Follow us on social media
Showing 42001 words to 45000 words out of 50786 words
gida yana tunanin hanyar da zai bi ya shawo kan Samha ta so shi gashi bashida lambar wayarta ballantana ya ringa communicating da ita ko ya samu ta saurare shi
Aranar Akram kwana yayi yana addu'ar Allah ya mallaka mishi Samha amatsayin matar Aurensa indai Alheri ce agare shi idan kuma ba Alheri bace a gare shi Allah ya cire mishi Santa a zuciyarsa
B'angarensu Samha kuwa bayan sallar ishai Suhaima ta zubo musu abinci a faranti suna ci har da Alhaji Nazifi dan tunda Hajiya Nafeesa ta rasu ya maye gurbinta suke cin abinci tare
Alhaji Nazifi kallon Samha yayi dake ta juya cokali tana cakalar abincin haka ta koma shiru shiru tunda Akram yace yana Santa tunani yayi watak'ila sabida K'in da takewa Akram ta koma haka
Murmushi yayi yace "Baby meyesa bakya cin abincin?
Samha d'agowa tayi tana murmushin yak'e tace " Babu komai daddy"
Girgiza kai Alhaji Nazifi yayi still da murmushi a fuskarsa yace "Baby kenan ai nasan meye yake damunki tunda yaron nan yace yana sanki kika bi kika takura kanki kina tunanin zan tilasta miki ki so shi to ki kwantar da hankalinki bazan miki dole ba yau yaron yazo ya sameni nace ya hakura dake zan bashi Suhaima ko Saheeba dan nasan su bazasu k'i shi ba"
Alhaji Nazifi da zai lura da ya hango tsantsar tashin hankalin dake kwance a saman fuskar Samha da ya jiyo irin bugu da tsallen da zuciyarta yake yi kamar ya fad'o k'asa
Alhaji Nazifi kuwa bai lura da halin da take ciki ba ya maida kallonsa kan su Suhaima dake cin abincin su hankalinsu kwance da alama basu damu ma da maganar da Alhaji Nazifi ya fad'a ba hasali ma kowace a cikinsu fata take ace Akram ita ya zab'a dan duk wace ta amsa sunanta mace mai aji da kyau bata da burin da ya wuce ace Akram ya zamo mallakinta
Alhaji Nazifi cewa yayi "Suhaima Saheeba nagayawa Akram ya zabi d'aya a cikinku tunda 'yar uwarku bata San shi kunga kuma babu yanda za'ayi na tilasta mata dafatan duk wacce ya zab'a a cikinku bazata watsa min k'asa a ido ba"
Murmushi kawai sukayi suka sunkuyar da kai alamar dukansu sun amince
Alhaji Nazifi kuwa murmushin jin dadi yayi dan yasan mai murmushinsu ke nufi
Samha kuwa wani irin jiri ta ringa ji yana Neman kayar da ita sabida tashin hankali murmushin data hango kwance a saman fuskar su Suhaima ba k'aramin d'aga mata hankali yayi ba
Babu Wanda ya lura da halin da take ciki har suka kamalla cin abincinsu suka mik'e dan dama idan suna cin abinci itace take tashi a karshe
A daddafe ta mik'e ta kai farantin kitchen ta wuce d'aki tana zuwa ta zube a k'asa wani zazzafan zazzabi ya rufeta atakaice aranar da mugun zazzabi ta kwana da mafarkan Akram
Suhaima da Saheeba ganin Asuba tayi bata tashi dan tayi sallahr asuba ba yasa suka nufi kan gadonta dan su tasheta
Sallati sukayi gabad'aya da suka ga halin da take ciki a rude suka d'agata suna tab'a jikinta dake tururin zafi
atakaice sai da Samha tayi kwana uku a asibiti kafin a sallameta tabi ta rame sabida tunanin Akram haka kawai take jin haushinsu Suhaima
Alhaji Nazifi kuwa sai lallab'ata yake yi shi da su Suhaima abunka da yar Auta
