Follow us on social media

Showing 6001 words to 9000 words out of 61825 words

Chapter 3 - EZNAH Sirrin Jini by Aysha Galadima

daga qauye tareda Anano.

Juyawa yayi yashige tareda maqala sakata ya nufi babban part 'din oga saheeb.

Zagayawa yayi ta qofar baya inda 'dan qaramin boys quarter din part dinsa Wanda ke 'daukeda Palo 'daya da room daya Sai toilet.

Ta qofar kicin din part dinsa zaka it's fadawa direct palon gwaggon Wanda anyi hakan ne Dan aikinta basaita zagayo ta qofar paloba Kuma nafeesa ce tasa akai Mata hakan sbd tsananin qaunarta da gwaggon hakama shima saheeb sosai Allah yasa Masa qaunar gwaggon da ganin girmanta.

Qwanqwasa qofar palon zaiyi saigata ta fito zataje can 6angarensu mum asee.

Da mamaki take kallonsa tace,

Mal jabiru lafiya naganka nan....

Baqi kikayi sunce baffa salisu da anono ne koma meye sunan na manta....

Da sauri ta nufi gate din cikin farin ciki dakuma fargabar Allah yasa lafiya wannan zuwa haka.

Shigo dasu tayi har cikin boys quarter palonta inda baffa daqyar ya zauna takawo musu ruwa suka gaggaisa baffa yace,

Dagacan muke gidanki aka kawo mu Nan.

To hamma salisu Allah dai yasa lafiya.

Anano ya nuna Mata ta waigo Sai alokacin ta lurada 'da ahannunta.

Zaro idanuwa tayi tana sake kallawa danta gasgata idanuwanta tace,

Na boni ni hindatu menene wannan ahannunki Anano.

Ba yanda kike tunani bane Nan dai yayi Mata bayanin komai ya 'dora dacewa,

Nakawota da kainane danta zauna agurinki idan komai ya lafa saita dawo.

Badan zuciyarta tagama aminta da zancen 'dan bana Anano bane jiki amace tace,

To shikenan zanyi magana da Mai gidan idan ya amince saimu zauna anan idan bai aminceba zamu koma gida Dan dama jiya da'akai kwana bakwai da rasuwar Mai 'dakinsa naso tafiya yace nayi zamana anan harsai yace na tafi.

Ba yanda bataiba dasu su tsaya suci abinci sukaqi musamman Usman da yake a firgice kamar ace qyat ya ruga da gudu.

Har titi suka rakasu suka tafi Anano da baffanta kamar karsu rabu musamman dayaga tana kuka ahankali.

Tundaga gida dama gwaggo ta kar6e 'dan tagoyasa shiyasa Koda suka juyo ananon ke tafiya ahankali tana share hawaye jitake kamar karta koma gidan.

Suna shigowa direct part din mum asee suka nufa Dan Inna ta gabatarda ananon daidai zasu shiga Kamal shikuma yafito cikin sauri zai fita saiji yai yayi karo da mutum ba zato.




Please ku ringa saurarawa kuga menene zai faru kafin ku ringa magana akan abinda yadace da Wanda bai daceba afterall karku manta novel ne is not reality so Dole wasu abubuwan zasu banbanta da reality so please take note#no bad comments ko Kuma judgen abinda bakusan qarshensa ba Dan bakusan me writer ta shirya rubutawa agaba ba...


#vote
#comment
#share
[9/21, 7:48 PM] Aysha Galadima: *_EZNAH_*🌹
_wattpad@mamuhgee_




*14*
Zaune baffa yake kan tabarma yayi zuru dawowarsa masallaci kenan
Jafar na gefensa zaune shima cikin rashin da'din Rai Sai aliyu dake tsaye gefe shima dai ran ba da'di
Hamma Yusuf  da Usman kuwa daga masallaci gidan mande direba suka nufa suka sanar dashi zasu bisa idan zai koma da safen sbd su dubo can din koza'a dace Dan Sam Babu Wanda ya rintsa a gidan tunda motar daliban ta iso aka nemi Anano ba'a gantaba Nan hankali yayi tsananin tashi gasu ubaidah da nusaiba Koda aka tambayesu Sai kuka suke su kansu basusan Ina Ina zasuce takeba mande direba kuwa kusan hankalinsa yafi na kowa tashi musamman dasu Yusuf sukace ga hukuma zasu miqasa matuqar ba'a gantaba ko Kuma wani Abu ya sameta.

