Follow us on social media
Showing 63001 words to 66000 words out of 93041 words
Chapter 22 - ZAUJATU JINNUL-ASHIQ Sirrin Soyayyar Aljani By AMEERA ADAM
"Yara dai Allah ya kawo musu mijin aure kar ka yi musu buƙulu, kai da ɗan'uwanka ba kun ɗorawa kanku bokon jaraba ba. To gaskiya bana son hassada Garba kuma na yanke shawarar haɗa Dubu da Soja don gaskiya ba za a zo ana yi mata gori ba tun da ƙawayenta kusan duka sun yi aure wasu ma sun haihu."
[7/23, 2:48 PM] Ameera Adam🌚: *DUBU JIKAR MAI CARBI*
©AMEERA ADAM
FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*
FREE PAGE 10
https://youtube.com/c/DuniyarHausaNovels
Ku dannan👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼 subscribe tare da alamar kararrawa domin samun shirye-shirye da sauran littafai.
Baba Abubakar da Aseem lokaci guda suka ɗago suna kallon Yaya babba, da ta ci gaba da zayyano zance ko a jikinta. Dubu na maƙure a gefe sai raba idanu take don ita kanta ba ta san da wannan shawarar da Yaya babba ita da Inna Furai suka yanke ba. A madadin fushi sai ma wani murmushi da Aseem ya ke yi, wanda kana gani za ka tabbatar da murmushin mamaki ne da tsantsar baƙin ciki. Yaya babba da bata kawo komai a ranta ba ta ci gaba da cewa, "Allah ya sani dama wannan ne dalilin da ya sa na aika kiranka kai da Soja, don kune maganar ta shafa ba su Munkaila ba. Waye ya haifa maka Soja bayan kai da uwarsa Nafisa?" Yaya babba ta tambayi Baba Abubakar. Shiru ya yi yana murmushinsu na manya, sannan ya ɗago da kai ya ce,
"Inno na ji daɗin wannan maganar ta ki, kuma ni zan fi kowa farinciki da wannan haɗin domin abin da ya yi Dubu shi ya yi Aseem. Amma wani hanzari ba gudu ba..." Da sauri Yaya babba ta katse zancensa da cewar:
"Don Allah Garba ka faɗi alheri ko ka yi shiru. Wannan fa abin farinciki ne, kuma me ye aibun Dubu yarinya san kowa ƙin wanda ya rasa. Ƙwaranƙwatsa dubu babu abin da Soja zai nunawa Dubu, kyau ya fita ko tsafta? Yarinyar da sai ta yi wanka sau uku a rana ko ba haka ba Furaira?" Inna Furai ta taɓe baki ta ce, "Ina dalili tun ba a ji ta bakin yara ba Garba za ka kawo mana hanzari, wannan kamar zazzage albarkar da ke cikin auren za ka yi. Gaskiya karka ɓata auren yara tun ba a je ko'ina ba, yoo Allah na tuba wane hanzari gare ka da ya wuce ka sa albarka?"
Baba Abubakar ya sauke ajiyar zuciya yana faɗin, "Inna ni fa baku fahimce ni ba. Ina nufin su yaran a fara ji ta bakinsu don kar ayi abu ba da son ransu ba. Amma idan kuna faɗin haka sai in ga kamar kuna nuna Dubu da Aseem ba ɗaya ba ne a wurina." Yaya babba ta washe baki ta ce, "Shi dai Soja na san ai ba zai ƙi ƴar uwarsa ba, ita kuwa Dubu kar ku ji ta, na san ta yanda zan shawo kanta." Aseem saboda takaici miƙewa ya yi ya fice daga ɗakin, Yaya babba na ganin haka ta saki dariyar farinciki tana faɗin,
"Ai na gaya muku wannan shiru-shirun da yake yi wallahi aure yake so, ja'iri ga shi nan kunya ta kama shi ya fita yana sunne kai, yoo waye zai samu Dubu bai yi farinciki na? Alƙur'an ana auren ku basu wata tara sai dai ku ji haihuwa, Soja wai mu zai yi wa hikima bai san na daɗe da gano lagwansa ba." Baba Abubakar ya yi shiru yana nazari domin ya san ba ƙaramin ruwa Yaya babba ta kunto masa ba, saboda ko makaho ya shafa fuskar Aseem ya san yana cikin yanayi marar daɗi. Saɓanin Dubu da ba za ka tantance ainihin halin da take ciki ba, na farinciki ne ko baƙinciki ba.
