
ya fashe da dariya sanan ya tsugunna shima yace "wu wu" da karfi sosai, haka yadinga wu wu
yana matasawa kusa da karen yana tsalle har karen yabar wajen, shirun dataji yasa ta dago
kanta ta kalli hanyar fita taga ba karen littafin ta dake watse akasa taga mahaukacin ya dauka
yanata yayyagawa yana kara da wasu gwalangwalan yanaci, jikinta har rawa yake tana
kallonshi ganin hankalin shi nakan litttafin yasa ta ruga aguje tafita daga wajen, haka ta dinga
gudu harsai da takai bakin titi, machine ta tsayar tahau sai goge hawayen dasuka ki tsayamata
take tayi, saida suka kai anguwar su daidai kusa da gidansu ta sauka malam tagani tsaye
yanata kallonta da alamu dama ita yake jira, kallon mai machine din tayi tace "bari na amsoma
kudin" ahankali ta karasa wurin Baba tana share hawaye anatse yace "meya faru? Ya akayi
kikai datti haka daga ina kike?" fashewa tai da kuka tace "faduwa nayi Baba akan karfe kaina
zafi yake yi ma" hannu yatura a aljihu yace "sannu kidinga yi ahankali nawa zaki bashi?" "naira
dari" tafada batare data daina kukan ba, mika mata yayi taje tabashi sanan tadawo ta shige gida
hada Ido sukayi da Isyaka dake biyama wasu almajirai karatu ya mata alamu da hannu na
sannu ta gyada mai kai asabari ta daga tareda bude kofa ta shiga cikin gida. Babu kowa a
tsakar gidan hakan yasa tawuce dakinsu su Raiyana tagani tareda Mama suna bata haddan
dazasu bama Baba gobe da asuba yaji, zama tayi akan kujera tana share hawaye Mama ta
kafeta da ido tace "daga ina kike Bilkisu? Kin kaima Balaraba kudin nata?" wani irin racing heart
dinta ya shiga yi hakan yasa takara fashewa da wani sabon kukan tace "Mama wlh faduwa nayi
namaji ciwo akai?" kallo Mama tabita dashi gashi tayi wani irin mugun datti hakan yasa tace "a
ina kika fadi? Ina jakan ki? Ina kudin dana aikeki dashi?" tashi tayi a tsorace tai hanyar kofa
hakan yasa Mama ta bita da kallo, a tsorace cikin kuka tace "kudin nacikin jakata nabarta a inda
nafadi amma gobe da safe zancema Muji yakaini na dauko saimukai mata" hawaye takara
sharewa tana kallonta tace "kiyakuri dan Allah Mama" da sauri ta juya tafita daga dakin danba
karamin aikin Mama ba ta maketa dan akwaita da saurin hannu, dakin Umma ta shiga aiko duk
hankalin Umma yatashi anan ta kwana.
Wuraren takwas da rabi ta shigo dakin nasu lokacin su Layla harsun dade da tafiya makaranta,
Mama tasamu tana linke kaya afalo adan tsorace ta wuce uwar daka doguwar riga ta dauko
daga ghanamasgon ta na atampa kore sanan ta ciro milk hijabi daya kaimata har kusan kasa ta
saka tafito tasami Mama a inda ta barta ahankali tace "Mama zanje gidan Baaba daga nan sai
Muji ya kaini na dauko jakan na kai kudin" batare data kalleta ba tace "saikin dawo" fita tai daga
dakin koda tafita waje gidan Baaba tacema Baba zata hakan yasa baihanataba. Samun Baaba
tayi agaban murhu tana dafa dafadukan shinkafa da wake "Baba ina kwana, naga keken Muji a
waje ina yake?" kallon fuskar ta Baaba tayi tace "ya zaga bayan gida yanzu zaifito, maiya sami
idanunki sukai jajir haka" zama tai gefen Baaba ta goge hawayen dataji ya gangaro mata tace
"faduwa nayi nabar jakata wurin kuma akwai kudin Mama aciki datace nakaima Balaraba
dillaliya" cikeda damuwa Baaba ta kada kai tace "to Allah dai yasa kisami kudin ajakan yanda
duniya tabaci yanzu, kai Muji ina kake ne fito ka kaita kafin rana tayi kowa ya fito ayi gaba da
