Follow us on social media

Showing 15001 words to 18000 words out of 26903 words

Chapter 6 - KUYANGA Daga Bauta Zuwa Daraja by Nabilancy Lu

08 Jul 2026

19

wasu kwanaki baizoba

Sannan takara tabbatarwa lallai yadau zafi da ita

Sati Daya da maganar cikin da *KUYANGA* Tazo dashi daga turai YARIMA yadawo

Magana ta yada ko ina na cikin gidan sarki

Wasu suna yarda na yarimane wasu kuma suna ganin bazai zama nashiba tunda ance yawonta take da maza dataje turan


KARSHEN TIKA TIKI TIK!!

Dawowar yYarima yasa kowa agidan yashiga murna domin ansan tunda yadawo kasar za,a samo matsaya akan cikin *KUYANGA*


Tana Zaune adaki tana tunanin data sabayi Zulaihat ta shigo da Sauri tace mata


"Zeenatu yi sauri kidauko hijabi muje an aiko sanarwa daga Fada Sarki nabukatarki agun Yarima yana can fadar da Kaf Ahalin Gidan za,ayi Zubeben kwarya...


Gabantane yafadi tareda dafe kirji take hawaye suka hau zarya akuncinta

Zulaihat tajata jiki tace mata "daina kuka kwantar da hankalinki me gaskiya yana tare da Allah Abinda kika Sani shi zaki fada kada kiji tsoro kada kuma kirage komai

*KUYANGA* Tahau gyada kanta taredajin karfin guiwa ajikinta

Zulaihat tace " muje inrakaki fadar......



πŸƒπŸΌβ€β™€πŸƒπŸΌπŸ‘­πŸšΆπŸΌβ€β™€πŸšΆπŸΌπŸ•΄πŸ½πŸ‘ͺπŸ‘©β€β€β€πŸ’‹β€πŸ‘©πŸ‘¨β€β€β€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€β€πŸ‘© fans kutaho rakiya mana

Duk masoyin *KUYANGA* kada yasake abarshi abaya ataho arakata Fadar *SARKI ABDALLAH*


MUJE ZUWA FANSπŸ˜…
[7/31, 11:29 AM] Ummi Tandama: πŸ“Ώ *KUYANGA...* πŸ“Ώ




*_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```


https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation




*Nabilancy Luv* πŸ’˜
(Auntyn S&S)



55-60


CARBI ne ahannun *KUYANGA* datake ja ackn burmemen hijabin dayake jikinta Addua kawai takeyi Akan Allah yabata Nasara yashige mata gaba yakuma dorata akan maimartaba


Gaban tane yafadi ganin yanda fada ta cika da ahalin gidan daga matansa da yaransa YARIMA da LAMIDO da kuma fadawa da Galadima da sauran masu mukaman gidan Bayi ne kawai basa gurin

Kowa ita yake kallo itako kanta akasa tasami guri anesa dasu tazauna Zulaihat ma ta xauna kusa da ita

Maimartaba yana ganin shigowarta yayi Gyaran murya ganin tazauna nesa da mutane duk aka nutsu ana kallonsa

Yace " *KUYANGA ZEENATU* Ke muke jira kuma adalilinki muka taru anan Dan haka kidawo tsakiyar mutane kizauna domin ki amsa tambayoyi daga bakina

Tayi saurin tashi tabi umarni takoma tsakiyarsu inda fadawa suka bata guri akusa da Yarima dayake kusada Sarki LAMIDO na gefen yariman Wanda tunshigowar *KUYANGA* Yazuba mata idanu yana kare mata kallo

Bayan ta zauna Mai martaba yawatso mata tambayar data rikita mata kwanya

"Dawa kike tarayyar fasikanci a kasar waje ???

Ahankali tace " Bakowa,

Yace "To waye yayi miki ciki?

