Follow us on social media
Showing 9001 words to 12000 words out of 50786 words
abubuwa haka kamar na bankwana sau uku ta na fita ta dawo idan suka tambayeta mai ta dawo yi sai tayi murmushi tace ta dawo ne tayi musu Sallama Ashe sallamar k'arshe take musu Ashe tafiyar da ba'a dawowa zatayi
Alhaji Mamman fashewa yayi da kuka yana "Ya Allah ka tonawa wadanan azzuluman asiri Allah ka hanasu zaman lafiya a gidan duniya Allah ka wulak'antasu Allah ka dai-daitasu"
Kuka Alhaji mamman keyi sosai
Ahankali mazan suka fara mik'ewa suna Barin palon dan za'ayiwa Hajiya Nafeesa wanka a suturceta akai ta gidanta na gaskiya
Ciki kuwa Saiam gajiya tayi da buga k'ofar ta sulale k'asa tana "Mummy ki tashi kice baki mutu ba baccine ya d'aukeki"
Ahaka tayi ta sumbatu tana kuka ak'arshe ta koma tana sauke ajiyar zuciya ahankali wani irin bacci ne yayi awon gaba da ita ko minti biyar batayi da bacci ba tayi mafarki yanda take kwance Hajiya Nafeesa ta bud'e k'ofar d'akin ta shigo fuskarta d'auke da wani irin murmushi exactly kayan data sa ne ajikinta har da hular net d'in
Zumbur Saiam ta mik'e tana nunata da hannu tare da cewa "Mummy dama baki mutu ba ni nasan mafarki nake yi ba mutuwa kikayi ba"
Murmushin da Hajiya Nafeesa ke yine ya juye zuwa b'acin rai tafara magana tana
"Haba Saiam Akan me zaki ringa Min kuka alkawarin da kika d'aukar min kenan kada ki sake ki k'ara zubar min da hawaye mutuwa Riga ce a Wuyan kowa idan lokacin tafiyarka yayi babu makawa sai ka tafi Dan haka nima lokacin tafiyata ne yayi addu'arku kawai nake bukata
" Haba Saiam karfa ki manta kece babba ke ya kamata ki ringa kwantar wa da kanenki hankali ki zame musu tamkar uwa Daddynku na cikin wani hali kiringa kwantar masa da hankali ki zama jajirtaciya Dan Allah Saiam idan kun tuna ni kuyimin addu'a kawai karku manta azumin danace Ku rama min"
Saiam da sauri tace "to mummy wai yaushe zaki dawo muna bukatarki mummy"
Wani murmushi Hajiya Nafeesa tayi daya sata masifar kyau da haske tace "Saiam da kunsan inda zanje ayanzu da baki ce na dawo ba da Baku wahalar da kanku kun zubar da hawayenku ba inda zanje yafiye min inda na Bari sau dubu dan haka kucigaba da min addu'a Saiam kina so inyi fushi dake"?
Da sauri Saiam ta girgiza kanta
Hajiya Nafeesa tace " to karki k'ara zubar da hawayenki karki k'ara bari kannenki suyi kuka ko daddynku maza tashi ki tafi d'akinku kije kiyimin addu'a kafin akaini makwancina"
Duk mafarkin da Saiam tayi baifi cikin minti biyu ba da sallati ta mik'e zumbur tana bin ko ina na d'akin da kallo gani take kamar ma ido biyu Hajiya Nafeesa tazo mata ba mafarki take ba maganganun da Hajiya Nafeesa tayi mata sai amsa kuwaa yake a kunenta
Da sauri ta nufi k'ofar ta fara jijjigawa tana cewa a bud'e mata
Adai-dai lokacin da aka gama yiwa Hajiya Nafeesa sutura aka sata a tsakiyar d'akin
Ganin bugun k'ofar da Saiam take yayi yawa ne yasa
