Follow us on social media
Showing 39001 words to 42000 words out of 73194 words
dan kam munada tabbacin d'an mu ba mahaukaci bane to amma ayanzu gashi zaka tambatar maduniya cewa Kai mahaukacin ne sabida idan wannan Sha Sha shan tunanin naka yafita to tabbas duniya zata tabbatar cewa d'ana Saraki wanda nafiso duk duniya qwaya d'aya tilo mahaukaci ne shi idan ku hakan ta tabbata to tabbas baqincikine zai kasheni nida Abbeen ka "
Fashewa da kuka Ammin tayi ganin haka yasa Maher saurin miqewa ya rungumai ta cikin Matu'kar razana daganin kukan Ammin shi shima kukan yasaki yace " Ammin wallahi nayarda cikin jikin Iftahal nawane Ammin Allah na gasgata hakan " tureshi Ammin tayi daga cikinta tace " qarya kakeyi Saraki bazan yarda dakaiba sabida yanzu ka koyi qarya zansaka doctor tayi gwaji idan har aka tabbatar cewa wannan cikin nakane to kasani zan juya bayana dakai har abada dukda son danikeyi maka sabida ayanzu nasan zaka amince ne sabida ganin fushina dakayi badan ka amince dagaske cewa cikin naka bane Saraki tabbas kana cutarmin da yarinya duba agogo kafita tun safe Kuma kasan batada lafiya amma se yanzu kake dawowa "
Sosai Maher yasaki kuka ya durqushe gaban Ammin yace " wallahi Ammin har cikin zuciyata nayarda cewa babyn jikin Iftiih!!! nawane kuma daga yau nayi miki alqawarin cewa zan kuka da Iftiih!!!! da babyn kamar yadda zan kula da kaina amma bazan boye mikiba Ammin har yanzu banajin son Iftiih!!!!! Cikin zuciya ta sede Ina matuqar tausayinta sabida yadda iyayenta sukayi fushi da ita sannan ayanzu naji son babyn tamkar rai na Ammin " d'an murmushi Ammin tayi cikin zuciyar ta tace " tabbas zakaso Iftahal Soma Mai tsanani amma afili cewa tayi " idan har kanaso nayarda da gaskiya kake fad'i to kaje kabama Iftahal kaquri kuma naga farinciki da kwanciyar hankali atare da ita kafin nabar USA sannan inaso naga tsananin qaunar babyn cikin idanunka da zuciyar ka idan kuma bahakaba ni kad'e nasan matakin dazan d'auka akanka tashi gabani guri
Fatan alkairi gareku baki d'aya semun had'u ranar Saturday muji shin Maher zai iya bama Iftahal haqurin wane irin salo zai d'auka wajan sata farinciki kamar yadda Ammin tace to Allah yasadamu da dukkan alkairin shi yayi mata jagora akan dukkan lamarin mu Ameen ๐คฒ๐ป
Comments please
_Marmyn Zarah Ce_ ๐๐ป๐๐ฅฐ
๐ก *!!!FURUCI!!!* ๐ก
๐๐๐
๐
*((((( Murd'add'iyar Soyayya)))))* ๐โฃ๐
Story and written
BY
NPEEDY A AJI ๐ธmarmny Zarah๐ธ
Dedicated
To
My lovely
*Ummi*
And
Lovely
Daughter
*Zarah*
KAFAD'I ALKAIRI KO KAYI SHIRU ๐คซ
My Novels
1 NAYI RAYUWA DAKE
2 SANADIN ACCIDENT 2019
3 SAKAYYAR CUTA
4 RUFAFFIYAR ZUCIYA
5 HAYATUL MAHAYAT
6 MUGUN SARTSE
Loading....... ๐๐
๐ก๐ FURUCI!!!!!๐๐ก
BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM
Ina masoyana ha'ki'ka iname baku ha'kuri akan abinda zakuji yanzu ada banida niyyar yin hakan yanzuma wani daliline yasa hakan Allah yasa zakufahimceni wannan book d'in nakud'i ne 200 kacal nasan nafi karfinta agareku ko kyauta zakuiya bani
ZAKUTURO NAIRA 'DARI BIYU KACAL TA ACCOUNT NUMBER NAN FIDDAUSI ISHAQ
0005556335
JAIZ BANK
IDAN AN TURA A YIMIN SCREENSHOT DIN TRANSACTION DIN KO KUMA KATIN 'DARI BIYU NA MTN WHATSAPP NUMBER NA