Hawaye na zuba a idonta tace " cikin jikina bana kowa bane illah na YARIMA!

fadawa suka hau salati
Yayinda Sarki ya rintse idanu jin yasami jika Dan gaba da fatiha a ckn gida

Suko matan kirji suka dafe alamun mamaki

Yarima kuwa fuskar sace ta nuna bacin rai tsababa ji yake tamkar yashaqeta ta mutu akan wannan tonon sililin datayi masa


LAMIDO kuwa girgiza kai kawai yk yi na al,ajab sannan yana mamakin yayan nasa da wannan hali

UMMAH mahaifiyar Yarima Ta dakawa *KUYANGA* Tsawa "karya takeyi munafuka saikin nemo Wanda yayi miki inma ackn turawan da kika barosu kika gudo


Sarki ne yatsawatar mata akan tayi shiru

Yajuya kan Yarima yace masa " YARIMA ya abin yake? kanada tabbacin naka ne ko ba nakaba?

Yarima yaji sassanyar Tambaya sai yahau gyada kai yana fadin "Ranka ya Dade bansan da maganar ba baninayi mata cikiba

Sarki yace " to wanene?

Yarima yayi shiru

Jin yayi masa shiru yasa yaci gaba da tambayarsa

"Sau nawa kataba Kusantar ta?

Nan ma yayi shiru kansa akasa yahau fidda xufa

Ganin haka sarki yace " tun anan alamu sun nuna cikin kane Dan haka bazaka wulakanta Rayuwar yarinya kaci riba ita ta wulakantaba Dolene ka Aureta....

"bazai yiyuba!

Cewar UMMAH tafada ranta abace

" don ci baya sai D'ana ya Auri KUYANGA gaskiya da sake

Mai marmataba yanunata da yatsa "kishiga taitayinki Fulani idan Dan kine nima nawane nama fiki iko dashi danhaka magana dole abita in anason zaman lfy dani

YARIMA yadukar dakansa yana magana ahankali " Ina Neman Alfarma ayimin rai walh bana sonta akwai wacce nakeso mun mayi alkawarin yin Aure atsakaninmu ayimin kowanne irin hukunci amma banda wannan

Galadima yayi Gyaran murya yace "kwantar da hankalinka Yarima Munanan ma baza.ai hakaba kaidai katsaya da gaskiyarka inhar bakai kayi cikin nan ba Ai jini zai nuna dazarar ta haihu za a auna jininka da abinda ta haifan agani

Galadima yadubi *KUYANGA* duk don yakamata da laifi sbd yana goyon bayan Yarima yace mata

" Ke Wanene shaidarki akan wannan lamari?


Tadago dakai ahankali tana tace "SAHABI shine Shaidata domin shine yadawo dani daga kasar waje

YARIMA yazaro idanu yana mamakin lafazinta wato Ashe SAHABI munafukin Sane?

Galadima yace mata " wanene kuma SAHABI?

Tace "Abokin Yarima tun acan yasan wasu abubuwan

Nan tahau bada labari tiryan tiryan Har takai karshe tana fidda kwalla a idonta

Kowa agun yaji labarin KUYANGA me taba zuciya Wanda masu tausayi agun harda hawayensu irinsu MAMAH da FAATU

Haka LAMIDO yacika da tausayinta zufa taringaa karyo masa agoshi yana gogewa

Sarki yakalli Yarima daya sunkui dakai alamun rashin gaskiya yace masa "Maza kira SAHABI awayarka kasaka handsfree kowa

Jiki asanyaye yakira wayar SAHABI yabarta a bude sunajin tana ring

Saida takusa katsewa kana Sahabin yadaga

Sarkine dakansa yahau masa magana

SAhABI yanutsu awaya jin martabane dakansa

Duk yanda ake ciki dai da mai martaba yazayyane masa kana yakara da koro masa Tambaya

SAHABI yakadu dajin hakan tabbas yasan abin babbane
Nan yagyara zama yafede masa biri hr wutsiya bai rage masa komai ba na abinda yasani duk domin yaga yafutar da *KUYANGA*

Yarima yaita mamakin SAHABI nayanda yake zayyano bayanai

Da sarki yagamaji yaiwa SAHABI godiya yakashe wayar

Ran sarki yagama baci akan musantawar da Yarima keyi

Yarima yahau sose sosen kai jin Sarki yace masa " kaji abinda abokinka yace anyi hakan?