Bayan kwana biyu da aka sallamota daddare wajen k'arfe biyu tana kwance tana tunanin Akram sai juyi take sirarran hawayen nadama na bin kuncinta sai yanzu take data sani k'in amincewa Akram sai yanzu take data sani data d'orawa kanta girman kai tak'i k'arbar soyayyar Akram yanzu gashi Akram ya hakura da ita zai zabi d'aya daga cikin 'ya'yyenta ya Aura
Juyawa tayi ta kalli su Suhaima dake baccinsu peacefully duk abinda take yi Saheeba na kallonta dan juyawa tayi da zumar gyara kwanciyarta ta hango samha na Jan majina tana sharar k'walla mamaki ne ya rufeta tayi kamar bacci take yi
Samha kuwa durowa tayi daga kan gadon ta nufi Palo dan ta sha kukanta ta gode Allah
Tana ficewa Saheeba tayi sadaf sadaf tabi bayanta
A 3 seater Samha ta kwanta ta bud'e wayarta ta shiga Zgallery ta bud'o hotunan Akram tana kallo tana shafa kan wayarta hawaye sai zubowa suke a idonta
Saheeba dake jikin labule ta d'an bud'e dan ta ringa hango abinda Samha ke yi mamakine ya k'ara rufeta data hango tana kuka tana shafa hotunan Akram
Samha kuwa magana ta fara yi ahankali Saheeba ta k'asa kunnenta dan ta jiyo ta
"Ina San ka Akram ina Kaunarka Girman kai da taurin zuciya zai sa na rasa ka bansan yanda zanyi rayuwa babu kai ba ina kunyar na koma wajen Daddy ince inasanka yanzu ya zanyi Akram"?
Kuka take sosai har da sheshek'a
Saheeba kuwa ahankali tayi baya ta koma d'akinsu jikinta a sanyaye bata tsaya b'ata lokaci ba ta tashi Suhaima ta rik'e hannyenta sukayi wajen palon suka kuma lab'ewa
Samha kuwa surutanta take ita kad'ai tana shafa screen d'in wayarta sai da suka ji duk abinda take cewa a k'arshe ta rungume wayarta a kirjinta tana sauke ajiyar zuciya
Suhaima tsaki tayi lokacin da suka koma ciki tacewa Saheeba "Kece fa baki sani ba wlh na dade da sanin tana San sa tsabar munafirce da taurin zuciya yasa ta Dage bata San shi aikuwa sai na wanata na wajigata zan gayawa Daddy gaskiyar tana San shi ni gobe ma hirarsa zan tayi zance ina sansa sai zuciyarta ta kusa bindiga zan kyalleta"
Murmushi Saheeba tayi tace "kai Aunty Suhaima Auta ce fa"
Tsaki Suhaima ta k'arayi tace "Autar fa dalla jekiyi kwanciyarki Ashe shiyasa ta ringa ma rashin lafiya takaicina ma Daddy yaringa lallab'ata akan ta so Akram Ashe ta dade tana sansa"
Takun da suka jiyo ne ya sa suka hau gadonsu da sauri suka rufe ido kamar masu bacci
Samha kuwa sai da ta lelek'a fuskarsu taga bacci suke ta hau kan gadonta ta kwanta ta na sauke ajiyar zuciya sabida kukan da tayi........
[8:15PM, 4/22/2018] +234 813 272 6929: 🌑 🌑 *B🅰K'IN D🅰RE*🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑
*Written by*
💅💅 *Sadnaf*💅💅
*A heart touching story*
® *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛ'Ş_
#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com
*Follow me on Wattpad@Sadnaf*
*Page 20*
*FINALE*
B'angaren Akram kuwa yana ta tunanin yanda zai fuskanci Alhaji Nazifi yace mishi babu wacce tayi mishi a cikinsu so d'aya tak Samha yake yiwa Yazeed babu yanda bai yi dashi ba akan ya hakura da Samha yace Sam idan ba Aure ko mutuwa tayi ba babu abinda zai sa ya hakura da ita dan duk addu'oi da istahara da yake yi akan Allah ya mishi zabin da yafi Alheri Samha yake gani a matsayin matarsa kuma yana ji a jikinsa Samha matarsa ce ahaka dai ya d'aure akan zaije ya samu Alhaji Nazifi ya gaya mishi halin da yake ciki Dan kar yaji shi shiru