Inna data fito 'daki sanye da hijabin datayi sallah dashi ta gaida baffan bai amsa mataba sbd takaicinta dayakeji na yanda take qoqarin nuna ko inkula kan 6atan na Anano Wai ita kawaici,
  kicin ta nufa tafara qoqarin hura wuta.

Harara baffa yabita da ita Rai a tsananin 6ace cikin hasala yakira sunanta ta qaraso gabansa daidai Nan idonta ya sauka kan Anano dake tsaye qofar shigowa.

Jafar ne yafara ganinta bayan inna yayi saurin miqewa cikin farin ciki tareda hamdala yakira sunanta da 'dan qarfi.

Da sauri baffa ya juya batareda ya balbale Inna da fadan da yayi niyya ba ya miqe Yana cewa,

Alhamdulillah ya Allah,,,,

Qarasa shigowa cikin tsakar gidan tayi ahankali qafafuwanta na hardewa kamar Wadda kwai ya fashewa aciki tazo gaban baffa ta tsaya tareda sunkuyar da kanta qasa sabbin hawayen fargaba da tsoro na gangaro Mata.

Cikin tsananin kulawa da farin ciki baffa ya riqo hannunta 'daya ya nufi tabarmar daya taso Yana cewa,

Ananon baffa me.....

Cak ya tsaya Jin Bata motsa daga inda takeba yayi saurin juyowa Sai alokacin ya lura da Inna da aliyu dasuka kasa motsi sun qurawa ananon Ido cikin wani irin yanayi
Maida kallonsa yayi ga ananon saiyaga tuni sautin kukanta yafara fita ahankali.

Sakin hannunta yayi tareda fuskantarta cikin  damuwa da kulawa zaiyi magana idonsa ya lurada  abinda ke hannunta dunqule cikin farin hijab 'dinta.

Kallonta yafarayi tun daga samanta zuwa qasa,
Gabaki 'daya jini ne a uniform dinta ga fuskarta datai jajir ta kumbura...

Daqyar ya tattaro yawu ya ha'diye suka wuce maqoshinsa daqyar kamar zasu yankesa yakalli ananon cikin son yaqar wani tunanin dakeson shigarsa idonsa qyar akan hannuwanta yace,

Ananon baffa meya sameki Kuma menene wannan a hannunki?

Inna da tuni tafara mantawa da kawaici cikin tsananin fargaba ta matso tareda Kai hannunta dake rawa zata bu'de baffa yayi saurin riqe hannunta still idanuwansa nakan Anano yace,

Anano meya sameki?
Kafadamin idan ba wanine yayi Miki mummunan illa ba....

Kuka tasake fashewa dashi Mai qarfi daidai shigowarsu Yusuf suka qaraso da sauri saidai suna qarewa kayan jikin Anano kallo gabansu yayi mummunan fa'duwa sbd sun saddaqarda fyade akayiwa 'yar qanwar tasu
Bango Yusuf ya dafe Yana karanto innalillahi cikin tsananin tashin hankali.

Usman ma cikin tashin hankalin ya sulale qasa zaune jafar dayake da tsananin sanyi da karyayiyar zuciya tuni yafara hawayen tausayin 'yar qanwarsu da aka 6atawa rayuwa aliyu kuwa baffa yayi saurin riqewa ganin zai iya zubewa qasa sbd halinda yashiga.

Cikin zafin nama da takaici inna ta fuzge hijabin Saida jaririn yakusa fa'duwa cikin wani mugun sauri Anano tayi saurin zubewa qasa ta taresa tareda qanqamesa da sauri jikinta na rawa shikuwa jaririn Sai alokacin yasaki wani irin kukan jarirai Wanda tunda yafado Sai alokacin yayi kuka.

Yusuf,Usman,aliyu da baffa kusan dukaninsu atare suka zabura sunakai kallonsu ga jaririn Dan sai alokacin suka sanda akwai wani Abu acikin hijabin Anano din.