Aka je aka bud'e mata k'ofar da sauri ta fito daga d'akin har tana tuntub'e
Cak ta tsaya ta kurawa makarar dake tsakiyar d'akin ido an lullub'e Hajiya Nafeesa da farin likkafani
Ahankali ta ringa tafiya har sai data k'araso gaban makarar ta tsuguna ahankali wasu siraran hawaye suka zubo mata
Da sauri ta d'auke hawayen da bayan hannunta ta runtse idonta cikin dakewa da karyayar zuciya tafara karanta suratul Rahman cikin wani irin rawar murya mai d'auke da kuka aya goma kawai ta iya karantawa tafara jero addu'oi tana yiwa Hajiya Nafeesa Addu'a 'yan d'akin kuwa sai ameen suke cewa
Ganin maza sun fara shigowa zasu zo su d'auki gawar Hajiya Nafeesa ne yasa hajiyar su Nafeesa zuwa ta janye Saiam
Aikuwa kamar ta zuga su Saiam dasu Safna tuni suka fashe da wani irin kuka suna kallon makarar Hajiya Nafeesa da akayi sama dashi kuka suke sosai suna shikenan mummy ta tafi
Duk inda ka kai da taurin zuciya sai ka zubar da hawaye
Saiam kamar d'aukewar ruwan Sama tayi sauri ta tsayar da kukan da take ta kamo hannun su Safna gabad'aya tafara goge musu hawaye tana "mummy tace kar mu sake mu zubar mata da hawaye idan ba so muke tayi fushi damu ba tace muringa mata addu'a kawai"
Tausayin Saiam ne ya k'ara rufe duk wayanda ke d'akin dan sun d'auka duk zafin mutuwar Hajiya Nafeesa yasa Saiam ta fita hayyacinta bata San mai take cewa ba
Fad'ar mutanen da suka sallaci gawan Hajiya Nafeesa b'ata bakine dan sai da aka kashe hanyar da motoci suke wucewa dan inda makabartar yake da dan tazara sosai daga gidansu Hajiya Nafeesa ahaka aka kai Hajiya Nafeesa dubanin mutane na yabon hallayenta na gari banda kananan yara da har dasu aka je binneta suna ta kuka Hajiya mai raba musu alewa duk ranar juma'a ta mutu
Idan ka kalli yanda su Saiam suke zaune waje d'aya suna Jan carbi hawaye da majina na zubo musu lokacin da zaka fara hawaye ba sani zakayi ba
Bama sa iya amsa gaisuwar da ake musu ciki kuwa har da saurayin Saiam da Safna da zasu Aura suna ganin halin da su Saiam suke ciki sai gashi hawaye ya hau zubo musu sabida adaren da Hajiya Nafeesa zata rasu da suka zo zance suka je suka gaisheta haka kawai ta hau yi musu wa'azi da nasiha tana kan kujera sanye da hijabi da fararen hakoran maccanta sai murmushi take she is very social and civilized dan har ga Allah har suka je gida suna yabon halayenta ashe mutuwa na nan tafe
Saiam cikin dakushashiyar muryarta ta kalli Suhaima tana tambayarta inda Samha take da Daddy dan duk abinda akayi basani tayi ba
Anan Safna ke ce mata suna asibiti Alhaji Nazir ya kaisu jijjiga kanta kawai tayi ta mik'e aka hau tambayarta ina zata je
Cikin muryarta da bata fita tace zata je asibitin ta gano halin da suke ciki dan tamkar yanzu Hajiya Nafeesa ke ce mata ta kwantarwa da Daddynsu Hankali da kanenta
Fawazz Saurayinta da sauri ya mik'e yace zai kaita asibitin
Saiam ko kallonsa bata yi ba tayi waje kamar iska zai d'auketa ....
