"[1/7, 9:31 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 1 Nimcyluv Bright pens. second batch *Marubuciyar. ❤🔥* *Mijin malama* *Munafukin miji* *Moon* *Idan ba ke* ..... E.t.c and now *MUTALLAB* "* for some reasons. Akwai copywrite kar a haɗa mini ducoment, banda YouTube a bar mini kayana" haƙƙina ne* "Jami'an tsaro ne ta ko'ina cikin kayan kaki ma bambanta, duk da cewa yammacin ranar lahadi ne a watan" Fabrairu bai hana ta gane fuskarsa ba. Cikin tashin hankali jikinta na rawa da kyarma ta nufe shi tare da "ƙoƙarin cakomo wuyan babbar rigarsa tana furta cewa ""Shi ne, wallahi shi ne, daman na ce zan gano shi""" a gigice mutumin dake ƙoƙarin shiga motarsa da aka buɗe masa ya yi baya yana mai ƙarewa matar kallo sosai sai dai ya kasa gano ko wace ita? Daga ina me kuma take buƙata. """Wace ita?"" Ya furta yana tambayar zuciyarsa tare da kallon gefe. ""Wallahi shi ne, mugu azzalumi sai ka" "yi kuka, ka wulaƙanta "" Jin furucinta ya saka ƴan'jarida dawowa kan ta, suka fara tambayar ""Kin san" "shine? Mene haɗinki da shi?"" Kafin ta yi magana wani ya ce ""Arrest her, ku kamata""" "A hankali ya jingina da jikin motar can ya numfasa yana kallon yaronsa ya ce ""Wace ce? Na santa ne? To" "me ya sa take abu kamar ta sanni?""" """Sir da gaske ta sanka bana jin ko mutuwa ta yi ta dawo zata manta fuskarka, kuma zamanta a raye yana" "nufin abubuwan da yawa dole a yi wa tufkar hanci, kar a bari ƴan'jarida su samu ganawa da ita, even your securites, wannan matsalar kai da kai ce kuma zata shafi kimarka"" cike da mamaki ya yi ta kallon yaron nasa na tsayin sacanni da ƙyar ya cije leɓe ya ce ""To ina na santa? Me ya sa zata zama" "damuwata?""" """Sir ita ce wacce ka saka aka kawo maka ita, wacce ka yi wa fyaɗe a lokacin ,""" """Ya isa!"" Ya ce yana jin jiri na neman ɗauke shi, ya dubi tarin jama'ar da suke wajan can ya yi murmushi" "yana ɗauke fuska sai kuma ya ƙurawa yaron idanu ya juya ya kalli matar ya gyatsine fuska ya ce ""kuma ta" "kasance a raye ya haka? To a yi hanzarin toshe wannan ɓarnar ya zama kamar ba a yi ba""" """Amma me ya kamata a yi mata?""" """A yi mata allurar hauka, wacce ake yi duk shekara da wata wata kana a kaita gidan yari, life in prison har" "ta mutu. Bayan haukan zata mance komai, su ƴanƴan talakawa wama ya damu da su mutu ko su yi rai bata da wani mai tsaya mata kai mutuwa ma za ta yi"" yana faɗin hakan ya shige mota. Tana takure a jikin ƙofar ɗakin da aka ajjiyeta idanunta ƙur a kan photonsa zuciyarta sai zafi take mata wani abu ya tsaya mata. Da sauri ta juya jin an buɗe ƙofa wani mutum ne sanye da farar riga ya rufe fuskarsa hannunsa riƙe da ƙaton sirinji iya ruwan allurar da ya yi ja abin tsoro ne, ta fara ja da baya amma a haka ya fincikota tare da yin cilli da ita,ta faɗi saman carpet bai tsaya jiran komai ba ya caka mata allurar a ƙashin" bayanta wajan spinal cord ihu ta fara da birgima idanunta ya shiga ƙaƙƙafewa jikinta na sandarewa ta dinga buga kanta da jikin bango tana buge-buge a hankali jini ya fara fitowa ta cikin hanci da bakinta tabbacin allurar ta amshe ta za kuma ta yi aikin da ake buƙata a jiki da ƙwaƙwalwarta. ****** Cikin sauri suke tafiya a wani ɗan dogon lungu mai duhun gaske tsarin wajan gabaɗaya a ƙuntacce yake kamar zunubin gidan yari. Magana suke ƙasa-ƙasa ɗaya daga cikin su kuma yana duba agogon dake hannunsa tare da duba cikar lokacin fuskarsa a haɗe take sosai. Sai da suka kawo ƙarshen ginin suka tsaya ya ɗaga kai a hankali ya dubi saman da kansa ke taɓowa ya ɗan rusuna sai kuma ya dubi jami'in "tsaron dake wajan ya yi masa nuni daya buɗe ƙofar. ""Yes sir!""" Bayan ya sara ya ƙame ya buɗe ƙaton kwaɗon yana toshe hanci saboda wari da zarnin wajan. SP Gali ya kalli team ɗin nasa cikin bada umarni ya ce """Ku jira nan, idan akwai damuwa zan muku alama na san dai he can't do anything, ba zai iya komai ba""" "gabaɗaya suka jinjina masa kai tare da zagaye ƙofar fuskar kowannen su manne da baƙin gilas. A hankali Sp Gali ya tura ƙofar ya shiga yana durƙosawa saboda rashin girman wajan. Tunda kafin su ƙarasu wajan ya san da zuwan nasu har aka buɗe ƙofar tare da shigowa, yana durƙushe inda yake ya kifa kansa a ƙasa hannunsa dunƙule ya damƙe abu wanda tun kafin a kawo shi gidan abu yake a hannunsa, yin duniya yaƙi" buɗe abun balle a san menene shi. """Hey you!"" Sp Gali ya ce yana saka ƙafa tare da buge ƙafarsa ganin yaƙi motsawa, tamkar gunki haka yaƙi" "motsi ya kuma ƙi ɗago kansa Sp Gali ya shiga kallon wajan ya rasa wanne irin hali ne da wannan yaron mai baƙar zuciya da taurin kai ya sauke numfashi cikin kwantar da murya ya ce ""Ni idan na ce maka ina da tausayi na yi maka ƙarya, amma ka saka zuciyata karaya kana bawa kanka wahala kana bawa jami'anmu wahala. Me zai hana ka sauƙaƙa mana wahalar nan ka faɗa mana gaskiyar abin da ya faru a wannan rana kuma a wannan daren? Me ya sa ka aika abin da ka aikata? Ka kashe matarka, ka kashe ta har lahira kuma kaƙi magana shekara uku kenan kana wajanmu ka rainawa hukuma hankali da kotu, kai baka da zuciya ne dame kake taƙama saboda kana da tsari a jikinka ƙarfe ba zai ratsa naman jikinka ba, muna da kalolin azaba nau'i-nau'i amma gaskiya muke buƙata, ka amsa cewa ka kashe matarka a zaman" "kotu na yau shikenan sai a yanke maka hukunci daidai da zaluncin da ka aikata""" "Har Sp Gali ya kammala maganarsa bai motsa ba, babu alamun zai ɗago kai balle ya tanka. Sp ya miƙa" hannu zuwa hannun mutumin dake dunƙule da abu zai amsa a firgice ya ɗago kansa yana buɗe dara- daran idanuwansa akan Sp Gali sai da zuciyarsa Sp ta motsa saboda wani mugun jaa da idanunsa ya yi. Fuska ɗaure ya yi wa Sp kallon warning har lokacin bai yi magana ba dukkan naman jikinsa rawa yake kamar zai kaiwa Sp damƙa fuskarsa baibaye da gashi kansa ma cunkus yake ba'a gane kamanninsa sosai saboda cikar gashi. "Sp ya duba lokaci sai kuma ya shafa kai ya ce ""SCORPIO"" nan ma ya sake ɗago kai da sauri ya zubawa Sp" "idanu ""Idan ka bari na gano cewa kai ne Scorpio """ "Ya cije baki yana miƙewa tsaye ya furta ""Zan addabi rayuwarka, gwara ka zauna a iya wanda ya kashe" "matarsa da dai ka kasance kai ne Scorpio. Mene asalin sunan naka?"" Ya tambaya yana juyawa kamar zai fita saukar gurnanin da ya ji ya saka ya yi saurin juyawa idanunsa ya sauka wanda ake zargi da kashe matar tasa yaga ya dafe kai da hannu bibbiyu yana jujjuyawa ya dinga haɗa kansa da bango cikin sauri Sp" Gali ya ce """Team"" a guje suka shigo hakan ya saka ɗan ƙaramin ɗakin cika fuskar Sp ba wasa ya ce ""Ku danne shi a" "karɓo abin hannunsa dole mu san mene babu mamaki zamu samu hujja a ciki"" yana cewa haka ya fita yana amsa kira. Ganin sunyo kansa ya yunƙura gabaɗaya ya fisu faɗin ƙirji da damtse amma suka rufar masa sanin cewa sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi ya saka shi damƙe hannunsa da kyau yana ɓoye abun da suka karɓa, kokawa suke da shi ya dinga haɗa su da bango ya kama hannun ɗayan ya karya bisa dole suka fice a wahale. Sp ya saka wasu manyan mutane fito da shi suka ɗaure shi da ankwa tare da sarƙa" tun daga ƙafa har zuwa kansa. A harabar Criminal Investigation department CID aka tsaya dashi domin tafiya zuwa kuto a rana ta "ƙarshe wanda ke nuna ko a sake shi, ko a kashe shi ko kuma ya tafi gidan ɗan'kande. Team guda ne masu matuƙar basira da ƙwarewa akan aikinsu team ɗin ya haɗa da wanda yake ɓangaren Legal section, Anti- human trafficking, Medical Staff, Legal services, NDLEA, FID Federal investigation department. Gabaɗaya idanunsu yana kansa kowanne yana karantar yanayinsa amma shi ko a jikinsa banda faratansa na hannu dana ƙafa da aka ciccire wajan gana masa azaba babu wani rauni a tattare da shi sai matsanancin baƙi da ya yi ya zama kamar mahaukaci saboda shekarun daya ɗauka a kulle daga kuto zuwa state cid zuwa Fid amma har tsayin shekarun bai buɗe baki ya yi magana da kowa ba, babu kuma wanda ya damu daya tsaya masa. Suna ta surutai ƙasa-ƙasa duk yana jinsu har sanda wani yake cewa ""Babu hanyar da za a" "tilasta shi ya yi magana ne? Muna buƙatar muryarsa""" "Sp Gali ya ce ""Ina zargin wani abu game da matarsa daya kashe""" """Wanne abu? A binciken da mukai a wajan iyayen yarinyar tun farko ita ta nuna tana son shi, shi da ita" "class mate ne kuma age mate, tun suna shekaru 15 a secondary school suke soyayya. Me ya sa ya zaɓi ya kashe ta? Sun ɗauki shekaru tare bai taɓa yunƙurin rabata da duniya ba sai ranar da aka ɗaura musu" "aure? This is complicated"" C.i.d Research ya jinjina kai ya ce" """Duk binciken da aka yi shine a ruwa, gwajin hannu, yatsun hannu da sahun tafin ƙafa da CCTV camera" "na kan titin unguwar da aka kai amaryar tasa duk bincika shine""" Shiru sukai suna tunanin gabaɗaya kansu ya ɗauki zafi. Yana da can inda yake ya ja idanunsa ya lumshe yana fesar da iska daga cikin hancin wacce hucinta ya sauka har saman fuskarsa “BESTIE” haka ya ji saukar muryarta a kunnensa kamar yanzu ne suke tare da ita. Ya sake lumshe idanunsa yana jin saukar dariyarta sosai ya tuna lokacin yana zaune shi kaɗai a cikin class ranar aka dawo hutun makaranta shi kaɗai ne zaune ciki yana sanye da farar riga sai wando blue black ya ɗora ƙafarsa ɗaya saman benci tare da yin baya. "A hankali ta shigo cikin class ɗin hannunta riƙe da lunchbox da textbook sai school bag data goya, hijab" ɗinta daidai da ƙirjinta ita ce ta fara shigowa da mamaki take kallonsa zuciyarta na bugawa ta je ga zauna "inda yake ta zuba masa idanu sai kuma ta ce ""Ka yi holiday assignment?""" "Ya buɗe manyan idanunsa bai ce komai ba ta sake ƙasa da murya ta ce ""Na san bama ka yi ba ka daina" "haɗe mini fuska, ka naso a yi ta faɗa da kai da teachers"" nan ma bai kula ta ba a hankali taci sautin da cikinsa yake yi sai ta jawo lunchbox ɗinta ta buɗe tare da tura masa gabansa ta ce ""Your breakfast, ka ci kafin a shigo na san baka karya ba"" sai a lokacin ya buɗe idanu ya juya gabaɗaya yana kallonta sosai ta yi" ƙasa da murya kamar zai yi faɗa sai kuma a hankali ya ce """Kuma ga mayunwaci ko?"" Ta yi murmushi ta ce ""Da ƙyar na jure ban biyoka gida ba, na yi kewar ka" "sosai bestie"" ya yi mata shiru sai kuma ya haɗe fuska sosai yana janyo abincin yaga dankali ne aka soya" da ƙwai ya yi ɗan tsaki ya ajjiye spoon ɗin ya damƙa ya kai bakinsa ta yi saurin kama hannunsa ta ce """Kai baka iya komai bane? Sai a yi maka dariya cin abinci da hannu"" ya ware idanu sai kuma ya murtuke" "fuska ya ture hannunta a hankali duk da muryarsa a kumbure take ya ce ""Ki daina kusanta kan ki dani, ni fa ba ɗan iska bane""" """Laaa Allah Ya baka haƙuri kai duk abin soyayya baka iya ba"" a taƙaice ya ce ""Ke kika santa"" ta ja baya" "tana ɗaga hannu ta ce ""Lalala to shikenan ni dai ƙaddararka ce, na faɗa a gida a yi mini aure, ka san me" "na ce?"" Ya girgiza mata kai kawai yana sake damƙo dankalin yana dannawa cikin bakinsa saboda yunwa" ko gani baya yi sosai ta buɗe gorar ruwa ta miƙa masa a hankali ta ce """Na ce su yi mini aure wallahi bana son karatun nan, na ji aure nake so kuma na faɗa musu kai nake so," "amma wai ban isa ba karatu ya zama dole kuma shekaruna sun yi kaɗan amma ai ma girma shekararmu 15 years fa, ko kai baka isa aure bane?"" Ya yi mata shiru sai ta fashe da kuka sosai ta ce ""I love you so much Bestie, don Allah ka aure ni zan zauna dakai a duk yadda kake ka taimakawa rayuwata"" ya zame hannunsa tas ta miƙa masa tissue ya goge ya ja baya yana lumshe idanunsa har yanzu students basu fara" "shigowa ba, ta ɗan yi gaba kamar za ta shige masa ya cikin tsawa ya ce ""Zan kwaɗe ki kuwa""" """But what if i told you i love bestie? You mean the world to me, wallahi aure nake so ba karatu ba"" ta" faɗa tana shassheƙar kuka sai a lokacin ya kalleta fuska babu walwala ya dubi yadda take kukan sosai ya ce """Ke, babanki ne ya mutu? Ko uwarki ce?"" Ta girgiza masa kai ya sake haɗe fuska yana rarraba idanu a" "cikin ajin kamar mai neman wani abu can ya ce ""To kece za ki mutu kenan?"" Ta girgiza kai sai kuma ta ce ""A'a""" """Kukan fa?""" """Na soyayyarka ne bestie taɓa ƙirjina ka ji wallahi ni ce ƙaddararka ba zaka gane hakan a yanzu ba, da ina" da ikon cire abin da nake ji a ƙirjina da na yi hakan ina jin dama na mutu na huta kuma idan ban aure ka "ba zuciyata zata iya bugawa""" """To gwara ta buga na huta da na ci, shekaruna 15 za ki lalata ni da batun aure, ke tashi ki ware daga nan" "ɗauki kwananki kar ki ƙara kawo mini abinci"" ta miƙe jiki a sanyaye zata bar wajan ya nuna mata" "lunchbox ɗin daya cinye komai ""Ko daɗi bai yi ba abincin""" "Sai a lokacin ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta yi kukan ba, dimples ɗinta na lomawa ta ajjiye masa" "500 ta yi waje tana cewa ""You're my darling jarumina, i love you Mai dawa da jeji"" ta faɗa tana sake yin dariya tare da yin waje......." Ya yi saurin dafe kansa jikinsa na rawa yana jin dariyar nata na yi masa amasa kuwwa a kunne kamar "yanzu ne take yi jikinsa ya ɗauki rawa sosai daidai lokacin aka tura shi cikin motar shiga babu biya, aka nufi kuto. Tun kafin a shigar da shi suka ci karo da wani saƙo daya basu mamaki ainun suka tsaya suna kallon juna sosai cike da tsoro da shakku musamman Sp Gali ya juya ya kalli wanda ake zargin a karo na" farko yaga ya yi wani irin murmushin kefen baki wanda ya bada sauti kamat na tsaki yana murza kai gefe. "Cikin sauri Sp Gali ya ce ""Amma wane ya yi hakan? Bayan ba a gama bincike an tabbatar da hakan ba," "mene matsayin ran yarinyar daya kashe ina matsayin iyayenta"" ""Sp Ghali ka yi abin da aka ce, kuto ta" "wanke shi daga zargin da ake yi masa ku sake shi ya tafi gida baku da ikon riƙe shi""" "Sp Gali ya girgiza kai cike da damuwa ya ce ""Sir kana nufin bashi ya kashe ta ba"" cikin tsawa ya ce ""Ko" "shine ya zaka yi? Ka yi abin da ya dace a matsayinka na jami'i Sp Ghali karka matsa"" jiki a matuƙar sanyaye Sp Ghali ya kunce shi tas ya ce ""Congratulations. Ka sani shari'a saɓanin hankali ce"" shi dai bai ce komai ba ya ciri biron gaban rigar Sp Gali ya fara yi masa rubutu a tafin hannunsa dam zuciyar Sp ta buga ganin ya rubuta kalmar SCORPIO kafin ya yi magana tuni ya juya ya fara tafiya cikin sauri duk da" rashin kuzarin da yake dashi yana jin inda iskar ƴanci ke ratsa jikinsa yana shaƙa tare da kaiwa hunhunsa. Kano/Birget Dambe suke yi a tsakiyar tsakar gidan mata wajan uku ne kowacce da ɗaurin ƙirji ga tukunyar abincin dake saman murhu. Banda sautin hayaniyarsu babu abin da ake ji hatta Malam dake waje da Almajirai yana jin yadda suke aibata juna da zagin juna hakan ya saka ya miƙe riƙe da bulala yana ajjiye allon hannunsu da yake rubutu ya yi cikin gidan. """Ke har kin isa ki ce za ki hana Mufeederh abinci a gidan nan? Wace ke?"" Cikin ɗagawa Inna Binta ta ce" """Ni Binta matar malam ki faɗa mini nawa Mufee ta bayar aka haɗa wajan yin abincin nan? Ke uban yaran nan bai bada kuɗin abinci ba, ba zai yiwuwa yara su haɗa kuɗi kuɗi a siyo dusar awara a yi dambun nan ki ce wai na zubawa Mufee ba ƴar banzar yarinyar da bata da kunya, kina kallo sauran ƴan'uwanta suka fita nemo kuɗi ita ta yi kwanciyarta tunda ƴar mai ce ai yanzu sai ta ci hantar ubanta Malam gashi can" "yana zaman banza ba fuss""" "Mama dake ƙoƙarin ganin ta wafcin dambun a kwano ta ce ""Daɗin abin dai ba yaranki kawai suka haɗa" "kuɗin ba, hadda Saudat ko Zaituna?""" """A'a ba ruwan Zaituna tun jiya nake ganin hazo-hazo a idanuna cikina banda salati ba abin da yake," "Saudat da ciwon ciki ta kwana Olser ta buge ta saboda yunwa ki yi ta kan ki kawai wannan rayuwa Allah dai ya fisshe mu, amma yunwa za ta yi ajalin rabin jama'a a wannan zamanin"" Mama Zaituna ta faɗa tana turo kwanan Saudat da nufin a zuba mata ta ɗan tsakura a ciki ta yafa a nata cikin. Inna Binta ta shammafe ce ta yi sama da tukunyar kasancewar ta sharifiya ta ce ""Wallahi sai Mufee ta ci abincin nan"" Mama Zaituna ta ce ""To Allah Ya isa daman kun saba cin kayan Allah Ya isa in sha Allah sai ta yi aman" "shi"" Inna Binta ta ji an cauɗa mata bulala a ɗuwawu ta yi saurin dire tukunyar ta ce" """Kan uba wanne mai tsautsayin ne haka?...,"" shiru ta yi ganin Malam ya ce ""Kina sake magana ina ƙara" "cauɗa muku shasha kawai mara kan gado""" "Ya juya wajansu ya ce ""Mayu marasa godiyar Ubangiji kawai akan abinci duk maƙota da unguwa sai" "anjiku"" Inna Binta ta ce ""Yaushe rabon da muga sisi taka banda masifar tsiya kana bamu za mu yi haka ne?"" Kan ta ya yi da bulala ta yi saurin waftar dambun a hannu ta yi ɗaki tana ""Ohho dai na ɗiba na mai" "da mugun miyau""" Haushin karnuka suka ji wanda rabon da su ji shekaru uku kenan gabaɗaya suka juya wani ihu Mama Zaituna ta yi tare da fatali da dambun da ake ta yin masifa akan shi har zaninta na kuncewa zuwa ƙasa ta yi saurin juyawa zata ɗakko ta zame da ɓawan albasa ta faɗi dif a ƙasa Kasancewar ƙatuwa ce sosai ta fasa ƙara da jan ɗuwawu ta shige ɗakinta hankali tashe. Shi kansa Malam sai da zuciyarsa ta motsa saboda tsoro ya dinga kallon karnukan da idanu yadda suke ɗaga jela tare da zaro harshe waje jibga- jibga dasu sai zagaye wanda ya shigo suke yi. Da ƙyar Malam ya ja numfashi ya ce """Muɗallabi Ɗanmalam nake gani haka? Ya suka sake ka basu kashe ka ba, ni na ɗauka ma tuni ka mutu" "wallahi, ikon Allah"" sosai kansa ke masa ciwo kamar zai rabe ga wani ciwo da jikinsa yake yana jin fatarsa" "na rawa, ya yi baƙi sosai amma manyan idanunsa na nan kayan jikinsa duk a yage ya zubawa Malam" idanu. """Kai Muɗallabi ba da kai nake magana ba? Yanzu da suka sake ka me suke nufi ka kashe ƴar mutane a" "banza kenan? Ba zan goyi bayan gaskiya ba dole na je wajan jami'an tsaron yanzu na bi ba'asi""" Cikin sauri Ammo ta fito daga ɗakinta jin sunan wanda aka kira zuciyarta har rawa take tana fitowa suka haɗa idanu dashi ya kafe jikin bango a hankali yaran gidan suka fara fitowa ya dinga bin guntattakin "yaran da kallo wasu duk bai san su ba. Ya