Follow us on social media

Showing 3001 words to 6000 words out of 61825 words

Chapter 2 - EZNAH Sirrin Jini by Aysha Galadima

jira sauran bayaninba ya nufi gate din daidai Nan Kamal ya fito da sauri Yana tambayar abba abinda ke faruwa cikin damuwa.

Murmushin gefen baki mum asee dake tsaye bakin windon bedroom dinta dake sama tasaki tareda cewa,

Not bad bullet.,,,
Sbd dabararsu ba laifi tayi Dan yanxu bamai ta6a tunanin maza sukayi aikin za aita bincikene akan mace ce takasheta.

Hmmmnn and I will make sure nikuma Naga na qara lalata tunaninsa  gurin binciken mitswww stupid bastard..

Juyawa tayi tabar bakin windon tareda fadawa toilet ta fiddo spray na pepper tafara fesawa cikin idanuwanta duk da tsananin azabar datakeji kamar zata shide Amma taurin Rai da qarfin baqar zuciyarta ya hanata dainawa
Cikin qanqanin lokaci idanuwanta sukai wani irin mugun kumbura sukai jajir Banda tsiyayar hawayen azaba ba abinda suke daqyar ta it's alwala ta fito hartayi sallah tagama idanuwanta Basu daina tsiyayar hawayenba.

Kodata idar jiki a sanyaye ta sauko Palo cikin hijab din anan ta tararda Abba da Kamal a tsattsaye sun saka gawar agaba jiki duk a mace ga jabiru gefe Sai sambatu yake sbd nafeesat mutuniyarsace sosai.

Gwaggo Hindu Mai Taya nafeesar Zama tuni ta zube qasa Banda kuka ba abinda takeyi hakama fadime da Deborah masu aiki Suma hawayen suke Dan kuwa suna tsananin qaunarta Dan itace kawai Mai mutumta mutane agidan.

Baya mum asee tayi cikin tsananin tashin hankali tareda sakin saririn kuka tana Kiran sunayen Allah yakurah data fito bedroom dinta tayi saurin tareda cikin damuwa itama.

Waya Abba yafitar tareda barin palon yafara Kiran uwayenta ya sanar musu kafin yakira saheeb Amma Sam wayarsa Bata shiga nandai yakira duk yanuwa da jamaarsa yasanar musu da rasuwar.



Qarfe Tara da rabi na safe suna airport ten jirginsu zai tashi jin sauran thirty minutes din yake kamar basa tafiya.

Wayarsa dake kashe tun jiya ya fiddo tareda kunnawa kamar jira ake saiga Kiran Kamal yashigo wayar
Kallo 'daya yayiwa screen din ya mayar da wayar sbd badashi yake buqatar wayaba yanxu.

Yana kallo Saida Kamal yayi Masa Kira bakwai kafin ya daina kiran,
Nemo number Abba yayi ya Kira Sai yajisa line busy sai kawai ya sake kashe wayar tareda miqewa riqeda black smiones leather jacket dinsa da iPad da wayarsa dakuma passport dinsa tareda ticket zayyan na gefensa shima Amma waya tunda sukazo yake waya Sai time din ya kashe Yana saka wayar a aljihu tareda gyara zaman jacket dinsa Mai zanen sojoji.


Tunda suka shiga jirgi ya kwantarda kansa tareda rufe idanuwansa Dan he's having this feeling something is not right.

Zayyan datun a airport Abba yakira yasanardashi jikinsa yake a sanyaye sosai rasuwar ta daki zuciyarsa Dan kuwa yasan tabbas amininsa yayi rashi babba Dan har abada bayasa ran zai Kuma samun maisonsa kamar nafeesat Dan kuwa ta soshi ta qaunaceshi ayanda yake da rayuwarsa da Babu farin ciki ko ka'dan.

Yayita yunqurin sanardashi saiya fasa sbd baimasan ta inda zai fara sanar Masa rasuwarba musamman yanda suka fara ganin haske yafara shigowa duhun rayuwarsa ta sanadin nafeesat da cikinta Amma gashi lokaci 'daya Allah ya karbi baiwarsa.