Nikam sai dai kuyi maneji Allah dak'yar nayi wanan
Mutuwa rigar kowa wacce ba cirewa ta d'auki Hajiya Nafeesa jikanta sarki buwayi Hajiya Nafeesa Allah ya jikanki rabbi shi yayi kiranki kullum muna ta tunaninki muna yabon halayarki
Ya Allah ya Allah ya gufuru ya Allah ya Allah Ya Allah gafarta mata ya
Allah ya Allah馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶 Allah kasa mucika da kyau da imani
[2:34PM, 4/7/2018] 鈥�+234 806 462 6766鈥�: 馃寫 馃寫 *B馃叞K'IN D馃叞RE*馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫
*Written by*
馃拝馃拝 *Sadnaf*馃拝馃拝
*A heart touching story*
庐 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_莎蓻 蓶啤艐'脓 啤艐俪醿� 蓻艐脓蓻艡脓膮谋艐 艐蓶 蓻蓶懦膯膮脓蓻, 醿撑� 莎蓻 膮俪艦啤 脓啤懦膯骚 蓶 骚蓻膮艡脓 啤蕜 艡蓻膮蓶蓻'艦_
#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com
*sadaukarwa ga dukanin masoyana na zahiri da badini da wayanda na sani da wayanda bansani ba Sadnaf na kaunarku kamar yanda kuke kaunarta ana tare insha Allahu*馃檹馃檹馃檹馃檹馃檹馃檹
Page 5
Ogansu Sai daya gama shek'a ayarsa da linder ya fito ya shirya a cikin manyan kaya kai ahaka idan ka ganshi zaka d'auka mutumin arziki ne Dan har da su hula yasa
Yana fitowa daga d'akin su Lion suka mimmik'e har da Akram da kansa ke balain ciwo Hannunsa a sak'ale yake a k'ugun Linder ya sakar musu wani jairin murmushi yana
"Killer lion scorpion black Akram Ni zan tafi Port Harcourt wajen iyalina zan dan huta haka kamar na 3weeks kafin mu kuma fita wani operation d'in inda nake tunanin wanan karon kano muka nufa dan akwai wani Alhaji Buba mai gwala gwalai yana da balain kudi ina nan ina monitoring d'insa akwai wata servant d'insu Habiba ita nakeso na jawo jikina in sakar mata kud'i ta bani details d'insu sosai da yanayin gidan immediately ina gama samun Duk wani information akansu zan kiraku Ku fara shirye shiryen daya kamata"
"Sanan kafin lokacin idan kuna da wani uzuri zaku iya zuwa kuyi amma kwana uku kawai na Baku dukanku Ku dawo do I make my self clear"?
Da sauri dukansu suka gyad'a Kansu suna yes boss
Daga haka ogansu yasa kai ya fice daga palon suna take mishi baya still yana rik'e da kugun Linder dan shi zaiyi dropping d'inta a hanya
Sai da Killer yasaka mishi brief case d'in kud'inshi abayan boot kafin ya ja da baya Ogansu kuwa yaja katon jeep d'in yabar harabar gidan
Ciki suka koma gabad'aya kowanensu yafara shirin tafiya uzurinsa akwai masu zuwa su duba iyayensu irin su Lion da sukayi wa iyayensu karya akan aiki suke a Abuja akwai irinsu black dake da iyali da suma suka shirgawa iyalinsu karya akan suna aiki a abuja
Akram ya rigasu shiryawa gabad'aya dan ji yake kamar akan k'aya yake
Kallonsu Lion yayi fuskarsa d'auke da murmushi adai dai lokacin da yake rataya jakarsa a kafad'arsa yace
" to ni kunga tafiyata zanje naga parent d'ina da siblings d'ina zan kai musu d'an abunda muka samu insha Allahu bazan wuce 3days da boss ya d'ibar mana ba"
Dukansu murmushi sukayi dan haka kawai Allah ya had'a jininsu da Akram shiyasa ma koda an fita operation dashi baiyi komai ba basa damuwa
Killer ne yace " same here muma zamuje muga namu iyayen akwai kanwata ma da za'ayi bikinta nasan suna nan suna zuba ido dan dani suka dogara Nima zan kai musu abunda ya samu"
Murmushi kawai Akram yayi a zuciyarsa yana tausayin halin da suka jefa Kansu sabida talauci yana tausayinsu ranar da asirinsu zai tonu asaka musu ankwa a hannu all they are a doing is for d sake of their family
Duk rashin aikin yi ne ya janyo musu fad'awa halaka ciki kuwa har da rasa imaninsu tunda basu d'auki kisan kai abakin komai ba
D'aya bayan d'aya ya bisu ya rungume yana ce musu sai sun dawo nan da kwana uku daga haka yasaka kai ya fice daga gidan dayake ji tamkar prison bai zame ko ina ba sai head quarter d'insu na Ss