jakar, a ina kika fadin?" ahankali tawani narke ma Baaba tace "ahanyar makaran tarmu jiya da
yamma" daidai nan Muji yafito daga bayi tareda ijiye butar hanunshi nan gaban rijiya Baaba
tace "oya zoka kaita ta dauko jakarta" ta kalli Bilkisun tace "kin Karya?" girgiza mata kai tayi
Baaba tace "karya to saiku tafi" girgiza kai tayi arude tace "a'a nidai samin akula naci acikin
keke napep" tashi Baaba tayi ta dauko wani kula adaki ta fito ta bude tukunyar ta deban mata
shinkafa da waken dayawa ta rufe tabata tace "ki tabbata kincifa kinsan cikin ki baison yunwa"
ta kwalama Muji daya shiga daki abinshi kira "wai mekake yi aciki ne?" fitowa yayi rike da key
ya kalleta yace "muje" tashi tsaye tayi rike da kular ta suka fita waje keken suka shiga ya tada
yace "a ina ne kika yarda jakan?" tagumi tayi gabanta na faduwa tace "chan ta wuraren school
dinmu, tafiya suka dingayi har sukakai wurin suka shiga layin har zuwa karshen layin adaidai ta
bakin bolan tasa yay parking duk suka fito, komawa bayan Muji tayi ta labe hakan yasa ya juyo
ya kalleta yana nazarin fuskarta yace "me wai? Ina jakar to? Uban meme kikazo yi anan wajen
bola wakika gani anan?" nuna mishi ginin tayi tace "yana cikin nan jakar kuma wani mahaukaci
ne aciki, ni tsoro nakeji ka shiga ka daukomin" tafashe da kuka, tsaki Muji yayi yajuya yana
kallon ginin yay hanyar shiga tana biye dashi abaya ko ina na jikinta narawa, tsayawa Muji yay
abakin kofa yana kallon mahaukacin dake sanye dawani bakin riga t-shirt daduk ta barbarke
dakuma dogon wandon jeans dashima dukya barbarke, sai yago fallen littafin ta yake yana
turawa abaki yanaci, jin Muji ya tsaya yasa tadan leko ta bayan shi dan taga meyake kallo,
sosai taga mahaukacin yanata tura paper abaki yana taunawa daga gani kasan yunwa yakeji
wani irin mugun tausayin shine taji ya shigeta saisa ashe jiya yaje ya sato buredi, da sauri ta
juya takoma keken ta dauko kulan abincin da Baaba ta bata dabata tababa tadawo tabi ta gefen
Muji ta shiga ciki jikinta na rawa, nesa dashi ta tsaya ta bude kulan abincin tana bashi amma ko
kallonta baiyiba saima tauna takardan dayake yi abinshi, kara matsowa tayi ta mikamai har
lokacin bai kalleta ba, tunawa datayi jiya yanata buga kula a bango yasa ta buga marfin kulan a
bango yay kara sosai, da sauri taga yadaga kai yana kallonta wani irin faduwa gabanta yayi
dum! Amma duddu haka saida ta mikamai abinci tanadan kwanto da kulan sabida ya hango
abinda ke ciki, baiyi ko motsi ba saima kallonta dayake tayi yana sosa kunne, ahankali tadan
tsugunna taga yabita da kallo takara nunamai kulan amma baikarba ba kaman ma baigane
metake cewaba hakan yasa ta daga hannunta na dama ta nunamai sanan tasaka hannun a
kulan ta debo abincin ta nunamai sanan ta kai bakinta tasaka aciki tana taunawa tanamai
murmushi atsorace, da sauri taga yataso yayo kanta da gudu ta matsa baya ta jingineni da
bango kaman zata shige zuwa yay gabanta ya fizge kulan da karfi harsaida abincin yadan zube
ya zauna nan gabanta ya daga hanunshi shima sama ya nunamata kaman yanda tayi sanan
yasaka akullan ya debo yakai bakinshi yafaraci da sauri da sauri murmushi taga yayi daya
bayyana dimples dinshi daduk jikakken paper ya makale akai yacigaba daci kaman zai hada da
kulan sai kallonshi take a tsorace jikinshi fatar jikinshi duk baki baki kaman mai aiki a gareji.