Yagyada kansa

Sarki yace "Kasan da saninka Inta haihu zan daura muku Aure da ita sannan ayanzu Alhakin kulawarta yadawo kanta sbd abinda ke jikinta

YARIMA bai yi maganaba

UMMAH Ranta yabaci sosai da jin sannan hukunci

Take Sarki yasallami kowa aka watse

Kwana biyu da faruwar hakan YARIMA yabar gidan batareda Sanin kowaba ckn dare yagudu ko UMMAH bata saniba

Yahada kayansa yasilale cikin dare yatafi inda yafito

Da labarin yashiga ckn gidan ba karamin tashin hankali mahaifiyarsa tashiga ba Don hartahau zargin waiko Asiri akai masa dahar yabar gida


Abu kamar da wasa saida yakwana hudu labari ya isa fada

Tabbas Sarki ya guntsi bakin ciki awannan ranar yasan Yarima yanason yakun yatashine kawai tun aranar yakara tabbatarwa kansa cewar Yarima bai cancanci yaxama sarki ba

Tuni aka hadu kowa da kowa afadar Sarki domin shi yakira taron

Inda yabayyana musu bakin cikin dayake ciki

Yace da *KUYANGA* dafarko inaso kizama me daukar kaddararki haka Allah yatsara miki naso inga yarima ya aureki domin Asirinki yarufu kedashi dinma

To gashi Allah baiba yanunan ban isaba yawatsan kasa a ido yagudu yabar kasar


Dan haka inaso kikwantar da hankalinki da zarar kinhaihu zan karbi abinda kika Haifa hannu bibbiyu nayi miki Alqawarin baxaku wulakantaba ke dashi Dan haka wanene kike so ackn gidananna fadawa ko ckn BAYI xan muku Aure domin inwanke miki zuciya

*KUYANGA* tayi shiru kanta nakasa

Ayayinda MAHBUB dake ckn mutane nesa da ita yadago dakanta yana kallonta gashi dai har ynzu yana sonta to amma wani Abu ma sukar ransa inya tuna ta yaudareshi duk da azaman farko da akayi babushi ankawo masa Rahoton cewa Ba da saninta komai yawakamaba Yarimane ya cuceta

Yana so yafurta kalma abakinsa ya gagara jiyayi mai martaba yayi masa kwarjini bakinsa yayi masa nauyi

Yaso yafurta shine maaoyinta na asali na gaskiya da akai musu kutse arayuwa aka rushe musu farin ciki

Allah cikin ikonsa MAHBUB saiya kasa magana Allah yanufi LAMIDO Da maganar data furgita kowa harni

Hannu LAMIDON ya daga yana fadin "Ranka ya Dade ka Amince min Na Aureta domin inraya sunnar manzan Allah nakuma shiryi taimaka mata kota halin kaka domin naji zuciyata ta kwanta da ita....

Kallon kallo UMMAH suka hauyi da Jakadiya hakama MAMAH takalli FAATU yayinda FAATUN takalli Mai martaba domin jiran Abinda zai yanke akai....



To muma fans da writers sai mubi layi afada domin jiran tacewar Sarki Abdallah


πŸ™‡πŸ™‡πŸΌβ€β™€πŸ§–πŸΌβ€β™‚πŸ‘©β€β€β€πŸ’‹β€πŸ‘©πŸ‘¨β€πŸ‘¨β€πŸ‘¦β€πŸ‘¦πŸ‘©β€πŸ‘§β€πŸ‘¦πŸ‘©β€πŸ‘§

Muje zuwa
[8/1, 3:17 PM] Ummi Tandama: πŸ“Ώ *KUYANGA...* πŸ“Ώ




*_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```


https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation




*Nabilancy Luv* πŸ’˜
(Auntyn S&S)



60-65



AFIRGICE *KUYANGA* ta dago dakanta takai kallonta ga LAMIDO daya furta wannan kalami wanda azatonto ko karya kunnenta yajiye mata saitaga da gasken ne jin Abinda Mai martaba yace

"LAMIDO da gaske zaka Aureta? Har zuciyarka ka Amince?

LAMIDO da fuskarsa ke cike da Murmushi da Annuri yace "Na Amince har ckn raina babu wasa ko yaudara zan Auri *KUYANGA ZEENATU* ko domin inga asirin gidannam bai buduba kuma don itama inrufa mata Asirin Amma inhar kaida mahaifiyata kun Amince

Mai martaba yayi murmushi yace "Nidai na amince nakuma yi farin ciki kafitarni kunya domin banzamo me kyamatar talaka ba ko bawa na duk daya muke mu dasu gun ubangiji Saidai ko mahaifiyarka xamuso muji ta bakinta domin bata hakkinta.