08135419440 akwai saban group wanda zansaka duk wanda yabiya in sha Allah typing kullum amma banda ranar Friday
DUK WANDA YAFITAR MIN DA BOOK TOFA SHIDA ALLAH NASAKE FADA SHIDA ALLAH
INA GODIYA A GAREKU MASOYANA ALLAH YABAR ZUMUNCI DA SOYAYYA NPEEDY A AJI TAKUCE HAR ABADA
๐
ฟ 37 to 38
Tashi Maher yayi cikin sanyin jiki yashiga bedroom binshi da kallo Ammi tayi cikin zuciyar ta tace " tabbas naga canji atare da Kai Saraki lalle zuwan Iftahal yazama alkairi agareka " juyawa tayi tafita tanajin dad'in yadda Maher ya tabbatar mata cewa ya amshi cikin tana fita parlour tazauna tadubi Akeey Zaffar kafin tayi magana yamiqa mata wayar ta yace " Abbee ne yakira Ammin ashe doctor ne yayi kusan ajalin Gimbiya kay amman fa abin yabani mamaki yadda Abbee yayarda da doctor ashe maci amana ne to yanzu gashi yamutu abanza Kuma Allah inada tabbacin cewa wanda yasashi aykin shine yayi ajalinshi dan Kar asirin shi yatonu ayni wallahi Ammin dan bana nan ne lokacin da aka d'auki doctor darman akan matsalar Saraki dabazan bariba sabida nima zan iya dubashi kuma in sha Allah yasamu lafiya yazama dole aqara saka tsaro akan Saraki da Iftahal sabida inada tabbacin akwai wata aqasa basuyi niyyar kashe Saraki ayanzu ba tabbas sun lura cewa gimbiya zata zamar musu barazana ne akan Saraki shi yasa sukeson kaudata yazama dole agano duk wanda yakeda saka hannu cikin wannan lamarin "
Ajiyar zuciya Mai qarfi Ammin tasauke tadubi Iftahal cikin tashin hankali tace
" Gayamin duk yadda abin yafaru ? " babu musu Iftahal tayi mata bayanin komi hadda allurar data hana doctor yayi mishi batare dasanin shiba da duk maganar dataji doctor yanayi a waya sannan tad'aura dacewa tun daga wannan lokacin duk abinda Prince zaici ko yasha sena had'ashi da ruwan addu'a tashi tsaye Ammin tayi cikin matuqar tashin hankali tace " ya Allah suwaye suke neman halakamin yara ? lalle yazama dole agano kosuwaye " itako aunty Bahijjat kuka takamayi sabida tsananin tausayin Maher da Iftahal jawo Iftahal tayi tarungume ta tace
" Tabbas ke alkairi ce agun Sarakin mu kin cancanci yabo kuma in Sha Allah babu wanda zai iya rabaku kuna tare har qarshen rayuwa in Sha Allah sekin mahaifa mana yara masu yawa " tsayin lokaci suna ahaka sannan Iftahal tamiqe abincin Maher tad'auka tanufi saman shi shiko Maher bayan fitar Ammin dayashiga bedroom zama yayi bakin bed yazuba tagumi yana tunanin yadda zai iya bama Iftahal haqurin tabbas ayanzu ya gamsu dacewa cikin Iftahal nashine amma shikuma bayason haihuwa yanzu sabida gani yakeyi takurashi yaran zasuyi cikin wannan tunanin yatashi yashiga toilet yayo wanka yafito d'aure da towel dede lokacin Iftahal tashigo kallo d'aya tayi mishi tayi saurin kauda kai sabida yadda surar jikin shi take a bayyane sosai tayi fad'uwar gaba saurin aje tiran tayi tajuya kafin takai bakin qofar taji muryar shi cikin kasala yace