B'angaren su Samha kuwa washegari Alhaji Nazifi na fita Suhaima ta hau tambayar Samhar da ta tasa breakfast d'inta agaba ta kasa ci sabida tunanin Akram akan me yake damunta haka take tunani kwana biyu bata gane mata
Samha d'aurewa tayi ta saisaita kanta Dan kar su d'agota tace musu babu komai kawai Mummy ce ta fad'o mata abunka da Wanda yake jiran kiris take hawaye ya hau zubo mata
Saheeba ta guntsa dariyar da ta taho mata dan tasan karya Samha take yi San Akram ke dawainiya da ita
Suhaima kuwa tab'e baki tayi tace ta dai fad'i gaskiya ba abinda ke damunta ba kenan akwai dai wani Abu da take b'oyewa yake nukurkusarta a zuciyarta
Samha kuka ta fashe dashi tana ita babu abinda take b'oyewa daga haka ta mik'e da gudu tabar palon ta nufi d'akinsu
Suhaima harara ta bita dashi tana ce mata munafika Saheeba kuwa sai Dariya take dan tasan zallar yarinta ke damun Samha
Aranar hawan jini ne kawai basu sawa Samha ba Dan har d'aki suka bita suna hirar Akram kowace na cewa Allah yasa ya zab'eta har suna fad'ar irin San da suke mishi Samha kuwa duk inda ta kai ga San ta d'aure sai da ta fashe da kuka Dan ji tayi gwara su rufeta da duka akan maganganun da Sukeyi su kuwa sai dariya suke aransu
Bayan kwana biyu Akram ya shirya shi da Yazeed suka nufi gidansu Samha Dan ya gayawa Alhaji Nazifi gaskiyar abinda ke ransa daga nan kuma ya shigar da maganar yazeed akan San da yake yiwa Saheeba
Har palon Saukan bak'i aka sauke su Akram dan Alhaji Nazifi yasan da zuwansu sai da ya lek'a d'akinsu Suhaima yace su shirya bak'onsu ya zo duk wacce ya zab'a a cikinsu ta k'arbeshi da hannu bibiyu
Samha da bata da aikin Da ya wuce kwanciya da tunani tabi ta rame tayi zuru zuru sabida tunani wani irin mik'ewa tayi kirjinta kamar ya fad'o k'asa dataji abinda Alhaji Nazifi yace
Su Suhaima kuwa da gangan suka nuna farincikinsu a fili Dan so suke Samha tayi admiting tana San Akram da kanta
Alhaji Nazifi halin da yaga Samha a ciki ne yasa ya zuba mata ido yana "Baby Lafiya kuwa mai ya sameki"?
Samha kuka ta fashe dashi Alhaji Nazifi yayi Sallati yana nufar inda take hannyenta ya ruk'o yana tambayarta abinda yake damunta kamar k'ara zugata yayi ta kara volume d'in kukanta Dan agaskiya bata jin zata iya shiru ta cutu gwara ta gayawa Alhaji Nazifi halin da take ciki
Su Suhaima kuwa ido suka zuba mata suna jiran suji mai zatace
Aikuwa Hakan da ta gani yasa ta sadda kanta k'asa tana tunanin yanda zata fito ta gaya musu halin da take ciki
Alhaji Nazifi kuwa ganin tak'i magana ne yasa ya mik'e ya kalli Suhaima yace tazo ta tambayeta abinda yake damunta zaije wajen su Akram kar ya b'ata musu lokaci
Samha tuni hankalinta ya tashi Dan tasan idan ba fitowa tayi ta ajiye kunya da jin nauyinsu a gefe ba zata kwari kanta Akram yayi mata Nisa
Da Sauri ta tsayar da Alhaji Nazifi dake dab da ficewa daga d'akin tace " Daddy"
Alhaji Nazifi juyowa yayi yana kallonta
Samha kuwa tayi sauri ta sunkuyar dakanta haka kawai kuma taji wani irin kunya da nauyinsa ya rufeta
"Ya akayi Baby"?
A hankali ta d'aga kanta ta kalli su Suhaima da suka kura mata ido tayi sauri ta maida kanta ta sunkuyar gabanta na fad'uwa
Alhaji Nazifi kuwa ganin tana b'ata mishi lokaci yasa yayi tunanin shagwabar ta ne ya motsa tsaki yayi ya juya zai bar d'akin yaji siririn muryar Samha na cewa " Daddy wlh ina Sansa ina kaunarsa"?