FAATU tayi murmushi tace "Tunda har ka amince TAKAWA ainima dole in amince akullum Allah nakewa Godiya akan yanda mukai dace da samun D'a nagari wanda akullum burinsa shine yaga ya kyautata mana ya kuma bi sahun masu bin tafarkin ubangiji burinsa akullum yasami lada arayuwarsa kaga dole muzamo masu bashi goyon baya Allah yasa hakan yazamo Alkairi arayuwarsa

*"AMINNNN*"

Kaf Al,ummar gurin suka furta banda mutum biyu

MAHBUB da xcyrsa ta cika da kishi

Da kuma UMMAH da hakan bai mata dadiba

Mai martaba yadubi *KUYANGA* yace mata "Dazarar kin haihu za,a daura muku Aure da LAMIDO kigodewa Allah sannan duk abinda kika haifa mace ko namiji zamu karba da hannu bibbiyu Zansoshi kamar yadda nake son iyalaina tunda jinina ne za.a bashi kulawa sosai bakuma nafatan yataso cikin tsangwama ko bayan raina dan hakan ki Kizama me mika lamuranki ga Allah

*KUYANGA* Ta ckn ladabi ta Amsa tana godiya

Sarki yadubi LAMIDO yace "Asakamakon Wannan farantawar da kaimin ina me yi maka Albishir da cewa kaine zaka haye kan karagar Sarauta idan nayi murabus nan ba da dadewa ba Halayanka sunnuna kaine zaka iya rike masarautar nan ko bayan raina kacancnta babu haufi kaine adalin Mutumin da akullum ake nunamin amafarki wanda zai zamo sarkin garinnan Kadauko halayen kwarai na iyaye da kakanninmu kwarai ina godiya da Allah daya bani kai amatsayin D'a

Yadubi Tarin jama.ar da suka cika fadar maza da mata na gidan yaci gaba dacewa "Inaso kusheda daga yau LAMIDO Shine wanda zaizama jagoranku nan bada dadewa ba LAMIDO shine xai xama sarkin gobe da yardar Allah.

Take Gurin yahautsine da sowa da murna fadawa Suka hau Kabbara

Bayi mata tsoffin da manyan suka gau guda

Yayinda MAMAH ta rafka guda tareda cewa sarki "TAKAWA Allah Yaja da ranka muna taya LAMIDO murna kuma muna tayashi yin Godiya da wannan kyauta

Maimartaba yagyada kai yana murmushi

Dayake anyi tsit ana sauraren maganr MAMAH

Saijin kukan UMMAH Akayi ta dora hannu aka tana fadin "Shikenan burinku yacika kun raba D'ana da gidan ubansa kunyi kutunguilar da D'anku zai zama sarki kuma walh baku isaba

Sarki yadaka mata tsawa

Amaimakon tayi shiru saita mike tana fadin "walh baza,a dakeni ahanani kukaba. Tafuce fuuu tana kukan bakin ciki


LAMIDON da kansa yanuna godiyarsa ga sarki

Maimartaba yahau shafa kan LAMIDON yana fadin "Kacancnci hakan LAMIDO fatana harkullum Abinda kayi min na Farantawa to ubangiji Allah yafaranta maka kaima

LAMIDO ya amsa da "Amin, Aminn


Saida Sarki yabada umarnin tafiya sannan kowa yatashi yayi nasa guri


Jakadiya har sashin FAATU tabisu tana Rangada guda

Tareda fara yi masa kirari na sarakai

Saida tafaranta musu rai
Da kalamanta garesu masu dadin saurare sannan tafuta


Jakadiya
Tana barin Bangaren FAATU ta wuce sashin UMMAH Domin tayata Jimami da Alhini tunda tafi kowa sanin yanda UMMAH take da burin taga Yariman yazamo sarki

Ta tarar UMMAH tana waya da Yarima tana bashi labarin komai daya faru sannan Tabashi ixinin akan yadawo Gida maza maza akwai abinda take shirya masa akai