nufi Ammo ta yi saurin ɗaga masa hannu ta ce. ""Ina jin tsoron" "kiran ka a matsayin ɗana na ji na yi dana sanin haihuwarka wallahi""" Ya buɗe manyan idanunsa sai kawai ya ja ya lumshe yana ƙara yunƙurin zuwa wajanta kenan ya ji ihu a waje kafin ya motsa Goje ya shigo da sauri yana cewa """Mai dawa ƴan unguwa ne ɗauke da makamai wai za su ɗauki fansar. "" Da sauri MOH ya ɗagawa Goje" "hannu baya son ma a kira sunanta a kusa da shi zuciyarsa buɗewa take sosai. Goje ya sake cewa ""Ba ƴan" "unguwa kaɗai ba har da gajoji da cinnakun layi"" kafin Goje ya ƙarasa sun ji ana cewa" """Ba iya Mai dawa ba har Malam da babarsa yau sai sun mutu da duka mutanen gidan sai mun ɗauki" "fansar yarinyar daka kashe tunda jami'ai sun sake shi a banza"" Mutallab ya kalli karnukansa ya musu inkiya Tiger ne ya fara zuwa ƙofar ɗakin Ammo ya tsaya Rainbow ya je ƙofar gidan ya tsaya, Spider kuma ya tsaya yana kewaye Malam. Goje ya ce ""Kai ƙarfe baya cinka tsine baya ratsa jikinka su Malam sune matsalar"" bai magana ba kai tsaye ya nufi waje gaban Ammo ya faɗi ganin ba makami a hannun Mutallab. Inna Binta ta fito tana zunduma ihu tana jama'a su kawo musu ɗauki tana leƙa ƴar ƙaramar katangar gidan ganin tarin matasan da suke waje ɗauke da makamai ya saka Inna Binta kurma ihu tana faɗin ""Ya gafilan zanbi waya kashifal gammi "" Bata gama ba aka raɗa mata gora aka ta faɗo ɗaga" saman katangar ta baje wanwar a ƙasa Mufee ta fasa ihu tana yin wajan Inna Binta ganin haka sauran mutanen gidan suka shige ɗaki banda Ammo da Malam. Moh na fita suka yi masa ƙawanya kasancewar akwai shafi a hannunsa duk wanda ya daka sai ya baje a "wajan, suna da yawa sosai cike da rashin sanin cewa tsarin jikinsa ya karye ya shiga tsakiyar su ɗaya ya ɗauki dutse ya buga masa aka nan take ya fashe, wani ya ɗaga wuƙa ya soka masa a ciki nan take wuƙar ta shige Goje ya zaro idanu ganin sun yi nasara ya saka suka zagaye Moh suna kai masa sarawa, baya faɗa da makami bai san kuma ya ake yi ba, kafin wani lokaci sun kai shi kasa ko'ina na jikinsa jini ke fitarwa daidai lokacin tawagar mafarauta suka ƙarasu wajan tare da zugar karnuka faɗan ya koma tsakanin ƴan unguwa da mafarauta cikin mawuyacin hali Moh ya ja jikinsa a hankali jin wani yana waya da ƴan'sanda ji ya yi dama layya zana na wajansa a yanzu haka? Ya dinga tafiya yana jan jiki har ya bar unguwar ya shiga cikin wani waje mai kama da gonaki kuma jeji-jeji. Tana zaune cikin bukkar hannunta" riƙe da ƙwaryar nono ta ji an faɗo cikin bukkar a gigice ta miƙe tsaye... "*To ga dai shi nan ban san ya zaku amshe shi ba, amma tabbas zai zama daidai da ra'ayinku musamman" iyayenmu mata da maza da suke wasa akan yaransu. MUTALLAB zai zo da sabon salo in sha Allah za a yi kuka sosai kuma za a yi dariya fatana kar ku yi mini zagin da kukai a MIJIN MALAMA ku amshi labarin da hannu bibbiyu ku tayani isar da saƙon zuwa ga manya ta hanyar yin sharing saboda Allah* 08164069385 WhatsApp only "[1/7, 9:31 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 2 Nimcyluv Bright pens. Second batch * Warning... For criminal issues* "Cikin bukkar ya faɗa jikinsa jina-jina da jini sara ta ko'ina da ƙyar yake iya fidda numfashi, ya zube a" "gabanta idanuwansa a lumshe har yanzu yana jiyu sautin ihu da kukanta, ya kasa ceton ta, ta sake mutuwa, yaushe zata ci-gaba da rayuwa tana sake macewa akan idanuwansa? Ya cije jajayen laɓɓansa wanda jini ya ɓata sam bai damu da yadda yake shanye jinin yana koma masa ciki ba, a matuƙar fisge ya yi maganar mai sautin gurnani ya ce ""Na amince, da gaske na amince Abbasa, zan zama mata maza, ki mayar dani jinsin mace ina tunanin zama macen ya yi daidai da tafiyar ƙaddarata! Zan zama mata maza," "bana iya kwanaki ba, bana iya wa'adin sa'a ba, ba kuma iya na tafiyar sakwanni ba, ba kuma iya na" "gilmawar kwanaki ko shuɗewar watanni da nisan shekaru ba, a'a Abbasa, a'a Abbasa ina son zama mata" "maza ne na daidai da tafiyar agogo da adadin shekarun da zan yi a duniya""" "Yadda furucin ke fitar da kan su, da yadda yake magana idanuwansa na fiddowa waje duka jikinsa rawa" "yake da ɓari yana wani irin tsuma bakinsa har wani hayaƙi yake yi jijiyoyin kansa tamkar zasu ratsa fata bakwai su keto, ganin halin daya shiga ya saka Abbasa cewa. ""Iya zubin tunanin naka kenan? Iya jarumtar kenan? Mayar da suffarka zuwa abi mafi nakasu a rayuwarka? Ka zama mace shin ko ka mace" "da. """ """Abbasa!""" "Ya kira sunanta a karo na farko a tsawa ce, domin baya son tuna abinda take ƙoƙarin cewa ""Shikenan" "shikenan, zaka zama jinsi biyu, mai halitti biyu"" ya girgiza mata kai yana jin amo da sautin muryarta cikin wutar da suka babbaka ta ciki ""Kawai ki nakasta ni"" ""Tabbas zaka nakasa, zaka zama kamar jaririn da aka haifa yau, zaka zama riƙaƙƙe zaka gagara, ubanka zai alfaharin haihuwarka duk da tsinuwarsa na tattare da kai, zaka sake yi rashi, rashi irin wanda baka taɓa yin irinsa ba, zaka samu dukkan wata shahara da" "ɗaukaka da kake buƙata, amma zaka dauwama a matsayin mata maza""" Ihu ya fasa yana ƙoƙarin miƙewa tsaye da ya yunƙura gefen cikinsa yake sake buɗewa saboda shafcecen "saran da aka yi masa, jikinsa bashi da wani gurbin da babu sara.Abbasa ta miƙe ta ɗakko wani farin abu a hannunta tana zuwa kan shi ta danne shi da duka ƙarfin daya zo mata, ta ɗauki garin abun ta fara shaƙa masa a hanci yana shaƙa da ƙyar da sauri ya damƙi hannunta ya kifa fuskarsa da hancinsa gabaɗaya," "yana ihu da gurnani jikinsa na rawa ya fara sambatu, Abbasa ta ce ""A me ka zo waje na?""" """Taya"" ya bata amsa a raunace idanunsa na lumshewa. ""Wasu sun biyo ka ne?"" Ya girgiza kai can ya ce" """Cinnaku, Cinnaku na fi ƙarfin su"" ya dinga juyya kansa can ya ce ""Akwai Kimini a tattare dani, ya faɗawa ƙashi wani abu, sun nemi asawa da Tsohuwa. !"" Ya kasa cewa komai idanuwansa har yanzu na hango" yadda gangar jikinta take ci a wuta. "Ita dai Abbasa ta kasa cewa komai ta zuba masa idanu, ta dinga kallon yadda jikinsa je rawa a hankali" "kuma ya fara saki idanunsa ƙur a saman bukkar cikin fitar hayyaci da yanayi irin na maye yake sambatu tare da kiran sunayen da ita kanta mata sani ba. A hankali ta ce ""Mutallab"" bai amsa ba sai zuciyarsa kawai dake rawa ta hango hakan ne a yanayin yadda ƙirjinsa ke ɗagawa. Ganin ya zama kamar matacce" "tsoro ya kama Abbasa ta tuna ashe bai taɓa shaƙar abin da ta bashi ba a yanzu, maganin ƙarfe dana tauri" kawai yake sha gashi kuma zaman da ya yi na shekara uku a hannun jami'an tsaro ya sa tsarin ya karye. Ƙwarya ta ɗakko ta jiƙon wani magani tare da ruwa mai zafi ta fara danna goge masa jinin jikinsa sai a "lokacin ta lura da gabaɗaya farcen yatsun ƙafafuwansa dana hannu babu ga jikinsa duk alamar an jona masa shokin akan tilasta masa amsa laifin da babu wanda yake da masaniyar komai akai, sun yi masa haka ne da nufin ya amsa laifin kashe matarsa da ya yi. Ta sauke numfashi tare da kallon bakinsa a" hankali ta kara kunnenta a tausashe yake cewa. """Ina son ta, ina son ta zuciyata zata fito ita ce wajan ta uku me ya sa.... Ina jinta a ƙasan zuciyata"" Tunda" "suke bai taɓa yi mata zance ɗiya mace ba, haka bai taɓa magana mai tsayin da ya yi a yanzu ba, duk abin da ya saka Mutallab magantuwa ba ƙaramin abu bane ba. Miƙewa ta yi ganin kamar ya samu yin bacci ta fita waje zuciyarta cike da saƙe-saƙe." Unguwar ta yi shiru saboda zuwan ƴan'sanda wanda da ƙyar suka raba tsakanin mafarauta da jama'ar da "suka zo ɗaukar fansan wacce aka kashe zai ya zama kamar an saka kafiyo ne kasancewar babu wanda bai san labarin kisan rashin mutuncin da aka yi wa yarinyar ba. Tiger, spider, rainbow sune suke ta kai kawo a ƙofar gidan Malam saboda basu tsaro kamar yadda Moh ya saba musu ya raine su tamkar mutane hatta mara gaskiya suna ganewa. Da sauri suke tafiya hankali tashe gabaɗaya basa cikin nutsuwa ɗaya" "sai ɗaga hannu sama take ba'a jin maganarta sai sautin murya. ""Ki yi haƙuri""" Sa'adah ta ce tana shafa hannunta a ƙirji alamar ban haƙuri da yaran kuramen da zata gane ta girgiza kai "tare da sunkuyawa tana buga ƙasa ta ɗaga yatsa sama alamar rantsuwa. ""Allah Ya kyauta, da kin bari mun ƙarasa gani ai ya kori ji Bafullatana"" daidai nan suka ƙarasu ƙofar gidan ba kowa a rumfar Almajiran sai allonansu da rubar tadawa da ƴan rubobi na bara. Tiger ya ƙare musu kallo yana shinshina su sai" kuma ya ja da baya yana ɗaga ƙafa ya basu hanya suka shige cikin gidan. Da Inna Binta dake yashe a ƙasa suka fara cin karo jini na zuba a gefen goshinta ɗan tofinta a bankaɗe "Allah Ya sa ba yara a wajan cikin hanzari Sa'adah ta nufeta tana girgizata ta juya ta yi wa Bafullatana alama data bata ruwa bata fahimci komai sai kawai ta kinkimo ruwa bokici guda ta kwarawa Inna Binta ajjiyar zuwa ta sauke a firgice ta miƙe zaune tana furta ""Dambun Mufee, a kawo ɗauki jama'a dambun Mufee ƴan ta'adda za su kashe ni"" ta ƙanƙame hannunta jikinta ya jiƙe jagab amma har yanzu dambun na hannunta ta miƙe ganin Sa'adah da Bafullatana sai kuma ta ja tsaki ""Irin bala'i wallahi Ammo ta haifawa unguwar Birget masifa ɗai-ɗai da ɗai-ɗai zai dinga kashe mu yana zuƙe jininmu ku duba wannan" "yarinyar ma ya kashe ta kari na uku""" Idanun Sa'adah ya cika da hawaye amma ta ɗauke kai ba tare data tanka Inna Binta ba. Inna Binta ta "watsawa Bafullatana harara wacce ke ta ihu tana taɓo Sa'adah ta ja tsaki ""Kurman banza da wofi gayya masifar, daga haihuwar kurma sai ta ɗan jagaliya"" tana kaiwa nan ta shige daƙinta ta samu Mufee tana bacci ta yi maza ta tashe ta, tura mata ɗan guntun dambun ta yi a baki bayan ta cinye ta ce ""to sha ruwa kiji abin da kika samu sai kuma gobe, ki yi addu'a ki goge Allah ki gode Muhammadur Rasulullah. Banda ina buɗe ido a gidan nan kema mutuwa za ki yi saboda yunwa kamar taki ƴar'uwar"" sai kuma saka dariya" "sosai ""Inna mene?""" """Tukunyar dambu ta kife dan ubanki da tuni ba ki lasa ba kema"" Mufee dai ta buɗe manyan idanunta irin" na Mutallab tana kallon Inna Binta. "Ammo ta dinga bin Sa'adah da idanu ganin yadda take kuka kamar ranta zai fita, Bafullatana kuma ta" "haɗe rai sai girgiza kai take ""Ammo don Allah ina Mutallab yake? Da gaske ya dawo an sake shi? Sun wanke shi daga zargin da ake masa, yana ina?"" Ammo ta ɗauke idanunta zuwa can gefe tana kallon wani waje daban a ɗakin nata can ta ce ""Ki daina kira mini sunansa sallamamman yaron nan a kunnena" "Sa'adah, ki yi hankali watarana zai iya kashe ki""" """Ba zai taɓa kashe ni ba, duk lalacewar shi jinina ne ɗan'uwana ne a wannan halin da yake ciki na ɗauka" "za ki yi murna Ammo? Za ki ja yaronki jikinki ki nuna masa kulawa gudun kar ya sake lalacewa, kar ki ce za ki yi abin da kikai a baya duk lalacewar Mutallab kece wacce kika haife shi, tun yana ƙaramin kin san zuciyarsa yadda yake da zafin nama taurin kai. Kin san yadda yake da ƙulafucin uwa kodayaushe yana manne dake, me ya sa za ki yi haka?"" Miƙewa Ammo ta yi ta nunawa Sa'adah hanya ta ce ""Tashi ki tafi gidan mijinki, banga dalilin zuwanku ba ni bani da wani ɗa Mutallab kuma na sani kuskurena ya saka na haifeshi. Wallahi kika sake yi mini maganar tsinannen yaron nan sai na daina amsa gaisuwar ki har abada"" tana kaiwa nan ta fice ta bar musu ɗakin, fuuu Bafullatana ta fice daga ɗakin zuciyarta na yi mata zafi Sa'adah ta yi shiru ita dai tana mugun son ƙannin nata ai da ba haka yake ba, ya kamata su amshi" hakan matsayin ƙaddara! Washegari Malam na zaune a rumfa yana sauraren karatun wani sabon almajirin shi. Ɗanyaro ne zauna "gefe kusa da Malam yana lissafa sabbin kuɗin hannunsa ƴan dubu-dubu sai sheƙi yake ya duba yaga dubu biyar cif ya mayar aljihu ya zaro baƙar leda mai cike da gurasa da nama ya ya fara ci yana ajjiye lemo fanta a gefe. Ajjiye bulalar Malam ya yi ya ce ""Ɗanyaro ina ka samu kuɗi da nama haka?""" """Bani aka yi Malam"" kafin Malam ya sake magana Ɗanyaro ya miƙawa Malam baƙar leda guda mai" "ɗauke da gurasa a ciki da nama ya haɗa masa da dubu biyu ya ce ""A yiwa su Mufee girki Malam""" "Jiki na rawa ya amsa yana buɗe bakinsa ""Da kyau yaron arziƙi, ina ka samu kuɗi fal haka sana'ar me ka" "fara?"" Ɗanyaro ya girgiza kai kawai can kuma ya kalli Malam ya ce ""Bana yin sana'a, kyauta ake bani kullum, bani kaɗai ba har Muhajeed da Iro"" Malam ya yi sak tunani fal ransa ya sake kallon Ɗanyaro shekarunsa goma rak a duniya a hankali ya miƙe ya yi cikin gida." **** A kusan tare manyan motoci biyun suka tunkaro babban gate ɗin ganin ya rigata kai hancin motarsa ya "saka ta rage ta fiya, hannunta ɗaya a saman sitiyarin motar ɗayan kuma ta ɗan riƙe fuskarta a hankali ta lumshe idanunta gajiya ce a jikinta sosai da ƙyar take buɗe tuƙa motar don dai bata san wahalar driver ne." """Fiyya"" Ya kira sunanta a hankali cikin muryarsa mai cike da nutsuwa ta buɗe idanunta da sukai mata" "nauyi ta kalli wayarta ta manta video call suke yi ma suna haɗa idanu da shi ta ɗauke kan ta gefe tana ya motsa fuska ""Fiyya na miki wani laifi ne? Kin sauya""" """I am sorry ina driving we'll make a call later"" ya zuba mata idanu cike da so da ƙauna yana jin ina ma a" "janyo ranar aurensu da Fiyya a ce gobe ne? Ya sauke numfashi zuciyarsa na buɗe a hankali ya ce “I adore you Fiyya"" ta buɗe idanu ta kalli cikin idanunsa sai kuma ta murguɗa masa baki ya buɗe idanu sosai sai" "ya girgiza kai yana dariya ya matso da fuskarsa dab da camerar ""Na ji kamar ina shaƙar numfashinki """ "Ya yi shiru jin ana knocking ƙofar motar da take ciki, itama ta juya ganin wanda yake tsaye ya saka ta ɗan" "yi murmushi baya ganinta saboda duhun gilas ɗin motar amma murmushi mai kyau ne a fuskarsa. Ta cikin wayar ya ce ""Waye?"" Tana ɗaukar jakarta a taƙaice ta ce ""Yaya Junaid ne""" """Ok"" ya yi sai kuma ya ce ""Fiyya"" ta ɗago idanunta da sukai laushi ta kalle shi dasu can ƙasan maƙoshi ya" "ce “I love you Fiyya"" da sauri ta kashe call ɗin tana haɗe fuska ta ɗauki wayar ta fita daga motar." """Yaya J"" yana murmushi ya ce ""Manager"" ta ɗan yi murmushi kawai ya amshi jakar hannunta ""Me kika" "zo da shi""" """Ba kyau bincike J"" ya jinjina kai suka nufi shiga gate J ya kalli driver ya ce ""Ka shigo mata da motar, she" "left the key inside the car"" Fiyya ta marairai ce fuska tana mannewa jikin J ta ce ""Yaya J na gaji sosai""" """Sannu Manager, ko goyaki zan yi?"" Ta buɗe idanu sannu yake ta yi mata har suka shiga babban parlon" "gidan ƴan samari wajan biyar a zaune a parlon duk dawowar su daga aiki kenan. Wajan tare suka dinga cewa ""Sannu Manager"" ta shige tsakiyar su tana kwanciya a cinyar Marafa ta ce ""Thank you brothers, ku yi mini tausa akwai labari""" """Gulma dai ba labari ba, daka dawowa ko wanka ba ki yi ba kin zaunawa mutane a jiki ƙazamar banza""" "Shiru ta yi masa don basu fiye shiri ba sosai ta juya idanunta rufe, tana jin yadda Marafa ke ta danna mata farar ƙafarta. Yaya J kallonta kawai yake with different thinking running on his mind. Gabaɗaya suka juya jin tafiya cikin sauri ana sakkowa daga saman bene shiru duk sukai suna binsa da idanu domin basu san ya dawo gidan ba, hannunsa ɗaya zube cikin aljihu farar riga ce a jikinsa ta kakin sojoji a gaban" rigar wajan gefe an rubuta A.A MARAFA. """Kee!"" Ya faɗa a tsawace da sauri Fiyya ta buɗe idanunta lokaci ɗaya kanta ta sara sosai tsawar ta ratsa" "kanta, ta miƙe zaune fuskarsa babu walwala kamar yadda itama ta yi kicin kicin da rai ""Tashi a nan, stupid kawai"" ta miƙe tsaye tana murguɗa baki ko inda yake bata kalla ba ta nufi saman bene kai tsaye daƙinta ta nufa idanunta cike da bacci ta faɗa saman gado cikin ƙaramin lokaci bacci ya ɗauke ta. Firgigit ta farka jin sautin labaran ɗ da ake faɗa a gidan rediyo wacce take cikin ɗakin nata, ta miƙe tsaye ta ɗauki rediyon ta ƙanƙame a jikinta tare da lumshe idanunta wasu hawaye masu zafi suna shiga bin idanunta. Ta cikin idanunta take hango fuskarsa a lokacin da rigima ta haɗa su da ita sai take ganin" kamar yanzu ne komai yake faruwa. Students ne an cika sosai saboda class partyn da ake yi na kammala exam maza da mata babu teacher ko ɗaya tunda ta shigo hall ɗin makarantar tasu take duban inda zata ganshi. Cikin sa'a ta ganshi yana zaune saman window sanye da gajeren wando fari tas sai armless ɗin riga wacce duk aka yanke hannunta gashin kansa rabi a aske ya zubawa wani tafkeken gidan masu kuɗi idanu ta waje baya ko ƙiftawa kamar an ce ya juya ya ganta tsaye ta zuba masa idanu yaja tsaki kafin ta yi magana an shigo an "ce ""Mutallab, principal yana nemanka an kai ƙarar ka wai kana son Fiyya""" "Ya ware idanu abin da bai taɓa zuwa tunaninsa ba kenan sai kuma ya cije baki ""Shi principal ɗin ubana" "ne Malam Abdullahi kenan?"" Ya juya ya kalleta sosai ya ce ""Sai godiya, ni? Kuma ke hauka kenan""" """Kai ne mahaukaci"" furucin ya fita daga bakin Fiyya ""Kuma na yi maka nisa, kasan yadda nake da masoya" "a makarantar nan amma ni ubana ba soyayya ya kawo ni ba, karatu zan yi ina da buri mai faɗi da zan" "cimma"" Ya miƙe tsaye yana kallonta daga sama har ƙasa a ransa yana ƙissima abu ""Shi uban naki can ta" "matse masa, karatun banza kawai ka zama mai iko shine""" """Ba dai ubana sai dai "" Ya buɗe idanu sai kuma ya fasa abin da ya yi niyya ganin hawaye a idanunta" abin da bai taɓa gani ba. Da sauri ta fice daga hall ɗin ta zaga baya ta durƙushe a wajan tana fashewa da "wani irin kuka kamar zata haɗiye zuciya ""Daddy na shiga uku ina son Mutallab""" "Ƙanƙame redion ta yi tana sake fashewa da kuka jikinta har jijiiga yake ta ce ""Na shiga uku Daddy, ba zan" iya ba I can't do it ina son shi. "Kamar daga sama haka ya faɗo cikin gidan, jikinsa duk liƙe da bandeji jini na ɗiga kaɗan-kaɗan kwana" "biyu yana jinyar raunin bai san waye ya yi masa ɗinki ba. Idanunsa jajur har lokacin saboda bai gama dawowa daidai ba sai muzurai yake yi ya ja ya tsaya yana kallon murhun da aka sauke abinci akai ya juya ya kalli ɗanwaken dawar da Inna Binta ta yi ta