Agajiye ya k'arasa office d'inshi ya dafe kansa dake Sara mishi har yanzu yana jin ihunsu Samha a kunensa ko yaya ya runtse idonsa sai ya hango abubuwan da suka faru a Daren jiya
Haka kawai yaji ya tsani kansa yana tuhumar kansa shima da laifin shi awajen kisan Hajiya Nafeesa sai yanzu yake mugun daya sani da ya d'auki mataki tun a lokacin daya sani ya harbesu duka dayaga yanda Hajiya Nafeesa ke fad'i tashi akan ta kare martabar 'ya'yanta idan kuma ya tuna kwanan ta ne ya kare sai ya rage ganin laifinsa ahaka ya zauna wajen minti ashirin kafin ya iya mik'ewa ya Shiga band'akin dake cikin office d'in ya d'aura alwala yazo yayi sallar Azahar yana idarwa ba tare da b'ata lokaci ba ya nufi office d'in ogansu
Bayan sun gaigaisa kamar yanda suka saba da tambaye tambaye ogansu ya tambayeshi abubuwa daya k'ara samo musu akan Alhaji Bala
Akram jiki Asanyaye ya mik'a masa 'yar k'aramar Camerar dake hannunsa ogansa kuwa ya k'arba a dokance
Cikin minti biyar ya had'a camerar da system d'in dake gaban table d'insa
Tun daga yanda suka shirya da zasu tafi operation har zuwa yanda suka d'aure mai gadin gidansu Hajiya Nafeesa daya bud'e musu k'ofa tagumi ogansu yayi yana kallon system d'in dake gabanshi jikinsa sai rawa yake yabi ya jike da gumi duk da sanyin Ac dake ratsa office d'ind'in
Wani irin kad'awa idonsa yayi ya mik'e jikinsa na wani irin k'yarma "innalillahi wa inna ilaihi rajiun" kawai yake maimaitawa ahankali ya kalli Akram daya dafe kansa da hannu biyu k'walla na zuba a idonsa dan wani irin zafi yake ji a zuciyarsa dayake jiyo sautin kukan Hajiya Nafeesa da su Saiam magana ya fara yi yana
"Akram meyesa baka ceci rayuwar matan nan ba meyesa bakayi wani Abu dan kar Alhaji Bala ya harbeta ba tunda nake ganin abubuwa ban tab'a ganin abun tausayi irin wanan ba matan nan tabani tausayi fiye da tunanin mai tunani Alhaji Bala ya Dade yana abubuwa amma this time around his cup is full bama bukatar wani prove ko evidence wayanda muke dasu kawai sun ishemu enough is enough lokaci yayi da ya kamata mutane su San waye Alhaji Bala lokaci yayi daya kamata ace mutane su San irin sana'ar da yake yi"
Rawa jikin shi ke yi sosai idonsa jajawur
Akram kuwa ko magana ya k'asa yi dan shi kad'ai yasan halin da yake ciki
Ni kam waye wanan Alhaji Balan ne toh bari muji waye shi
Alhaji Bala haifaffen dan jigawa ne a kauyen kafin Hausa su hud'u iyayensu suka Haifa duka maza sun taso ne a cikin tsananin talauci dak'yar suke cin abincin sau biyu arana tunda Bala ya taso ya taso da masifar San kud'i dan idan ya zauna da mahaifiyarsa Saude haka zai taba ta labarin irin kud'in da zaiyi idan ya girma da abubuwan da zai mata da kanensa sabida mahaifinsu ya Dade da rasuwa ahaka Alhaji Bala ya taso da mugun San kud'i duk da mahaifiyarsu Saude na matuk'ar k'ok'ari dan taga ta sama musu ingantaciyar rayuwa
Alhaji Bala na da shekara goma sha biyu ya fara buga buga shine noma shine aikin gini sharar kwata duk wani Abu daya San zai shigo masa da kud'i yinshi kawai yake ahaka rayuwa tayi ta tafiya dak'yar ya gama primary sch a kauyensu inda daga nan ya tattara karatun ya watsar ya cigaba da Neman kud'i yana kula da mahaifiyarsa da kanensa uku Saidu Abubakar da zaidu ahaka Alhaji Bala ya ringa Tara kudin da yake buga buga inda ya Tara wajen dubu biyar a lokacin kudine masu daraja da yawa shawara yayi da mahaifiyarsa Saude da ta tsufa tukuf wanda a zahiri ba tsufan tayi ba tsabagen talauci ya tsufar da ita
Shawara ta bashi akan yaje birni ya saro shadodi da atamfuna masu kyau na manya da yara yanda basai aringa wahalar zuwa birni siya ba aikuwa take yabi shawararta dan babu inda ake siyarwa a kauyen
