Follow us on social media
Showing 204001 words to 207000 words out of 222800 words
tanaji ajikinta mutuwa zatayi,tanata kewar fahad wani lokaci Sadiya seta kirashi Su gaisa dan Aishar taji muryarshi,tarage damuwa,
Ana haka aka shiga azumi acan Su Aisha sukai nasu faseelat ciki be barta yiba sede ciyarwa akemata,
Ranar salla da fahad daita sune har gidan baba babba koina sunje barka da salla ,
Bayan kwana biyu da salla Su Aisha suka dawo lokacin da Mommy taganta seda ta firgita ta jeme kamar kallemu ,
Dawowar ta gidan yakara mata tension saboda tana ganin shige da ficen fahad dukda beda walwala ,taso tabashi hakuri da tayi niyyar tunkararshi seta kasa inta tuna halinda ya same Su ,
Bayan sati da salla yaje da faseelat gidan yanata nan nan daita ,
Lekowa kawai tayi ta gansu jininta yakara hawa zuciyarta taita zafi ,dan tuni tagane yasaketa kuma gashi batason konawa yamata ba,
Hawaye taitayi tana tarin bakinciki shikenan ta rasa yaya ?sede ta ganshi da wata yana nuna mata kauna,
Sukayi mintoci suka tafi ,
Se dare Sadiya tashiga dakin Aisha domin itakadai ke kara tausaya mata dansu mommy ma haushi take basu yanzu,
Ta sameta tana ta aman jini ta ruga ta kira mommy akatafi daita hospital,
Tunda suka shiga daita ba allurar dabaai mata ba amma takasa bacci sede pain din yarage hakanan aka medata rest room ,
Su mommy suka zagayeta suna kuka ,
Har wanshekare suna nan wurinta,
Aisha da jini ke shiga jikinta hawaye nata bin gefen idonta ta kamo hannun Sadiya tace"mutuwa zanyi kikiramin faseelat nabata hakuri dan Allah "muryar na rarrabuwa,
Sadiya tatashi tafita dagudu tana zuwa gidansu faseelat taita knocking faseelat tazo tabude ,tana ganinta gabanta yafadi,
Tana haki tace" anty kizo asibity anty Aisha bata lpy sosai tanata kiranki dan Allah kitaho "
Hawaye suka cika idon faseelat batasan lokacin da suka gangaro ba bako tsayawa daukar hijab daga ita se doguwar riga da gyalenta suka fita,
Tana cikin motar ta tana bin bayan Sadiya,
Suna isa dasauri tafita harta manta da ciki jikinta suka shiga dakin da Aisha take kwance,
Aisha na ganinta ta mika mata hannu tana hawaye faseelat ma nayi ,ta zauna gefen gadon,
Aisha tace"kiyafemun faseelat nacuceki na rabaki da mijinki for almost 5month ki yafemin ,mutuwa zanyi"
Faseelat tana kuka tace"bakimin komi ba anty nice namiki laifi kiyi hakuri ciwo ba mutuwa bane"
Aisha tace "ki yafemin mutuwa zanyi dan Allah ki rokarmin yaya yayafemin tun kafin na mutu na cutardashi naci masa amana"
Faseelat tace"ya yafemiki since be rike kiba "
Aisha tace"I want to see him before dyeing ki kiramin shi nasan zezo "
Faseelat tatashi tafita tashiga mota tana tukin ganganci taisa maaikatarsu fahad hankalinta tashe kowa se kallonta yake tasamu aka nunamata office nashi tawuce waiter nata mata magana tashige ciki ,
Fahad da yayi nisa atunani yadago fuska jin kukanta da kamshinta ya zuba mata ido yana kallon kayan jikinta da katon cikinta da yayi kamar yafashe ,yabude
Baki da niyyar yin masifa ,takarasa wurin shi tana kuka sosai ta zukunna gabanshi tace"dan Allah kayafemata kame data dakinta anty tana cikin ciwo sosai "numfashinta na daddaukewa ,
Ta cigaba da cewa " kazama me yafiya hero dan Allah kasamar mata kodan karamin wuri ne a zuciyarka ko kanaso ta mutu?to wlh idan baka hakura ba anty mutuwa zatai"
Ta mike ta kamo hannunshi yanata kallonta betashi ba tace"
dan Allah hero kazo kaga anty kataso kaga anty yadda ta koma "cikinta yayi wani irin juyi ta sakeshi ta rike cikin tana cigaba da kuka sosai,
Yayi sauri ya rikota yace" muje nagantan kiyi shiru kidena kuka "ya gyara mata gyalen ya kama hannunta suka fita ,yana jin haushin mazan da suka ganta haka,
A motarshi suka tafi tanata kuka sede kallonta yake zuciyarshi na ciwo,
Suna isa asibitin ya fito ya rikota suka shiga tare tanata kuka har time din,
A bakin kofa yasamu Su ramlat sunata kuka yatura kofar yashiga,
Kallo daya ya mata hankalinshi yatashi yanzu sunyi 2month besata a ido ba ,
Ya saki faseelat yakarasa bakin gadon datake kwance Mommy tafita daga dakin don ba karamin haushin fahad takeji ba,ta zubamai ido ne kawai,
Aisha da idonta ke rumtse tanata sallallami ta bude ido ,
Fahad jikinshi ya dauki rawa hawaye na zubarmishi yace" aisha ta Aisha kece kika koma haka?"