shiga daƙi ɗakko magi ta barbaɗa ko arziƙin yaji bai samu ba, yaja kwanon da hurɗu-hurɗu yake tura ɗanwaken kafin wani lokaci ya kammala cinyewa tas ya zube a wajan ya kwanta ya rufe idanu, wata nutsuwa yake jin daya kwanta a tsakar gidan mahaifin nasa. Ya yi kamar bacci yake yana jin Inna Binta ta lailayo ashar ta ƙunduma ta ce ""Wanne ɗan abu takazar ne ya cinye mini abinci Mufee wanne mayunwacin ne mara godiyar Ubangiji"" tsit ta yi ganin Moh kwance hannunsa duk manja taja baki ta tsuke ta ɗauke kwanan tana suɗewa a zuciyarta tana jan Allah Ya isa. Har ya shiga ɗakin Ammo ta bankaɗa labule ta ce ""Wallahi abincin da ɗan ta'addar ɗanki ya cinye mini Allah Ya isa, kawai kin haifa mana jaraba ko ɗanɗana ɗanwaken ban yi bafa ya cinye"" ta dinga zagin Ammo ta uwa ta uba ta shige ɗaki tana sake suɗe kwanon da ƙyar ta samu rancen ɗari biyu ta yi cefane" da ledoji ta dafa. Tana shiga ɗaki ba jimawa ta ji an bankaɗo labule sai ta zuciyarta ta buga ganin shi tsaye hannunsa riƙe "da gora ya suke askara a gefen ƙugunsa ga gori a hannunsa, ya juya ya kalli Mufee da hannu ya yi mata alama data fita cikin sauri ta fice tana fita muryarsa a daƙushe kamar dole ya ce ""Tiger spider a yi mata aiki"" manyan karnukan suka faɗa cikin ɗakin Inna Binta ta fara ihu tana maƙale jikin sif ""Nafsi nafsi jama'a na shiga uku ya Allahu Ya Rahmanu, don Allah ka yi haƙuri Muɗallabi zan bawa Ammo haƙuri ka rufa mini asiri kar Mufee ta zama marainiyya"" Haushi kawai karnukan suke Tiger na kai mata cafka Inna" "Binta ta fashe da kuka fitsari na bin ƙafarta ta ce ""Hal'àtaka hadisul gashiya ni Binta na shiga uku""" "Moh ya ce ""Sai godiya"" gabaɗaya karnukan suka tsaya cak Inna Binta na haki ta jiƙe gabaɗaya da fitsari" "har lokacin tana maƙale jikin sif kamar ba zai magana ba ya ce ""Bani ƙudin nan"" jiki na rawa ta miƙa masa ɗari biyar ɗin hannunta ya amshe ya yi waje ta sake sif ɗin ta fashe da kuka tana faɗin ""Tsinannen yaro manta ganin yaron dake son uwarsa kamar mutuwa ba irin shi"" Moh na fita ya leƙa ɗakin Ammo ta ɗaga kai tana ganinsa ta ɗauke fuska ya yi ta kallonta ya jima tsage kafin ya sauke labulan ya juya. Yana fita wani babur na tsayawa a gabansa aka cillo masa takarda da gudu aka ja babur ɗin tare da barin" wajan. Ya ɗauki takardar ya buɗe rubutu ne bai fi layi biyu ba a hankali ya fara karantawa. _Mai dawa baka gajiya? Sau dubu zaka kula mace sau dubu zamu kashe ta. Karo na uku kenan ga misali akan matarka nan_ da jan biro akai rubutun ya juya da sauri amma tuni babur ɗin ya ɓace ɓat waye wannan? Su duka shi ne silar mutuwar su kenan? Waya ya amsa hannun wani Almajiri ya kira wata "number ana ɗaga aka ce ""Sai godiya"" Ya numfasha" """Duk inda ƴan daba suke ka haɗa mini su"" ta cikin wayar aka ce ""Mene haɗinka da daba ko dai ka fara" "shaye-shaye a state cid ɗin?"" Moh ya cije baki ya ce ""Zan fitini mutane, na ji daɗin zama can""" """To me za su yi maka?"" Wannan yaran da suka sare ni iyayensu za su ɗauki sabbin ciki yau, ƴan cikin gari" "ne a yi mini kan me uwa jawabi"" yana faɗin hakan ya kashe kiran ya goge number tas ya lumshe idanunsa ya buɗe sai kuma ya cije leɓe zuciyarsa zafi take sosai ji yake dama ya yi kuka, amma ba a haife shi don ya zubar da hawaye ba ya ɗaga idanu sama ya ce ""Da gaske ni na kashe ta amma ba zaku taɓa sani ba"" daidai lokacin mafarauta suka kawo kai suna busa ƙaho da buga gangaga suka zagaye Moh ana ""Sai Mai dawa ina uban wasu ga namu wuya a ina wuya a daji, kai ne mai Tiger kai ne mai gadon tawada"" Jikinsa ya hau ɓari da karkarwa tsumin shi ya motsa idanunsa na ƙaƙƙafewa ya yi kururuwa tare da ɗaga gora sama ya ja ya ƙame sai jikinsa dake rawa ya fara ""La'ilahaillahu, sai ni ɗan babana Malam Abdullahi ɗan malam ɗan gatan Ammo ƙanin Sa'adah ƙanin Bafullatana waye ce bani ba Muɗallabi sarki Mai dawa da jeji"" gabaɗaya suka zagaye shi suna sake zuga shi daidai lokacin kuma suka ganta kamar" daga sama..... *In sha Allah za ku ji abin da baku taɓa ji ba * 08164069385 WhatsApp only "[1/7, 9:32 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 3 Nimcyluv Bright pens. Second batch "Da sauri ya nufe ta kamar zai kai mata cafka, ta yi saurin ja baya idanunta cikin nasa. Yana tangaɗi ya ja" "ya tsaya a gabanta tare da ƙura mata idanunsa da suke lumshewa, har yanzu jikinsa ɓari yake domin" basu daina buga ganga da ƙahon da suke busawa ba kamar masu yin gangi. "Hannunsa ya ɗaga musu cikin sauri suka daina abin da suke, cikin izza da gadara ya basu umarnin tafiya" "har lokacin idanunsa yana kanta ganin yadda take kallon shi kamar ya ta saba ganin halittarsa. ""Ban yi zaton a haka zan ganka ba, autan Ammo me ya sa?"" Ya ɗauke kansa yana haɗe fuska sosai ba wargi banda cewa ita ce ba zai taɓa tsayawa ba. Cikin raunin murya kamar za ta yi kuka ta ce ""Me za ka yi da wuƙa haka?"" Ya buɗe ido sosai sai bai magana ba, a hankali ma ya bi gefen ta zai huce ta yi saurin riƙe masa hannunsa tana faɗin ""Ni ɗin ma? Yau za a ji kan mu da kai, kar ka faɗa mini sauyin da ka yi ya" "zagayo har kai na?""" "Ya ɗago kai ya kalle ta ya kalli hannun data riƙe shi da shi, hannunta fari tas saɓanin nasa da yake mai" "kauri kuma baƙi irin na majiya ƙarfin nan wanda suke tashe akan shekarunsu. ""Don Allah ka tsaya mu yi magana, ni ko gidan ba zan shiga ba wajanka na zo"" ya cije bakinsa ya mai da kai gefe cikin muryar mai kauri ya ce ""Kin ci darajar Ɗan Amina, mene sakin?"" Ta girgiza kai kawai tana duban gefe dakalin dake wajan ta gani ta je ta zauna akai, ta yi masa alama ya zauna amma ko motsi bai yi ba, ta san cewa yana jinta amma hankalinsa na kan hanya sai waige-waige ""Mutallab ka kalle ni bafa wani zai kawo maka farmaki ba"" ta nisa idanunta cike da ƙwalla ta ce ""Don Allah kai ne ka kashe ta? Ba zargin ka nake ba Autan Ammo ni me iya rufa maka asiri ce idan ya zama kana da laifi ka faɗa mini gaskiya na maka" "alƙawarin ko Ammo ba zan faɗawa ba, ka kashe matarka ko ba kai bane?""" "Ya juya da wani irin sauri yana kallon fuskarta da take kallon shi cike da damuwa, idanunsa ya yi jajur" "naman jikinsa na motsawa ya kasa furta komai. Miƙewa Anty Hameeda ta yi tana girgiza kai kuka na cin ƙarfinta ""Ko minti ashirin ba mu yi da kai maka matarka ba, sai labarin mutuwar ta muka ji da kisan wulaƙancin da aka yi mata. Mutallab kai ne fa muka gani tsaye akan gawarta, kai ne fa riƙe da wuƙar da aka kashe ta da ita jikinka duk jinin matarka innalillahi wa'inna ilaihirraji'un na kasa yadda ka kashe ta, daman soyayyar da ka nuna mata na iya fatar baki ne?"" Wani irin ihu Anty Hameeda ta yi tana kaiwa jikin bango ganin ya ɗaga hannunsa ya yo kanta sai kuma ya tsaya cak, a hankali da baya da baya ya dinga ja yana ƙare mata kallo sai kuma ya taune bakinsa idanunsa kamar zasu zazzago don girma kallo ɗaya idan ya yi dasu sai an razana da ƙyar ya iya ware laɓɓansa biyu da sukai masa nauyi sosai ƙasan" zuciyarsa na ta fasa banda cewa Anty Hameeda ce tabbas da sai ya karya ta gida huɗu. """Ni na kashe ta, ta cancanci haka ne"" ya juya da sauri Tiger da spider da rainbow suka bi bayansa kamar" "zai tashi sama haka ya sha kwana. Zubewa Anty Hameeda ta yi a wajan tana rushewa da kukan baƙin ciki, su waye suke da saka hannu wajan lalacewar Mutallab? Ba komai ta sani ba ita ba ma'abociyar zaman garin bace ita da mijinta ta dinga kuka da ƙyar ta rarrashi kan ta, ta miƙe tsaye kamar zata shiga gidan nasu sai kuma ta fasa tana ƙoƙarin barin wajan ta ji Malam ya ce ""Hameedatu me kike anan ina mijin da yaran naki?"" Kanta a ƙasa ta ce ""Suna gida, ina yini Malam?"" Ya jujjuya yana kallon hannunta ganin babu komai ya ce ""Ba za ki shiga bane?"" Ta girgiza masa ""Zan juya wajan Mutallab na zo"" ya jinjina kai domin" ba wannan ne a gabansa ba. """Ba wata mutalla da zan iya samu a wajanki na siyo wainar rogo?"" Ta buɗe jakarta ta zaro kuɗi tana" "irgawa ya yi maza ya fisge ya ce ""Mene na lissafi? Maza jeki wajan yaranki kuma na ja kunnenki babu ke babu yaron nan idan ba su kike watarana ya ja miki masifar da za ki ƙare rayuwarki a gidan ɗan kande ba"" bata ce komai ba sai data juya zata tafi ta ce ""Duk lalacewar Mutallab kai ne ka haife shi, jininka na wanzuwa a nasa"" tana kaiwa nan ta yi gaba abinta saboda ɓacin rai da damuwa ko gabanta bata gani" sosai. Moh na kwance a saman wani dutse idanunsa a rufe tun bayan barin shi wajan Anty Hameeda ya zo "wajan ya kwanta, zuciyarsa a cunkushe take babu gurbin samun sauƙi a cikinta duk yadda ya ke son tuna waye shi me ya sa ya zama haka sai ƙwaƙwalwarsa ta yi hooking, ya ɗauki zafi sosai ta yi ta processing ya ji Ammo ɗinsa kawai yake son kasancewa da ita yanzu. Ya motsa kaɗan zazzaɓi ne sosai a jikinsa saboda saran da aka yi masa bai gama warkewa ba, baya kuma shan magani wacce zata iya kula da shi baya jin zai iya zuwa wajanta. Ya ƙanƙame jikinsa sosai abubuwa da yawa baya son tunawa sai ya cimma muradin zuciyarsa sai ya ɗauki fansa na abin da aka aika, sai ya bayyana abubuwa da dama tunda har suka bari ya shiga cikin gidan yari ya kuma yi shekaru uku a Cid ya rayuwa cikin masu aikata manyan laifuka. A sama" ya ji an kira sunansa """Mai dawa, sarki mai jeji"" bai buɗe idanunsa ba, bai kuma ɗauki murya ba haka baya buƙatar sanin waye" "don hakan babu abin da zai ƙare shi da shi. Ya nemi waje ya zauna yana furta ""Ka saɓe Mai dawa ka basar, fansa kake buƙata ba raunin zuciya ba, ka ajjiye tunanin baya ka fuskanci burinka ka zama abin da kake muradi kafin aga bayanka"" har lokacin bai buɗe idanu ba, ko inuwarsa bata motsa ba. Mangal ya ɗaga kai yana busawa samaniya hayaƙin sigari ""Idan kana son yin bacci cikin nutsuwa ka manta komai ya kamata ka sha wannan"" ya zaro abu a aljihu yana kalle-kalle sai a lokacin Mai dawa ya buɗe rinannun idanunsa ya juya ya kalli mai maganar irin kallon waye kai? Mangal ya ce ""Ka dake musulmi akul" "musulmu, zuwa na yi na taimaka maka""" """Riƙe wannan tiramol ce, ko doki ya sha sai ya gane barno gabas take kana afawa za ka ji zam-zam komai" "ya zama labari"" Mai dawa zubawa ƙwayar idanu shi bai taɓa shan ta ba, bai taɓa shaye-shaye ba ya juya ya kalli Mangal ""Da gaske zan yi bacci?"" ""Darr ne ai aikin wannan kamar yankan wuƙa ne, mai ƙirin ce da ƙyar aka bani ita ina karɓa na doƙu nan"" jikin Mai dawa na rawa ya amshi ƙwayar guda ɗaya ya cilla cikin bakinsa, yana runtse idanu ya yi shiru. Mangal ya zubawa Moh idanu a ransa yana jin wani daɗi da kuma farinciki bai taɓa yin aikin da za a bashi kuɗi masu yawan da aka ce ba irin na yau, gashi ya yi nasara Moh ya sha ƙwayar. Jikin Moh ya ɗauki rawar zafin zazzaɓi duk da irin dariyar da yake da ita, gashi duk inda ya motsa ciwon shi jini yake babu wani wanda zai iya duba lamarinsa sannu a hankali ya fara dafe kan shi da wani irin gurnani yaga sama na jujjuya masa ya ɗaga hannu da niyyar ya tare sama ya faɗo daga saman dutsen sai saka hannu yake yana tare sama a hankali kuma jikinsa ya fara saki yana jin wani shuu a tsakiyar kansa yana game jikinsa gabaɗaya zuciyarsa da tunaninsa suka dinga kissima masa kawai ya" kashe kansa ko ya cinnawa gidansu huta gabaɗaya kowa ya mutu har shi. Ganin laɓɓansa na motsawa alamar yana magana ba'a ji sosai ya saka Mangal matsawa tare da kafa "kunnensa a bakin Mai dawa cikin mawuyacin hali yake furta ""Safiyyerh... Safiyyerh...Safiyyerh"" Mangal ya maimaita sunan a fili “Safiyya?” wace haka? Ko ita ce wacce ta mutun wacce aka kashe? Ya miƙe" tsaye ya ɗauki wayarsa wata number daya haddace ya saka ya kira ana ɗagawa Mangal ya ce """Sakin nan ya kammalu, yanzu zan zo a taya na amshi fararen"" shiru ya yi yana sauraren mai maganar" "kafin ya ce ""Jira jira jira nifa cikin uwata aka haifan ba ɗan zina ba, na maka al'ƙawarin dole zan bawa Mai dawa ƙwayar kuma da sannu zai zama namu. Sai dai na ji yana kiran sunan wata ɗawa wai Safinu ko Safiya?"" Ya ƙara yin shiru ya numfasa ya kalli Moh dake kwance a wajan ya ce ""A'a Oga ni bana sabga da masu ɗan kwalin nan. Da ƙirin ka oga kanka baya kullewa a fice kake sai na doƙu yanzu"" Kashe wayar" Mangal ya yi kuma ya goge kiran cikin sauri kuma ya bar wajan. "Baya tantance halin da yake ciki, sai dai yanayin na yi masa daɗi sosai shi ba'a sama ba shi ba'a ƙasa yana" fatan ya dauwama har ƙarshen rayuwarsa. Duk da a cikin giyar maye yake bai hana shi gano fararen "kyawawan idanunta masu matuƙar ɗaukan hankali ba, a lokacin da take masa wannan duban ji yake" kamar ba zai taɓa aikata abu makamancin haka ba amma ƙuruciya da wawta ya saka komai ya wakana a lokacin da duk su biyun basu ankara ba. Gani ranar yake kamar yanzu a cikin idanunsa ya juya da ƙyar yana buɗe idanu zuwa gefe guda sai fara hango kansu su biyun a shekarun da suka huce suna tsaye tana jifansa da wani irin kallo. "Suna tsaye za su shiga practical a lokacin, ya jingina da jikin bango ƙafarsa ɗaya a jikin bangon ɗaya a" "ƙasa ya harɗe hannayensa duka biyun a ƙirji students ɗin yake kallo yana mamakin abin da ya saka ƴan mata ke burge wasu mazan, as a man kuma good man kawai ka nemi kuɗi ka yi arziƙi ka shahara a duniya shi ya fi, ka zama mai iƙo da faɗa a ji, ka zama wanda zai iya samun abincin da zai ci da safe kuma ya ci da rana ya ci kuma da dare ya bawa ƴan'uwasa da duk mai jin yunwa ya zamana kuma ka kasance mutumin da ake shakka duniya ta san da zamansa bawai kana namiji ka ƙare a wajan wata yarinya ba." Yana cikin wannan tunanin ya ji an ja mugun tsaki ya buɗe idanu ya ganta sosai ya buɗe idanunsa da suke a rufe kodayaushe cike da gashin idanu masu tsayi. """Kai ai babu macen da zata soka a school ɗin nan, sai dai kaga ana soyayya"" bai taɓa tsayawa ya tanka ta" "ba sai lokacin har zai mata shiru sai ya ce ""Ok"" ta haɗe fuska ""Saboda macen abinci ce ko iskar shaƙa daya zama dole Mutallab ya amfana dasu?"" Ta yi masa sheƙeƙe tana nuna masa ɗaliban makarantar da kana ganinsu zaka san iyayensu nada arziƙi sosai kowanne a students ƙuruciya da tashen balaga na ɗawainiyya da su. Ta ce ""Mata ai sune jin daɗin maza, kai fa mace ko kiss bata taɓa yi maka ba a school ɗin nan"" Mutallab ya yi ta kallonta daga sama har ƙasa ""Matar Moh zata zama mai irin halin MOH"" har ya juya sai yaga bata ci bulus ba ya tako har inda take ya zuba idanunsa cikin nata kamar yadda take kallon tsakiyar nasa idanun yana sake matso da fuskarta ""About the kiss, ƙilan Moh ya ji ƙan ki ya yi miki" "don naga shi kike buƙata""" Tsoro ya kamata amma ta dake ta fara ja baya ya yi saurin saka ƙata ya falleta kamar zata kita ya saka "hannu ya cafko gaban wandon uniform ɗinta ya dawo da ita dab dashi yana sauke mata numfashi a hankali kuma ya ɗora fuskarsa. ""Mai dawa"" kiran da aka yi masa ya saka bidiyon abin da ya faru a baya" "saurin gogewa a idanunsa har lokacin idanunsa na kafe waje guda sosai yake son sake tuna abin da ya faru a lokacin ya gagara. Goje ya ce ""Nan ka auno kenan, na samo sha ɗayan gayen nan. Ya naga kamar a buge kake?"" Goje ya faɗa yana tattaɓa jikin Moh ya ji zafi sosai idanunsa kuma ya kaɗa ya yi ja ya san babu abin da zai fahimta koda ya yi masa bayani ""Mene haɗin mafarauci da shaye-shaye?"" Shi dai ya yi shiru kawai zumbur kuma ya miƙe tsaye kamar wanda ya tuna wani abu ya juya idanu wuƙar da ya gani a jikin Goge ya fusga duk yadda Goje ya yi da shi amma ya kasa amsar wuƙar cikin sauri kuma ya mara" masa domin ganin me zai aikata? Tafiya suka dinga yi har suka kawo titi ya tsayar da mai napep ya faɗa shima Goje ya faɗa ciki. Shi kansa "bai san ina za a kaisa ba. Tafiya suka sosai har suka ƙarasu daidai wajan wani ƙaton kamfani wanda kaf Kano babu wanda bai san zaman wannan kamfanin ba. Iya haɗuwa ya haɗu ginin kamfanin ma abin sha'awa ne ga masu tsaro ta ko'ina. Ya tsayar da mai napep ɗin ya sauka ""Kuɗi na?"" Ya buɗe ido sai ya" "share ""Malam haƙƙina na daƙƙoka daka waje mai nisa ina da wajan zuwa"" Goje ya ce ""An cinye""" """Kut, ni da haƙƙina daman tunda na daƙƙo ku na ji kuna warin wiwi na san cewa ɓarayi ne ku, cikakken" "ɗan zamani ne nima ku bani kuɗina yanzu ku na daki kuɗin"" Goje ya ce ""dan babarka zo ka daka idan ka haifu"" mai napep ɗin ya share shi, ganin Mai dawa ya yi shiru yana kallo kamfanin ya nufi inda yake ya damƙi wuyansa ya ce ""Kai ka tsare ni ai ,"" kafin ya ƙarasa maganar Mai dawa ya damƙi hannunsa ya" "matse ya bada sauti ƙass har lokacin ya kafe kamfanin da idanu. Mai napep ɗin na ihu yana neman ɗauki Goje ya zaro wuƙa yana bubbuɗe jajayen idanu hakan ya saka ba wanda ya zo wajan kowa saurin barin hanyar yake gudun kar tsautsayi ya faɗa masa. Mai dawa ya saki karyayyen hannun mai napep ɗin ya ƙara damƙar ɗayan zuciyarsa na tafasa har yanzu ba komai yake ganewa ba, ya sake karya hannun" daman ba tare daya sake shi ba ya ce """Goje""" """Mai dawa sarki mai jeji, sai godiya""" """Kamfanin meye wannan? Na waye kuma?"" Goje ya kalli tafkeken kamfanin da manyan motoci ke ya" "shiga da fita kafin ya ce ""Sai godiya, ciki ne a kan sabgar nan bani da ilimi akan wannan massarafar""" Mai dawa ya saki mai napep ɗin da ya karya masa duka hannunsa biyu yana ja da baya a hankali ya ce """Ina son shi, ina son ya zama mallakina"" cikin sauri Goje ya ce ""Me kake so?""" """Kamfanin""" "Tana zaune akan kujerar dake haɗɗan office ɗin, cikin nutsuwa dake danna system ɗin gabanta files da" yawa cike saman table ɗin hankalinta na kan aiki sosai kana kallon fuskarta zaka san serious ce ita akan aikinta bata da wasa ko kaɗan. Brown suit ce a jikinta mai riga da wando ta yi rolling kanta da mayafi zagayayyiyar fuskar ta fito sosai ta saka wani shade a idanunta baƙi. Wayarta ta fara ƙara alamar kiran ta "san tunda ya fara ba zai daina ba, cikin nutsuwa ta murja kujerar ta yi ba, suu kuma ta kujerar zuwa inda wayar take ta ɗaga kiran tana sawa a hands free" """My manager"" ta ɗan buɗe idanu ta cikin glasses ɗin ta yi shiru tana ta danna system a hankali ya ce" """Maamah"" ya kira ta