Koda jirginsu ya sauka suka fito mota biyu ce tazo 'daukarsu 'dayar sojoji ne acike Sai 'dayar driver ne kawai Kuma shima soldier ne dukkaninsu cikin uniform dinsu suke suna ganinsa suka saurin sunkuyar da kawunansu cikin girmamawa sukace,

Wellcome sir.

Da Kai ya amsa musu tareda shigewa mota Nan take suka bar airport din a guje Dan dama yanada wuya kaga soldiers ba gudu sukeba.


Jabiru dake zaune bakin gate daga waje tareda wasu daga cikin masu gadin kusa dasu dasuka zo gaisuwa Yana hango wutar motocinsu duk da da Rana ne Amma yasan motocin soldiers din oga saheeb kullum akoda Rana a kunne suke ya miqe da sauri yayi ciki ya bu'de gate 'din gabansa na tsananta fa'duwa.


Lumshe fararen manyan oily eyes dinsa yayi lokacinda yaga harabar gidan da mutane duk da ma tuni wasu suka tafi
Wani sabon nauyi yaji ya qaru a zuciyarsa Akan Wanda yakedashi ya fito ya nufi gurinsu Abba dake jiran qarasowarsa yayi qasa dakai lokacinda wasu Yan uwan nafeesat maza ke Masa gaisuwa.

Shiru yayi batareda ya 'dagoba har Saida Abba ya dafasa cikin tsananin tausayawa yace,

Allah yaji qanta ya kawo maka sassauci Abdul.

Har magriba ta gabato Yana zaune kusada Abba kansa a sunkuye still
Ba Wanda baiyi mamaki da jinjinawa jarumta da qarfin hali irin nasaba Dan ko magana bayayi duk Wanda yai Masa gaisuwa Kai kawai yake 'dagawa idanuwansa sun rine Sai jijiyoyin kansa dasuka firfito ahaka har akai magriba kafin yashiga cikin gida inda ya tararda mum asee ba lafiya sosai Nan dai Dole yasa Kamal Kiran Dr sbd antabbatar Masa da ko ruwa taqi Sha tunda akai rasuwar Nan take tsananin qaunarta da tausayinta yaqara shigarsa Dan kuwa dan yasan soyayyarta garesa cikin jininta take.






Ana fitowa sallar asuba tafara hango qauyensu maimakon taji sassauci a zuciyarta saitaji hankalinta ya qara tashi gabanta ya tsananta fa'duwa ta tsaya cak tareda 'dago fuskar jaririn ta kalla hawayen idonta ya gangaro ya sauka har kan fuskarsa ta maidasa jikinta ta rungume ta nufi cikin garin zuwa lokacin gari yafara haske daqyar takai kanta qofar gidansu sbd yanda qafafuwanta sukai Mata nauyi suna hardewa ta tsaya bakin qofar gidan zuciyarta na bugawa da tsanani cikin fargaba da tashin hankali ta cira qafarta daqyar tasa cikin gidan.



Vote
Comment
And share
[9/21, 7:48 PM] Aysha Galadima: *_EZNAH_*🌹
_wattpad@mamuhgee_




*12*
Hannu ya miqawa 'daya daga cikin yaransa aka miqo Masa bindiga.

Ciro wata shar6ebiyar wuqa mai Kama da maciji yayi daga takarminsa tareda kallonta cikin rashin imani da rashin tausayi ya damqo wuyanta ya shage da qarfi yace,

Zaki fa'da Mana inda takardun suke ko kuwa haryanzu kinfi buqatar mu aikaki zuwa inda  uwar saheeb dinta?

Qoqarin jawo numfashinta dake shi'dewa take sbd shaqar ta rintse ido cikin azaba tafara Shure Shure tana qaqarin 6an6are hannunsa daga wuyan nata.

Cikin takaici yayi wurgi da ita ta fa'di tareda sakin Wani wahalallen nishi Nan take jini ya 6alle Mata ta 'dago daqyar ta bu'de baki tace,

Dan Allah kayi gaggawar kasheni....

Bata qarasa ba ya saitata da bindiga tareda take cikinta ahasale

Fitsari ne yakusa qwacewa Anano  cikin tsananin tsoro da tausayi yasata sakin qara da qarfi Dan tuni tagama jiqewa da zufa da hawaye jikinta ba inda baya rawar tashin hankalin abinda take gani.