Yaya babba cikin murmushi ta kalli Baba Abubakar ta ce, "Yanzu dai Garba ka je ka shaidawa Nafisa halin da ake ciki don a fita haƙƙinta na mahaifiya, kar ta ji magana daga sama don ma bata da fushi ba kamar Fauziya Matar Ado ba, kai gaskiya Garba duk cikin ƴan uwanka akwai wanda ya yi dacen mace irinka kuwa? Allah ya sani Nafisa macen arziƙi ce idan na zageta sai dai na yi mata ƙazafi. Suma ƴan uwanka zan shaida musu abin da yake faruwa don kar su ji maganar aure bagatatan, na san Sule da baƙar zuciya sai ya ɗau fushi da ni ba gaira babu dalili. Yo ko auren na yi musu ban sanar musu ka ga laifina Garba? Kai ne dai uban soja halak malak, wani ne ya haifa mini kai? Ni ina na iya gaba halin ƴan wuta, ina masoyiyar Annabi (S.A.W) me zai haɗa ni da wuta ana zaune ƙalau? A'a rabani da wannan falsafar zan sanar da su da kaina, kar shaiɗan ya ɗebe ni idan suka ɗau gaba da ni na biye musu, ana zaune ƙalau na tsine musu su ɓalɓace." Baba Abubakar ya zaro kuɗi a aljihu ya dire musu a gabansu ya yunƙura jiki ba ƙwari ya ce, "To shi kenan Inno Ni bari na wuce." Cikin haɗin baki Yaya babba da Inna Furai suka fara faɗin, "Ka gaida gida Allah ya yi albarka."
Yana fita Dubu ta ɓata fuska ta ce, "Wai ke Inno ce miki na yi ina son shi bayan mugu ne, baki ga irin wuyar da ya bani ba rannan." Yaya Babba ta rungumo Dubu cikin lallashi ta ce, "Ke yi shirunki, kin san me ya sa na yi wannan haɗin?" Dubu zuciyarta ɗaya ta girgiza, Yaya babba ta ci gaba da cewa: "Allah ya sani Dubu idan ba mutuwa ba zan iya rabuwa da ke ba. Idan kika auri Soja a cikin gidan nan za ku zauna, ga wuri nan a gyara masa ku yi zamanku. Amma idan bare kika aura kin san dole ki fice daga gidan nan. Na san irin rayuwar da za ki yi a can gidan? Sam! Ba zan laminta ba a rabani da Marainiyar Allah ina ji ina gani." Daɗi ne ya kama Dubu lokaci ɗaya ta washe baki cikin farinciki. Lokaci ɗaya kuma sai ta ɓata fuska ta ce,
"Inno idan ya harbe ni da bindiga fa? Wallahi ba shi da tausayi tsaf kashe ni zai yi." Inna Furai ta hau jinjina kai sannan ta ce, "Wallahi har kotun ƙoli sai mun je a kan shari'ar nan. Ke bar zancen bindiga tsaf za ki saye zuciyar shi, tun da da me na birnin za su fiki?" Dubu ta ci gaba da washe baki tana jin nishaɗi ita a dole za ta auri Soja kuma ɗan gayu.
A ranar Yaya babba da Inna furai suka gama isar wa da Mutanen gidan, hukuncin da suka yanke har suke ɗorawa da cewar, yara tuni sun haɗa kawunansu don Aseem tsabar kunya tun da ya fito bai dawo ba. Ita kuma Dubu ban da murmushi babu abin da take yi, nan fa ƙananan maganganu suka fara tashi a cikin gidan kowa da abin da yake tsakura yana isarwa.
Lokacin da Baba Abubakar ya fita a cikin mota ya samu Aseem, yana zaune ya haɗa kai da sitiyari. Har Mahaifinsa ya shiga bai sani ba ya zurfafa cikin tunani. Da kallon tausayi ya dubi ɗan nasa ya ce,
"Aseem!" Jiki a sanyaye idanu jawuri ya ɗago ya kalli Mahaifinsa, murya a shaƙe ya ce, "Na'am Daddy."