Inna ma ta razana matuqa da ganin jaririn duk da dama tayi zargin akwai wani Abu a hijabin Amma Bata ta6a kawo zataga jariri ba.

Qurawa yaron idanuwa sukayi cikin tsananin fargaba jafar kuwa jiki na rawa haryana tuntu6e yayi saurin Isa qofar gidan ya rufe harda maqala sakata Dan karma ajiyosu ko wani yashigo gidan.

Cikin rawar hannu baffa ya nuna jaririn Yana kallon usman dake kusa dashi yace,

Usman dubamin meye wannan kamar jariri nake gani....

Jiki a mace usamn yayi qasa da kai murya a sanyaye yace,

Baffa jariri ne a hannunta Kuma me Rai ba matacceba sabuwar haihuwa ma.

Anano''''' Baffa yakira sunanta cikin kammalalliyar murya.

Kasa 'dagowa tayi saima wani kukan data fashe dashi.

Sake Kiran sunanta baffa yayi ta rintse kumburarun idanuwanta da sukaci kuka harsuka gaji ta girgixa Kanta da yayi mugun nauyi sbd kukan datasha dakuma ciwon dayake Mata ta bu'de baki daqyar murya a dashe tace,

Baffa Dan Allah kayi hkr wlh ba abinda kuke tuna.....

Aliyu da tuni zuciyarsa tafara tafarfasa ya wurga Mata wani mugun kallo da jajayen idanuwansa a hasale yace,

Kifadi abinda ke hannunki na waye aka tambaya ba tareda 6ata Mana lokaciba.

Yawun tashin hankali da tsoro ta ha'diye tareda sunkuyar da Kai tace,

Nawane Amma bani....

Wani gigitaccen mari Inna ta saukar Mata tana 'dauke hannu aliyu ya sauke Mata nasa harsaida tayi zaman Yan bori.

Cikin tsananin hasala da zafin zuciya Yusuf ya karbi zancen Yana watsa Mata wani mugun kallo yace,

Dan ubanki Zaki bu'de baki kifa'da Mana 'dan uban waye ahannunki kosaina karya Miki wuya..

Kuka tasake saki tareda qara qanqame 'dan ta rarrafa gaban baffa da tuni jiri yakusa zubar dashi Saida jafar ya taresa ta riqe qafarsa da hannu 'daya cikin hawaye tace,

Baffa Dan Allah ka....

Hannu baffan ya'daga Mata daqyar Dan tuni bakinsa ya mutu Dan har wani rawa yaji zuciyarsa nayi sbd fargaba Dan har lokacin yakasa yarda da abinda ke Shirin tabbatuwa agabansa ya kalleta kalar tausayi murya a sanyaye yace,

Hassana..,

Rintse idanuwanta tayi zuciyarta na Kara karyewa Jin yau yakirata da ainihin sunanta.

Anano wannan yaron na hannunki nakeson kifadamin na waye dan ayi gaggawar mayar dashi tun kafin afara shigowa yi Mana barkar dawowarki agansa ayi Mana wani tunani Dan haka kiyi gaggawar fadar inda kika tsintoshi a mayar dashi Dan wallahi bazai zauna a gidan Nan ba...

A gigice ta 'dago hankalinta na tsananta tashi tuni idanuwanta suka qafe jikinta ya'dau sabuwar rawa.

Wata razananniyar tsawa dabai ta6ayi arayuwarsaba yayi Mata cikin qufula yace,

Ki bude baki kiyi magana.

Rawar jikinta ce ta qaru sbd baffa da tuni tsananin 6acin ransa ya bayyana

Kallon Yusuf baffa yayi Rai a6ace yace,

Kar6esa ka....

Cikin tsananin kuka ta qara qanqamesa tace,

Baffa dan Allah karka rabani dashi bazan iya rabuwa dashiba.....

Duka Inna da aliyu suka rufeta dashi lokaci guda Nan ta sake qanqame 'dan sbd Kar duka ya samesa abinda ya qara hasala kowa kenan Inna ta jawo icce tana cewa,

Gwarama mu kasheki cikin gida tun kafin ma wani yasanda abinda ke faruwa.

Riqe iccen Yusuf yayi yana kallon ananon yace,

'dan uban waye akace?