A rikice dukkaninsu suka waiga cikin tsananin tashin hankalo Jin qarar alamar ana ganinsu kenan.

Turesa tayi da qarfi tareda tattaro qarfi ta tashi takuma guduwa quryar dajin cikin azaba Dan tuni ciwon mara yafara cin qarfinta

A rikice yace yaransa subita shikuma ya nufi gurinda yajiyo ihun cikin zafin nama Yana gyarawa wuqar hannunsa Zama Dan Koma waye farke cikinsa zaiyi bayan ya qwaqwale idanuwansa daya gansu.

Tana ganin ya nufo gurinta hankalinta yayi mummunan tashi Nan take taji numfashinta na neman barin jikinta sbd tsoro a gigice ta miqe tareda kusawa itama dajin da gudu tana waiwayensa shima tuni ya dafe Mata.

Wata qatuwar bishiya tagani batareda tsoron me zata tarar acikiba tashige cikinta tareda Jan haki ta rufe jikinta tana 'dauke numfashinta tareda toshe bakinta sbd kukan dake qoqarin fito mata.

Sosai ciwo yafara cin qarfinta ta 'dafe mararta tana waiwayensu cikin azaba.

Jitayi an fixgota da qarfi a tsorace ta bu'de baki Anano tayi saurin rufe Mata baki tareda sake janyo haki ta rufesu.

Rintse idanuwa nafeesat tayi tareda sakin Wani azababben kuka tana toshe baki sbd azabar datake tsananin ji cikin mararta musamman yanda takeji ruwa nabin qafafunta.

Cikin tsananin kuka da tausayi Anano ta riqe hannunta sbd ganin mummunan halinda take ciki Amma ba halin wani motsi.

Ganin kamar nafeesar zata iya rasa ranta sbd yanda tafara mimmiqewa tana wata irin jijjiga yasa ta leqo kanta bataji motsinsu ba ta fito tareda kamo nafeesar suka fara gudu duk da nafeesar Bata iyawa sosai.

Gasu can ku kamosu su duka akashesu.

Waigawa tayi cikin tashin hankali kafin ta sake matse hannun nafeesat suka fara gudu.

Binsu sukeyi ganin kamar zasuyi musu Nisa yasa ya tsaya tareda saita bindiga ya harba musu.

Wani irin Nishi nafeesa tasaki sbd shigarta da bullet yayi ta fadi kife kan cikinta.

Kuka Anano tasaki cikin tashin hankalin dabata taba ganiba a rayuwarta ta sake kamo hannun nafeesar tanason tada ita.

Girgixa Mata Kai tayi cikin kukan azaba daqyar tace,

Ki tafi,kici gabada gudu karsu kamaki zasu kasheki kema.

Girgixa Kai Anano tayi cikin tsananin kuka tace,

Bazan iya tafiyaba.

Sake kamata tayi suna miqewa tsaye yasake harbowa still nafeesa yasamu tayi baya zata zube Anano tayi saurin riqo hannunta suka zube tare cikin rashin sa'a Ashe sun kawo kusada wani dogon cliff mai tsananin zurfi nan suka fara gangarawa suka fa'da.

Wani qaton dutsi kanta ya daka tasaki nishin azaba Mai qarfi Amma cikin dauriya ta daddafa ta tashi zaune ko gani sosai batayi ga wani irin juyawa da kanta keyi.

Daqyar ta lalabo nafeesa cikin azaba ta juyo da ita daqyar sbd a kife ta fa'do ko motsawa batayiba.

Jijjigata tayi cikin tsananin tsoro da tashin hankali.

Wani irin mugun Nishi taji nafeesar tayi Wanda yayi matuqar Bata tsoro Sai kawai taji Abu a gabanta.

Baya tayi a tsorace jikinta na makyarkyata zuciyarta na bugawa kamar zata bar jikinta.

Cikin qarfin hali nafeesa da numfashi ke qoqarin barin qirjinta ta kamo hannunta ta saka Mata wani irin zobe tareda damqe hannunta cikin azababbiyar murya da Bata fita tace,

Dan allah mena Haifa?

Cikeda tsoro jiki na kyarma ta matso takai hannu na rawa ta tabo murya na rawa tace,

Namiji.