A mamakince ya juyo Dan ya gaskata abinda tace yana juyawa yaga ta mik'e dagudu ta shige band'aki ta kulle
Suhaima da Saheeba kuwa dariya suka kyalkyale dashi suna tsokanar Samha akan da ta tsaya girman kai taga ikon Allah
Alhaji Nazifi kuwa maida kallonsa kan su Saheeba yayi Dan su mishi Karin bayani aikuwa suka hau bashi labarin irin San da Samha keyi wa Akram
Hamdala Alhaji Nazifi ya runga yi a zuciyarsa Dan Yasan Akram zaiji dadi idan yagaya mishi Samha ta amince girgiza kansa yayi cikin farinciki ya d'aga muryarsa yanda Samha zata jiyo shi yace "ai da kin tsaya girman kai kiga yanda kwad'o zai miki k'afa"
Samha kuwa dafe k'irjinta tayi tana mamakin yanda akayi Kalmar ta fito daga bakinta wani irin kunya da nauyin Alhaji Nazifi da su Saheeba ne ya rufeta ita da ta gama cika baki bata San sa sai gashi babu kunya babu tsoron Allah ta bud'e baki tace tana San sa ahaka ta mak'ale a band'aki ta kasa fitowa
Su Suhaima kuwa sai tsokanarta suke suna kwaikwayar muryarta lokacin da tace bata San shi
Alhaji Nazifi kuwa yana zuwa palon da su Akram suke suka zub'e a k'asa suna gaishe shi wani irin kunya da Nauyin yanda zai ce mishi baya San su Suhaima ne ya rufe shi
Alhaji Nazifi kuwa yana lura da yanda Akram ya takura kansa yak'i d'agowa murmushi yayi ya kira Sunan Akram
Akram ya d'ago yana kallonsa ce mishi yayi kar ya damu yasan yana jin nauyin ya fad'a masa baya San su Suhaima kar ya damu matar mutum kabarinsa Allah ya Riga da ya tsara Samha rabonsa ce dan ta amince zata Aure shi
Akram sakin baki yayi yana kallon Alhaji Nazifi dan badan yasan babu 'yar wasa a tsakaninsu ba da sai yace wasa yake masa
Yazeed cikin tsananin farinciki yace Alhamdulillah amma munji dadi
Akram kuwa fad'ar farincikin daya tsinci kansa a ciki b'ata bakine dan k'asa rufe bakinsa yayi da ace Alhaji Nazifi baya nan babu abinda zai hana shi taka rawa
Alhaji Nazifi kuwa addu'a Ya musu na Allah ya tabbatar musu da Alheri ya mik'e zai tafi Akram yayi sauri ya dakatar dashi yana sunkuyar da kai dan so yake ya mishi maganar Yazeed dan tundazu yake mitsininsa
Farinciki Gaza b'oyuwa yayi a fuskar Alhaji Nazifi bayan Akram ya fad'a mishi Yazeed na San 'yarsa da ta kawo musu ruwa ran nan
Alhaji Nazifi tambayoyi yayi wa Yazeed akan family d'insa da irin aikin da yake yi
Aikuwa ya samu gamshashiyar bayani akan family d'insu Yazeed dan kanin Mahaifin Yazeed abokinsa ne tare sukayi secondary school addu'a ya k'ara musu na fatan Alheri suka ringa mishi godiya ya mik'e yace bari ya turo su Saheeba
Yana fita Akram da Yazeed suka runguma juna suna murna Akram kamar ya jawo Samha gabansa yayi ta kallonta haka yakeji sai kallon bakin k'ofa yake yaga ta inda Samha zata b'ullo
Alhaji Nazifi kuwa d'akinsu Samha ya nufa fuskarsa d'auke da murmushi har a lokacin su Suhaima maganar Samha suke Samha kuwa na mak'ale a band'aki
Alhaji Nazifi tambayarsu yayi inda Samha take suka ce mishi tana band'aki tak'i fitowa
K'walla mata kira ya fara yi Samha kuwa kamar ta nutse dan kunya dak'yar ta bud'e k'ofar band'aki tafito kanta a sunkuye
Alhaji Nazifi murmushi yayi yace "jaira kawai ana so ana kaiwa kasuwa maza shirya kije gashi can a Palon bak'i yana jiranki Saheeba kema kije kina da bak'o idan kin dawo zan miki bayani akan shi"
Daga haka ya sa kai ya fice daga d'akin