AISHA tana hawaye tace"kayafemin yaya mutuwa zanyi kayi hakuri da abunda na maka"
Yanata kyarma ya rike hannunta yana hawaye yace"kidena fadar haka na dade da yafemiki ,kuma bazaki mutu ba Aisha idan kika mutu ya zanyi da rayuwa ta ,zaki samu sauki zamu cigaba da rayuwarmu kamar can baya "
Ta girgiza kai tace"mutuwa zanyi yaya inaji ajikina mutuwa zanyi"
Faseelat ta kara volume na kukanta tana matukar jin tausayin aisha,
Fahad ma kuka yace"kidena fada inasonki aisha har yanzu ina sonki inason nakara rayuwa dake akaro na biyu"
Tai murmushi tana kallonshi yace"I still love u aisha nayi nayi be ciru ba ,I truly love u and I will always will"
[9/7, 8:03 PM] SHALELE😍: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
8⃣9⃣
*Dedicated to my daughter(anti Mamie)* writer of *naga ta kaina,ustaziyya ko yar duniya,and now namijin duniya*
*ina makaranta namijin duniya karki yarda 200 ta hanaki bin buk din dan yanzu yake dadi wlh ga tarin darussa just kibiya 200 ta wannan number 0816 652 6167 ,idan ta bank ne zakiiya tuntubarta don samun account number dinta ,namijin duniya yayi wlh karki bari abaki labari,ina fans dina ku garzaya wurin diyata kusha nata basiran💃🏻*
*akwai wani novel dinta guda daya daban fadi sunanshi ba her first novel duk wacce ta turomun sunan novel din zata samu damar karanta littafin namijin duniya kyauta, amma mutum ukku kacal keda wannan damar hurry up write the name and send it to my what's up number 07063721063,after kinturo zaki cigaba da samu for free ,senajiku, duk meson shalele yaso diyata anty mamie 😘*
Allah subhanahu wata'ala said :- kullu nafsin za'ikatul maut,wa nablukum bishsharri wal khairi fitna,wa ilaina tur'jaun.
(Anbiya'i 35)
Ankabut verse 57:-kullu nafsin za'ikatul maut,summa ilaina turja'un.
"And certainly we shall test you with something of fear ,hunger,loss of wealth,lives,and fruits,but give glad tidings to the patients one's. Bakara 155
" who when afflicted with calamity say truly to Allah we belong and truly to him we shall return.156
Hawaye suka zubomata ta lumshe ido tabude tace "thanks nagode yaya da duk soyayyar da kanunamin"
Ita kadai tasan pain datake going through,
Ta dan juya kai ta kalli faseelat dake tsaye tana ta kuka tana share hawaye da gyale,tace"faseelat nagode da soyayyar da kika nunamin nida amira ,inafatan zaki mana takwara don nima mutuwa zanyi"
Faseelat takara volume na kuka ta rufe fuska tanayi ,Aisha tai murmushin ciwo ta meda kallonta akan fahad ,tana ta kallonshi,
Yanata hawaye hannun ta still anashi yace"I love you Aisha u r part of my life"
Kallonshi take tayi bako kyaftawa,yanata hawaye ,
Lura yayi numfashinta ya dauke idanun basa motsi jikinta ya saki,
Nan take jijiyoyin kanshi suka firfito yakara damke hannunta ya duke jikinshi na kyarma agabanshi daddy ya rasu now Aisha bayan amira,kuka kezo mishi yasamu ya hadeshi,
Ya dago fuska ya juya yana kallon uwar yaya, tanata kuka da alamu batasan ta mutu ba,
Ya tashi jikin na rawa ya tsayar da jinin dake shiga jikinta ya juyar daita sannan ya rufe mata ido ya nufi wurin faseelat daketa kuka ya kamo hannunta batare da yace komi ba ,
Ta kalleshi ta kalli Aisha da aka meda kanta yana kallon bango ,takara kallonshi tashin hankali karara fuskarta ,
Dakyar yasamu Yace "mutafi in medaki gida"
Tace" ta mutu ko ?anty ta mutu"