Shigowa Muji yayi yazo kusa da inda take a makale a bango ya tsaya tareda rike kwankwaso
yana kallon mahaukacin hakan yasa mahaukacin ya ijiye abincin yayo kan Muji yana daga
hannu zai dakeshi da sauri Muji yakoma baya yana kakkare fuskarshi da hannu, dariya
mahaukacin yayi sosai sanan yay wani irin tsalle ya dira agaban kulan yacigaba dacin abincin,
da sauri ta mike tsaye kudin Mama dake tsakar wajen ta tsugunna ta dauka tareda tattare
littafan ta tasaka ajakar ta kalli Muji daketa kallon Mahaukacin tace "mutafi" hararan ta Muji yayi
yace "sannu to kulan Baaba fa" kallon Mahaukacin tayi taga yanda yakecin abincin rabi na zuba
ajikinshi "Ke kalli wuyanshi" maganar Muji ne yasa ta janye idonta akan mahaukacin ta kallai ya
nuna mata wuyan mahaukacin yace "jibi wanan ba sarka bane a wuyanshi ba, rigar jikinshi
tadan rufeshi" yay maganan yana dan matasawa kusa da mahaukacin tareda dan tsugunnawa
yana leken wuyanshi dake cikin chain daketa sheki da sauri Muji yace "innalillahi ke Balkisu wlh
sarkan zinare ne, zokiga, zomu ciremai naje kasuwa na saida Allah yabamu, munyi kudi"
hararan shi tayi tareda jan tsaki bata tanka maiba saima tsugunnawa datayi tana kokarin daukar
byron ta dake kasan wurin, Muji ya kalleta kafin ya maida dubanshi ga mahaukacin yace "Allah
kadaima yasan meya haukata shin, halama irin yan iskan yaran nanne inbahaka ba meyake yi
da sarka yana namiji, yan iska kesa sarka fa irin mawaka da yan party dinan" cikeda masifa
tace "nidai baruwana na, baruwan ka da sarkan shi kasan ko garin hauka yasamo, kokuma ya
fizgema wasu" hararan ta shima yayi yace "tunda baki da hankali ba, ta ina mahaukaci zai iya
saka sarka da kanshi? Eh fadamin ta ina zai iya saka sarka harma ya boye ta tacikin riga, nidai
cirewa zanyi? Dan nasan karshen ta wasu su kwacemai" "sata fa kenan Ya Muji ittakulla" karan
yarda kulan da mahaukacin yayi yasa Muji yatashi da sauri yakoma baya itakuma tai hanyar
waje tafice da gudu, tashi tsaye mahaukacin yayi yafara tsalle tsalle yana gudu yana zagaye
wajen da sauri Muji yadau kulan yafita yana waigen mahaukacin.
*wai meke faruwane a novel dinga?*
*waye wanga mahaukaci?*
*waye mutumin nan da Dr ke kanshi*
*waye sangartattcen?*
Wanan shine last free page, idan har kanason cigaba da karanta wanan labarin dake kunshe da
abubuwa da dama mai nishadantar da kayatar da zuciya zaku iya tuntubana ta watsapp number
na kaman haka 07012181461.
Hanyoyin biya biyu ne kota kati wanda zaki tura MTN 200 ta number nan 07032934950 kokuma
ta banki 3107021073 first bank aisha Muhammad.
Labarin ga kuwa yanxu bama komi akeyiba kudai kubiyoni kucigaba da karatu❤
[7/15, 12:17 PM] Ummi Tandama: ♦♦♦ *SANGARTATTCE*♦♦♦
Maman Abd Shakur
4...
Free page
Alluran bacci Dr yasake mai sanan yay bacci, matar takara fashewa da kuka, Baba Sule da
Security suka fita daga dakin dan zuwa police station danjin ya ake ciki.