kamar yadda suka ce mata ta sake yin shiru domin bama ta jinsa sosai ""Fiyya ina miki magana?""" """Yaya J yaushe zaka fara ɗaukan aikinka very serious, ina kan aiki fa"" ya yi murmushi mai kyau tana jin" "sautin shi a kunnenta ""Sanda kika so na zama Mamaa""" """Uhm kiran fa?""" """Kin ci abinci, nina manta Captain ya saka na kira na tambaye ki"" cak Fiyya ta tsaya da abin da take ko dai" "bata ji daidai ba ""what?"" Ya ce ""Kin ji ai"" a taƙaice ta ce ""Na ci"" ya ce ""Good, ƙarfe nawa za ki tashi?""" """Ina da meeting Yaya J ka biyo ka ɗauke ni i can't drive cikina ciwo"" cikin sauri ya ce ""Subuhanallahi! Bari" "na zo na duba ki ko kawai mu tafi gida"" kashe wayar ta yi domin ba wani ciwon ciki da take so take ta saka kanta busy sosai ko zata manta da wasu abubuwan. Knocking aka fara tana ji ta yi shiru can ta ce ""In"" ya buɗe ya shigo idanunsa ya sauka a jikin sunanta dake manne a table ɗin “SAFIYYERH A. MARAFA”" "ya ɗauke idanunsa yana rusunawa ya ce ""Good day Maa""" "Da hannu ta yi masa nuni ya zauna bayan ya zauna, still idanunta akan system tana danna keyboard ta" "miƙo masa file ya ɗauka ya ce ""Wannan fa?"" A nutse ta ce ""I have to ask, daga ina file ɗin nan? Wanne kaya aka fitar aka samu ruɓanyar kuɗi kashi wajan goma cikin awa guda Accounter?"" Ya ɗan shafa kai ya" "ce ""Maa ni ma haka na gani, kawai aka ce na kawo ki saka hannu""" """To ba zan ba"" ta ce a taƙaice. ""Maa ya zama dole fa""" A hankali ta ɗago idanunta sai kuma ta cire glasses ɗin idanunta manyan fararen idanunta tas a kan shi "ya yi saurin ɗauke nasa idanun saboda kwarjin da ta yi masa ""Ni ce Manager, ka faɗawa duk wanda ya" "turo ka cewa ba zan ba, ina buƙatar explanation me aka siyar a kamfanina nan har aka samu shigowar" "kuɗi kimanin 5.1B cikin awa guda, ba details na abin da aka siya sai file na zuwan kuɗin kuma yanzu ana buƙatar fitar dasu daka account ɗin kamfani? This is complicated"" zai yi magana cikin tsawa ta ce ""Out of my office accouter"" cikin saurin ya miƙe tsaye yana ficewa daga officer ɗin. Numfashi Fiyya ta sauke ta rufe idanunta da sauri kuma ta buɗe jin an shigo ba tare data bada umarnin a shigo mata officer ba." Cikin sauri ta miƙe tsaye tana ɗan ja baya ta shiga ƙare masa kallo daga sama har ƙasa ta yi mamaki to babu security a ƙofar office ɗin nata ne? Da ƙyar ta ja numfashi tana saukewa ta ce. """Who are you? Waye kai." For more information 08164069385 WhatsApp only. "[1/7, 9:32 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 4 Nimcyluv *Bright pens. Second batch* Ƙarewa office ɗin kallo ya yi yana buɗe idanunsa akan Fiyya wacce ta ɗan ja da baya tana ɗauke kanta "gefe. ""Ya Allah i really missed her, Safiyya A. Marafa"" ya furta yana kallon makaken photon Fiyya dake cikin office ɗin kafin ya ƙarasa ciki murya a hankali ya ce" """Wa kike tunanin zai zo banda mijinki Fiyya? You're enjoying teasing me"" sai a lokacin ta sauke ajjiyar" "zuciya a ɓoye tare da ɗan yin murmushi mai kyau wanda ya saka shi lumshe idanunsa ya buɗe ""Like this. I missed you completely Fiyya ba shiri na dawo gida fa""" """Ina yini ya hanya?"" Ashraf na kallon files ɗin gabanta ya ce ""Allahamdulilah. Ya naki aikin Manager?"" Ta" "ce ""Lafiya, me ka zo yi a kamfanin ko kana da business damu ne?""" """Eh, babban business ma"" tana kallon system ba yabo babu fallasa ta ce ""Ohh"" kallon ta ya dinga yi" "yadda take operating system ɗin cike da nutsuwa fuskarta a kame ba wargi hakan bai hana kyan fuskarta bayyana ba ya ja numfashi ya sauke yana jin wani abu sosai na fuskarsa a kan Fiyya ya kalli agogon hannunsa ya ce ""Ko gida ban je ba, ina son na samu nutsuwa da kallon fuskarki dear"" kamar baza ta ce komai ba sai kuma ta ce ""Ok"" mamakin halinta na ko ina kula yana damunsa cikin damuwa yana sassauta" "murya ya ce ""Fiyya"" ta ɗago ta kalle shi sai kuma ta zame idanunta." """Na kasa fahimtar me kike nufi dani Fiyya anya kina so na kamar yadda nima nake son ki? I told you na" "dawo saboda ke amma ki ce mini wani ok? To hell with the ok ɗin na tsani irin wannan ɗabi'un naki, da na yi miki uzurin rashin sabo ne amma for good 5years muna abu ɗaya dake? Idan customers ne kya musu fara'a ki yi welcoming nasu, amma ni da zan zama mijinki kwana kwana nan kike ma haka, ko wanne gardi ya zo office naki kin zama wata kamar jerry abar kallon kowa"" ya girgiza kai cikin damuwa" da ƙunci yana zare gilas ɗin idanunsa tare da buga table ɗin gabanta ya ce """A cikin abu biyu dole ne a yi guda""" Kallon Ashraf kawai take ta tabbatar yana da anger issues tama rasa me za ta ce masa don takaici ya zo "har office ɗin ta kuma yana yi mata hayaniya, yana ƙoƙarin tara mata jama'a. Ko motsi ba ta yi ba, tana" "juya kujerar da take kai a hankali idanunta zube a kansa. ""Ina ji Ashraf"" bata taɓa kiran sunansa ba sai" yau hakan ya saka ya kalleta da sauri ransa ya ƙara ɓaci. """Aure ko aiki, ya zama dole ki zaɓi guda ɗaya a ciki""" """Ok"" ta sake cewa tana miƙewa tsaye tare da ɗaukar jakarta da wayarta da makullin mota ta zaga a" hankali zata shige shi ya yi saurin saka hannu ya riƙo nata hannun cikin sauri ta kalle shi tare da jefa masa wata iriyar harara sakinta ya yi ya matsa dab da ita yana sauke mata hucin numfashin ɓacin ransa dake fitowa tun daga ƙasan zuciyarsa. """Ki bani amsar abin da na buƙata kafin ki fita, aikin ki ko aure""" Ta taune leɓenta tana ware masa manyan idanunta sai kuma ta kalli wayarta tare da buɗewa ta shiga "wajan photos pictures ɗinsa ta nemo wanda ya yi kyau sosai ya saka ƙananun kaya lokacin bashi da lafiya ta je duba shi ya fito harabar gidan tana murmushi ta ce ""My patient, bari na ɗauki photo as evidence karka mutu bani photon nunawa yarana masoyin da ya tafi ya bar Fiyya"" a lokacin juyawa ya yi ya kalleta daga kwancan da yake ya wurga mata harara sai kuma ya miƙe tsaye yana nufar inda take ta yi saurin yin" baya tana masa wani irin murmushi ya tsaya yana kallon ta sai kuma ya ce """To make you clear, ba ki da wasu yara sai na Ashraf, ba ki da wani miji sai Ashraf ba wanda za ki yi wa" "takaba sai Ashraf. Ashraf na Fiyya ne Fiyya kuma ta Ashraf ce in sha Allah"" murmushi kawai ta yi bata" ce komai ba ta ɗauke shi photon yana langwaɓe kai gefe. Fiyya ta shafa screen ɗin wayarta tana kallon photon kamar yanzu ta ɗauka cikin muryar mara hayaniya "idan tasu ta ce ""Ya ce wai na zaɓa aiki ko shi, kar ya buƙaci jin amsar daga bakin Fiyya"" fisge wayar ya yi ""Dole ki bani amsa yanzu ba sai anjima ba"" ta gyara tsaiwa tana fuskantar shi da kyau a hankali ta matsa dab da shi ta ce ""Allah Ya baka wacce ta fi Fiyya"" Ashraf ya yi sak can ya ce ""Me kike nufi?""" """Ina nufin na haƙura da auren, na zaɓi aikin"" tana kaiwa nan ta fisge wayarta cikin sauri ta yi waje ya bita" "da kallo zuciyarsa na ta fasa. Tana fita ta kalli security ta ce ""Idan ya fito a rufe mini office"" waje ta yi ko Elevator bata tsaya shiga ba ta sakko ta bene dake a wajan 5 floor office ɗin nata yake. Sai gaisheta ake yi amma ba wanda ta saurara idanunta har dishi-dishi yake saboda ɓacin rai." Misalin 1:43 dare ya nutsa ana samawa zuciya nutsuwa ya yinda kowa yake bacci a lokacin ne safiyarsa "ta waye. Ya tsaya a ƙofar gidan yana kallon gate sosai ya jima a wajan kafin ya juya ya kalli Goge da Darma cikin hanzari Goje ya shiga buga gate ɗin gidan kamar zai cire shi, sun jima kafin daga bakin ƙofar suji an ce ""Waye?"" ""Buɗe"" Goje ya ce yana zare wuƙa tare da matsawa jikin ƙofar mai gadin a ruɗe yake" "sosai ya ce ""Kamarya na buɗe a wannan zamanin da muke cikin insecurity na sani ma ko ƴan fashi ne?""" """Sune"" Darma ya ce yana yin muzurai shi kaɗai ne a cikin su yake a buge shi Moh abin da Mangal ya" "bashi har yanzu bai gama sakin shi ba, shi ya sa ba komai yake ganewa ba. ""Wallahi ba zan buɗe ba, babu mamaki kun ji Alhaji Wada ya dawo gari shine za ku yi masa fashi""" """Ko ka buɗe gidan nan na rantse da Ɗan Amina na shigo sai na yi maka ɓalli-ɓalli"" ai kowa mai gadin ya" "ce ""Ka yi mini ɗari-ɗari ma amma babu abin da zai saka na buɗe daman ƙasa babu lafiya ga yaron can daya dawo abin tsoro ana ta surutu a unguwa ya kashe matarsa kuma ya shigo cikin al'umma zai lalata jama'a..."" Kafin ya ƙarasa faɗa Moh ya saka ƙafa ya daki ƙaramar ƙofar nan take ta ɓalle ya faɗa cikin gidan, da sauri mai gadi ya ja baya ba wani sanin Moh ya yi ba kawai zancen ya dawo kunnensa da labarin kisan daya game ko'ina a shekaru uku da suka shige. Goje ya daƙo mai gadin ya falle shi ya faɗi" """Kai har ana cewa ka buɗe ƙofa kana ƙi?""" """Goje""" """Sai godiya"" Moh ya numfasa yana durƙosawa daidai fuskar mai gadin ""Me ya ce a yi masa?"" ""Sai godiya" "ɗari-ɗari ya ce yana buƙatar tsini"" ihu mai gadin ya saka ya ce ""Wallahi tallahi ƙarya nake""" """Zaɓi ɗaya"" cewar Moh yana fito da askira ya ajjiye gefe ya sake fito da wata wuƙar ya ajjiye ya jima a" "duƙe kamar mai tunani sai ya ce ""Ko ɓalli-ɓalli ko ƴan uku ko na jaki""" """Ɓalli-ɓalli"" mai gadin ya ce da sauri ya ɗauka wani abun za a ɓalle da idanu ya kalli Goje da Darma suka" "riƙe mai gadin tare da juya shi yana ihu da komai Moh ya ɗauki ankarar ya dinga tsaga masa a baya jini na fitowa shi kansa zuciyarsa ce kawai ke ingiza shi ya yi hakan kuma daidai gani yake yanzu daidai yake da tsarar kowanne mutum haka ƙwaƙwalwarsa ke karantar da zuciyarsa. Tun mai gadin na kuka har ya yi laƙwas sai nishi yake fitarwa, suka yar da shi a wajan cike da tafiyar taƙama yana taku ɗaiɗai jikinsa na buɗewa cikakken namiji a tsaye matashi dake kan lokacinsa. Cikin sa'a ya samu ƙofar shiga babban parlon gidan a buɗe ya kutsa kai yana kallon tangamemen parlon ya dinga kallon komai, iya haɗuwa ya haɗu sai ƙarar a.c ya lumshe idanunsa ya buɗe ya jima kafin ya ƙara shiga cikin ɗaya parlon su Goje na" biye dashi. Alhaji Wada na zaune shi da iyalansa basu da jima da sauka daga ƙasar ba. Yana saman kujera matarsa "na gefe sai yaransa guda biyu mace da namiji kayan ciye-ciye fal a gabansu bama su damu da cin abincin ba sai ice-cream dake hannunsu suna sha. Da sauri Alhaji Wada ya miƙe tsaye yana kallon matasan da suka shigo ya juya ya kalli matarsa da yaran ya ce ""Su waye ku? Me kuka zo yi mini a gidana a irin" "wannan lokacin?""" Moh bai ce komai ya zaga ya zauna saman kujera ya jingina ya ɗora ƙafarsa a saman table ɗin yana kallon abincin Goje da Darma na tsaye sai muzurai suke yi cikin sauri Alhaji Wada ya ɗauki wayarsa zai "kira ƴan'sanda ""Ba wani abu da zai bani tsoro, yadda aka fara dakai dole a ƙare da kai Alhaji Wada""" """Waye kai? Me aka fara dani"" fuskar Moh a rufe ya saka hannu ya zame abin da ya rufe fuskar da shi" """Idan maye ya ci ya manta ai uwa ba zata manta ba, idan kare na yawo zabo na yawo za a haɗe ya ranar""" "ƙirjin Alhaji Wada ya buga ya yi baya da sauri ya ce ""Kai ne? Me na yi maka""" """Ba labari na zo baka ba, ba fansa na zo ɗauka ba na zo ka ganni kasan ina raye ina numfashi ka san cewa" "na cika ɗan babata Ammo Mai dawa nake sarki mai jeji, na gode Ɗan Amina da ka zama kai ne silar da ya saka na gano wasu abubuwan"" Alhaji Wada jikinsa rawa kawai yake ya ce ""Don Allah kar ka yi mini komai kar ka taɓa yarana basu san abin da ya faru ba"" ""Idan zan yi mana jira, idan na yi sai ta ɓaci. Ina je store ɗin gidan nan?"" Da hannu Alhaji Wada ya nuna masa hanya ita kam matar ta kasa motsi saboda tashin hankali bata taɓa ganin fuska mai ban tsoro irin wannan ba, yaran sai takurewa waje guda suke yi ko haɗa idanu da Moh basa son yi"" ganin har lokacin Moh bai tashi ba ya saka Alhaji Wada cewa ""kar ka ce zaka mini komai"" shi dai Moh kallon Alhaji Wada kawai yake zuciyarsa na tuna masa irin zaluncin da ya yi masa da hannu ya nuna masa yaran cikin kakkausar murya ya ce ""Ko dan waɗan nan, ba zan so su zama abin da na zama ba"" ya juya ya kalli Goje ya yi masa fito da inkiya suka nufi store ɗin kayan abinci kamar hauka haka suka dinga fito da buhun shinkafa katon na taliya da maroni su magi da galan na mai suka" jide waje guda. "Yana bada faɗi ya miƙe tsaye ya nuna kayan abincin ""Ka raba a masallaci ka haɗawa mutane da haushin" "kare guda goma-goma, ka kai har gidanmu"" Ya juya zai fita sai ya tsaya ya saka hannu a aljihu ya zaro kunama ƙatuwa baƙa ƙirin da ita ta ɗaga ƙari sama ya damƙi hannun Alhaji Wada ba tare da yaran sun gani ba, ya cilla kunamar ciki ya damƙe hannun. Azaɓa ta saka Alhaji Wada zubar da hawaye zufa na yanko masa sosai da sosai a hankali cikin ƙasa da murya ya ce ""Ka kira cinnaku ƴan'sanda kenan ka faɗa musu an yi maka fashi, idan sun tambayi waye karka yadda ka ce Mai dawa, ka ce SCORPIO"" yana kaiwa" "nan ya kashe kunamar ya soke jikin bango da sauri ya fice kamar walƙiya, su Goje suka mara masa baya." "Fiyya na durƙushe a gabansa kanta a ƙasa ji take dama tana da ƙarfin yin kuka a yanzu, ta kasa fahimtar" sai yaushe ne komai zai daidaita ya tafi daidai? Tana haɗiye abubuwa da dama ba tare da kowa ya sani ba bata bari a san rauninta amma yau ita aka saka gaba akan abin da sam bai kai ya kawo ba? Ita zaiwa haka?. """Safiyyerh A. Marafa""" Ya kira sunanta a karo na uku sai a lokacin ta ɗago kai ta kalli Daddy dake zaune saman kujera hannunsa riƙe da carɓi fuska ba wasa ya lura sai ya dage sosai akan Safiyyerh. """Ya kuka yi da Ashraf me neman auren ki?"" A hankali ta ce ""Ba komai Daddy""" """Ba komai Daddy, na gaji da jin wannan daga bakin ki Safiyyerh ke kina nuna mini ke mai wayo ce kuma" "kin girma kin isa ki yi handling dukkan wasu matsalolinki ko? Ke jaruma mai experience akan aikinta Managern FS WORLD INVESTMENT COMPANY? na yarda kina da wayo tunda na kasa sanin damuwarki tsayin shekaru na yarda kina da experience hakan ya sa cikin ƙaramin lokaci kika zama Manager but amma.."" ya yi shiru yana kallon ta sai kuma ya ce" """Safiyyerh kina buƙatar aure shine cika da ƙimar kowacce mace, me kike buƙata a rayuwa da ba a yi miki" "ba, wanne gata ban yi miki ba da kika ce kin fasa auren Ashraf?""" """Daddy ya ce na zaɓi aiki ko aure""" """Sai kika zaɓi me?""" """Aiki"" Daddy ya dinga kallon ƴar tasa shi ya rasa gane wani mataki zai ɗauka a kanta." """Ba za ki yi auren ba kenan, baƙin cikin jikoki kike mimi Maama? Sai na faɗi na mutu za ki yi auren me ya" "sa kika kasance stubborn ne, ko don kinga ina biye miki?"" Fashewa ta yi da kuka sosai ita kanta bata san" "kukan ya ƙwace ba, kalmar mutuwar da Daddy ya faɗa ya firgitar da ita sosai idan Daddy ya mutu ta shiga uku." """Daddy gasu Yaya J, su Marafa, su Captain Daddy me ya sa sai ni za a yi aure ne? Ni ce ƙarama fa nawa" nake gabaɗaya ko aure za ka mini ka ƙara mini lokaci Ashraf zafin zuciya ne dashi baya fahimta ta a "kodayaushe""" """Maama kuma taurin kai, ji da kai while zafin zuciya, Safiyyerh dole za ki yi aure"" runtse idanunta sosai" kenan duk abin da take ya tashi a banza? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un me ya sa Ashraf zai yi mata haka me ya sa zai haɗata da mahaifinta? Ta kasa cigaba da kukan abu ya tsaya mata a wuya sosai. Har Daddy ya je bakin ƙofar shiga sashinsa ya tsaya ba tare daya juya ba ya ce """Cikin satin nan zan ɗaura miki aure da Ashraf in sha Allah""" "Dum! Haka ta ji zuciyarta ta buga da ƙarfi har tsakiyar kanta kuma ta ji hakan, ta runtse idanunta sosai" "take ƙoƙarin jan numfashi ta kasa ta yi saurin riƙe wuyanta da take jin kamar an soka mata abu a ciki saboda zafin da yake. Cikin sauri J ya ƙarasu parlon daman ya shigo da nufin yiwa Daddy sai da safe ya nufeta yana riƙo hannunta ya ce ""Manager lafiya? Mene?"" Kafin ta bashi amsa Marafa shima ya shigo ya nufe ta, haka Dr Hash gabaɗaya suka zagaye ta suna tambayarta lafiya kasancewar suna mugun son ƙanwar tasu kamar rai. Hannun J ta riƙe gam tana nishi hawaye na zubu mata sosai ta kasa magana hakan ya saka Dr Hash miƙewa ya ɗakko ruwa mai sanyi ya yiwa J alamar ya ɗago ta, a hankali ya dinga" bata ruwan tana sha ya zame rubar ruwan. """Junaid kwantar da ita saman kujera ko ka kai ta ɗaki""" """Bari ta ƙara jin dama dama a dai ƙaro gudun acn ta fi shaƙar iska da kyau"" cikin sauri Marafa ya nufi" wajan ƙaro a.c a hankali suka ji an ce """Kar ka ƙaro"" ya juya ya kalli Captain dake zaune kan kujera abin shi yana dannawa, yana zaune Daddy" "ya kira Fiyya duk maganganun da sukai yana zaune har halin data shiga. ""Captain daman kana ciki kana kallo Maama ba lafiya?""" """Ni na ɗora mata?""" """Amma baka ce mata sannu ba, she's our little sis our favourite"" kallon da Captain ya yi wa Marafa ya" "saka dole ya yi shiru dukkan su ba wanda ya iya cewa Captain komai domin sun san hali basa shiri da Fiyya bai shiga sabgarta ba, duk abin da ya shafe ta babu ruwansa da shi. Ko magana bai fiya yi ba ana" ganinsa kowa ke nutsuwa domin shine babba a cikin su Fiyya kuma Auta. Fiyya ta yi lamo jikin J tana sauke numfashi Dr Hash na riƙe da hannunta jin jikinta ya fara ɗaukan zafi sosai. Da ƙyar ta lallaɓa J na riƙe da ita suka haura sama duka sauran mazan suka bi bayansu banda Captain da yake harkar gabansa. Wajejen 2:30 Daddy ya sauke numfashi yana kallon yadda take sauke numfashi a hankali ko a baccin "bata da walwala ya juya ya kalli Captain dake tsaye hannunsa zube cikin aljihu ""Aliyu me na ragi Maama da shi a duniya dana kasa fahimtar meke damunta? Ita ɗaya ce mace ƴata laifi ne don na so ta yi aure?""" Captain dai ya yi shiru idanunsa a saman fuskar Fiyya Daddy ya miƙa hannu ya taɓa goshinta ya ji har "lokacin da zafi daman ya fi ƙarfin awa guda zaune a wajan, yana cikin Captain ya buɗe ƙofa ya shigo da" "tunanin babu kowa cikin ganin Daddy ya saka dole ya tsaya. ""Maama ki yi mini alfama ki yi auren nan, shi" "ne abin da za ki yi ki faranta rai na"" ya gyara mata hannunta daya lanƙwashe kana ya miƙe tsaye zai fita" """Aliyu mu je""" """After you daddy""" Daddy ya jinjina kai ya fita yana janyo ƙofar. A hankali Captain ya nemi waje ya zauna a