Aikuwa cikin sa'a ya saro kayan dan kayan basa sati ake siyesu har da masu kawo mishi kud'i ya hada masu lefe awanan lokacin
Watarana yaje birni zai sari kayan an gama loda mishi kayan a mota kenan zai hau yaji ana ta mishi horn abayansa
Juyawa yayi yaga wata had'adiyar mota ya had'iyi wani irin yawu dan sai ka isa zaka iya siyan motar kafin ya gama karewa motar kallo aka bud'e k'ofar motar aka fito buhun hannunsa ya wurgar ya tafi da gudu ya rungume abokinsa Ukashat da sukayi primary sch tare
Sai da ukashat ya kalleshi daga sama har k'asa kafin yace ya yaganshi haka
Shi dai Alhaji Bala baki a sake kawai yake bin ukashat da kallo da kayan jikinsa da motarsa
Horn mai motar ya ringa yiwa Alhaji Bala dan yazo su tafi
Ukashat kuwa yace yaje ya hau zai biyosu abaya
Aikuwa haka akayi har k'ofar gidansu Alhaji Bala Ukashat ya bisu sai da aka gama sauke kayan gabad'aya Sanan Alhaji Bala ya nufi wajen ukashat dake hakimce a cikin motarsa yana yatsina fuska kamar Wanda yaga kashi d'aya barin Alhaji Bala ya bud'e ya shiga ya zubawa ukasha ido yana mamakin yanda akayi yayi kud'i acikin shekara takwas kawai da sukayi da rabuwa abunda burinsa kenan arayuwa
Agurguje Ukasha ya gayawa Alhaji Bala silar samun kud'insa ta hanyar armroberry inda wani ya mishi hanya shima anan shima yace idan Alhaji Bala yana so yayi bankwana da talauci to shima yazo yayi joining d'insu da farko Alhaji Bala k'i yayi amma da Ukasha ya kwadaita mishi irin kudin da ake samu atake ya amince
Kaninsa Saidu ya d'ora akan kayansa akan ya cigaba siyarwa
ya shirgawa Mahaifiyarsa karya akan ya samu aiki a birni adduoi Saude ta bishi dashi ba tare da b'ata lokaci ba yabi Ukasha suka tafi
Dayake masu aiki irin nasu Ukasha partner in crime kawai suke nema da hannu bibbiyu suka k'arbi Alhaji Bala aka hau yi mishi training d'in yanda ake sata da magana da hannu ido da yanda ake Harbin bindiga ogansu gabad'aya a lokacin wani ne inyamuri ana ce mishi Chris
Bala duk da yadan sha wahala kafin ya saba ya ajiye tsoro a gefe hakan bai hana shi iya training d'in da suka mishi ba
Inda bayan sati uku da joining d'insu suka fita operation daddare suka tare wasu matafiya masu tafiya Port Harcourt aranar zallar rashin imani suka yiwa matafiyan Dan dama ogan nasu ba musulimi bane ballantana yayi imani
Bayan sun k'wace musu kaya da dukiyoyi sai da suka yi raping d'in matan dake cikin motar gabad'aya acikin su takwas sai da suka samu mata bibbiyu ciki kuwa har da Alhaji bala da bai tab'a sanin mace ba
Ogansu na tsaye akansa yayi raping wata yar shekara takwas da mahaifiyarta sai kuka suke banda wayanda suka susuma
Wata ce ma ta dage tana musu gardama sosai tak'i yarda da ogansu Chris sai ihu take
A fusace Chris ya janyo hannun Alhaji bala ya damka masa bindiga yace yana so ya fasa kwakwalwar matar da ta Goya jaririn da bai wuce wata biyu ba tunda tak'i yarda ta bashi had'in kai
Jikin Bala ne ya hau rawa sabida bai tab'a kisan kai ba yacewa Chris ba zai iya ba aikuwa a fusace Chris ya buga mishi gindin bindiga akan ha harbeta ko shi harbeshi
Alhaji Bala yana rawar jiki ya harbi matar da ke ta sallati da yaronta abaya
Tunda ga lokacin Alhaji Bala shima ya Faso gari suke fita garuruwa fashi idan sunyi fashi ma sai sunyi wa mace fyade
Tuni yayi kud'i yayi ginin bullo a k'auyensu ya Gina wani katon shago ya zuba kaya kanensa suke kula da shagon
Saude Albarka kawai take sa mishi
Watarana kuwa sun fita fashi da yamma a lokacin basu fiye zuwa gidajen jama'a ba sai dai su tare matafiya akan hanya su k'wace musu dukiyoyinsu da kudinsu
A hanyar Abuja suka yi fashin inda ogansu Chris