Yarima ya amsa da to zaidawo nanda kwana uku ko
biyu

Kai UMMAH ta hada da guiwa tareda dayin shiru na minti Talatin

Jakadiya na gefe taa jiran tafara kawo gulma da soki burutsin karya Data saba donta sami fada agun Fulanin

UMMAH tadago takalleta tace mata

"Jakadiya jeki kya dawo anjima ayanzu baxan iya maganaba ina ckn wani hali banda lokacin zanta wata magana kibari nahutawa bakin cikin dana dauko afada

Sum sum jakadiya ta tashi tafuce guiwa asage


Itako *KUYANGA* Kwana tayi ba ci basha Sai dakyar Akwana na biyu da Yin abun sannan Zulaihat data matsa mata taci abinci kadan duk tasaka damuwa ackn ranta

Zulaihat tace mata "walh kigodewa Allah ma ayanzu ji nake dama nice ke kuma nasan bani kadai ke wannan tunanin ackn bayin gidan nanba domin kin xama "yar baiwa tunda gashi Allah yakusa "yantaki

Zaki zamo matar sarki Surukar Sarki.……

"Uwar Shege ko Shegiya kuma ba.

Cewar Zeenatun tana matsar kwallah

Zulaihat tace "kibar fadin hakan domin inma shegene ko shegiya duk kafin yafito duniya ne ko tafito duniya domin Kinji ta bakin Sarki yakarba kuma za,a bashi kulawa zai zamo tamkar d'a ko "ya me "yanci to balle LAMIDO natare dake kinyi matsayin da bakowacce zata iya takashiba ackn mu *KUYANGIN* Gidan kema kinsan hakan

Zeenatu tace "hhhmmm ke kike ta wannan tunanin ni tunani na yatafi ga masoyina MAHBUN tausayinsa nakeji yanzu shikenan ……

Zulaihat ta daga mata hannu "saurara niarki dameni da xancensa domin banga yayi hobbasa yanuna soyayyar da yake mikiba agun dan da,a ce sonda yake miki har zucine da kafin LAMIDO yace wani abu akai tuni shizaice

Dan Allah kicireshi aranki tunda yanzu bake kadai bace ba,bafa ason me ciki da shiga damuwa balle kuma abinda zaki haifa me matsayine agidan

Zeeatu tace "Zulaihat da alama bakisan radadin soyayya a zuciba Ni LAMIDO baya gabana Mulkin gidannan baya gabana ko arzikinsu kawai Matsayina nake tunawa ayanzu


Zulaihat tace "ke nifa Allah nagodewa da bai nufi MAHBUB da magana akan kiba agun natabbata da tuni LAMIDO baice komai b.……

Sallamar Wata yar matashiyar yarinya ce cikin bayi tashigo dakin nasu takatseta tashigo musu da ladabi tagaidasu

Zulaihat tace "Laminde ya akai akwai wani abune?

Laminde tace "Ustaz ne yace Zeenatu taje yana waje.

Da sauri Zeenatun tace mata "kije maza kice masa ina zuwa

Ta xira hijab tabi bayan Laminde data futa da mintina uku

Yau ya canxa gurin tsayuwa can gefen hanya yaja tunga yatsaya yana jiranta

Tun daga nesa yakura mata idanu yana kallonta tayi haske fuskarta taxamo yar kuyas tayi kyau saidaita rame

Takasara gareshi da sallama tagaidashi

Ya amsa yana kallon yana fadin "ZEENAH ina sonki amma dole inbarki, yanzu kinmin nisa kinfi karfina.……

takatseshi dacewa "kadaina fadin haka komai nufin Allah ne matar mutum kabarinsa saikaga muna tamune Allah na nasa zai iya kuma canza lamarin aduk sanda yaso bamu zataba kaifa malamine kasan hakan kazama me tawakkali mana kana fa da Sani....