gefen gadon ya "zuba mata idanu sosai, a nutse a kamo hannunta ya riƙe cikin nasa jin jikinta zafi sosai ya saka ya saki hannun ya ɗakko towel da ruwa ya dinga goga mata a goshi har lokacin yana riƙe da hannunta har sai da zafin ya ragu, bai tashi ba yana zaune aka fara kiran sallar farko cikin sauri saki hannunta ya miƙe tsaye yana haɗe fuska J ne ya shigo a hankali ya bi Captain da idanu har ya fice daga cikin bedroom ɗin na" Fiyya. ***** Cikin gidan ya faɗo babu ko sallama Inna Binta na zaune har za ta yi magana ganinsa tsaye ya saka ta yi shiru da bakinta. Yau ranta fari tas an yi musu rabon abinci Malam ya basu ya ɓoye sauran. Ɗakin Ammo ya nufa yana ɗaga labulan ɗakin ya ganta zaune tana ɗaura kuɓewa tun kan ya shigo jikinta ya bata yana hanya saboda gabanta daya tsananta faɗuwa. "Ya shiga ɗakin ya zauna ita dai bata kalle shi ba, sai kallon ta ya ke yi can ƙasa da murya kamar ba shi ba" "ya ce ""Ina yini Ammo?""" "Miƙewa ta yi maimakon ta amsa masa, ya cije bakinsa yana rufe idanu kwanon abinci ya jenyo ya buɗe" yaga taliya ce jallof ta ji albasa nan da nan yawunsa ya tsinke ya tuna rabon shi da abinci har ya manta. """Alhaji Wada ya bawa Malam, idan da zuciya ai ba za ka ci abincin daya bamu ba"" cak ya tsaya yana" "kallon abincin kamar zai tashi sai kuma ya nutsa hannunsa ciki ya ɗebo lauma zai kai bakinsa cikin sauri aka ce ""Allah Ya isa ban baka ba ida ka ci abincin nan"" Malam ya kalli Ammo ya ce" """Bana ce kar ki yarda ya shigo gidan nan ba? Wato har abinci kika bashi ko?"" Ta girgiza kai ta ce ""Ɗauka" "ya yi""" Jiki a sanyaye Moh ya miƙe ya fice daga cikin ɗakin yana saka ƙafa ya banko ƙofar da ƙarfin gaske yana "zuwa daidai inda Inna Binta ke gyara shinkafa ya saka ƙafa ya yi fatali da farantin shinkafar ta tarwatse ya yi waje kamar zai tashi sama. Ta dafe ƙirji tana rafka salati ""Ƴar gwamnati ce fa Allah ya isa wallahi""." "Goje ya dubu Mangal ya ce ""Me ka bashi wai? Yake wannan sambatu da mimmiƙar haka?""" """Sha fara kaga aljan ce, ita za ta yi aiki a jikinsa, daga sama aka bani ita"" Goje ya juya ya kalli Mai dawa" "ya sauke numfashi cikin damuwa ya ce ""Dole sai ka koya masa shan waɗannan abubuwan ne?""" """A'a ina zaune ya zo mini kamar an koro shi yana huci ya ce na bashi irin abin da na bashi kwanaki" "saboda damuwar zuciyarsa ta kau ya manta da komai ni kuma na bashi sha fara kaga aljan""" """To gashi nan yana ganin aljanin ai"" da ƙyar ya samu ya yi bacci a wajan. Bayan ya farka Mangal ya bashi" "abinci ya girgiza kai ""Mai dawa idan kuɗi kake so ina da hanyar da zan yi maka ka dinga samun kuɗi sosai cikin sauƙi har ma ka taimaki wasu"" tunda ya farka sai lokacin ya ɗaga kai ya kalli Mangal alamar ina ne? ""Bangar siyasa kasan yanzu muna gab da fara shiga sabgogin siyasa uban gidana cikakken ɗan siyasa ne," "shima yana da uban gida kuɗi zaka samu sosai a sabgar nan ina faɗa maka""" """Kai ni"" kawai ya iya cewa yana miƙewa tsaye." Suna zaune a wani haɗaɗɗan parlo inda suke karɓe wa su yi meeting na sirri. Gabaɗaya suka kalli MUTALLAB TAHHB SCORPIO ɗaya daga cikin su ne ya ce. """Mene sunanka""" """Mai dawa""" """Kai mafarauci ne?"" Ba tare daya kalli mutumin ba ya ce ""Darr"" babban mutumin ya jinjina kai sosai ya" "zaro wani photo a aljihu ya ce ""Kafin mu yi maka bayanin su waye mu, me muke buƙata da kai, fara ganin wannan ka saka dai a ranka mu ƴan siyasa ne""" "Shi dai Mai dawa bai ce komai ba, aka ajjiye masa photon a gabansa ""Ɗauki ka buɗe ka gani mana""" "Wani daga cikin mutanen ya ce ""Manager ce a FS WORLD INVESTMENT COMPANY aiki za ka yi mana a" "kanta kafin mu faɗa maka aikin mene ka fara ɗaukan photon kaga wacece"" a sanyaye ya ɗauki photon kafin ya kai idanunsa kai...." 08164069385 For more information WhatsApp only "[1/7, 9:32 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 5 """Safiyyerh Abdu Marafa Manager ce a Kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY kuma ƴa a wajan" "tsohon leccara, muna buƙatar ka yi mana kidnaping ɗin ta"" Moh Kallo ɗaya ya yi wa photon da suka bashi ya ɗauke kai" """Ka santa?"" Shi dai bai ce komai ba." "Eng Ali wali ya dinga kallon Moh yana tunanin abubuwa da yawa a ransa kafin ya ce ""baka gama ganin" "photon bane, ko da yake yana da kyau da ƙare mata kallo maybe ka zama silar mutuwar ta ko ka kashe" "ta da hannunka, ka ya zama dole ka gane kamamminta""" "Goje ne ya ɗago kai da sauri yana kallon Eng Ali wali kafin ""Sai da kai mai gida wannan aikin ai ko ni zan" "iya yin shi ba sai Mai dawa ba, ka huta ka sarara mai gida""" Eng Ali wali ya yi murmushi yana jingina da kujera ya ɗauki ƙafarsa ya ɗora akan ɗaya ya kalli Mai dawa "wanda ko motsi bai yi ba sai jujjuya photon da aka bashi yake. ""Ko Mangal ba zai iya aikin nan ba da ya fika wayo a sabgar balle kai da na sani yanzu, shi wannan Mai dawan idanunsa na kalla na san zuciyarsa za ta iya aikata komai""" "Ya yi shiru sai kuma ya ce ""Ni ɗan siyasa ne babu mamaki ka taɓa ganin poster na ko bana, shekaruna" "takwas ina riƙe muƙamin Ɗan majalisa na tarayya a jam'iyyar da nake ta kara, bani da ra'ayin haƙura da kujerata kamar yadda ake yi mini kirarin idan na yi na gama na karya kujerar. Siyasa jinina ce Mai dawa, bana jin akwai wani dalili da zai zo ya saka na haƙura da kujerar na amma wannan karon na yi karo da muruci wanda yake shirin yi mini wahalar dafawa ko ta halin yaya ne dole na sake hawa kujerar nan a karo na huɗu. Hon Maɗatai yana tare da manya wanda suka san kan siyasa ciki da bai dole mu fito da salo na musamman wanda zai kai su ƙasa. Hon Maɗatai shine ɗan takarar jam'iyyar hamayya kuma yana da ƙarfi har yanzu ba'a san mene rauni ko aibun shi ba amma akwai jita-jitar data zo kunne na domin" "tabbatar da gaskiyar al'amari ya saka na kawowa cikin jama'ata""" Sai a lokacin Mai dawa ya ɗago kansa ya ɗan kalli Eng Ali wali kamar ba zai ce komai ba sai ya cije baki yana karkatar da kai gefe ya haɗa hannayensa biyu suka bada sauti mai ƙara cikin wata murya ta izza ya ce """Mene haɗin ta da maganar yawar ku?""" "Eng Ali wali ya ce ""Wa kake magana""" """Ita ɗawar mai ɗan kwalin?""" "Cikin rashin fahimta Eng Ali wali ya ce ""Meye ɗawa da ɗan kwali kuma?"" Mangal ya yi murmushi yana" """Ka fice Mai gida, ɗawa da mai ɗan kwali mace kenan ake kwafa maka zancen"" Ya ce ""Yaran naku sai ku""" Miƙewa Mai dawa ya yi tsaye yana ɗora ƙafarsa a saman farar kujerar dake parlon kallonsa kawai Eng Ali "wali ya yi bai ce komai ba. Sai wani ya ce ""Mai dawa farar kujera ce fa?"" ""Ko takaddar jikinka zan ɗora ƙafa akai"" wanda ya yi maganar ya yi saurin kallon farar shaddar dake jikinsa fara tas da ita sai ya ja bakinsa ya yi shiru. Moh ya kalli gefe yana furzar da iska daga bakinsa ya ce" """Me ya sa ka neman, bayan kana da gajojinka?""" """Saboda kai ne baƙuwar fuska a cikin wannan sabgar tamu, ba wanda zai gano cewa a tsagina kake za ka" "yi aiki mai kyau hankalina ya kwanta da kai Mutallab"" wani irin kallo Mutallab ya jefa masa idanunsa sun sauya kala ya yi murmushi ya ce" """Oh Mai dawa da jeji, ya batun yarinyar ka santa ne ko ka taɓa ganin fuskarta?""" """Na santa ko ban santa ba ina jin bashi kake buƙata ba. Yaushe kake so a kawo maka ita?"" Girgiza kai Eng" "Ali wali ya yi ya ɗauki ruwa ya kurɓa ya ajjiye kana ya miƙe tsaye yana zagaye parlon hannunsa a baya ""Ka jira umarni na, kawai ka zama cikin shiri a koyaushe zaka iya jin kira. Akwai gidan dana samu a bayan gari zan baka makullin ko ka ɗakko ta can zaka ajjiyeta kai ne zaka dinga kula da ita har yanzu lokacin da muka shirya abin da mukai niya, a cikin gidan akwai kayan aiki irin naku wanda za su sama muku" "nutsuwa""" "Goje ya jinjina kai cike da jin daɗi kafin ya ce ""Mai gida za a siya mana mota mai iska kamar yadda muke" "ƴaƴan iska?""" """Za a yi muku komai, ku riƙe amana. Sai dai kawai sharaɗi ko da wasa kar ku nuna kun sanni idan ina" "buƙatar ganin ku a wannan gidan zamu dinga haɗuwa, ku buɗewa kowa idanu kar ku ji tsoro da shakkar komai ni zan tsaya muku har zuwa ci zaɓe"" Moh ya ce ""Bayan cin zaɓan fa?""" """Kamarya?""" "Ya buɗe manyan idanunsa sosai a kan Eng Ali wali a karo na farko ya ƙare masa kallo ""Mene farashin" "aikina?"" ""Nawa kake so?"" Ya yi shiru yana tunani can ya ce ""Zan sanar""" "Eng Ali wali ya ɗakko ƙatuwar bana da fastoci ya bawa Goje da yawa ya ce ""Kuje ku fara da aikin liƙawa" "wannan a unguwanni da saƙo da lungu ya zamana babu wanda ake ganin sai Eng Ali wali, bayan wannan akwai wani dattijo da yake zuwa gidan rediyo yana yi sojan baka kuma duk ni yake kushewa yana son jiƙa mini aiki a tabbatar an saka shi yin shiru da baki da kowacce hanya"" kuɗi ya ciro daga cikin Aljihu ya miƙawa Goje ya ce ""Aje a yi caji a huta"" har Moh zai juya sai kuma ya tsaya ya cake waje guda kamar" "saƙago ya ce ""Me ya sa kuke son a kamata?""" """Aiki ne kawai naka wani abu ba sai ka sani ba, mune shuwagabanni ku dai a baku kuɗi da kayan" "sararawa shine"" kai tsaye Moh ya ce ""To nemi wani"" Eng Ali wali ya ce ""Me ya sa? Bayan kai ka cancanta?""" """Ba zan ba""" """Shikenan na gane, Safiyya Abdu Marafa na faɗa maka ƴa ce wajan tsohon leccara, yana kawo mini" "barazana a sabgar siyasa tare da nuna rashin cancanta a fili. Matasa na jin maganarsa abin da ya zaɓa kuma da shi suke yin aiki a yau ɗin da muke ciki matasa sune siyasa ina so a sa shi yin mubaya'a dole. Kasan da yawan lokaci Malamai suna kawo mana cikas"" Mai dawa ya jinjina kansa alamar ya ji sai dai bai" "yi magana ba a hankali ya duƙa yana buɗe hannu ya ce ""Sai godiya""" """Sai godiya"" Mangal da Goje suka faɗa suna zagaye shi. Cikin sauri kuma ya fice daga cikin parlon suna" mara mishi baya. "Eng Ali wali ya dubi wanda ke zaune sai kuma ya yi dariya sosai ya ce ""Amfanin su kenan fa babu wani" "aiki da ɗan daba zai iya yi maka banda bangar siyasa kashe kashe da sare-sare mu kuma sai mu jefe su da abin da sukewa""" Fiyya na tsaye gaban madubu tana gyara rolling mayafin kanta yau ma suit ce a jikinta ta mata riga da "wando blue black ta amshe ta sosai ta kalli kanta a madubin she missed the old Safiyyerh komai nata sabo take jin shi, ta ji kamar ta rasa wani abu mai amfani a tattare da ita amma mene? Shi ne abin da sam ta gaza fahimta ko a cikin bacci. Ta sauke numfashi tare da ɗaukan wayarta da jakarta tana ƙoƙarin buɗe ƙofa ta fita Ummi na shigowa cikin ɗakin Fiyya ta yi baya tana bata hanya kafin ta ce ""Good morning Ummi"" daga sama har ƙasa Ummi ta kalle ta sai kuma ta je can bakin gado ta zauna tana sake" "kallon Fiyya ""Ina za ki?"" ""Ummi Company""" """Junaid told me ba ki da lafiya, na yi bacci da wuri"" a hankali ta ce ""Lafiya lou nake Ummi ga alama kin" "gani zani aiki""" """Fiyya bana son irin wannan shigar taki, kuma ki haƙura da aikin nan yau za a kawo kayan auren ki"" da" "sauri ta ce ""Aure kuma Ummi? Ba sai nan da watanni ba?""" """To Daddynku ya ce cikin satin nan""" """Shikenan zan je aiki""" """A'a ki haƙura yau"" marairai ce fuska ta yi sosai kamar za ta yi kuka ta ce ""Ummi akwai buƙatar na je, ina" "da meeting da ma'aikata ba zan jima ba"" Ummi bata san damuwar Fiyya dole a hankali ta ce ""Allah Ya tsare ki dinga kula ke dai macace ba namiji ba, kina lura da abubuwa da kike yi"" Fiyya ta yi dariya tana yin waje ta ce ""Kuma ki saka tsoron Allah a ran ki Fiyya ban da wulaƙanta jama'a, al'umma ta Annabi ce""" "Ummi ta girgiza kai kawai ta ce ""Wato kin haddace kenan""" """Dole na Ummi""" "Cak ta tsaya tana riƙe kan ta Ummi ta ce ""Subuhanallahi Fiyya kina lafiya? Ba za ki haƙura da zuwa aikin" "nan ba?"" Ta ɗan ya tsuna fuska da nuna alamar ba komai ta ce ""Kawai na ji kaina kamar an saka mini shocking"" gaban Ummi ya faɗi sosai sai bata nuna ba ta kama hannun Fiyya suka sakko ƙasa." "Dr Hash ne ya fito shima sanye da farar riga ta likitoci Fiyya na kallonta ta ce ""Likita bokan ture, kuma" "fiɗe ku ɗinke""" """Kamar wasu mahauta"" ta yi murmushinta mai kyau tana lumshe idanu ""Barka da safiya Dr"" ya yi mata" "murmushi ""The whole Manager in the world"" Ta buɗe ido shima ya buɗe kafin su ce komai J ya fito shima yana cewa ""In the world mana, wannan kamfanin nan ku ina ne basu da reshe ni dai watarana zan zauna ki bani labarin kamfanin sosai na ji ai na yin wanda yake da shi"" ""Kai Yaya J nima ban san ko na" "waye"" ya buɗe ido ya ce ""Ban gane ba?""" """Da gaske nake Yaya ban san asalin me shi ba, kawai dai na san ni Manager ce""" """Ji nake Ashraf's father is the owner of the company""" "Ta tura baki gama tana harar shi ""Kuma ka sani kake tambayata"" ya ɗaga mata gira ya ce ""Zan zo ki nema" "mini alfarma wajan surukin naki nima ya bani ko messenger ne"" bata kula shi ba. Ɗago kai ta yi suka" "haɗa idanu da shi yana zaune ya watsa mata harara yana ɗauke kan shi gefe ""Aliyu ba yau zaka tafi bane"" ya yi shiru a hankali kuma ba tare daya ɗago kai ba ya ce ""A'a""" """Ok na ɗauka yau ne, ni wallahi duk firgitar dani kake mutum ba walwala kamar a filin yaƙi nan fa gida ne," "amma kodayaushe kamar an yi maka dariya ko yaya ne ka dinga murmushi""" """Ban iya ba Ummi""" """Murmushin ne baka iya ba Aliyu? Ka gwada zaka iya"" ya miƙe tsaye yana yin waje ""Ban san yadda zan" "ba"" ""Ina kwana Captain?"" Fiyya ta faɗa tana haɗe fuska ko inda take bai kalla ba ya yi waje abin shi. Shi dai J murmushi kawai yake yi halin Captain na bashi malam sosai suka jera shi da Fiyya suka fita. Mota ta shiga yana ɗaga mata hannu shima ya shiga tasa motar kowa ya kama hanyar wajan aikin shi. Fiyya na driving a nutse ta hangi wata mota na bin duk inda ta yi sai ta taɓe fuska ko a jikinta a fili ta ce ""Ɗan" "wahala ko waye""" "Daddy dake zaune bayan shigowar Ummi cikin parlon sama ya kalleta ya ce ""Me kike cewa Ummi?"" Ta" "damuwa ta ce ""Kwana biyu ba a amshi maganin Fiyya ba, kuma kamar ciwon zai tashi"" ya ajjiye littafin hannunsu yana saka glasses ya ce ""Wani abin ya faru?"" Ta numfasa yana faɗin ""Irin abin da ya faru kwana ki tana jin kamar ana mata shocking a kanta, ni wallahi bana son ma ta dawo daidai bana fatan ubangiji ya ƙara gwada mini tashin hankali dana gani shekarun baya"" Daddy ya jinjina kai ""Nima addu'ar da nake a raina shi ya sa ma na matsu kawai a yi ai maganar auren nan, wallahi bana son Maama ta" "dawo old Safiyyerh""" """In sha Allah hakan ba zai kasance ba""" Meeting hall ɗin ya yi shiru sai muryarta dake tashi cikin faɗa tana ɗan buɗe hannayenta tare da yin "baya ta ce ""Wanne irin rainin wayo da hankali ne, file ɗin dana ajjiye shi a office ɗina ina jiran a kawo mini proof hujjar abin da aka fitar aka samu shigowar kuɗi zuwa asusun kamfani kamar yadda Accounter ya faɗa mini shine za a ce wai na yi signature a file aljana ce ni da zan taso da gida na zo kamfani na saka hannu, idan zan saka me ya sa ban yi ba tun da file ɗin ya zo table ɗina?"" Ta miƙe tsaye tana kallon su gabaɗaya duka maza ne ita kaɗai ce mace ta koma ta zauna tana juyi a kan kujerar ""I need to find out the truth, meke faruwa a wannan kanfanin. Md da kai da secretary za ku kai ni na duba ko'ina a wannan kamfanin yau ɗin nan, kai kuma Director ka kawo mini record ɗin komai daga watan daya shige zuwa yau ɗin nan, ina buƙatar statement yanzu a office nawa"" ta sauke numfashi fuska a haɗe sosai ""An" "gama"" secretary ne ya kalleta kamar a tsora ce yake ya ce ""Manager akwai baƙi da suke jiran ki""" File ta ɗauka ta miƙe tare da ficewa daga cikin meeting hall ɗin. Bata nufi office ɗin ta ba inda suke "ganawa da baƙi ta nufa ta tura office ɗin a hankali a hankali ta yi sallama ta shiga. Manyan mutane ta gani su biyu zaune a kan kujera kana ganin su ba sai an yi magana ba ta zauna kan kujera mai cin mutum biyu a ladabce ta ce ""Ina kwanan ku? Welcome to FS WORLD INVESTMENT COMPANY i am Safiyya A. Marafa how can i help you?"" Wani rushehen mutum ne daya Hakim ce a kan kujera ya dinga kallon ta kamar zai haɗiye ta idanunta dai na kan system tana ta dannawa da aikin tura saƙo can ta ɗago kai suka" "haɗa idanu ta sake kame fuska ta ce ""How can I you? Ta ya ya zan iya taimaka muku""" """Ba ki gane ni ba""" "Sarai ta gane ko waye ta ce ""Yau na taɓa ganinka""" """To ma sha Allah. Sunana Hon Maɗatai zan saka hannun jari ne a cikin wannan Company""" """Ok, me kake buƙata?""" "Ya gyara zama sosai ya ce ""Za a dinga bani shinkafa, suger, wake a kan farashin yadda Company yake" "siyarwa ni kuma zan ɗora kaso 50 domin cin riba amma daga lokacin Company ba zai sake siyarwa da kowa kaya ba sai ni"" Fiyya ta dinga kallon shi sosai a ranta tana mamakin son zuciyar wasu ya suke so talakawa su yi da ran su ne? Burin shuwagabanni talaka ya faɗi ya mutu saboda yunwa? Ta yi jim sai" kuma ta ce """Da wata ce matsayin Manager ba Safiyya A. Marafa ba do wataƙila ka samu wannan damar a yanzu ina" "maka murna da cewar we're not interesting anymore, da wannan zai fi kyau ka buɗe naka masana'antar ka nemi matasa marasa aikin yi wanda suke lalacewa ka basu abin yi"" ya dinga kallon ta can ya ce ""Kin" "san waye ni? Ƴan'mata ki bi a hankali fa""" """Ai ba a yi wa Fiyya maimaici Hon Maɗatai ba zamu baka hannun jari ba You can leave"" ya miƙe tsaye" "yana jin ba'a taɓa yi masa wulaƙancin da yarinyar ta yi masa ba ""Safiyyerh ko? Ki bi a hankali haɗuwar farko ce wannan, zan tafi amma zan dawo""" Ficewa ya yi rai ɓace zuciyarsa na zafi. Fiyya ta ɗauki kayanta ta nufi office. A hankali take bin bayan Md "da Secretary ɓangaren kayan abinci aka kaita kana da mai daga can baya wajan shara inda ake ajjiye bukar kamfanin ta dinga jiyo wari da sauri ta nufi wajan Md ya ce ""Manager sharar kamfani ce nan"" bata kula shi ta nufi wajan sharar tana rufe hanci da f facemask kamar an ce ta juya idanunta ya sauka akan" yatsun hannu guda huɗu da suke a leda ƙuda na bin su. Tunda ya nufu layin su tiger na biye masa baya hannunsa riƙe da gora yara suke watsewa sai waje ake "bashi hatta