Tai luuuu zata fadi ya tarbeta sede har ta suma ya ida zauniya kasa yasaki kukan dayake dannewa faseelat na jikinshi a sume ,
Jin kukan yayi yawa mommy ta shigo dakin ta ganshi rikeda faseelat yanata kuka,
Ta kalli gadon Aisha ta kuramai ido gabanta na faduwa taisa tana juyota taga babu rai jikinta ,hawaye masu zafi suka kara wanke mata fuska ,acikin ranta tace "ka kashemun diya son"
Ta zauna ta Dora Aisha jikinta tana kuka shikenan tayi bankwana daita shikenan ta tafi bazata kara dawowa ba,
Kukan Su momy yasa Su ramlat shigowa itada Su anty salma suka samu Aisha ta mutu dakin yakacame da kuka ,
Asibitin dake very silent takacame da sautin kuka nurses biyu suka shigo suka ga abinda ke faruwa sune suka kawo gado suka dora faseelat dake lifeless suka tafi ceto rayuwarta fahad ko nanan zaune yakasa tashi se kukan dayake kamar mace,
Mommy kam zuciyarta ciwo take sosai ,
Anty salma ce ta dauki Aisha datakoma sakwaf bayan sun rufeta suka fita daita ,dukkansu suka Mara mata baya basujira likitoci ba suka tafi abinsu ,
Faseelat kam suma tayi bayan sun samu ta farfado tanata kuka jinin ta ya hau sosai sukasa mata drip da allurai ciki dandanan bacci ya kwasheta ,
Fahad seda yakara shan kuka sannan yatashi yanjin jiri beko leka faseelat ba ya tafi gidan mommy akan hanya yakira wani yaronshi akawo likkafani ,sannan yakira sabeer ,
Sabeer na kitchen gimbiya fatouma tasashi aiki kiran fahad yashigo ya dauka yanata goge zufa yace"dude what's going on?".
Sheshshekan kukan fahad ta katseshi ,hankalinshi ya tashi yace"meya sameka aboki?"
Fahad na hawaye yace"I loss my Aisha ,Aisha ta tamutu "
Sabeer yace "innalillahi wainna ilaihi rajiun!!!!" Akidime saboda yaji mutuwar,
Murya sanyaye yace "kayi hakuri fahad Allah na jarabtar imanin ka yaga yadda zakayi kayi hakuri Allah yajikanta yakara maka hakuri na tausaya maka"
Fahad yace"thanks agidan mommy zaai janaiza "
Sabeer yace"I'm on my way yanzu"yakashe wayar yafita dasauri,
Fahad naisa dangin mommy sun cika gida angama hada ruwan wankanta yaje wurin mommy yace "mommy kubarni nai mata wanka kubari nai mata sutura plssss"yanata hawaye
Mommy tace"to kai zaka mata ,but plss kadena kukannan"
Yadaga kai ,yashiga dakinda Aisha take shiya mata wanka yanata hawaye aka kawo likkafani yasa mata yayi zaune wurin yanata kallon gawar,
Dandanan labarin mutuwar Aisha yabazu acikin garin dangin babanta dangin mommy Su Umma D's,bayan mutane suntaru aka kaita makwancinta ,
Kamar na amira kowa yatafi seshi da sabeer da yake taya amininshi hawaye ,
Yana zukunne yanata mata addua ganin de baze bar wurin ba yasa sabeer yadago shi suka nufi mota yanata waigen kabarin nata,
Jiri keta dibarshi dakaganshi kasan yana bukatar temako hakan yasa sabeer wucewa dashi asibity ,suna isa sabeer yace"plsss friend kayi hakuri kadauki kaddara karka bari wannan abun yayi affecting lpyarka ,I know kaga jarabawar mutuwa ,rashin daddy ,rashin amira and now Aisha amma duk da haka kayi hakuri yanzu zamushiga doctor ya dubaka "
Fahad dake dafe da zuciya yace"before that inason ganin faseelat bata lpy ta suma kuma she's alone"
Sabeer ya zaro ido jin wata kuma ya meda damuwar yace"don't worry zata samu lpy "
Fahad ya daga kai suka fita sabeer rike dashi suka shiga,
Office din okato sukafara zuwa yadubashi jinin shi yahau sosai kuma ga zuciyarshi dake ciwo to shima yana bukatar bedrest ,
Fahad yace"where is my wife?"