Ha'diye sabon kukan dayazo mata  tayi Kai tsaye tace,

Nawa ne.

Fixgota Inna tayi  tajata ta jefa 'daki batai wata wataba ta zare wandon makarantar dake jikinta wani razanannen salati tasaki tayi baya tana Kiran sunayen Allah jikinta tuni yayi sanyi yanxu Kam kukane ke Shirin qwace Mata ta fito kallo 'daya tayiwa baffa saita sauke Kai hawayen datake dannewa suka gangaro

Zuciya baffa ya dafe Sai kawai sukaga yayi baya ya zube Yana wata irin jijjiga jafar da Usman sukai kansa Yusuf kuwa waje ya nufa da sauri Dan Kiran mande direba sukai baffan qauyen gabansu wurin sani Mai chemist Dan su shine likitansu.

Aliyu kuwa dakin da anonon take tana fidda kuka Mara sauti hakama yaron tuni ya kara'de gidan da kuka ya nufa a zuciye yahau jibgarta baji ba gani Inna ma zubewa tayi qofar 'dakin tana hawaye cikin mummunan tashin hankali da sanyin jiki.

#vote
#comment
#share
[9/21, 7:48 PM] Aysha Galadima: *_EZNAH_*🌹
_wattpad@mamuhgee_



*15*
Jiki na rawa su Usman suka kwantarda baffa Kan tabarma suka hau you Masa firfita ahankali yafara rage jijjjigar numfashinta ya 'dan farawa rage zaburewar dayayi ya lumshe idanuwansa yayi shiru Yana karanto sunayen Allah a zuciyarsa Dan yasamu nutsuwarsa ta daidaita ya fuskanci Anano Dan haryanxu shi bai yarda da wannan shegen 'dan Mai kukan kwa'di ita ta haifesaba.

Usman ne ya miqe yashiga daki ya qwace Anano daga dukan da aliyu ke Mata cikin tsananin bacin Rai yace,

Wai Kai aliyu meyasa baka auna komai kayisa cikin mizanin hankalin cikakken 'dan Adam ne?

Kana tunanin dukan dakake Mata zaisa ta fa'di gskia ne ko kuwa?
Mitssw''''yaja 'dan qaramin tsaki tareda riqo hannun Anano ya miqar da ita Amma Sam ko tashi Bata iyayi ya miqa hannu zai kar6i yaron tayi saurin 'dago kumburariyar fuskarta ta kallesa saitaga fuskarsa a ha'de ba alamun wasa saita miqa masashi jikinta na rawa gabanta na fa'duwa.

Kwantarda yaron yayi yariqota ta fito tana tafiya daqyar ya kalli jafar da duk yayi zuru zuru yace ya debo Mata ruwa a bokiti tayi wanka.

Ta gefen Inna ta wuce tana kallon yanda innar ke keta faman goge hawaye ta maida kallonta gurin baffa yanayin data gashi acikine yasa hankalinta tashi ta juya 'daki  duk suka bita da kallo

Jaririn ta 'dauko jiki a tsananin sanyaye ta nufi gurinda baffa yake Yusuf yayi saurin daka Mata tsawa Rai a6ace.

Qin tsayawa tayi saidata Kai gaban baffa ta durqusa hawaye nabin fuskarta murya na rawa tace,

Baffa don Allah karka Bari zargi yasa ka cutatar da kanka,
Wallahi wallahi wallahi baffa ban ta6a aikata Zina ba,
Ban ta6a ra6ar ko wani Mai akatawaba,
Wannan jaririn nawa kamar yanda Wadda ta haifesa tabanishi kuma nafada muku da farko Amma wlh baffa bani na haifesa ba.....

Wani mugun kallo aliyu da Yusuf harma da Inna ke binta dashi sbd Jin abinda take fa'da Wai an Bata kyautar jariri.

Baffa kuwa jajayen idanuwansa ya bu'de ahankali ya kafeta dasu cikin rawar murya kamar zaiyi kuka yace,

Anano Abu 'daya nakeson nasani akan jaririn Nan Wanda shika'dai ne damuwata Kuma daga kin fadamin gskia wlh zuciyata Zata iya 'daukar koma meye sauran bayanin
Anano jaririn Nan na waye?