almajirin Malam sai da wasu suka bar wajan banda Ɗanyaro dake zaune yana danna sabuwar wayar daya siya sosai Malam yake ji da shi yanzu lokaci zuwa lokaci yake yi malam alheri na kuɗi ga nama da yake kawo masa, sai dai cikin dare Ɗanyaro zai lallaɓa ya gudu ba zai dawo ba sai safiya. Moh na ƙoƙarin shiga gidan Malam ya tare ƙofar ya ce ""Na haifi yaro sunan shi Muɗallabi amma yanzu bani da wannan yaron na bar wa ƴan iska shi da ƴaƴan banza tunda ya zama shaiɗani ba zaka ja mini masifar da zan mutu a gidan ɗan kande ba"" Moh zuciyarsa ta fara tafasa har wani hayaƙi ke fita ta cikin bakinsa ya dinga kallon asawan nasa ya kasa cewa komai ya leƙa surar gidan ko zai ga Ammo amma sai Inna Binta" "dake suɗe tukunya tana faɗin ""Matsalata ɗaya a duniyar nan abinci idan na ci na ƙoshi Mufee ta ci ni fa" "ko a jikina"" Juyawa Moh ya yi kamar zai yafi sai kuma ya nufi saman katanga ya kama ya dire ta cikin" "gidan Inna Binta ta zabura tana faɗin ""ƙulna naru ƙulni bar dan wasalamun Allah Ibrahim, auzubillahi"" jikinta sai rawa yake masifar tsoron Mai dawa take kamar ran ta sauran jama'ar gidan duk suka shige ɗaki banda Mufee da ta yi tsaye tana kallon shi sosai idanunsu yake iri shi bai san wace ita a gidan ba, bai" damu daya sani ba yara ne kamar yaƙi wasu iyayensu basa cikin gidan. Labulan ɗakin Ammo ya ɗaga ya ganta zaune tana ninke kaya ya fi minti goma tsaye kamar zai juya sai "kuma ya shiga cikin ɗakin idanunsa akan kwanon abinci sosai yake jin yunwa idanunsa na rufewa ya miƙa hannu zai ɗauki abincin Malam ya ce ""Kana ci zan maka Allah Ya isa ka tashi ka bar mini gida tsinannen yaro"" da sauri Ammo ta kalli Malam sai kuma ta ɗauke kai." Jikin Moh ya fara rawa jijiyoyin kansa na mimmiƙewa jin uban daya kawo shi duniya na yi masa Allah Ya "isa ya yi ƙasa da kansa idanunsa kamar za su fito waje ya ji babu abin da yake buƙata sai ƙwayar da Mangal ya bashi ya sha, ita kawai zata sauke masa abin da yake ji ya manta da komai, yaushe ne zai zama daidai kamar kowanne mai rai an ci zalin shi an lalata masa rayuwa. Ya miƙe da sauri yana banko" "ƙofar ya yi waje ""Sallamammen yaro Allah dai ya rabani da ƙaddara na huta""" "Kai tsaye Moh dabarsu ya nufa yana zuwa suka mimmiƙe Darma na faɗin ""sai godiya Mai dawa sarki mai" "jeji, wani ya ce ba kai ba yanzu mu fito mu yi farfesun hanjinsa""" Yanayin fuskar Mai dawa a bar tsoro ce ya takure waje guda yana jin kamar zuciyata zata fito waje don "baƙin ciki. ""A sama yake ku bashi sha fara kaga aljan"" cewar Darma Mangal ya girgiza kai ya ce ""Ba za ta" "yi masa ba, kawai a yi masa allurar fenta""" """A'a ta yi masa girma yaushe ya faɗo sabgar kar ka luda masa ya yi mana na jakuna yanzu"" zaro sirinjin" "ya yi Moh ya ƙurawa siririn idanu ganin yadda Mangal ke zuƙo ruwan ciki ya fara girgiza kai da ƙyar ya ce ""Kar ka yi mini Ka bar ni da tunanin bana son mantawa"" kokawa suka fara yi da shi ya ɗauki Darma ya buga da ƙasa Mangal ya faki idanunsa ya caka masa allurar a gadon baya. Jinjiga ya fara sosai cikin ƙaramin lokaci ya yi shiru yana jin shi kamar a samaniya yana yawo yanayin ya yi masa daɗi sosai ya ji zuciyarsa wasai a wannan yanayin bacci ya ɗauke shi. Can cikin dare ya farka kam shi ya yi masa nauyi har yanzu bai dawo daidai ba, babu komai a cikinsa ya miƙe tsaye yana layi kamar zai faɗi Mangal ya ce" """Mai dawa""" "Ya yi masa shiru yana ɗaukar wuƙa ya soke ya ɗauki fitila ya riƙe ""Dare ya yi ba, kana fita waɗancan" "ɗankokin za su iya kama ka gashi babu da goge a hannu ka zauna, kasan kuma ƴan cikin gari sun shigo sun samu labarin mun yage musu poster bama wannan ba ɗazo an ga gawar wani to ana tunanin mu ne kuma yaron ɗan cikin garin ne fansa suka zo ɗauka,na bibiyi abun shi yaron ƙwacan abar magana ya yi" jama'a kuma sun fara ɗaukan doka a hannunsu suka rufe yaron da duka har ya mutu. Su Cokali kuma ba "za su haƙura ba kar muna zaune su ci mu da yaƙi""" """Sai godiya""" "Ya furta da ƙyar daga nan sake yin shiru yana shirin barin wajan kamar zai kifa ""Ina zaka ne? Ka dawo ka" "kwanta""" """Kai fa ba Malam zan haɗaka da Rainbow""" """Shikenan ina zaka yanzu"" ya cije leɓe zuciyarsa na ayyana masa abin da zai yi shi ne daidai allurar sai" "gaibu take faɗa masa a hankali ya ce ""Zan kashe Malam ya baza lahira""" For more information 08164069385 WhatsApp only "[1/7, 9:32 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 6 *Bright pens... 2nd batch* * for the adults and criminal side please just take it as a lessons* "Goje daya farka daga bacci ya yi saurin miƙewa yana furta ""Malam ɗin zaka kashe mahaifin naka?"" Ya yi" "shiru bai yi magana ba, yana sake riƙe wuƙar a hannunsa da kyau duk jikinsa rawa yake, ga wani irin ciwo da kansa yake yi masa sosai, idan ya tuna abubuwan da aka aikata masa sai ya ji zuciyarsa ta bushe ta kuma ƙeƙashewa. Ya saka ƙafa ya banga je Mangal dake tsaye zai shige Goje ya yi saurin shan gabansa yana ɗaure fuska sosai ya ce ""Saboda kana jin kanka a sama ta bakwai kake jin komai za ka iya yi? Me ya sa ba zaka yarda sarki sammai ke yin komai ba, mu fa ba haihuwar ta zubar bane ko yaya ne mun san abin da ya dace kashe mahaifinka ba shi ne mafita ba Mai dawa"" ya ɗaga jajayen idanunsa kamar zai ci babu yadda ƙwaƙwalwarsa take faɗa masa ba daidai haka komai na duniyar yake yi masa babu daɗi" maƙoshinsa na yi masa zafi da raɗaɗi wani abu ya tsaya masa da ƙyar ya iya buɗe bakinsa ya ce """Ya zan yi?""" "Kai tsaye Goje ya ce ""haƙuri, ka bi komai a sannu mai dawa ita gaggawa aikin ƴan annaru ce. Kashe" "Malam a yanzu ba zai rage maka kashi goma a cikin ɗari na damuwar da kake ciki ba, iya wuya iyaye ne su""" """Ba iyaye na bane, ka bari ko ɓalli-ɓalli na yi masa"" ganin da gaske shirin tafiya ya ke yi ya ce ""Idan kaga" "ka bar wajan nan sai dai ni za ka fara kashewa"" Ya ƙuri da idanu yana kallon Goje har wani hayaƙi ke fita ta cikin bakinsa ya wani cije gefen baki yana karkatar da kai gefe. Kamar wasa Goje ya ga Moh ya nufe shi da wuƙar shima yaƙi matsawa yana ganin kamar wasa ne yana ƙoƙarin kawai Goje sara su kaga mutane kamar daga sama sun zagaye su. Moh yaƙi motsawa sai Goje da ya yi baya ya cake yana zazzaro idanu tare da ɗaga gora sama. A kallon farko Mai dawa ya gane cinnaku ne ƴan'sanda sai ya ɗauke kai" shi Goje bai faɗa da labarin ba saboda shigar fararen kaya suka yi. """Eng Ali wali ya aiko mu wajan ku kawo muku kaya"" sai a lokacin Mangal ya ƙarasu yana tale ƙafa ya ce" """Kaya sun sauka da zafin su kenan yallaɓai, amma eh kun razana mu shigowa ba notice sai mu ɗauka dire aka yi mana"" ɗan'sandan ya yi murmushi kawai ya ce ""Kuna da kamar Ali wali za ku ji tsoro? Kune matasan da yake ji daku a yanzu musamman wannan da naga ko kallo bamu ishe shi ba"" Goje ya juya ya kalli Mai dawa da yake kallon wani sashi daban alamar baya ma jin me suke cewa ""Mai dawa sarki me" "jeji wajanka aka aiko mu domin aikin bana yara bane""" """Faɗi""" Moh ya ce yana bada faɗi ba tare daya kalli da ɗan'sandan ba. Abu ya fito da shi a jaka ya miƙawa "Mangal ya amsa ya ce ""Ka a dana kada a je a yi ta sha ana ɓarna, Eng Ali wali ya ce akwai fita ta musamman kuma ƙauyen da za shi basu da kirki dole tafiyar sai daku a ranar zaku cake ku bawa samaniya yazo ta yi hadari"" Mangal ya buɗa ya ce ""Dar hakan ya yi mana, sai Eng Ali wali ko ana su ko ba'a su ya zama dole don uwatar"" Police ɗin ya juya kan Mai dawa a hankali cikin magana mai muƙamin" ya ce """Ka taɓa jin mai suna Scorpio?""" """Wa?"" Goje ya ce da sauri yana kallon Mai dawa da sai a lokacin ya juyo ya kalli Jafar shima Jafar ya kalle" shi da kyau ya ce """Akwai matsala ne babba, Scorpio yana yi wa Eng Ali wali barazana, yana da babbar hujjar da zai iya" "kawo masa matsala a mulkinsa kuma babu shakka ko waye Scorpio akwai alamar ya shirya fito na fito da Eng Ali wali, to muna jami'ai ba zamu bari ba tunda a jikin shugabannin da ƴan dabarun mu muke samun namu rabon. Ali wali yana buƙatar ka taya shi gano waye wannan Scorpio da sunan shi kawai ake ji ba" "kamanni""" """Kamarya kenan?""" Mai dawa ya tambaya a taƙaice yana jin ƙirjinsa na buɗewa saƙo ya fara isa kenan a fili kuma ya sha kunu "sosai. Jafar ya dafa kafaɗar Mai dawa ya ce ""Kamar kai yanzu kowa ya san sunanka Mutallab inkiya Mai dawa saɓanin shi da sunan Scorpio kawai muka sani, babu wanda Eng Ali wali ya yarda da shi sai jami'an Dss ka baza jama'arka su tayaka binciko asalin waye Scorpio akwai kyauta mai yawa idan hakan ya" "tabbata, kuma ya ce ka faɗi kome kake so zai baka""" "Wani irin kallo Moh ya dinga yi wa Jafar na kan kaga biri, biri ya ganka kifi na ganinka mai jar koma sai" "kuma ya ɗaga kai sama yana kallo sama cikin kumburarriyar murya ya ce ""Bayan Dss da shi uban gidan naku waye ka ji yana neman SCORPIO?"" Jafar ya ce ""Me ya sa kake tambaya?""" """To kuje ku yi aikin da kan ku"" ya faɗa yana juyawa cikin sauri Jafar ya riƙo shi ya ce ""ka dinga" "sassautawa zuciyarka da fushi. Bayan Dss akwai jami'ai mafi hatsari da suke neman shi idanu rufe FID Federal investigation department, basu da imani wannan mutanen jami'ai ne da ba zaka taɓa tunanin ta" "ina zasu cimmaka ba, suna iya zuwa a suffar mahaukata ma ko mai neman taimako, su kakkarya mutum" "ko su kashe shi ko haukata shi ba wani abu bane a wajan su""" """Suka kasa kama Scorpio?"" Jafar ya watsa hannu ya ce ""Sannu sannu da zarar sun gane kamanmin su," "babu mamaki su ɓullo ta wata hanyar kafin hakan ta fara ka ruga su kai hari,mun gama magana da kai" "Mai jeji"" ya yi shiru bai ƙara cewa komai ba ""Ka yi shiru?""" """Ka bada sha ɗayanka, zamu jauwalo ka idan akwai sagi"" cewar Goje Jafar ya girgiza kai ""Ka bar shi ya yi" "magana"" Moh ya sake kame fuska babu wasa kuma yaƙi cewa komai sai ma fito daya fara yi yana kallon bindigar dake hannun ɗaya ɗan'sandan. Bisa dole suka juya suka tafi ba tare daya tanka su ba,daman Goje ya san ba maganar zai yi ba. Goje ya juya ya kalli Mangal da yake zuƙar wiwi a hankali ya ce ""Ka" "raina musu hankali waye Mai dawa waye Scorpio""" """Ni ne, MUTALLAB TAHHB SCORPIO""" Mai dawa ya ce yana zare idanu waje manya gwanin tsoro da razani har sai da Goje ya ja da baya don bai taɓa ganin halittar idanu kamar ta Moh ba ƙwayar ta juye kamar bata mutane ba kuma sai ƙara ware manyan idanun yake yi. """Akwai matsala Moh idan suka gano cewa kai ne Scorpio, za su yi maka illa gwara ka ɓace kawai daga" "yankin kafin komai ya sarara"" ""Gawata za su iya gani su haƙura da nema na"" Ya furzar da iska daga cikin" bakinsa kansa ya yi masa nauyi """Goje an yi sake tunda aka bari na je state cid,ba san komai ba amma a fitar dani. Zan iya haƙura da" "komai banda abin da yake damuna a zuciya ni da kai na zan bayyana cewa nine Mutallab Tahhb Scorpio da zarar na cika muradina na abin da na yi niyya""" """Mai dawa""" """Sai godiya""" """Ina tunanin ka haƙura ka bar wa Allah komai duk zamu baza mu je gare shi ya yi mana eh hisabi"" Moh" "ya taune harshe yana kaɗa leɓe tare da saka harshe ya kashe wuƙar dake hannunsa ""Zafin nake ji a" "zuciyata zan yi ɓarna, zan sha jini""" """Kamar wani maye? Shi Ali wali ɗin me ka yi masa ne?""" "Mai dawa ya ja idanunsa ya lumshe ko yaya idan ya yi shiru sautin kuka biyu yaje ji a kunnen shi, tare da" "jiyo ƙarar wutar dake cinye jikin nata hakan ya saka baya iya runtsawa idan ba wani abu ya afa ba haukwata shi ake son yi. ""Na yarda da kai Goje, ka ci amanata askira zan saka maka a maƙoshi"" ""Ni ɗan halak ne. Yanzu ya batun Manager ɗin? Ka santa ne na ji baka bashi amsa ba"" jin ya yi shiru ya saka shi" cewa """Ko dai ka san Managern kamfanin?""" """Karka ka daman""" ***** Fiyya na zaune a saman gadonta tunda ta dawo take kwace tunani ne fal a cikin zuriyarta ga wani irin "tsoro da bata taɓa jin shi ba, a karo na farko ta ji tana son sanin komai da komai na Kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, da duk mutanen da suka saka hannun jari a ciki data rufe idanunta yatsun hannun take ganin da aka yanka aka zuba cikin leda sosai taga rubutu jikin ledar amma ta manta bata duba ba. Ta juya a hankali tana kallon wayarta kamar mai tunanin wani abu kuma sai ta ɗauki wayar tana dannawa numbersa ta kira aka danna line busy. Har zata ajjiye wayar sai ta ji an kira ta zubawa" sunan idanun kafin ta ce. """Ashraf...""" Kiran ta ɗaga ta kara a kunne ta yi shiru ta cikin wayar ya sauke numfashi da ƙyar muryarsa a hankali. """Na ji tsoro Fiyya"" ta ɗan tura bakinta gaba kamar yana kallonta muryarta mai daɗi ta ce ""He said he was" "scared"" ya ƙara fidda numfashi kamar tana gabansa ""Maama kina wahalar dani da kika zaɓi aikin nan na kusa mutuwa, na ji ba zan iya barin ki ba kuma ke ce dai wacce nake so Fiyyar nan tawa""" """Ba na ce ka daina ce mini Maama, why not Fiyya kawai?"" Kamar mai raɗa a hankali Ashraf ya ce ""I am" "sorry bestie me""" Dum! Haka ta ji kan ta ya yi masifar sarawa da sauri ta dafe kan nata tana jin kamar wani abu na janta a "gigice cikin faɗa ta ce ""Karka sake kira na da wannan sunan"" ta cikin wayar ya ce ""Ba zan sake ba amma lafiya kike? Yanzu kike mini magana cikin soyayya Fiyya me ya sa sometimes kike abu kamar bake ba?" "Are You okay?""" """Kai na ke ciwo""" Tana cewa haka ta kashe kiran ta cillar da wayar nata zuwa gefe guda. Da sauri ta miƙe babu ko hula a "kan gashinta yana tashi sama tana dafe da kanta bata ganin ko gabanta duhu ne a cikin idanunta haka ta dinga sauka akan matattakalar benen. Karo ta yi da mutum cikin sauri ta kama hannunsa tana ɗorawa a kanta ""Yaya J kai na zai cire wani abu nake ji, ciwo yake mini kamar ana jana"" gabaɗaya ta rikice ta" ƙanƙame shi har zufa ke tsattsafo mata. Kama hannunta ya yi ya jata saman kujera taƙi sakin shi ya zauna a hankali tare da zaunar da ita ta yi saurin ɗora kanta a cinyarsa ya riƙe mata kan yana murza goshinta nata very careful kar ta ji zafi. Sun jima kana ta shiga sauke ajjiyar zuciya numfashinta na sauka ya ɗan leƙa fuskantarta yaga bacci take ya saka hannu ya juyo da fuskarsa yana zuba mata idanu ya riƙe hannunta har lokacin bai ce komai ba. """Aliyu""" "Da sauri ya saki hannun nata yana zame ta ya miƙe tsaye Ummi ta kalli Fiyya ta kalle shi ta ce ""Ita kuma" "lafiya take bacci a nan? Yaushe ta shigo gidan ai lokacin tashi bai ba?"" Captain dai ya yi shiru ta juya ta kalle shi sosai ta ce" """Lafiya take?""" """Ban sani ba""" """To ya naga kana haɗe rai duka zaka kawo mini me kai komai naka babu walwala Aliyu ka dubi girman" "Allah ka dinga murmushi shifa yin murmushi sunna ne ta ma'aiki"" ya shafa kan shi yana zuba hannu a aljihu cikin gaskiyarsa ya ce ""Ban iya ba wallahi Ummi ki koyan""" """Shi murmushin? Allah ya rufa asiri to wannan matarka ta shiga uku"" yana dai tsaye bai ce komai ba." """Maama?""" """Ummi""" """Maama ta shi yammaci za ki yi ƙunci ko ciwon kai idan kikai bacci"" ta buɗe fararen idanunta suka haɗa" idanu ta sha kunu sosai tana tura baki ya zabga mata uwar harara ta yi baya zata koma baccin. """Kee"" ya kira sunanta ta buɗe idanu ""Tashi kafin na yi balle da wannan silar ƙafafuwan"" miƙewa tsaye ta" yi ta murguɗa masa baki bata ce komai ba shi kuma ya yi kamar zai juya ya damƙo hannunta ta ƙwalla ihu daidai nan Daddy ya shigo parlon cikin sauri ya sake ta. """Da kyau Soja gwara ka nuna ƙarfinka akan ɗiyata, yanzu zaka tattara ka koma inda ka fito""" Captain ya juya ya bar parlon gabaɗaya yarinyar haushi take bashi har zuciyarsa. Daddy ya kalli Fiyya ya "ce ""Maama, yaushe za ki girma ina ganin wawtar wanda ya ɗauki muƙa min Manager ya ba ki wallahi""" """Daddy kune kuke raina ni wallahi, na girma am matured enough"" ya girgiza kai kawai kasancewar t.v. na" "kunne aka fara karato taƙaitattun labarai. Sunan Scorpio aka fara ambata matsayin wanda jami'an tsaro na hukumar FID Federal investigation department suke nema idanu rufe. Dake t.v a hankali ta juya ta kalli mai karanto labaran matashin ɗan jarida dake aiki a gidan t.v na VOA juyawa ta yi ta ce ""Daddy ɗan" "bani aron wayarka""" """Ki yi me da ita?""" """Wayata zan kira, ina son fita ne wajan Kinal"" ya miƙa mata wayar ta ɗan jim tana ɗaga hannunta tare da" "copy na wasu numbersa sai kuma ta miƙa masa bayan ta yi deleting tana murmushi ""La la la na tuna inda" "na sata""" "Ya kalli t.v ya kalleta ya kuma kalli wayarsa, ya dai amsa a ransa yana mai jin tsoro da mamakin kaifin" "tunanin Maama. Ummi kuma ta ce ""Ayi ta neman mutum kamar kiyashi shi kuma ya rasa sunan da zai" "sawa kan shi sai kunama?"" Daddy bai yi magana ba Ummi da abin ke ta cinta ta kalli Fiyya dake shirin" "haurawa sama ta ce ""Maama ta shi me ya yi ne?""" """Ummi ina zan sani, idan kika ɗauke yadda ake juya biyar ta zama goma ba abin da Fiyya ta sani"" tana" "cewa haka ta haura cikin sauri tana nanata numbersa dake kanta cikin sauri ta yi wanka ta shirya cikin abaya ta yi rolling tare da fesa turare sauri-sauri take a haka ta sakko hannunta riƙe da waya ko jaka bata ɗauka ba. Daddy ya dube ta ya kalli lokaci ""Wai zuwa wajan Kinal baya tashi sai yamma? Ita Kinal ɗin nan" "ta dinga zuwa mana zai fi""" """Daddy ba jimawa zan yi ba, na jima ban je ba mun gaisa ba""" """Maama bani da nutsuwa haka kawai idan kika fita gari ya hargitse bani number Kinal ɗin nan na kira ta""" "kafin ta yi magana J ya yi saurin ƙwace wayar Fiyya ya ce ""Bari na kira maka ita Daddy"" babu sunan Kinal a jerin wanda ta yi waya dasu yau cikin sauri ta amsa ta ce ""Number Kinal a kashe yaje fa J wai ni yarinya ce na san yadda zan kare kai na no body can come and hit me"" Ta kalli Daddy da Ummi ta juya ta kalli J" "ta ce ""To tsoran na mene ni Safiyya A Marafa?""" """Allah Ya tsare Maama jeki"" amsawa ta yi da amin ta raɗawa J kunne ""J akwai gulma yau bari na je na" "dawo"" tana fita harabar gidan mota ta shiga ta yi mata key cikin nutsuwa dake driving har ta fita ganin ta" hau kan titi ta dubi bayan motarta ta cikin gilas