Doctor yace"don't worry shock data samu yasa tai loosing breath dinta sede itama she have similar problem da naka domin jininta yahau amma she will be okay"
doctor yasa aka kaisu dakinta tanata bacci tana sauke numfashi ahankali,
Hawaye suka cikawa fahad ido suka gangaro ,
Ya karasa bakin gadon shiko sabeer na bakin kofa yana kallonta,
Fahad ya duke jikin gadon yafashe da kuka,
Yana kuka yake cewa"they all gone suntafi sun barmu"
Hannunta yafara motsi da alamu tanason tashi ,
Sabeer yayi sauri ya rikeshi yace "plsss stop this crying karka tadata she need to rest mutafi they're waiting for you"
Yajashi suka fita dakyar suka samu ya kwanta akasa mishi ruwan amma idonshi ko rufewa beba,
Se lokacin yayi wa sabeer magana yakira Abba yafada mishi faseelat na asibity suka kamo hanya ,
Ummi na zuwa ta zauna gefen gadon faseelat arude tanata dubata ,
Ya omer da Abba na gefe ,
Faseelat din duk tafita hayyacinta,
Kukan Ummi ya tada faseelat ta farko tanata hawaye tana kallon ummi tace"Ummi anty ta mutu tatafi kamar amira"
Ummi tace "kiyi hakuri Allah yajikanta,ki daure karki sawa kanki ciwo"
Taita rarrashinta ,
Fahad na kwance drip nashiga sabeer na gefe yanata kara masa waaxi,
A can gidan mommy Umma nacan tuntuni sede mommy takara hawa da akace mata fahad bayagun karbar gaisuwa ,cikin ranta tace"yana wurin matarshi itada yakeso ta rayu son bemin adalci ba bemin koda rabin abinda na masa na alheri ba ,"itama seda jinin ta ya hau seda aka kira mata doctor,
Se marece aka cirewa fahad drip yatashi yayi salloli sannan suka nufi dakin da faseelat take,
Ummi na zaune beko kula daita ba yaje ya zukuna gefen gadon ya kamo hannun faseelat da har lokacin take kwance ,dukkansu suna hawaye faseelat tace"hero bata mutu ba ko?Dan Allah kace bata mutu ba"Se kuka ,
Yana kuka yace"she's died Aisha tana makwancinta "
Tana ta kuka tace"nata baka hakuri nata fada maka bata lpy kamata hakuri mutuwa zatai inbabu kai amma bakaji ba"
Yana kuka yace"I'm sorry nakasa manta abinda tamin ne ,kuma I don't know halinda take ciki wlh danasani da na medata tuntuni"sunata kuka,
Ummi da sabeer sunata kallonsu basu fahimci komi ba ,
Ganin kukan bana karewa bane yasa sabeer janshi suka fita gidan Umma yawuce dashi time din ta dawo ,shi kuma ya wuce gida yanata tunanin abunda yafaru,
Fahad nata ma Umma kuka tanata hawaye itama tana bashi hakuri dakyar ta samu kanshi ta debo abinci tafara bashi spoon daya kawai yayi ya dauke kai,
Yananan wurinta se Maghreb ya fita yaje masallaci yayi salla yawuce gidan mommy,
Dakin mommy yawuce direct ya samu anty salma nata mata fifit dukda AC dake dakin zufa take tayi,
Yaje ya zukunna gabanta yana kuka yace"mommy Dan Allah kiyafemin ,wlh bansan halinda Aisha take ciki ba what I only know is halinda nake ciki kiyi hakuri wlh name data dakinta kafin ta mutu"
Mommy dataci kuka tai hamdala idonta lumshe tace"son bakai ka kashe Aisha ba ciwo ne ya kasheta katashi kabar bani hakuri "
Yace"mommy inajin nine silar mutuwarta Dan Allah kuyi hakuri"
Mommy tace"to nayi hakurin amma dama bakai komi ba ,katashi katafi masjid ga kiran salla can"
Yace"thanks mommy " yatashi ya fita ,
Anty salma tabishi da harara tace"wai anty kinsan me kk cewa?"