Wani wahallalen Nishi nafeesa tasaki tareda sake damqe hannun Anano murya a karye tace,

Dan Allah ga amana Nan Allah yabaki sbd zuwanki Nan ya nuna kina cikin wannan qaddarar kema,
Nice na haifesa Amma kece Zaki Zama uwarsa sbd wannan itace qaddararmu.

Cikin tsananin kuka da tsoro murya a shaqe Anano tace,

Dan Allah ki daina magana kina bani tsoro..

Wasu hawaye ne suka gangaro gefen idon nafeesar murya na karyewa tace,

Nabaki shi halak malak matuqar Zaki iya riqesa sbd koya koma gidan mahaifinsa kashesa za'ayi kamar yanda aka kasheni hakama za'a kashe mahaifinsa...

Sunan mahaifinsa ABDUL SHAKUR Amma ana kiransa da SAHEEB AB..... Bata qarasaba jini ya 6alle Mata daga mahaifarta Ba qaqqautawa,

Kuka Anano tasaki Mai qarfi lokacinda taga numfashinta ya fita Koda Bata San komai akan mutuwaba ta tababbatarda mutuwace tayi Amma qwaqwalwarta takasa yarda da hakan jiki na rawa tafara
Jijjigata  da qarfi cikin kuka Mai tsanani tace,

Meyasa Zaki mutu kibarmin 'danki alhalin bansan ya zanyi dashiba,
Meyasa qaddara ta raboni da abokanaina na taho na tararda wannan mummunar qaddarar.

Kuka takeyi sosai jikinta ba inda baya rawa.

Cikin sanyin jiki takai hannunta dake matuqar rawa ta 'dauki yaron Sai kawai ta fashe da wani sabon kukan sbd tsananin tausayin kanta da nasa daya shigeta Dan ko kuka baiyiba bare wani motsi sbd azabar dayasha kafin a haifesa tasan Kuma ba lallaine Suma su samu tsira da ransuba daga hannun Yan daban.

Hijabinta ta zare tareda na'desa aciki ta kaisa qirjinta ta rungume ahankali Nan take taji tsananin qaunarsa na shiga jininta.

Cikin kuka tace,

Bansan dalilin dayasa Allah yakawoka rayuwata ba,
Wannan qaddaratace kaman yanda mahaifiyarka ta fa'da,
Na rungumi wannan qaddarar da hannu biyu nayi alqawarin riqeka tamkar Dan dazan Haifa,
Nayi alqawarin Zama jajirtacciyar uwar da bazan Bari Akira da gurbataccen sunaba matuqar ina Raye Kuma nayi alqawarin jure komai zai biyo.,,

Kukantane yafara qara sauti tayi saurin cusa Kai cikin qafafuwanta sbd  Kar sujiyo sautin kukan..



#vote
#comment
#and share
[9/21, 7:48 PM] Aysha Galadima: *_EZNAH_*🌹
_wattpad@mamuhgee_




*16*
Ahankali baffa ya 'dago ya kalli yanda take aikin cikin sanyin jiki duk saiyaji qaunar yarsa da tausayinta Dana yaron ya qara shigarsa ya bu'de baki ahankali yace,

Zo Nan Anano.

'dauraye hannayenta tayi ta taso ahankali ta zauna kusadashi ya kalleta dakyau yace,

Anano bazamu bar yaron nanba a gidan Nan sbd mumaganganun dake yawo zasu Bata Miki suna su Bata Mana zuria shiyasa na yanke shawarar Yusuf da Usman zasu kaisa binni gidan marayu.....

Kaka tasake ahankali batareda yakai qarshen zancen nasaba.

Shiru yayi Yana sauraron kukan nata ganin batada niyar dainawa yasa ya dafa kanta yakira sunanta.

Bata 'dagoba saidai tadan tsagaida da kukan.

Cikin tsananin qaunarta dake rinjayarsa kowane lokaci yace,

Anano wlh da inada wani zabin bayan wannan da bazan rabaki da 'dannan ba sbd koba komai mun taimakesa Kuma bamusan baiwar da Allah 6oye cikin alamarinba saidai vanida wani zabin kodan gudun lalacewar sunanki.