" Iftiih!!!! " tsayawa tayi amma takasa juyowa shiko kallon bayanta yayi cikin zuciyar shi yace " hmmm wai tana nufin kunyata takeji bayan tariga tagama ganin komi nawa gaskiya girmana yagama zubaiwa " sake kallonta yayi sannan yace " Ina zaki ? " Parlour zankoma idan kagama kintsawa senadawo " Iftahal tafad'i hakan cikin sharqewar murya " d'an jim Maher yayi sannan yace " dawo kizauna " dawowa Iftahal tayi Amma idanunta suna qasa cigaba da kintsawa yayi bayan yagama shafa mai da turarukan jiki singilet da bonshok yasaka sannan yagayra sumar kanshi takowa yayi zuwa bakin bed inda Iftahal take zaune d'an dubanta yayi yadda tawani takure sassanyar ajiyar zuciya yasauke sannan yazauna tsayin lokaci amma yakasa cemata komi miqewa Iftahal tayi cikin in ina tace " bari naje ? " tana fad'in haka tajuya
Babu zato taji yajawota tafad'a saman cinyar shi hannuwanshi yasa yad'an rungumota cikin natsastsiyar muryar shi yace " Iftiih!!!! kiyi haquri abisa rashin fahimtar ki danayi akan babyn dake cikin ki tabbas ayanzu nasan ban kauta mikiba kiyi haquri " shiru yasakeyi nawani lokaci itako Iftahal dad'i yasa takasa furta koda kalma 1 zuwa can yasake cewa
" Ayanzu na tabbatar wannan babyn " yashafa cikinta sannan yacigaba dacewa " nine uban shi kuma Ina matuqar son shi " jin haka yasa Iftahal saurin juyowa wata irin runguma tayi mishi wani irin yanayi Maher yaji yaziyarceshi saurin tureta yayi daga jikin shi yawani tamke fuska bubanshi Iftahal tayi tasakar mai murmushi tamke fuska yasakeyi hafin ta yunqura cikinta yasake murd'awa riqe cikin Iftahal tayi tace wassssss Allah cikina Prince saurin yin kanta yayi
sosai yake gudu da motar har seda yagujema wa'inda suke binshi sannan yashakwanar hakun shi daga gurin babu hanya se wani makeken ruwa Mai zurfi fitowa yayi yakira waya bayan an d'aga yace
" Oga angama doctor darman yamutu sede wani bashiba kaga kenan babu yadda za'ayi aganoka suma duk iya binciken su bazasu ganoba domin kuwa ayanzu zanjefa motar cikin ruwa sannan nabar duk inda CCTV camera take " dariya yasaki sannan yace angama daga haka yakashe wayar tura motar yayi cikin wannan ruwan sannan yabar gurin wata hanyar yabi ba wadda yabiyoba
Egypt
Wata irin dariya Alhaji Tukur yasaki sannan yazauna yace " ni akwai wanda ya isa yagano shirina ay wallahi duk wanda naga ze'batamin shiri ko asirina zetonu sanad'in shi to wallahi sena kawar dashi " sake bushewa da dariya yayi dede lokacin babban d'an shi yashigo zama yayi kusada shi cikin damuwa yace " dady gaskiya inada matsala yakamata ace nayi aure amma duk yarinyar danaje gurinta idan har ubanta zai ganni seyacemin Allah yakiyaye yabani yarshi uban nawa dababu wanda yasan silar dukiyar shi Wai katara maqudan kud'i amma babu wanda yasan asalin kasuwancin ka gaskiya dady yakamata nasan silar wannan dukiyar taka konasamu amsar bayarwa " wata irin tsawa Alhaji Tukur yasakar mishi
" Kai Son lalle ka Isa wato nine yau kakeson yima titsiye lalle ka Isa tashi kabani guri idan kasake yimin irin wannan banzar tambayar wallahi se ranka ya'baci company nawa gareni supermarket nawa shaguna nawa amma shine har za'acemin wane irin kasuwancin nikeyi sannan Ina ruwan jama'a da asalin dukiyata ? " bayan fitar yaron Alhaji Tukur yami'ke cikin fusata yace " lalle yazama dole nacanza takuna "
Cikin masarautar Sarki Zaid