wata ajjiyar ta sauke mau nauyi ta rufe idanunta ta buɗe sai kuma ta ɗauke hanyar ta nufi wani titin daban a zuciyarta addu'a take yi sosai. ***** Eng Ali wali na zaune a parlo cikin wani gidansa da yake ganawa da ƴan siyasa masu mara masa baya a "kujerar shi. Ya dubi CSP chief Superintendent of Police ya ce ""Ina son ku ɗauke idanunku akan yarana, ko me kuke buƙata zan baku idan ɓarna sukai zan ji da komai"" Csp ya ce ""Hon yaushe za mu cigaba da zuba idanu ƴan dabarka suna yin yadda su kaga dama a garin nan musamman a unguwar Birget gashi lamarin na shirin haddasa faɗa tsakanin ƴan cikin gari da su ƴan Birget, mu jami'ai ne mun san gaskiya muke take" "ta""" """Ku cigaba da takewar su wannan yaran suna da wa'adi dana samu na ci zaɓe ko inuwata babu mai gani" "a cikin su. Don haka ku rufe idanunku a toshe kunnuwa, zuwa gaba har matsayi zan saka a ƙara maka mu yi ƴan dabaru"" CSP ya jinjina kai Eng Ali wali ya ɗakko kuɗi mai yawa ya miƙa masa yana cewa ""Idan kun" kama masu dilar ƙwayoyi da kayan maye na san ana miƙa su hannun NDLEA ko? Ka tabbatar ƙwayoyin "na zuwa wajan Jafar shi kuma zai bawa yarana, kar ka sake sunana ya fito daman ai ƴaƴan asara ne ko an" "kama su ba za su taɓa furta ni suke yi wa aiki ba, lastly magana akan Scorpio ɗin nan yana neman bani ciwon kai bana son ya zama damuwata, idan F.i.d suka riga ku kama shi akwai matsala""" """Karka damu hon mun zuba yaran mu ta ko'ina""" "Eng Ali wali ya ce ""Lallai Scorpio ya zo hannu kafin zaɓe""" Cikin sauri Fiyya ta fito daga cikin motarta tana shiga cikin wajan data zo a reception ta tsaya na wasu "mintina tana zaune ta fito tana murmushi ta ce ""Ikon Allah kamar tare kuke?"" Fiyya ta buɗe idanunta sosai ta ce" """Wa?""" """Captain yayanki""" "Gabanta ya faɗi ta kasa cewa komai Kinal ta zauna ta ce ""Wallahi zuwan shi biyu fa, nima dai na yi" mamaki amma ya ce aiki yake dubawa shi ne ya leƙo mu gaisa har ma na tambaye shi ke sai bai bani "amsa. Amarya ya kike ya sabgogi""" """Good. Yanzu lokacin ku ne Kinal siyasa ta matso ana ta fama da habaice-habaice""" """Kamarya habaici?""" "Fiyya ta cire gilas ɗin idanunta ta ce ""babu abin da mawaƙa suka iya sai habaici wallahi ku zagi wanda" "kuke so kuma ku yabi wanda ku kaga dama"" Kinal ta yi murmushi ta ce ""A'a ni ba ruwana idan an kira ni" "dai waƙa ina yi amma ai ni ta soyayya nake yi tunda a nan na fi kauri, ina nan ina shirya miki ke da" "Ashraf"" Fiyya ta sauke numfashi ta ce" """Ina cikin matsala Kinal ban so faɗawa kowa ba wallahi""" """Subuhanallahi matsala wacce kuma? A kamfanin ko gida ko wani wajan?""" """Kema kin san a gida ba wanda zai mini komai sai mai baƙin halin nan, tunda ya dawo ya uzzura mini ko" "parlo bana fitowa mutum sai baƙar zuciya ɗan wahala kawai aikin kawai"" Kinal dai ta zuba mata idanu kafin ta ce ""Mene damuwar?""" """Kwana biyu da suka shige ana bibiyata kullum idan na fita, harta nan wajan da na zo sai da aka biyo ni," "ni ba damuwata kai na ina tsoron su Daddy su sani kin san abu idan ya same ni tashin hankali suke shiga. Kinal ban san su waye ba me kuma suke buƙata saboda bani da issues akan kowa wallahi na ji kawai ina son sanin wanda ke following nawa duk inda na je gwara mu yi fito na fito da shi, da na ce ko na yi hayar ƴan daba nima suna take mini baya?"" Kinal ta buɗe idanunta sosai ta ce ""Daman na fara zargin kina da taɓin hankali Fiyya, ke yanzu ina kika san inda ƴan daba suke bare ki je? Bakya tsoro ko shakka ai matsalarki police ne wannan ina ganin a gayawa Captain kawai"" tsaki Fiyya ta yi tana miƙewa tsaye ""gwara duk abin da zai same ni ya zaman da dai na faɗawa Captain ni ina da abin yi"" ""Ƴan daban za ki yi" "haya yanzu kenan?""" """E"" sai kuma ta koma ta zauna cikin nutsuwa ta kalli Kinal ta ce ""Akwai abubuwan da bana ganewa" "kwana biyu kamfaninmu ina son na yi bincike duk abin da na samu ba daidai ba wallahi sai na kaiwa hukuma Kinal yatsun hannun mutum na gani a cikin kamfanin fa?"" Kinal ta zare idanu waje ta ce ""A'a ki fara samun mai kamfanin ku yi magana dashi tunda ke ce Manager"" ""Sai yanzu na fara tunani, i wonder aka bani Manager a kamfanina bayan akwai maza da yawa sosai da na yi tunanin ko experience ɗina ne" "yanzu kawai na ji ina zargi""" """Zargin me?""" "Ta ɗaga kafaɗa ta ce ""I don't know, na fara bincike dole zan gano gaskiya"" Kinal ta ce ""To ki bi a hankali" "Please Fiyya we care about you ni ma zani anniversary na makarantarmu FGC dana shigo Kamfanin gobe," "har waƙa na yi mana yanzu haka wani Eng Ali wali na yi wa waƙar da aka saka ni"" shiru Fiyya ta yi tana" "nanata sunan FGC a ranta ""Na ji kamar na san makarantar nan fa""" """Ke da ba ita kika yi ba ina za ki sami, ni a can na yi secondary school kinga""" """Haka ne bari na je""" """To ki kula Please kar ki saka kan ki cikin matsala don Allah Fiyya"" murmushi kawai Fiyya ta yi tana ficewa" daga cikin studio ɗin. ***** Kamar an cillo shi haka yaga Mai dawa ya faɗo masa cikin office ɗin nasa da yake tare da manyan "mutane sosai tun kafin ya yi magana ya ce ""Kowa zai iya tafiya"" duk suka fice ya ɗaga kai ya kalli Mai dawa ya ce" """Ka daina zuwa ina nake ni zan dinga neman ka""" """Ka yi ƙarya""" """Ni nake maka ƙarya Mai dawa?"" Ya wani haɗe fuska tamau fuskarsa ɗauke da sabon yankan da aka yi" "masa jiya har yanzu ba'a gyara ba. ""Kai ai ba Malam Abdullahi bane da ba zan ce kana ƙarya ba""" "Eng Ali wali ya jinjina kai ya ce ""Me ya kawo ka yanzu? Har cikin office nawa""" """Ka saka ni aiki har biyu, da kamo maka ɗawar can da nemo Scorpio"" ya shagiɗar da baki gefe ya yi fito" "wanda ya cika office ɗin sosai ""Na je gidan asawanta jiya""" """Kana nufin gidan Abdu Marafa?"" Ali wali ya ce yana miƙewa tsaye cike da tsoro Mai dawa ya ɗaga ƙafa" "ya ɗora a saman table ɗin gaban Ali wali ""sharaɗin kawo maka ita barewar shi ne mallaka mini kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, aikin Scorpio kuma ka saka cinnakunka cire hannu daga sabgar ka bar mini ni zan nemo maka shi, bana haɗa aiki da wasu""" "Ali wali ya ce ""Mene haɗina da kamfanin nan? Karka saka ni rigimar da tafi ƙarfina da ka san ma'anar" "abin da FS WORLD INVESTMENT COMPANY yake nufi ba zaka haɗa kan da shi ba, wannan Kamfanin ciwon idanu ne"" Mai dawa ya ce ""Ni Mutallab Tahhb ɗan babana Abdullahi da inkiya Mai dawa bana harin abu na haƙura, wannan kamfanin shi ne burina"" Ali wali ya goge zufa ya ce ""baka san kamfanin ba shi ya sa a ba ki yake maka wahalar faɗa ni Ali wali sabgar siyasa na sani na saka gaba, ka bar ni a haka" "ba zaka saka ni a masifa ba""" """Waye mai kamfanin?""" """Sannin hakan daidai yake da tunuwar asirin manyan mutane da dama, ka bar komai yadda ka sani""" "jinjina kai Mai dawa ya yi ya ce ""Zan maka jahilanci ne, ka riƙe amana ka bi sharuɗan da na ce zan maka komai ni ɗan daba ne kai mai neman iko da muƙa mi ni na sare na kashe mu bauta maka shi ne. Batun kamfanin zan yi bincike da kai na, kar ka zama butu don wallahi sai na yi maka daƙiƙanci""" """In sha Allah, daga nan har bayan zan yi maka komai""" """Dar zan doƙa yanzu sai godiya""" "Yana fita Eng Ali wali ya ɗauki waya ya kira Csp ya ce ""Waye Mutallab yaron da ya fito daga wajan state" "cid kwanan nan bayan ya yi shekaru uku a wajan su"" ta cikin wayar Csp ya ce ""Sunan shi dai Mutallab ya kashe matarsa aka aka kama shi, daga baya kotu ta sake shi a zama na ƙarshe ba wanda ya san dalili"" Ali wali ya kashe wayar yana sauke numfashi a fili ya ce ""waye MUTALLAB?""" For more information 08164069385 WhatsApp only. "[1/7, 9:32 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 7 *Bright pens... 2nd batch * The door is open... Ga masu buƙatar ayi musu tallah. Na hango wasu ƙwailaye a conversation group da Mikiya writers Maman Sayed ta ce a faɗa muku akwai maganin gargajiya cikin sati guda komai zai kankama haɗaɗɗan maganin da Fiyyar Ashraf ke amfani da su ta ce a baku numberta ba... 08063114606 "Washegari da safe Fiyya na ƙoƙarin buɗe ƙofa ta fito da nufin zuwa office ya rigata buɗe ƙofar, kallo ɗaya" "ta yi masa ta ɗauke kan ta zuwa gefe a hankali kuma can ta ce ""Ina kwana?"" bai amsa ba sai cewa da ya yi ""You told Abba za ki wajan wata, amma kin yi ƙarya ina kika je?"" Manyan idanunta ta ɗago ta kalle shi ta ce ""Ƙarya kuma?"" Ya rufe ƙofar ya tsaya ""Idan kina yi mini kamar ba ki gane ba, kwaɗa miki mari zan yi maybe it will help you to understand it very well"" ita mamakin shi take yi ""Ni fa Manager ce business zai iya fitar dani ko'ina"" ya buɗe mata manyan idanunsa sosai sai kuma ya ce ""ina kika je"" ta tura baki gaba sosai ta yi gefensa za ta shige ya saka hannu ya fisgota kafin ta yi motsi ya ɗago fuskarta ya wanka mata mari ƙwayar idanunsa tamkar zata fito waje yana ihu a saman kan ta ya ce ""Idan na sake maimaita miki" "tambayar sai na tabbatar yatsun hannuna sun kwanta fuskarki""" """Sai dai ka kashe ni"" ta yi maganar ko gezau gefen fuskarta ya yi jajur dakakkiyar zuciyarta kuma ya saka" "ta nuna ko a jikin ta, ƙasan zuciyarta kuma wani zafi da raɗaɗi take ji ""ni kike cewa na kashe ki?"" Hannu ta saka zata ƙwace nata hannu idanunta cikin nasa ba tsoro ta ce ""Me kake so na yi maka? Ka shigo kana tambayata abin da ban sani ba, ka saka hannu ka mari fuskar da kullum nake shafa mata mayuka masu tsada, ni ka mara ban maka komai ba, tunda ka tsane ni ka kashe ni kawai"" da ƙyar ta iya ƙare maganar saboda muryarta dake rawa Captain ya saka hannu ya sake ɗauke fuskar Fiyya da mari yana huci ya ƙara ɗaga hannu zai mare ta cikin sauri ya tsayar da hannun nasa ganin hancinta na fitar da jini sosai kuma" yaƙi tsayawa. "Ta yi masa ƙuri da idanunta da ruwa ya kwanta a ciki, jinin kuma bai fasa zuba ba daidai nan aka buɗe" ƙofar tare da shigowa ciki da sauri Fiyya ta nufi wajan Daddy ta riƙe shi tana fashewa da kukan dake cin "ran ta jikinta har wani irin rawa yake yi da ɓari jinin dake fita a hancinta kuma ya shiga ɓata masa farar rigar jikinsa. Daddy ya juya ya kalli Captain daya haɗe fuskarsa ""Aliyu me ka yi mata?""" """Ni kuma?"" Ya tambayi daddy irin bai ma san me ya faru ba ""To ita da waye haka ji bi yadda take kuka" "hancinta na jini kuma kai na gani a ɗakin, dole kasan mene ya faru"" cikin damuwa daddy ya yi maganar wacce sai da ta bayyana saman fuskarsa ya ɗago Fiyya yana duban ta sosai ya ƙara kallon Captain" """Maama wannan jinin fa? Daman kina yin haɓo ne wani abun Aliyu ya yi miki?"" Ita dai Fiyya taƙi cewa" "komai sai shassheƙar kuka take yi numfashinta na yin sama, Daddy duk ya rikice baya wasa da al'amarin daya shafi Maama ko kaɗan a ƙasan zuciyarsa yake jin soyayyarta ya kuma tabbatar ita ce rauninsa Fiyya kawai za a taɓa a iya nakasta rayuwarsa. ""Ya isa daina kukan haka nan, Allah Ya nuna mini sati mai kamawa ki tafi gidan mijinki ni ma zan fi samun nutsuwa da hakan zan fi samu nutsuwa idan kikai auren" "nan Safiyyerh""" """I love you daddy"" Fiyya ta ce a hankali tana rungume daddy ya shafa kan ta cike da soyayya ""daddy love" "Safiyyerh"" tuni Captain ya fice daga cikin parlon. Anty Turai da zuwan ta gidan kenan ta ce ""Ikon Allah. Yaya kai ne kake ɗaurewar yarinyar nan gindi wallahi ka lalata da soyayya take yin abin data ga dama, ko" "Aliyu baka tambaya abin da ta yi masa ba ta wannan figaggiyar yarinyar kake""" """Fita daga ɗakin nan Turai"" rai ɓace Anty Turai ta fice tana zabgawa Fiyya harara ranta duk a ɓace." "Daddy ya kalli Fiyya sosai kamar zai yi magana sai kuma ya ce ""jeki wanke fuskarki I'll drop you""" """Daddy daman i missed your drive wallahi"" murmushi ya yi mata a duk santa zai kalli Fiyya sai gabansa" "ya faɗi ya juya a hankali ya dubi picture ɗinta dake gaban madubi sanye da kayan graduation ta yi wani kyakkyawan murmushi ta rungume hannunta tana kallon gefe guda. Ya ƙarasa ya ɗauki photon ya shafa a hankali ""Maama na ni kamar na yi ba daidai ba, bani da wani zaɓi ne i am sorry Safiyyerh Abdu Marafa"" ya lumshe idanu ya buɗe a kan photon ""kina tunanin kin yi girman da za ki iya kula da kan ki, ki" "kuma yankewa kan ki hukunci? Maama ba kin san komai ba a rayuwa you're nothing but a stubborn girl""" Ya ajjiya photon ya ɗauki wayarta babu wani password a kai dudduba abu ya fara a nutse yana yi yana "kallon ƙofar banɗaki can ya sauke ajjiyar zuciya ya ajjiyar wayar daidai nan ta fito. Ya yi waje yana ""Ki" "same ni a ƙasa""" "Suna tafe a hanya daddy na driving a nutse ta ce ""Daddy"" bai kalleta ba yana dai sauraren ta domin" "program ɗin da ake yi da Eng Ali wali a redio shi ne ya ɗauke masa hankali. ""Zan raka Kinal FGC""" "Wani burki ya ja a kusan tsakiyar titin Fiyya ta dafe kai tana ""Subuhanallahi""" """Mene haɗin ki da FGC Maama?""" """Daddy Kinal zan raka suna yin taro na makarantar zan bita idan na tashi aiki"" zufa har fitowa daddy take" "a saman goshi sunan FGC ba ƙaramin gigita masa lissafi ya yi ba. ""ba za ki ba"" shagwaɓe fuska ta yi ""don Allah daddy wallahi na ji ina son zuwa""" """Wallahi mistakenly kika je shegiyar makarantar nan sai ranki ya ɓaci kuma sai kin daina fita hatta aikin" sai kin ajjiye. Wallahi Safiyyerh Abdu Marafa idan kika je za ki san waye Abdu sai na zane miki jiki da "carbi ko bulala"" ta yi ƙasa da kanta zuciyarta duk babu daɗi idanunta na cika da hawaye tun tana ƙarama take yin biyaya a komai akan abin da ya yi crossing da buƙatar daddy." "Hannunta riƙe da jakarta ɗaya hannun wayarta data kara a kunne suna magana da Kinal, duguwa ce" "hakan yasa bata fiya saka takalmi mai tsayi ba suit ce jikinta as always fara tas mai riga da wando ta yi rolling da black ɗin mayafi idanunta sanye cikin wani shade glasses mai kyau a hankali take tafiya tana ɗan jinjinawa mutanen kamfanin kai with so much respect tana da girmama mutane kawai rainin hankali ne bata ɗauka ""Kinal ki je kawai idan na koma gida za mu yi magana, daddy ya hana"" yadda ta yi furucin" ya bayyana ainihin abin da take jin a zuciyarta. """To shikenan nima na zo studio ne zan yi waƙa idan na koma gida zan shirya za mu yi video call na nuna" "miki cikin FGC ɗin"" Fiyya ta ɗan taɓe baki daidai lokacin da take isa bakin ƙofar office nata security ya" "matsa ta buɗe ta shiga ta buɗe idanu ganin Ashraf zaune a office ɗin ""Kinal mu yi magana anjima"" ta cire" wayar tana kallon Ashraf daya miƙe tsaye yana mata murmushi """Kuma da permission ɗin wa ka shigo?""" """Wake neman permission idan ana batun ganin mata, na zo ganin matata ne"" ta ajjiye jakar hannunta" "tana zama saman duguwar kujera ""Sannu mai mata"" ya miƙe ya dawo kan kujerar yana leƙa fuskarta" """Miji ɗaya gare ki a duniya kuma nine"" cikin wasa ta ce ""Ai kowa ba zan aure ka don ka ji""" """Funny Fiyya"" a yanayinta na rashin damuwa da soyayyar ta ce ""How are you?"" Yana kallonta yana ji" "wani abu sosai game da ita ""Fiyya na yi kuskure wallahi bana sanin ina shige limit ɗina sai na yi wani abu. Ni na san ba wani sona kike ba amma idan kika yi haƙuri watarana za ki ji son nan ko yaya ne kullum kina ƙara nesanta kan ki dani yayinta zuciyata ke ƙara kusanto kanta gare ki. Komai da lokacin shi idan mukai aure muka rayuwa inuwa guda I'll definitely be honest to you, ina jin kishin ki a ƙirjina ne a nan nake ji" "kina mini motsi Fiyya"" ya nuna ƙirjinsa saitin zuciyarsa sai ya ɗan juya gwanin tausayi" """Amma bakya so na""" """Who told you that?""" "Ashraf ya buɗe idanunsa ""When are you gonna tell me you love me?"" Tana kallon shi tana murmushi ita" "tana son shi sosai kawai bata san ya zata nuna bane sometimes rigimarsa ke sawa ta bijire itama ta miƙe tsaye tana danna kiran number messenger bayan ya ɗaga ta ce ""Call Md for me, ka kira mini Md da Secretary hadda accouter"" ta ajjiye ta ce ta haɗa shayi a cup guda biyu ta saka cokali tana miƙawa Ashraf" "ɗaya idanunta cikin nasa ta ce ""San da aka kai ni gidanka matsayin mata"" ya lumshe idanu ya buɗe" """I'll wait as far as you're with me. Abin da kawai nake buƙata shine ki so ni. Ki so ni ko da kaɗan cikin" "yadda nake sonki ne""" ***** Anty Hameeda na sunkuye a madaidaicin parlon gidanta tana duba jarkokin lemon ginger ɗin da take "siyarwa ta ji hucin mutum da sauri ta miƙe sai kuma ta yi baya a razane ganinsa tsaye a gabanta yana waige-waige kamar wanda aka biyo ga wani irin yanka a ƙarƙashin wuyansa da alama yanzu akai masa jini ja zuba, ya yi zuru-zuru sai huci yake yi naman jikinsa musamman na ƙirjinsa na motsawa ""Ɗan autan Ammo wannan hucin fa kamar an biyoka wani abun ka yi? Wane ya yanke ka haka me ka yi masa?"" Bai kula ta ba ya juya ta bi bayan shi kitchen taga ya nufa ba jimawa ya fito da kwanon abinci daidai nan" wata mata ta fito tana ganin Mai dawa ta yi saurin sakin butar hannunta ta ce """Wannan tantirin ƙanin naki uban ne ya zo yi mana a gida? Yaushe ma aka sake shi innalillahi wa'inna" ilaihirraji'un mugun ji da mugun gani Ubangiji ya kare Allah wadaran ƴan daba ya tsine musu albarka ya "saka su fita a cikin ajalin su"" matar ta faɗa hawaye ya cika idanun Anty Hameeda ta ce ""Baba ina laifin ki" "ce Allah ya shirya ɗa fa na kowa ne bawa kuma sai me shi, ciki ne mai haife-haife baka san me Ubangiji" "ya ɓoye ba suma fa ƙaddara ce ba wanda ya zaɓi yadda rayuwarsa zata kasance""" """Ai duk wani ɗan daba ƙarshe wulaƙantacciyar mutuwa ce ko idan sun sha ta faɗa musu babu daɗi su" "kashe kan su, ko kuma su haukace garin shaye-shaye ko garin faɗan daban su a kashe su. Allah wadai"" Moh dai bai yi magana ba abinci kawai yake ci hannunsa ko wankewa bai ba duk jini Anty Hameeda ta shige ɗaki bayan ta share hawayen idanunta lemo ta ɗakko masa da ruwa ta ajjiye tana kallon yadda kusan rabin fuskarsa ya yi tabo da yanka yaro ba ya kalle shi ihu zai yi ba annuri a fuskar nan. Duk yawan abincin ya cinye ta sha ruwa ya shanye lemon tas ""Na Ammo yanzu kana jin abin da ka zaɓawa rayuwarka shine daidai ka ji tausayin mu don girman Allah. Wallahi daka kasance cikin