Yana fita Suhaima ta rangad'a gud'a tana sun kusa shan biki Saheeba kuwa tunda yace taje tayi bak'o jikinta ya hau rawa dan bata tab'a tsayawa da Saurayi ba da taimakon Suhaima suka shirya duk da Samha nonok'ewa take yi Suhaima kuwa sai tsiya take mata har bak'in k'ofar palon ta rakasu ta juya
Dukansu sanye suke da dogwayen riguna iri d'aya sai dai bambamcin kala na Samha bak'ine na Saheeba kuma Pink
Samha kuwa sai da ta rufe fuskarta ruf jikinta na d'an rawa har suka isa palon da su Akram suke
A tare suka amsa sallamar da sukayi musu Akram kuwa ya zubawa Samha ido da ta rakub'e a bakin k'ofa kanta a sunkuye
Wani wawan ajiyan zuciya ya sauke daya sa sai da Yazeed ya d'ago ya kalleshi
Saheeba ce tayi k'arfin halin gaishe su dan Samha sabida rawar da jikinta yake yi ta k'asa bud'a bakinta
Yazeed ne ya amsa sabida hankalin Akram na kan Samha dake neman shigewa k'asa
Sai a lokacin Saheeba ta d'aga kanta suka had'a ido da Yazeed gabanta ne ya yanke ya fad'i take itama jikinta ya hau rawa
A takaice aranar zancen kurame akayi su Akram ne kawai suka ringa kid'ansu suna rawarsu dan su Samha basu tab'a tsayawa da namiji da sunan zance ba
K'asan zuciyar Samha kuwa duk fitar maganar Akram sai taji kamar k'ara rura mata wutan San shi ake a zuciyarta
Saheeba itama tunda ta had'a ido da Yazeed taji ya kwanta mata aranta
Akram babu yanda baiyi ba dan yaga fuskar Samha amma fir Samha tak'i bud'a mayafin data rufe fuskarta dashi akan dole ya hakura dan ko magana tak'i tayi mishi
Sai wayarsa ya mik'a mata ta ta sa mishi number ta ta mik'e da sauri tabar palon
Yazeed shima lambar Saheebar ya k'arba dan itama kunya ya hana ta saki jiki suyi hira
Tunda ga lokacin soyayya mai zafi ya shiga tsakanin wannan masoya kowace kullum tana mak'ale da waya a kunne idan kuwa basa waya to suna musayar messages
Suhaima itama tuni ta fara kula wani Saurayinta Khaleed da bata bashi fuska ada itama ta shiga sahun su Samha
A cikin kankanin lokaci manya suka shiga maganar kafin kace me ankawo kud'in Aure da sa rana lokaci guda aka sa ranarsu Suhaima nan da wata uku masu zuwa Wanda yayi dai dai da gama exams d'in Samha
Akram da Samha kamar su had'iye juna sabida so duk da a filli idan yazo bata wani nuna mishi so sabida kunyar shi da take ji amma idan a waya ne ko a chatt tayi ta nuna mishi irin San da take mishi
Watarana yazo zance shi da Yazeed yana tayiwa Samha hirar bikinsu da yanda zai kasance Samha kuwa murmushi kawai take mishi bata cewa komai aranar kasancewar bak'in kaya ne ajikinsa haka kawai bak'in Daren da suka zo gidansu da Alhaji Bala ya fad'o mata Wanda hakan ya d'an sa gabanta fad'uwa tare da kura mishi ido
Akram tsayar da maganar da yake yi yayi dayaga yanda ta kura ya mishi ido ya kirata da Sunan da yake kiranta dashi yace "Soulmate lafiya kuwa kike kallona haka"?
Samha kuwa take hawaye suka hau tsare a kumatunta data tuna Hajiya Nafeesa da jajircewar da tayi dan kar a keta musu haddi
Kau da kanta tayi daga kallonsa ta cigaba da zubar hawaye
Hankalin Akram kuwa idan yayi dubu ya tashi a gigice ya hau tambayarta abinda ya faru
Samha kuwa ta k'asa magana sai hawaye dan kamar a faifai take hango duk abinda ya faru a ranar take wani mugun tsanar Alhaji Bala ya k'ara darsuwa a ranta
D'aga idanuwanta da suka rine suka koma tamkar garwashi tayi ta zubawa Akram da jikinsa ya fara rawa yana tunanin abinda ya sata kuka
Murya a dak'ushe tace "Akram