Sabbin hawaye ne suka gangaro Mata ta share murya a dake tace,

taimakon uwarsa nayi lokacinda take naqudarsa Kuma tana haihuwarsa ta rasu.

Tsit sukayi jafar kuwa hambadala yasaki a bayyane aliyu da Yusuf suka bisa da mugun kallo cikin takaici dansu Basu yardaba.

Baffa kuwa tsareta yayi da Ido tsawon lokaci kafin yace,

Anano gskia Kika fa'damin?

Kai ta 'dago ahankali tace eh hawaye na sake gangaro Mata.

Yusuf da Usman ya kalla yace,

Suje inda tafada subi hanyar adubo gawar azoda ita.

Kanta ya maido kallonsa Nan take yaji zuciyarsa ta yarda da ita 'dari bisa 'dari ya riqo hannunta cikin nutsuwa yace,

Anano na yarda dake tako wanne 6angare Kuma natabbatarda bazaki aikata Koda makamancin hakanba Dan haka kiyi qoqarin ganin konan gaba baki rusa yardataba.

Kai ta 'daga ahankali gabanta na fa'duwar wane hukunci baffan zai yanke akan yaron.

Inna ya kalla Koda Bata fa'daba fuskarta ta nuna tashin hankalinta ya 'dan ragu saidai itama kamarsu Yusuf hankalinta bai kwantaba sosai da zancen ananon.

Cikin nutsuwa yace,

Ki tashi ki 'dora ruwa Anano tayi wanka.

Badan tasoba ta miqe ta nufi madafarsu tafara ha'da itace.

Anano kuwa har ruwan yayi zafi tana durqushe agurin Saida jafar ya cika Mata bokiti ya sirka yakai Mata qofar bayi takuna ta miqe jiki a sanyaye ta shiga 'daki ta tube ta fito sum sum tashige bayin.

Duk da tana cikin tashin hankali da damuwar makomar jaririn sosai taji da'din wankan Dan Nan take taji ta'dan warware ajikinta.

Tana gama wankan kafin takai ga fitowa yaron yatashi Nan take ya kara'de gidan da kuka cikin sauri ta janyo zaninta ta 'daura ta fito
Turus tayi jikinta na saki sbd ganin ba Wanda ya motsa cikinsu kamar basusan da acikin gidan ake kukanba.

Sanyi qalau jikinta yayi Dan kuwa taga tabbas ko barinsa ya zauna gidan baffa yayi bamai qaunarsa.

'dakin tashige bayan ta aje bokitin hannunta ta zauna kusada yaron Nan itama tafara nata hawayen Dan kuwa tasan daga ita harshi suna tsaka.

Saidataji kukan harya fara sanyashi laushi takai hannu ahankali ta 'dauke tareda qura Masa Ido Dan Sai alokacin tafara kallon fuskarsa.

Farine sosai Kuma da gani ba lallaine yayi baqi ba duk da dai bazata iya cewa ga fuskar mahaifiyarsa ba sbd komai yafarune cikin duhu..

Numfashi ta sauke ahankali cikin zuciyarta tace,

Allah yasa su hamma su gano gawarta asuturta kodan jaririn.

Sallama aka fara kwadowa a qofar gidan baffa ya kalli qofar da sauri zuciyarsa na 'dan tsinkewa ya miqe daqyar tareda tattaro 'yar nutsuwa ya nufi qofar aliyu nabin bayansa.

Murmushin qarfin hali yasaki lokacin dayaga Mal Garba maqwafcinsa yace,

Aa Mal Garba Kaine da safennan.

Cikin 'yar damuwa yace,

Nine Mal salisu an gari lafiya?

Lafiya qlau Mal Garba ya iyalin?

Alhamdulillah nace ko anji want bayani akan Anano kuwa?

Washe baki baffa yayi cikin qarfin hali yace,

Eh kaga shaf na manta na sanar maka tun a Daren jiyan tadawo Wai Ashe ita da qafa ta qaraso daga can rugar nuhu shiyasa ta iso dare sosai.

Masha Allah Abu yayi kyau dama dai nace ne nazo naji halinda ake ciki Kan 6atan nata Allah ya tsare gaba.