Mommy tace "nasani mana kibar maganar yanzu Allah de yabani lpy"
Anty salma tace"to amin"
Saudat tazo daga abuja koda taga wucewar fahad da harara tabishi don duk gani suke shiya kasheta,
Acan Egypt Su lady duk gobe zasu sauka Nigeria suda mazansu,
Haka Su khadija dake sudan ,
Bayan isha'i yakoma asibiti ya samu anata daru da faseelat takicin komi yaje kusa daita ya zauna yace"meyasa bazaki ci abinci ba?kinaso babies Su samu matsal? Dan Allah ki tausayamun faseelat yanzu idan wani Abu ya sameku bansan yadda zanyi da rayuwata ba"
Ta share hawayen da suka gangaro mata tace "I will eat"
Ya amshi abincin yafara bata tanaci tana ajiyar zuciya,
Ummi de fita tai tabasu wuri, aranta tana da niyyar da an sallamesu suwuce gida da ita se ta haihu sannan ,don kullum kara zubewa takeyi ,
My condolences to Aisha fans Allah yasa maku hakurin rashinta,
[9/8, 2:59 PM] SHALELE😍: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
9⃣0⃣
*Manzon Allah (S.A.W)yace bawata musiba da zata samu musulmi face Allah ya gafarta masa zunubansa koda kayace daya taka*
*Naji dadi ga masoya da sukamin fatan alheri ,adua da jinjina nagode sosai Allah yabar kauna .*
Bataci sosai ba yazo ze bata ta rike mai hannu so daya ya kalleta ya dauke kai takura mai ido duk yayi wani kala ta kyafkyafta ido tameda hawayen da suka zo mata murya dishe tace "kaci abinci kuwa?"
Yayi shiru be kalleta ba kanshi kasa ,
Tanajin matukar tausayinshi tace"plsss kaci abinci banaso wani abu ya sameka"
Dakyar yace"bazan iyaba I gone through a lot of pain ,faseelat kode naiwa Allah wani laifi yake jarabta ta?"
Hawaye suka gangaro mata tace "kodaya Allah yakan jarabci mutum idan yanason sa don ya kankare masa zunubansa "
yafashe da kuka ,
Ta rike kanshi tana sharemai hawaye tace"kayi hakuri nasan akwai ciwo amma kadena kuka kadena sa wani abu aranka,kasawa ranka dangana Allah zebaka ladar"
Ta cigaba da share mai hawaye ,yayi shiru zuciyarshi na zafi ,ya kalli katon cikinta yadora hannu akai yaji yana motsi ahankali
Ya kalleta yace"basa movement sosai ,kinajin wani abu?"
Tace"a,a maybe kodan mommynsu ta rasu ne "
Ya dauke hannu sukayi shiru sunata tunani tunawa yayi da Ummi yatashi tsaye yace"natafi gida seda safe ki kula da kanki kiyi bacci"
Tanata kallonshi ta daga mishi kai kurum ,yajuya ya fita,
Hawaye suka kara gangaro mata ta rasa yadda zatayi amma jitake ita takashe Aisha mutuwar amira tayi kukan sabone, wannan kuma tanajin kamar itace ta aikata ,
Ummi ta dawo dakin taga tana kuka ta zauna gefenta tace"nide da nice ke da bazan zauna inata mata kuka ba addua zantayi mata don ita tafi bukata "
Faseelat tace"Ummi dole nai kuka ina tuna yadda anty ta nunamun so nikuma nai mata butulci na auri mijinta har hakan yazama sanadiyyar faruwar abubuwa da dama Ummi nayi danasani "
Ummi tace"to ai sekiyi ki zauna kita surutai marar maana dan ubanki time dinnan ba har seda na nuna banason abun ba kika nace kika haukace seshi,rabone ke tsakaninku gakinan da yan hudu danhaka seki roki Allah gafara kita rokar mata rahma zataji dadin saninki a rayuwa"
Faseelat tace"insha Allah Ummi ,anty tana cikin jindadi a lahira domin ta tuba kuma tayi nadamar abinda tayi baya tayi umara tayi hajj "
Ummi tana ta kallonta tace"wai me tayi ne ?dama sun rabune dashi kafin mutuwar ta?"
Faseelat ta girgiza kai tace"a,a kawai de kuraren rayuwa,Kikamani Ummi zanje toilet nayo alwala"
Ummi ta kamata ta kaita zukunniya dakyar tashi dakyar haka abun yake tagama suka fito ta kabbara salla daga zaune tanata nafilfili tana dadewa cikin addua tana fadawa Allah bukatun ta,
Ummi tun tana gyangyadi har ta kishingida a gadon bacci ya kwasheta,
Fahad yana isa gida ya sheme kan kujera a falo yanata tunani ,yanzu Aisha nacan cikin kabari amma yana mata kyakkyawan zato,
Ya dade kwance sannan ya tashi ya shiga bedroom yayi alwala yafara salloli ,can kusan asuba bacci ya dauke shi kunsan shedan ya tsani sallar asuba acikin salloli ita tafiwa mutane wuya dan da lokacin yayi sekaji lokacin kakejin dadin baccin,Allah kakaremu daga sharrin shi,
Se can ya farka anata kabbarori alamun antada salla yatashi