Layla ne ta shigo dakin ta kalli Bilkisu dake kwafe note tace "Anty Isyaka na falon Baba yana
jiranki" satan kallon Mama dake tsefema Raiyana dogon gashin ta tayi taga ko kallonta batayi
hakan yasa taidan murmushi tadau dogon hijabin ta tafita daga dakin, dakin Baba tai sallama ta
shiga, daki ne mai fadi wanda kusan littatafan addinine suka cikashi, koina agyare ga kamshin
turaren wuta, daga gefe kuma isyaka ne dayaci gayu cikin normal shadda abinshi sai kamshin
turaren duri yake yanata kallonta akunyace ta zauna nesa dashi akan tabarman tana wasa da
hijabi tace "ina yini" kara gyra zama yayi tareda lankwashe kafa ya hade tafukan hanunshi yana
murzawa yana murmushi yace "barka da zuwa Bilkisu gimbiyata, gimbiyan duka matayen garin
nan, gimbiyar dake mulka zuciya ta, saurayinyar mata mai gadon zinare" dariya tayi ta kawad
dakai dan ba karamin kunyan shi takeji ba, Isyaka amintaccen almajirin Baba ne, tun yana
karamin yaro aka kawoshi almajiran ci wajen Baba harya girma, shekaran shi 25 yanzu, yanada
aikin hannu dan ya iya aikin hula da aikin su shadda, Baba yariga yabashi Bilkisu tun tana yar
yarinya, yanzu haka ita yake jira dazaran ta zana jarabawa za'ayi auren su yakoma da ita
kauyensu nachan hanyar sokoto.
Dan gyara murya yayi yace "bakice komiba mar'autul saliha? Ya karfin jiki" anatse tace
"Alhamdulillah na warke ai tun dazu" wata torchlight phone yaciro daga aljihun rigar shi yazo
gabanta ya ijiye mata akan hijabi yace "gashinan ki rike inaso mudinga waya tanan" da sauri ta
kallai sai kuma ta make kafada ta kwaye fuska kaman zatai kuka, ashagwabe tace "a'a nidai
bazan karba ba, Baba bayason muna amfani dawaya Allah kabarshi nagode" tunda take
maganan yakafe ta da ita hakan yasa ta dukar da kanta kasa, dan ajiyar zuciya ya sauke kafin
ahankali yace "har yanzu kinki dena shagwaban nan ko, dan Allah kidena mini ji nake kaman
zan mutu idan kinayi, ina kaunar ki dayawa Bilkisu, yanzu dai Baba yariga yaga wayar ai yama
yarda nabaki saisa nakawo miki, gwara munayi munadan taba waya ko? Muma muyi soyayyar
yan gayu" gyada mai kai tayi tana murmushi daya bayyana fararen hakoran ta tace "nagode"
dariya shima yayi cike da murna yace "bari namiki waka" dan zaro ido tayi tana kallonshi
yamata wani irin kallo yace "dukda ina malami ai dole na koyo waka nama gimbiyata dan na
faranta mata rai" dariya ta sake yi harda rufe fuska, dan gyara murya yayi hakan yasa ta tsayar
da dariyar tana kallonshi, yawani kalleta yana nuna ta da hannu yace "Bilkisu na yarda dake,
dauki amanata ki rike, kin dace da zama dani, Bilkisu gimbiyar raina, Bilkisu hasken idaniyata,
Bilkisu ina kaunarki, Balkisu tauraruwan raina, Bilkisu abun kaunataaa" bakaramin dadi wakan
yayi mata ba sosai ta dinga dariya tareda boye fuskar ta cikin hijabi, "ya isa haka dariyan to
yawan dariya baida kyau a addinin mu, tashi kije ki kwanta akwai school gobe" addu'a yayi
sanan ya mike tsaye yace "saikuma gobe ko, kiyi alawa kafin ki kwanta zan kiraki tawaya cikin
dare sabida kitashi kiyi salla ko" gyadamai kai tayi yafita daga dakin yana mata murmushi,
hakan yasa itama ta tashi sanin Baba nadakin Umma yasa takoma dakinsu ganin Mama tai
bacci da Layla aka gado, yasa ita tadawo falo ta kwanta kan dagon kujera 3 sitter wacce dama
anan take kwana itakuma Raiyana 2 sitter take kwana kokuma wani zubin su kwana akasa.
Da asuba bayan sunyi salla duk dakin Baba sukaje karatu ya koya musu Qur'ani, hadisi da
fiqhu, bayan sun biya wanda yabasu jiya harsai wajajen karfe shida sanan suka fito, kitchen ta
shiga dan hura wuta Raiyana kuma taja ruwa dan wanke bayi da makwarara, itakuma Layla
tadau tsintsiya sharan tsakar gida, suna gamawa duk suka diba ruwan zafi sukaje wanka sukaci
dumamen su da kokon da Bilkisu ta dama sanan suka tafi makaranta. Gyara dakin Mama tayi