Yace "Duk na susuce Zeenatu ayanxune akwanakin nan biyu da faruwar lamarin naji kaunarki ta karu araina tamkar ana kara rura wutarta ma

Kokinsan YARIMA yadawo Gida adaren jiya labarin yakarade gidan nan. Sarki ko kallonsa baiyiba haryanzu yayi fushi dashi kuma duk akan ne "yar baiwa

Duk da gabanta yafadi jin ya ambaci sunan yarima sai bata nunaba a fuska ta dake tareda kawar da maganar ma tace masa

"Ko awane hali nake bazan manta dakaiba bakuma zan daina son kaba kaine kadai wanda naso a afarko da karshe ackn Duniyar nan ……


Adaidai lokacin da *KUYANGA* Ke furtawa MAHBUB wannan daddad'an kalma ar daidai lokacinne Allah yakawo yarima yazo xai girfta ta gun yahangosu yabiyo ta jikin katangar da suke tsaye kunnansa yadebo masa wannan kalami da muryarta yawatso akunnansa

Yaja da sauri yatsaya baya so su ganshi domin dan ita kawai yabiyo ta gurin

Rintse idanunsa yayi wani abu yaji yana masa yawo akirjinsa

Tabbas yau yakara aminta da zargin dayake mata na soyayya da MAHBUB duk da ta taba tabbatar masa amma kalaminta na yau yakara bashi haske

Ya dafe kansa domin Wani hali yashiga Akanta yadawo adalilinta tun daya hada kayansa yabr kasr yakoma turai yakas sakat Allah yajarabceahi da azababbiyar kaunarta dayaji batun da mahaifiyarsa ta gaya masa na LAMIDO zai Aureta bakaramin tashin hankali yashiga ba domin yasan shirinsa yagama baci

Nemanta yakeyi ido arufe ruwa ajallo Donsu keb'e yanuna mata nadamarsa ya amshi cikin nasa domin ta yarda dashi yakuma roki alfarmar tarakashi gun Sarki Ta tayashi neman yafiya
Yasan ita din me hkr ce da biyayya bazaisha wahalar taba

Waishin ma tawace hanyar zaisamu hakan? Anya bai makaro ba kuwa hhhhhh fans kufito ku gaya masa πŸ˜†πŸ˜…πŸ˜‚πŸ€£




Muje zuwa
[8/2, 5:04 PM] Ummi Tandama: πŸ“Ώ *KUYANGA..* πŸ“Ώ




🌈 *KAINUWA WRITER'S ASSOCIATION*
{United We Stand and succeed;Our Ambition is to entertain & motivate the mind of reader's}



*Nabilancy Luv* πŸ’˜
(Auntyn S&S)


*KAFIN AYI NISA KAI TSAYE INA MIKO GAISUWA DA GODIYA GA D'AUKACIN "YAN CIKIN GIDAN NABILA'S ONLY 4 STARS WRITERS MA,ABOTA KARANTA KUYANGA MUSAMMAN MASU COMMENT*





65-70


A SANYAYE Yarima yajuya da baya don gara yakoma kada wani cikinsu yaganshi su rainashi

Yakoma sashen mahaifiyarsa ya tararta tana Safa da marwa atsakar dakinta tana buga hannunta daya cikin daya tana kwafa da alamar har yanzun ranta abace yake tana kuma ckn halin damuwa

Tana ganinsa tahau fadin "Ya Akai yarima kasame tane?


Yazauna akan kushin yana fadin "Bansami ganawa da itaba UMMAH natarta ne da wani Kazamin bawa da take so..,UMMAH Takatse shi da sauri

"Au dama ackn gidan nanma akwai wanda take soyayya dashi ? Ashe haka tazama yarinyar to da alama ma cikin agida tayishi kenan

Yarima yadago da sauri yadubi mahaifiyarsa da jajayen ido yace "A,a UMMAH tunjiya Dana dawo nagaya miki cewar Wannan cikin fa nawa ne kada ki kakabawa wani makaskanci mana jini na karba.... " Dakata!

Ta dakatar dashi da daga murya ranta abace

"Wai bazaka daina kiran cikin jikin *KUYANGA* da sunan mallakin kaba,walh inkai ka karba to ni ban karb'aba domin bazan yarda da shege ace shine jikanaba jikanma ajikin baiwa Allah yakiyaye dama ajikin wata baturiyar ne ko " yar sarauta da sauki

Yarima yace " Amma ai u UMMAH shi .mahaifina
yakarba ballantana ke da kike mace kikafi sona.

Tace "Dan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login