"Dukda ban shiga zuciyarka ba amma san wannan hukuncin ba lallai ya yi maka daɗi ba." Kamar mai jira ya shagwaɓe murya yana faɗin, "Yanzu shi kenan Daddy duk abin da su Inno suka faɗa, komai ta ce sai dai ku hau ku zauna? Gaskiya ni kam babu yanda za a yi na auri waccen yarinyar. Yarinyar da kowa ya san bata da nutsuwa, don Allah Daddy ya za a yi ma na auri wata Dubu? Never wallahi." Ya ƙarasa maganar a shagwaɓe kamar zai yi kuka. Baba Abubakar ya yi murmushinsu na manya ya ce, "Rashin nutsuwarta ba komai ba ne idan har kana sonta, kai namiji ne za ka iya nusar da ita akan abin da ya dace." Cikin hanzari ya furta, "Ni ba na ma sonta, Allah ya sani ta nemi wani ta haɗa ta shi amma ba ni ba."
A karo na biyu Baba Abubakar ya sake kiran sunansa, "Aseem." A marairaice ya ɗago ya amsa sannan Mahaifinsa ya ci gaba da cewa, "Inno fa mahaifiyata ce kana ganin zan iya kaucewa umarninta, idan har ina neman albarka duniya da lahira? Su fa iyaye biyayya ake musu akan duk abin da suka buƙata matsawar bai saɓawa mahallici ba, ko da kuwa baka ƙaunar abin sai ka ga wata rana abin ya zame maka alkairi." Murya a raunane Aseem ya ce, "Daddy nima ban taɓa saɓa umarninka ba, amma maganar gaskiya idan aka tilasta ni na auri Dubu sai dai na barta a gidan nan, na yi tafiya ta."
"Da ka wulaƙanta ƴar ɗan'uwa bayan ka aureta; ai gara ka ce mini ban isa na saka ko na hanaka ba. Zan yi ƙoƙarin ganin na shawo kan Inno idan ta amince shi kenan, idan bata amince ba, ka yi haƙuri ka amshi ƙadaddararka hannu bibbiyu, ka san kowanne bawa baya kaucewa ƙaddararsa, ta yiwu alkairin na gaba kai da kanka za ka ji daɗin haka. Saboda sautari muna ƙin abin da shi ne alkairi a tattare da mu sai daga baya mu fahimci haka." Shiru ne ya ratsa Aseem ya kasa furta komai, zuciyarsa ban da zafi babu abin da take yi masa. Jiki a sanyaye ya tuƙa mota suka wuce gida, kowa na saka da warwara a cikin zuciyarsa.
Tun shigar su cikin gidan Hajiya Nafisa ta fahimci gabaɗaya babu mai cikakkiyar walwala a tattare da su, har ta fi damuwa da damuwar Aseem saboda Baba Abubakar ba wani zaman daɗi suke yi ba, duk akan maganar komawarsu Ɗangwauro. Aseem na shiga ɗaki ta bi bayansa, a ɗaki ta same shi yana kaiwa da kawowa haɗe da kaiwa bango naushi. A ɗan tsorace ta fara watsa masa tambayoyi:
"Lafiya Asem? Wani abin ne ya faru da ku daga kai har Daddynku na ga baku da walwala?" Murya a can ƙasa ya ce, "Mommy babu komai, kawai wurin aiki ne suka kira ni akan wani issue ɗin." Kallon tsaf ta yi masa tana son gano gaskiyar abin da ya faɗa sannan ta ce, "An ya ba wani abin ne yake faruwa a Ɗangwaro ba?"
Da sauri ya kalle ta sai kuma ya ɗauke kai gefe saboda ambatar sunan garin, ba ƙaramin dawo masa da ɓacin rai ya yi ba, ya zauna a gefen katifarsa ya dafe kansa da hannu bibbiyu ya ce, "A'a Mommy." Taɓe baki ta yi ta ce, "Idan ma wani abin kuke ɓoyewa indai Hajiya babba ta kafe kai da fata na san ko ba daɗe ko ba jima zai fito fili." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin.