Gagarumin biki aka shirya na murnar samun cikin Iftahal hjy Himla tsaye cikin parlour ta gefanta qawartace cikin tashin hankali tace " lalle kuwa akwai matsala matar Saraki da ciki lalle Babu shakka yafara samun lafiya yazama dole cikin nan yazube dan Kam idan har tahaihu akwai matsala Hajiya Niyat kiduba kigani labarin cikin kawai akema wannan bikin inaga haihuwa ? "
Ta'be baki hjy Niyat tayi tace " hmmm ay wallahi ni wartarki nagani danice datuni Saraki yabar duniya to tsaya nabaki shawara kinga tunda bakida aure zuwa wani waje ki zauna bazai Zama matsalaba abinda zakiyi kije kisamu mama ki marayrayce kice Mata mama Kinga tunda matar Saraki cikine da ita Kuma kinsan halin yaro to zaki kizauna har ta haihu idan tahaihu seki dawo Kinga kenan zakisamu damar zubda cikin sannan kikashe Saraki cikin sauqi "
Wata irin shewa hjy Himla tasaki tace " tabbas wannan shawara taki tayi Kuma Kinga inada tabbacin mama zata amince idan kuwa mama ta yarda shikenan amma babbar damuwar tawa itace Saraki dan gaskiya bama shiri dashi nasan idan har mama zata nemi shawarar shi to tabbas zece a a " tsaki hjy Niyat tayi tasake cewa " amma kuwa kinbani mamaki to wallahi kisan duk yadda zakiyi kiga cewar kinje USA idan Kuma bahakaba to ki tabbatar kamar Saraki yayi mulkin wannan masarautar ne kinga kuwa idan har yahau wannan kujerar toku ku tasubuce muku kenan tunda gashi har yasamu magaji tun kafin yahau kan kujerar sarautar "
Jinjina Kai hjy Himla tayi tace " ayko bazai yiyuwa "
Nigeria
Juyawa Shukura tayi cikin matu'kar 'bacin rai tana shigowa parlour tanufi bedroom d'in ta fad'awa tayi saman bed tasaki kuka Mai tsuma zuciya dede lokacin Ummi tashiga cikin bedroom d'in zama tayi bakin bed tadubi Aunty Shukura tace
Kuyi ha'kuri da wannan Ina busy ne yau haka gobema shiyasa ma banyi typing d'in safeba muna hidimar walimar sauka ne gobema nadare zaku samu zuwa jibi in Sha Allah zaku samu posting 2 nagode sosai
Comments please
_Marmyn Zaray Ce_ ๐๐๐ป๐ฅฐ๐ก *!!!FURUCI!!!* ๐ก
๐๐๐
๐
*((((( Murd'add'iyar Soyayya)))))* ๐โฃ๐
Story and written
BY
NPEEDY A AJI ๐ธmarmny Zarah๐ธ
Dedicated
To
My lovely
*Ummi*
And
Lovely
Daughter
*Zarah*
KAFAD'I ALKAIRI KO KAYI SHIRU ๐คซ
My Novels
1 NAYI RAYUWA DAKE
2 SANADIN ACCIDENT 2019
3 SAKAYYAR CUTA
4 RUFAFFIYAR ZUCIYA
5 HAYATUL MAHAYAT
6 MUGUN SARTSE
Loading....... ๐๐
๐ก๐ FURUCI!!!!!๐๐ก
BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM
ZAKUTURO NAIRA 'DARI BIYU KACAL TA ACCOUNT NUMBER NAN FIDDAUSI ISHAQ
0005556335
JAIZ BANK
IDAN AN TURA A YIMIN SCREENSHOT DIN TRANSACTION DIN KO KUMA KATIN 'DARI BIYU NA MTN WHATSAPP NUMBER NA
08135419440 akwai saban group wanda zansaka duk wanda yabiya in sha Allah typing kullum amma banda ranar Friday
DUK WANDA YAFITAR MIN DA BOOK TOFA SHIDA ALLAH NASAKE FADA SHIDA ALLAH
INA GODIYA A GAREKU MASOYANA ALLAH YABAR ZUMUNCI DA SOYAYYA NPEEDY A AJI TAKUCE HAR ABADA
๐
ฟ 39 to 40