Amin Amin Mal Garba nagode.

Bayan tafiyarsa baffa ya Jima tsaye Yana tunani kafin suka juya suka koma cikin gidan Kai tsaye inna ya kalla yace,

Ki kimtsa yaron ki goyesa duk tsanani Kar kibari agane da akwaisa acikin gidannan.

To tace badan ranta yasoba saidan Bata qetare umarninsa ta miqe ta sake 'dora wasu ruwan.

Cikin qanqanin lokaci Inna tayi Masa wanka ta gasashi sosai ta 'debi sabuwar madarar shanu tabasa yasa sosai Nan take yayi luf bacci Mai da'di ya daukesa takuwa goyesa bayanta tasaka hijab bazaka taba cewa akwai 'da a bayanta ba.

Sai alokacin Anano ta'danji sanyi aranta take Kuma mamakin yanda takejin yaron har tsakiyar ranta.

Kamar jira ake Inna ta goyesa Nan take jama'a suka fara zaryar zuwa barka da dawowarta dakuma ganinta da'akayi.

Su ubaidah sunxo Nan suka hauta da fadan tafiyarta datayi Bata tsaya musu ba.

Itadai murmushin yaqe kawai take musu
Koda suka tambayi kumburin fuskarta da Jan idonta cemusu tayi batai bacciba ahanya qunama ta cijeta.

Sosai suka tausaya Mata duk da sun fahimci kaman Bata cikin walwala hakanan suka qarashi firarsu suka tafi.

Su Yusuf kuwa duk iya bincikensu Basu ga wata gawaba haka suka dawo suka sanarwasu baffa qarshe dai aka tattara zancen aka aje Sai bayan kwana biyu tukuna a yanke shawarar abinyi.

Tunda tadawo kusan komai ya canxa Mata ba kamar da ba da kowa gidan keji da ita kamar su lasheta Amma yanxu kaf yayunta iyakacinsu da ita ta gaidasu idansunga dama su amsa idan basuga damaba su qyaleta baffa da jafar ne kawai ke kulawa da ita Sai Usman idan yaga dama shima,

Inna kuwa kadaran kadahan ga baffa dayasata kulada jaririn Dole badan tasoba.

Sosai hankalin ananon hankalinta yafara 'dan kwantawa sbd ganin anbar zancen saigashi Randa sukai sati 'daya kwatsam zancen yafara fita Wai akwai jariri agidan Nan maganganu suka fara yawo hankalin baffa yafara tashi musamman da zancen yafara yaduwa Wai 'dan na Anano ne tunda dai ba Wanda zai haihu a gidan.

Zaune suke a tsakar gida yau duk sunyi jugum jugum bamai magana Sai Inna daketa aikin Kai kawon girkin dare datakeyi Anano kuwa tana zaune tana yiwa Inna wanke wanke jiki a sanyaye sbd tun Daren jiya taji hirar Inna dake bawa baffa shawarar akai yaron gidan Mai gari ace tsintarsa akayi.

Cikin sanyin murya baffa yace,

Idan muka kaisa mukace tsintarsa mukayi kenan mun bada damar daza'a yarda da zargin da ake Mana sbd zaaga meya Hana tun farko mukaisa Saida aka ganomu,

Kawai dai na yanke shawarar aikasa can binni gidan marayu kamar yanda Yusuf yace tun farko.

Da wannan tunanin ta kwana ta tashi sosai taji hankalinta yatashi sbd tausayinsa dakuma qaunarsa dake maqale aranta.




#vote
#comment
#share
[9/21, 7:48 PM] Aysha Galadima: *_EZNAH_*🌹
_wattpad@mamuhgee_





*17*
Ja baya yayi da sauri cikin 'dan 6ata fuska Yana qare musu kallo.
A 'dan ladafce gwaggo tace,

Yi hakuri kamalu Bata lura dakai bane baquwace duk a takure take shiyasa.

Kallon ananon yayi tundaga sama har qasa Nan take idanuwansa suka kyallo Masa kyanta da dirinta dazai fita matuqar tasamu kyakkyawar rayuwa musamman dogon hancinta daya qarawa fulani  face 'dinta kyau da tsari.

Wani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login