Aseem ya ƙi sanar da Mahaifiyarsa ne saboda ya san Daddynsu ba zai taɓa sanar mata a wannan ranar ba, duba da yanayin zaman da suke a wannan lokacin. Uwa-uba kuma ya san idan ya gaya mata kamar ya ƙara hura wutar tashin hankali a tsakanin iyayen nasu ne. Lokaci ɗaya tsanar Dubu ta mamaye zuciyarsa don duk ita ce silar komai, dukda hali irin na mahaifiyarsa tun da ya taso bai taɓa jin suna sa'insa ita da Mahaifinsa ba. Amma lokaci ɗaya ta tarwatsa farincikinsu ga auren iyayensu, da yake tangal-tangal tun da har lokacin Hajiya Nafisa na kan bakarta da ta koma ƙauyen nan, gara ya sallameta ta kwashi ƴaƴanta, ta riƙe a wurinta ko sa samu irin mijin da take buri da fatan su samu. Kamar yanda ta gama yi wa Aseem tanadin ƴar ƙawarta, saboda komai ta fi so su yi cikin bajinta da harkar girma.
A daren ranar ya haɗa kayansa tsaf a cikin jaka, washegari da sassafe ya wuce Lagos da yake acen yake aikinsa. Wannan ya ƙara tabbatarwa da Hajiya Nafisa tabbas akwai wata a ƙasa, amma zafin zuciya irin nata ya sa ba za ta iya tambayar mahaifinsa don jin abin da yake faruwa ba. Kuma ta lura shi kansa har lokacin baya cikin walwala, ga yawan waya da ta ga yana yi da ƴan'uwansa. Ga shi ba wata kyakkyawar alaƙa gare ta da facalolinta ba, bare ta kira ɗaya daga ciki don ta ji halin da ake ciki ba.
BAYAN SATI BIYU
Duk wani daɗin baki da dabara irin ta tsofaffi Yaya babba ta yi wa Dubu, kuma tuni ta ji ta aminta da Aseem a matsayin mijin aure. Don ba ƙaramin ƙawatawa Yaya babba ta riƙa yi mata ba, tana nuna mata irin rayuwar jin daɗin da za ta yi matuƙar da auri Aseem, hatta wanki ta daina sai dai ya ɗauko mai yi mata. Kan Dubu ba ƙaramin girma ya ƙara ba don ji ta yi duk faɗin garinsu babu wacce ta yi dacen mijin aure sama da ita.
Tuni maganar auren Aseem da Dubu ta karaɗe cikin ƙauyen Ɗangwauro, mutane da yawa mamakin wannan haɗin suke yi ganin Aseem cikakken ɗan gayu amma ya ƙare a auren Dubu. Cikin dangi sai tsegungumi ake da wannan maganar, lokacin da labarin auren Aseem da Dubu ya isa kunnen Hafsa ƴar wurin Hajiya Fauziyya, zama ta yi dirshen tana kuka don duk duniya babu wanda take so da ƙauna sama da Aseem, amma rana tsaka a ce wai Dubu ita ce za ta aure shi. Tun daga ranar ta bar walwala bata da aiki sai zaman ɗaki, ga shi an yi tambayar duniya ta ƙi faɗa, sai dai ta ce bata jin daɗi.
A wannan lokacin saura kwana uku tariyarsu a Ɗangwaro, sun gyara sashensu da sauran ɓangarorin gidan, gidan ya fito kamar a birni. Har fasalin ƙofar gida suka sauya suka rushe gaban gidan, suka saka ƙaton gate wanda mota za ta iya shiga har harabar wurin da suka zagaye da ya zama wurin parking space. Haka bikin su Dubu a lokacin saura sati biyu cif, su Yaya babba har an fara gyaran Amare. Aseem da Dubu a gefen sashen su Yaya babba aka gyara musu, gini ne mai ɗaki uku sai kitchen da banɗaki. Sai Salisu da Zulfa suna maƙota da su Dubu, Bilalu da Murja suna maƙotaka da Baba Auwalu sai kuma Bashari da Maryama a suke maƙotaka da su Baba Adamu. Duk gyaran da ake wa amaren Yaya babba da Inna Furai sune jigo da ragamar komai.