" Haba Shukura yafakamata kisan cewa Allah shike tsarama dukkan wani bawanshi rayuwa kuma bai Isa ya canzaba dan haka kid'auka wannan itace kaddarar ki sannan kisani Allah yasa Zayyat shine mijin ki Kuma babu canji sabida yazama dole ki d'auki haquri zuwa jibi iyanzu kinzama matar Zayyat dan haka garama kibar wannan kukan " tashi Ummi tayi tafita itako Shukura kamar anqara izata cigaba da kukan tayi sosai tana sake tunanin yadda zata zauna da Zayyat matsayin miji shigowar qawarta yasata d'an sassauta kukan tashi tayi zaune cikin damuwa qawar tata tadubeta tace " haba Shukura karfa kijama kanki wani ciwon yakamaki abinda kikasan babu makawa to yafazama dole kiyi haquri dashi yanzu Kinga gashi har baqi 'yan biki sunfara cika gidan ku amma ke babu abinda Kika farashiryawa to ay gasu Aysha nan zuwa idan sunzo Kinga yazama dole kitashi muje wajan gyaran jiki " tashi Shukura tayi tsaye tace " wa zanyima gyaran jiki wancan yaro ? Allah yasauwa'ke aykinga yadda kika ganni haka to ahaka zanzauna Babu maganar wani gyra irin na Amarya dan Kam ni bana d'aukar wannan auran matsayin aure na har yanzu inaganin qaddarar zata sauya sabiba banaji ajikina cewa wannan qaddara tace " ajiyar zuciya Aminta tasauke tace " to ayko yakamata kisama ranki cewa wannan itace kaddarar taki kuma babu makawa dan haka kitashi muje ayi abinda yakamata kokuma wallahi naje nasamu Abba nasanar dashi "
Jin hakan yasa Aunty Shukura saurin miqewa Sabida tana matuqar tsoran Abban ahaka cikin rashin so Aunty Shukura tabari akayimata komi na Amarya amma cikin zuciyar ta baqinciki ne cike kasancewar auran mutu 2 ne yasa hidima takacame kamar mai baqi daga nesa duk sun halla sosai ake hidima kud'i kuwa ankashe su tamkar paper safiyar ranar asabar aka d'aura auran Ibrahim Ishaq da Fadila Musa se auran Zayyat Aminu da Shukura Ishaq shikenan Allah yariga yayi hukuncin shi jin labarin an d'aura auran yasa Aunty Shukura shiga cikin mawuyacin hali jitakeyi kamar zata mutu a'bangaran ango kuwa shima yashiga cikin damuwa wane irin zama zasuyi shi kawai yake tunani daqar akasamu Aunty Shukura tafito wajan yin hotuna
d'an dubanta yayi seda gabanshi yafad'i sabida wani irin kwarjini datayimai cikin qasada murya yace " kinyi kyau sosai " wani irin kallo tayi mai shiko murmushi yasakar mata yasake cewa " haba Uktee karfa mutane sugane cewa bakison wannan auran haba kisaki ranki Mana " wani banzan kallon tasakeyi mai d'an kauda kanshi yayi yajawota jikin shi nakuwa jama'a suka d'auki tafi shiko Mai hoto yafara d'aukarsu ahaka idan ran Aunty Shukura yayi dubu seda ya'baci a wannan lokacin hakan yasa ba'a gama yin pictures d'in ba tabar gurin misalin 6pm aka Kai amare katafaran gidansu wanda Abba yaginamusu musamman a cikin unguwar su part 3 ne na Yaya Ibrahim yana kallon na Zayyat se d'ayan dake kallo su ko wanne yayi matuqar had'uwa a part d'in yaya Ibrahim shida abokan shine dakuma qawayen amarya itako Amarya tana saman cushion zaune fuskarta rufe da mayafi tashi tsaye Yaya Ibrahim yayi yace " to abokai Ina godiya Sosai agareku inayima kowa fatan Isa gida lfy to kunga dare yafarayi yanzu 8:40 yakamata narakaku ko kukuma qawayen amarya su Yunus zasu saukeku " tasomai sukayi da tsaya suna fad'in ko bakaceba yanzu zamu tafi dad'in abin muma munada matan mu qawayen amarya sune dajin haushi sabida sukam idan Abba da Momyn su zasu nufa muko gidan mu zamu " dariya qawayen amarya suka saki sukace dad'in abin ay muma manu lokacin Yana nan zuwa " daga haka sukamiqe Sallam sukayi musu kowa yatafi bayan fitar su