Cikin kuka ahankali tace,

Baffa Dan Allah karka biyewa maganar mutane ka fasa abinda kayi niyya na taimakawa marayan Allah dabaisan kansaba.

A qule Yusuf yace,

Ke dallah ki rufe Mana shegen bakinki badan shegen iyayinki da rawar kanki ba da duk haka Bata faruba,
Wannan yaron yagama barin gidannan Dan wlh bazai zaunaba.

Cikin takaici Aliyu ya kar6e zancen da cewa,

Wama yasani ko shegene uwar tasa ta Haifa.

Katsesu baffa yayi da cewa,

Koma dai meyene shi yaron bayada laifi tako Ina Kuma kamar yanda Anano tace munyi niyar taimakawa sabida Allah Kuma zamuyi.

Tunda suka fara magana Inna ko inda suke Bata kallaba sai lokacin takallesa cikeda mamakinsa tace,

To yanxu abinda takeson shi kake nufin za'ayi kome?

Eh'''yafada Kai tsaye tareda kallon jafar da tuni jaririn ke hannunsa Yana 'dan jijjigasa sbd dagashi Sai Anano ke saukarsa a gidan Sai Inna idan zatai Masa wanka Amma ko baffa Sam bai ta6a daukarsaba iyakaci dai Yana tausayinsa shima sbd ananonsa nasonsane kawai.

Cikin sakewar fuska yace,

Jafar meye shawararka akan hakan?

Kallon yaron yayi yakuma kalli Anano datai zuru cikin hawaye Sai yaji tausanta da 'dan yakalli baffa yace,

Baffa shawarata 'dayace
Komai zakayi kayisane domin Allah badan waniba kokuma badan abinda wani zai fa'daba..

Murmushin qarfin hali baffa yasaki cikin jinjina Kai yace,

Usman da jafar ku shirya zuwa jibi zamukai Anano gurin gwaggwonta tareda yaron zuwa wani lokaci idan komai ya lafa saita dawo.

Ajiyar zuciya Inna ta sauke duk dai bahaka tasoba tasone su yarda qwallon mangwaro su huta da quda Amma ko ahakan da sauki sbd itadai dama damuwarta zaman yaron ne agidan bataso ga ananon da shegen taurin Kan tsiya sbd samun daurin gindi daga baffan.

Yusuf da aliyu kuwa miqewa sukai suka ficewarsu sbd takaicin hukuncin da baffan yanke na barin yaron.

Anano kuwa jikinta ne yayi sanyi ta matsa ta riqo hannun baffan ta kallesa hawaye na gangaro Mata tace,

Baffa Allah zai saka maka da mafificin abinda kayi Koda a bayan ranka ne.

Shafa kanta yayi yace,

Allah yabiyani ta hanyar kawo farin ciki da haske Mai dorewa a rayuwarki ananona.

Jafar ne ya katse yanayin nasu na shaukin uba da 'ya ta hanyar cewa,

Yaron haryanxu bashida suna..

Fuskar Anano baffa ya kalla yace,

Anano za6ar Masa suna.

Sunkuyar dakai tayi cikin fargaba tace,

Abdulshakur..

Su Inna sunaji suna gani baffa yasa jafar ya Kama rago 'daya ya yanke aka ra'dawa yaron suna abinma Sai ya daina Basu takaici sbd ganin yanxu Kam su baffa kawai wahalar ta fasha sukam sun cire hannunsu musamman aliyu daya tsani Koda ganin yaron.

Kafin jibi ranar tafiyar tayi gata da kulawa sosai baffa da jafar suka shiga nuna Mata harma da Usman yanxu da ananon ke basa tausayin ganin Allah ya 'dauki son abinda batada alaqa dashi yasa Mata kamar jininta saiyake ganin hakan da wani 6oyayyan sirri daga Allah.

Ranar dazasu tafi sosai tayi kuka kamar ta tafi kenan musamman dataga Inna na farin ciki da tafiyar tasu Dan har Allah Allah take su wuce.

Basu shiga motar mandeba sbd gudun tsegumi Kai tsaye doguwar tafiya sukai da qafa har bakin babban titi kafin suka shiga motar shiga yola.

Tunda suka iso taji hankalinta yafara tashi Dan hakanan takejin fa'duwar gaba.