Sai dai duk wannan budurin da ake yi mai gayya mai aiki, Mahaifiyar Aseem bata san wainar da ake toyawa ba har sai ana gobe tariyarsu, a lokacin da suke tsaka da hatsaniya ita da mijinta. Suma ganin Manyan akwatuna ta yi a ɗakinsa kishi ya rufe mata ido don a tsammaninta idan sun koma Ɗangwaro aure zai ƙara. Bayan ya gama sauraronta ya saki murmushin ƙeta don ya san muddin ya sanar da ita abin da yake faruwa ba lallai ta samu damar runtsawa a ranar ba. Saboda yana da tabbacin Aseem bai sanar mata da abin da yake faruwa ba, saboda har lokacin shi ma ɗaukan maganar yake kamar almara. Kafin lokacin akwai lokacin da Baba Abubakar ya kira a kan maganar kayan lefe, amma babu wata tsayayyiyar amsa da Aseem ya bashi. Hakan ne ya sa ya bugi ƙirji ya yi masa komai, saboda idan ya biye ta tashi ya san babu abin da Aseem zai yi.
Shi kuwa Aseem har kullin sai ya yi yunƙurun sanar wa mahaifiyarsa halin da ake ciki, amma fargabar tashin hankalin da za a shiga sai ta hana shi, don haka ya danne a bari Mahaifinsa ya sanar mata da kansa. Kuma dama sun riga da sun yi maganar shi da Mahaifinsa ya ce masa kada ya gaya mata har sai shi ya tunkareta ya gaya mata.
Bakinsa ɗauke da murmushi ya ce, 'Kanyan ɗanki Aseem ne za a kai masa na aure, yanzu haka saura sati biyu bikin dama ko baki tambaya ba yau na yi niyyar sanar da ke." Ku san suman tsaye ta yi jikinta har rawa yake ta ce, "Idan ma wasa kake min don Allah ka fito ka gaya mini gaskiya, idan aure za ka ƙara ba sai ka ɓillo min ta wannan sigar ba." Bai tanka mata ba ya buɗe durowar kayansa ya zaro katin ɗaurin aure ya miƙa mata. Hannu na rawa ya karɓa ta fara karantawa da yake ɗaurin auren mutane da yawa ne, sai ba za ido take don ta ga sunan Aseem da sunan Amaryar da za a aura mata ba tare da ta santa ba.
Ƙauyen Ɗangwauro.
"Inno kullin haka kike faɗa amma fa har yau ko kirana a wayarki bai taɓa yi ba, kina ganin su Zulfa kullin cikin waya suke." Dubu ta faɗa tana kwaɓe fuska. Yaya babba ta washe baki ta ce, "Kin san Soja da kunya, tun yana yaro duk cikinku babu mai kunyarsa. Allah na tuba wacce kunya gare ku rannan ina jin Zulfa tana waya akan gadona, munafukar yarinyar ta ɗauka bacci nake har cewa take ko Lobin-lobin ko I Lobiyu. Wai har da cewa tana kewarsa. Don Allah Dubu ki ji mini falsafar rashin kunya ta dubi gardi kamar Salisu ta ce, tana kewarsa wannan bata cancanci istigifari ba?" Dubu ta bushe da dariya ta ce, "Yasin Inno kaɗan ma kika ji." Inno ta dafe ƙirji a tsorace sannan ta ce:
"Au tana faɗin abin da ya fi haka? Amma dai Zulfa an yi ƴar banzar yarinya, ta yi ta sunne kai ƙasa kamar mumina ashe shakiyya ce." Dubu ta ɗauko wayar Yaya babba ta ce don Allah Inno ki kira min shi."
Yaya babba ta ƙanƙance ido tana kallon wayar ta ce, "Kin san dai ba iya nemo lambarsa na yi ba, duba ki kira shi." Cike da ɗoki Dubu ta fara dubo lambar Aseem sai da, A ɗin kawai ta riƙe amma takamaimai sunan Aseem ba ta san shi ba. Sai da ta kira mutane biyu waɗanda sunansu