Direct wata qaramar unguwar talakawa suka nufa cikin adaidaita jafar dayasan gidan Yana nunawa Mai napep 'din inda zaibi.

Har bakin kwanar layin gidan aka ajesu Nan baffa ya biyasa suka gangara suka shige lungun.

Ba wata tafiya sukaiba suka iso gidan jafar ne agaba Yana kwada sallama suna shiga Dan qaramin tsakar gidan asiya matar qanin mijin gwaggon daya rasu ta fito 'dakinta tana Sanya hijab tana ganin jafar ta washe baki tana musu sannu da zuwa tareda 'dauko musu tabarma tana cewa,

Gashi kuwa gwaggon batanan tanacan gidan datake aiki rasuwa akai musu matar gidance ta rasu gurin haihuwa.

Allah sarki Allah yaji qanta....cewar jafar dake qoqarin juyawa waje yafadawa baffa da Usman gwaggon batanan.

Kallon hijabin anano asiya tayi ganin Sai muqu muqu take batason asan meyene aciki tace,

Ananon gwaggo bazaki zaunaba.

Qoqarin zaman take jafar yasake shigowa Yana kallon asiya yace,

To Wai zamu samu Wanda yasan can gidan da gwaggon take Sai akaimu?

Eh Bari nakira Bello yananan waje saiya kaiku yasan gidan.

Qofar gidan ta nufa saidata gaisadasu baffa kafin ta kirawo bellon a gidan maqwaftansu inda suke kallon qwallo 'dakin abokinsu.

Sallama sukai Mata suka nufi titi Bello Kam Yana tare Mai adaidaita kwatancen gidan yayi Masa Dan shikam baiso ya rasa kallon qwallonsa Dan yau wasar na zafi sosai.

Yana fara kwatancen Mai adaidaita yace ya gane sbd gidan ba wani a boye yakeba idan kaje anguwar danma masu adaidaita da mashin Sam basa shiga layin Dan mugayen soldiers din dakecin uwarsu na gadin gidan.

Nesa ka'dan da gidan ya tsaya ya nuna musu gidan da hannu suka biyasa ya juya suka nufi gidan kowannensu gabansa na 'dan tsinkewa sbd ganin gidan da akace nanne ga sojoji dasuke hangowa tun daga nesa.

Wangale qaton gate din sukaga anyi wasu jibga jibgan motoci suka fito aguje kamar zasu tashi sama ta qarshen ita ta tsaya sauran sojojin dake qofar gidan suka fa'da ciki aka figa da qarfi harsaida su baffa suka daka wani mugun tsalle suka ra6e gabansu na qarasa tsinkewa Dan Anano tuni taji ta tsinke tana adduar Allah yasa ba anan gwaggon zata zauna da itaba sbd Allah yagani arayuwarta ba abinda ta tsana take tsoro irin soldier.

Baffa ma Kam wani irin mugun yawu ya ha'diye na tsoro da tausayin ananon Dan shima Kam Yana tsoron kaki( kunsan Fulani da tsoron soja😂😜 just kidding)

Usman damashi tuntuni atsure yake tunda suka iso yaga mutane sunyi Masa yawa Dan harwani jiri jiri yake gani Dan baita6a fitowa birni duk cikinsu jafar ne kawai Mai zuwa shima sbd visiting din ananon ne idan tana makaranta.

A darare suka Isa bakin gate din kusan atare suka 'dan sauke ajiyar zuciya ganin ba soja ko 'daya days saura.

Cikin Yar fargaba jafar ya qwanqwasa qaramar qofar qatoton gate din dayake jabiru na kusa Yana hamdalar samun yancin aikinsa oga saheeb Yakoma da gayyar sojojinsa.

Bu'de qofar yayi Yana ganinsu ya fito tareda jawo qofar Yana kallonsu a 'dage sbd daka gansu kaga fulanin qauye futuk ananon cema ta'dan banbanta ka'dan acikinsu.

Ganin irin kallon dayake musune yasa jafar jiki amace yace,

Dan Allah gwaggo hinde muke nema.

Sake kallonsu yayi dakyau kafin yace,

Wa za'a cemata sunxo?

Kacemata baffa salisu ne yayanta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login