wannan rayuwar gwara ka dinga aikata abubuwan da kake a baya, jibi yadda ka yi muni ka zama ƙazami sai warin dauɗa kake yi. Na je gida sun ce sun fi sati uku ko gilmawar ka basa gani wai malam aure zai ƙara kuma da ƙyar idan ba Ammo zai saka ba, na rasa wake bashi kuɗi ya fi son ya yi ta auri saki ana haifa masa yara yana" "kasa kulawa da tarbiyyar su""" Tamkar bada shi take ba haka ya yi ko gezau can ya miƙe tsaye ta ciro kuɗi dubu ɗaya ta bashi ya kalle ta ya kalli kuɗin idanun nasa a rine kamar gauta yaƙi amsar kuɗi ganin inda ya nufa hannunsa riƙe da wuƙa ya saka Anty Hameeda ihu ta ce """Me za ka yi ka rufa mini asiri kar ka kashe mini aure na shiga uku"" ko kallon ta bai yi ba, ya ɗaga labulan" "ɗakin Baba tana sujjada ya same ta. Tsartuwa ya yi ya fito da kunama ya cilla mata a cikin hijabi kafin ta ankare ta ɗago jin abu na bin bayanta kamar kunamar tsafi ta shige mata riga ya zaro askira ya daidaici ɗuwawunta ya lafta mana wani uban yanka, baba ta saki ihu tana ta shiga uku ya yi saurin fita askirar na" zubar da jini da. Yana fita su spider suka rufa masa baya. A cikin wani kango ya kwanta ya yi shiru cikinsa zafi saboda faɗan da sukai da ƴan cikin gari akan fita wajan kamfel da sukai kilashin. Ya rufe idanu zuciyarsa na buɗewa wani irin ɗaci yake ji a cikin maƙoshinsa wani a ya tokare masa kamar yanzu komai ke faruwa haka yaga magic ɗin idanunsa ke hasko masa bidiyon komai ta ciki inda take tsaye. Yana zaune a gida a lokacin yana jin yadda karatun Almajirai ya cika masa kunne ya yi kicin-kicin da fuska. "Ammo ta kalle shi ta ce ""Yau kuma waya taɓa jarumin Ammo?"" Ya yi mata shiru don bai fiya cewa komai ba idan ran shi ya ɓaci kafin ta sake magana wani yaro ya yi sallama ya ce ""Wai bestie ya zo in ji bestie""" """Waye bestie? Injiwa jeka tambayo""" "Mutallab a lokacin bai motsa ba ya hakimce kamar sarki kansa a ƙasa yaron ya dawo ya ce ""Wai in ji" "Safiyyerh matar Mutallab bestie""" "Baki buɗe Ammo ke kallon Mutallab ta ce ""Na Ammo yaushe ka yi aure bani da labari yau naga abin da" "ya fi ƙarfina, yara ƙananu daku wacece Safiyya"" ya miƙe tsaye daga shi sai gajeren wando ta wata riga ƙarama ""ban san ta ba""" """Ikon Allah""" Fita ya yi yana shan kunu ganinta tsaye suna haɗa idanu ta yi ƙasa da kan ta. Ya dinga kallon ta yana jiran "ya ji mene ""meye ne?"" Ya tambaya." "Hawaye ya gani a idanunta fal ""Ni a gidanku zan kwana"" tar ya gama buɗe shanyayyun idanunsa a kanta" """wanne gidan?"" Ta nuna masa gidan ""sai ki ce ke wa?"" Tana masa shagwaɓa wacce daman ya san hali" """Matar Mutallab, baka zo makaranta ba yau ba kyau fashi"" da wani irin ƙarfi ya ce ""Safiyyerh!"" Gani an yi" kanta. *** “Safiyyerh” ya ƙwalla kiran sunanta yana zabura kamar yanzu ne abin ke faruwa jikinsa duk rawa "yake ganinsa shi kaɗai a kangon ya saka ya kifa kansa zuciyarsa na wani irin tsalle tana huci jijiyin kansa sun fito sun yi kwance saman kan shi. Ƙwayar Rohypnol ya ɓalle ya haɗiye har huɗu ya yi shiru jikinsa ya yi weak yana ganin kangon na jujjuya masa lokacin gudu yadda idanunsa suka gane masa cikin jini kwance saman gado ya sake faɗo masa, ya dinga jujjuya kansa ƙwaƙwalwarsa ta tsaya cak kamar wacce ta yi hooking da sauri ya zaro takardar daga cikin aljihu tsoron ƙara kalla yake ya yi saurin damƙe ta cikin hannunsa sai kuma Ammo ta faɗo masa a rai bai damu da jinin dake fita a wuyansa ba ya yi kwance a" ƙasa shi kaɗai kamar maraya. "Yammaci liƙis yana zaune gaban ta, ya kalleta a karo na farko ya ce ""Me ya sa kika buƙaci na ce ina son" "company?"" Abbasa ta ajjiye abin hannunta ta kalli cikin bukkar ta ce ""Sanda ka faɗa mini waye Mutallab," ka bani labarinka zan faɗa maka hujjata tare da dalilin cewa ka cewa Ali wali kana son kamfanin FS "WORLD INVESTMENT COMPANY""" """Bakya tsoro na kashe ki?"" Ta dube shi ta saka hannu tana goge masa wajan ciwon ""ba zaka iya kashe ni" "ba babu abin da zaka iya yi wa Abbasa. Ya batun zama mata mazan? Mene dalilin daya saka kake so ka zama?""" """Bana son haɗa danganta da kowacce kurciyya, ba idan aka yi baru aure kenan ana wani abu ba, to bana" "so ba wacce za ta yi sha'awar zama dani mata uku kenan babu su saboda ni ki mayar dani mata mazan""" """baka watarana zaka iya buƙatar lafiya ko kasancewa da mace""" """Sai godiya kafin lokacin na cika muradaina na baza ƙiyama ki mayar dani"" ta dinga kallon shi ta ce ""Ka" "tabbata ka yi tunani""" """Ki aikata kawai""" """An gama, riƙe wannan"" abu ta bashi ya amsa ya sha ba jimawa bacci ya ɗauke shi. Bai san lokacin daya" shafe ba sai farkawa ya yi ya gan shi an wanke masa ciwon an saka audiga ya yi shiru yana jin he just missed something very important. Message ɗin Eng Ali wali ya gani kan yana son ganinsa da gaggawa ya tura masa address ɗin wajan. Mai "dawa na tsaye yana kallon Eng Ali wali da ya yi badda kama ya zame facemask ɗin fuskarsa yana kallon Mai dawa ya ce ""Mai dawa"" bai magana ba sai fito yake yi." """Abdu Marafa ya shiga gidan rediyo yau da safe ya sake jaddada ra'ayinsa akan ƙin takara ta yana kuma" "janyo hankalin matasa da su farka a daina amfani da su, domin yanzu matasa sunw siyasar wannan mazanin. Gwara youth su haɗa ƙungiya suna fitar da wanda suke ganin ya cancanta ya zana shugaba ba irina ni Eng Ali wali ba. Mutallab a fara shirin ɗakko yarinyar nan yadda zamu saka harshen Abdu Marafa" "ya yi laushi dole zai kawo kasa ya yi mubaya'a a gare ni Eng Ali wali"" Mutallab dai ya yi shiru abin shi." """Mutallab ina magana ka yi shiru?""" """Yau kake so a kawo ta ko gobe? Kai yanzu tukun mene ra'ayin naka akan matasa?""" """Bangane ba""" """Ka gane mana, ka zama ɗan halak cikin gyatuma idan ka ƙi cika mini alƙawari bayan cin zaɓe zan maka" jahilci. Jinin malam Abdullahi ke guna a jikina idan na so dole na janyo maka farinjini amma na daina wannan sabgar yanzu. Na rantse da ɗan Amina ka yi mini ba daidai ba za kaga ba daidai ba ɗan malam "nake ka daina ganina haka"" Ali wali yace" """Ai kai ƙanina ne, amma waye kai? Zan so jin tarihinka ka faɗa mini waye kai Mutallab?"" Nan da nan" "Mutallab ya sake haɗe fuska tamau ya yi shiru. ""Shikenan zan maka komai ka tabbatar ka sato mini" "yarinyar nan babu lokaci ban san me Hon Maɗatai yake shiryawar ba amma shirun da ya yi yana nufin komai. Sai batun nemo Scorpion""" """Zan tafi zan aiko Mangal anjima"" yana faɗin hakan ya fice kamar walƙiya." "Kwana biyu da faruwar abin da Captain ya yi bata ta ɗauke walwala daga gidan kodayaushe tana sama," "tun lokacin bata sake jin motsin shi ba. Abubuwa da yawa ke damunta yadda ciwon kai ke damunta tana jin kamar ana jona mata wani abu, bata iya bacci. Ga matsalar kamfani da kullum manyan kuɗaɗe ke shigowa cikin asoson kamfanin an rasa daga ina? Ta yi duk binciken daya kamata ta kasa gano bakin zare masu gadi sun tabbatar mata da cikin dare manyan motoci na zarya a kamfanin hakan ya saka ta ɗauki niyyar dole yau zata saci hanya ko wajan ƙarfe ɗaya na dare ta fita tana jin hakƙin kula da kamfanin yana kanta ne. Ta ƙara adding number cikin jerin numbersa ɗin abubuwan da take buƙatar sanin abu kai ma'ana hadda hujjar daddy na hanata yin wasu abubuwan. Miƙewa ta yi tare da yin wanka ta tare da alwala ta gabatar da sallar issha ta yi addu'a sosai da azkar wanda ke sanya mata nutsuwa tare da kusantata ga Ubangiji. Fiyya ta dinga kallon kanta cikin madubi sometimes tana jin kamar ba ita ba, she" missed the old Safiyyerh. Buɗe ƙofar akai tare da shigowa """Zaman ɗaki manager ta fara kenan?"" Murmushi kawai ta yi tana juyawa ta saka hijabi" """Yaya J, how are you?"" Ya yi murmushi" """Nothing without manager, ki fito daddy na kira an kawo invitation card"" ta haɗe fuska ya yi baya yana" "ɗaga hannu ya ce ""cut me out Fiyya da kan shi ya saka akai yi komai"" ""wai dole sai an yi mini aure ko me daddy ke tsoro?""" "Shiru J ya yi sukai waje ta samu Dr Hash zaune ta ce ""Dr good day, ina gefen kan mutum na ciwo yana" "ganin reflection na wasu abubuwa what was the problem?""" Dr Hash ya ɗago kai haka J da kuma Marafa Ummi ma kallo Safiyyerh take daddy na zaune yana ji bai "ɗago ba. Ta buɗe musu manyan idanunta Dr Hash ya ce ""Me kike gani?"" Kawai ta haɗe fuska ta ce ""babu"" wajan daddy ta ƙarasa ta durƙusa har ƙasa ta kashe shi ya miƙo mata waya Ummi ta ce ""Ki zaɓi furnitures ɗin da kike so"" ta yi sak tana kallon su dai daddy ya Aman wayar ya ce ""Babu buƙata, zuciyata ta kasa nutsuwa zan yi requesting da an ɗaura auren kawai Ashraf ya bar ƙasar dake"" da sauri ta kalli daddy ""Daddy aikina fa?"" ""Za ki bar aikin"" ta girgiza kai ta ce ""ba zan maka musu ba daddy kai mahaifina ne ina yin biyayya a komai, amma don girman Allah ka bar ni daddy akwai binciken da nake yi a kamfani da zarar na kammala zan je duk ƙasar da kake so idan ma ƙare rayuwata ne a can zan yi"" daddy bai kulata ba ya miƙe ya bar wajan J yana jin babu daɗi Ummi ma ta yi shiru babu yadda za ta yi da daddy idan abu akan Maama ne sai dai a kalle shi ta jawo Fiyya jikinta ta dinga bata haƙuri tana kwantar mata da hankali, Fiyya ta rungume Ummi tana kuka. Kamar kullum J Kalla ne yake sanar da an samu gawar wani babban mutum mai suna Alhaji Haladu da aka shiga aka kashe har gidan shi ana kuma zargin Scorpion ne saboda shaidar daya bari na sunan Scorpion a jikin bango. Ta dinga kallon screen ɗin t.v sai" "kuma ta miƙe ""kin ci abinci?"" Ta girgiza kai ""na ƙoshi an yi mini formatted folder a wayata Yaya J""" """Formatted kuma ko dai kin shiga wani wajan ne"" ta ɗaga masa kafaɗa ranta duk a ɓaci. Kwanciya ta yi" sukai waya da Ashraf yana ta mata maganganun masu daɗi har ta yi bacci. "**** Idanunta ya kalla muryarsa a hankali ya ce ""There's something about you that make me feel like" "you actually use magic about me, many things I do because you, many things I don't even know or remembered when I started doing them. The love I have for you is so real baby. Yet, ban san me ya sa zuciyata take yawan bijiromin da kokwanton yiwuwar samunki a rayuwata ba. I love you Safiyyerh""" “I love you Safiyyerh” A gigice ta farka daga baccin tana ihu da ƙanƙame pillow jikinta na rawa sosai da ɓari da sauri Daddy ya "buɗe ƙofa ya shigo haka Ummi da Yaya J wajan karfe biyu na dare ""Fiyya mene? Maama mene?"" Ta" sakko daga kan gadon a gigice ta nufi wajan daddy bakinta na rawa ta kama hannun daddy ta ce """Mutallab daddy, Mutallab who is Mutallab?""" For more information akan littafin MUTALLAB. Via 08164069385 WhatsApp only Na'ima Sulaiman Sarauta Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[1/7, 9:32 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 8 *Bright pens... 2nd batch* """Daddy na ji kamar gangar jikina ta wanzu da wannan mai sunan, na ji ƙirjina ya mini nauyi numfashina" "ya taɓa gauraya da nashi daddy ina jina kamar bani ba, daddy who is Safiyyerh? Daddy tell me something about me, don Allah wallahi zuciyata bugawa take i missed something very important..." "Daddy!""" "Ganin duk sun yi mata shiru ya saka ta girgiza daddy da hannunta biyu ""waye Mutallab daddy?"" Duk" "suka sake yi mata shiru kamar basu fahimci me take nufi ba Dr Hash da bai jima da shigowa gidan ba saboda aikin kwana ya yi a asibiti ya nufi inda Fiyya take tsaye yana leƙa fuskarta ya ce ""Mutallab kuma?"" Ta kasa magana sai bin su take da idanu daddy ya yi namijin ƙoƙarin wajan kama kafaɗun Fiyya ya ce ""Maama waye haka? Kinga irin abin da nake faɗa miki akan muhimmanci da ƙarfin addu'a kina sake da" "gaske kina wasa da azkar""" "Sakin daddy ta yi ta nufi wajan Ummi ta ce ""daddy na san ke za ki faɗa mini"" nan ma Ummi ta kama" "hannun Fiyya ta ce ""Mamaa ban san me kike nufi kowa kike magana akai ba, kamar mai iskokai ki farka kina surutai mene haka kike safiyyerh?"" Da sauri ta saki Ummi ta nufi wajan Yaya J ganin ta nufu shi ya yi saurin juyawa ya fita da sauri yana dafe kan shi. Fiyya ta sake juyawa wajan daddy jikinta duka rawa yake da ɓari kamar mazari ta kama hannun daddy ta ɗora a saitin ƙirjinta idanunta na cika da hawaye bakinta" na rawa da ƙyar ta ce """Ni ban buƙaci sanin wani abu bayan hakan ba, ban ce dole na san wani abu ba ka yi mini alfarma ka" "faɗa mini waye shi waye Mutallab? Daddy please...!""" Kasa magana ta yi jin an tsira mata sirijin allura ta runtse idanunta ta saki daddy ta juya a hankali ta kalli "Dr Hash ta sake nutsa ganinta cikin idanunsa ta kalli allurar hannunsa sai kuma ta yi murmushi ta sake juyawa ta kalli photon daddy dake gefen gadonta ""why? Me ya sa ake mini allura daddy i love you"" sai kuma ta lumshe idanunta jikinta ya saki ta ji kanta ya mata nauyi tunaninta na ruɓanya gudun zuciyarta na ƙaruwa, kamar wacce ake yi wa updating haka take jin ƙwaƙwalwarta ganinta zata faɗi ya saka daddy ya riƙota ya jima bai ji tausayin abu ko wata halitta a duniya irin Fiyyarsa ya dinga kallon fuskarsa cike da so da ƙauna a hankali ya kwantar da ita saman gado ya ɗora kan ta a saman cinyarsa ya dubi Dr Hash ya" ce """Hashim ya zan yi da Fiyya ta fahimta me zan yi Hashim, Awais ya ya zan yi da Maama?"" Ya faɗa yana" kallon Marafa duk suka kasa magana Ummi idanunta ya yi jajur baccin da basu koma ba kenan sukai spending sauran lokacin wajan Fiyya sai addu'a yake yi mata. Dab da asuba ya miƙe ya fice daman shi ya yi saura ya kulle ƙofar. Duk da nauyin da kanta ke mata bai hana ta motsa ba saboda kiran sallah wanda hakan alama ce ta "cewa kai musulmi ne da zarar lokacin asuba ya yi dukkan wani rai a duniya daya kasance musulmi sai ya motsa, bakinta ɗauke da addu'a ta ce" ” لاَ ْ ُ هلل لاِ ي أْ َ انا َ ْ ُ َ ا أَ اَ َ ا إول َ ه "لاَ ُ رو""" "muryarta da ƙyar take fita a hankali ta ji an ɗan matsa hannunta, ta motsa yatsun hannun ta ji shi sarƙe" "dana wani ta rufe ido ta san cewa Yaya J ""ni ka cika mini hannu""" Ya buɗe ido ganin yadda ta murguɗa masa baki bai motsa ba a hankali ya zare yatsun shi ganin tana ƙoƙarin juyo da fuska zuwa ina yake ya miƙa hannu da sauri ya kashe hasken ɗaki the same time ya miƙe ya fice yana rufe ƙofa ta bi door way ɗin da kallo. **** Ammo na zaune a cikin ɗaki kamar yadda ta saba kodayaushe Malam ya ɗaga labule yana daga tsaye ya "kalli Ammo ya ce ""Ba dai tunanin wancan gantalallan kike ba? Kamar wacce aka ce na mutu kike takama ki yi ni ɗaki kwana ɗaki, to idan ma shine ki sawa zuciyarki ruwan sanyi da salama ki sallama shi, yanzu ke ba kifi samun nutsuwa ba da bakya ganin gilmawarsa yana saka miki faɗuwar gaba"" ita dai bata tanka shi" ba ta cigaba da aikin da take yi. Ya sake duban ta da kyau yana furta """Aure zan ƙara na hango wata ƴar duma-dumar bazawara fara tas sakin wawa ku yanke shawara a cikin" "ku wa zan saka"" a sanyaye ta ce ""Allah ya sanya alheri, duk wacce ka saka babu komai ko ni ɗin ce""" Malam ya juya zai fita Anty Hameeda ta shigo idanunta zuru-zuru alamar ta yi kuka gaban malam ya faɗi "ya ce ""mene kuma Hameeda?""" """Malam wajanka na zo da Ammo don Allah ku saurare ni"" ya yi jim sai kuma ya yi ɗakin Ammo ta bi" "bayansa gaishe su ta yi kafin cikin sanyin murya ta ce ""Ammo ke uwa ce kin ɗauki cikin Mutallab watanni wajan 11 ɗaya yake zaune kafin ki haishe shi, kin ji zafi da raɗaɗin naƙida wajan haihuwarsa, kin shayar da shi kin goya shi a bayanki, kin bashi abinci, kin ƙaunaci Mutallab sai dai ƙaunar da yake miki kamar har ta ninka wacce kike masa, idan bashi da lafiya baya yadda kowa ya taɓa shi sai ke ban san yaushe ne ko yaya ne ya zama haka ba, labarin da nake da shi akan Mutallab ba cikakke bane, zamana a Lagos ya saka ban san wasu abubuwan ba, kin ƙi faɗa mini yadda ya zama haka kin hana a faɗa mini, shin bakya jin rauni irin na uwa? Ƙauna irin ta uwa da ɗanta, duka bakya jin hakan kike barranta kan ki da autanki Ammo, hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar kar ki manta kalmar da ake cewa idan ka ƙi naka duniya ta so shi, idan ka so naka duniya ta ƙi shi, Ammo ga duniya da bakin jama'a na rige-rige kai" "Mutallab kabari idan kyautata zaton watarana za a kashe shi ko ya je inda ba zai taɓa fitowa ba..,""" """Allahamdulilah da zai mutum ai da ya sawwaƙa mini da ƴan'sanda Mutallab masifa ya zame mini ni na" "gode Allah da bana ganinsa cikin idanuna"" kallo malam kawai Anty Hameeda ke yi da ƙyar tana haɗiye abu mai ɗaci a maƙoshi ta ce" """Dukkan iyaye suna saka hannu cikin abin da ya fi gaban sanin mutane.Kowannen su yana ba da kaɗan" "daga jikinsa. Ta haka, abin da ya yi girma a cikin uwa ya zama mutum. Saboda haka, ba abin mamaki ba" "ne, sa’adda da aka haifi jariri, mutane sukan ce _mu’ujizar haihuwa_ , haƙiƙa, haihuwar yara ita ce" "hakƙin iyaye na farko. Da farko, jarirai suna dogara ƙwarai ga iyayensu, amma sa’adda da suke girma," suna buƙatar fiye da a mai da hankali ga abincinsu kawai. Suna bukatar taimako domin su yi girma a "tunaninsu, a motsin rai, a ɗabi’a, da kuma a ruhaniya." "Domin su yi girma da kyau, yara musamman suna bukatar iyayensu su yi ƙaunarsu. Ko da yake yana da" "muhimmanci a furta kalami na ƙauna, ya kamata ayyuka su tokara hakan. Haƙiƙa, yara suna bukatar misali mai kyau daga iyayensu. Suna bukatar ja-gora a ɗabi’a, mizanai da za su bi a rayuwa. Kuma suna bukatar wannan tun suna ƙanƙanana zuwa gaba. Abubuwa masu ɓata rai suna iya faruwa kuma suna" "faruwa sa’adda da ba a taimaki yara ba har sai da ya makara"" kukan da take dannewa ya ci ƙarfinta" """Ammo idan Malam bai fuskanta ba ki daure ki gane don girman Allah, shi kaɗai autanki ɗanki tilo ɗaya" "namiji da Allah Ya ba ki idan babu ranku shi ne zamu kira da sunan uba, zai mana walicci a ko'ina bai kyautu don ƙaddarar Ubangiji ta kitta a rayuwarsa ku ce za ku juya masa baya ko wofitar da rayuwarsa har haka ba, akwai hakƙin iyaye akan yara haka akwai hakƙin yara akan iyaye shin kina buƙatar Ubangiji ya tuhume ki da hakƙin Mutallab? Allah da kan shi cikin hadisi mai girma ya ce; ƴaƴanku amana ce kuma kiwo ne a gare ku, lallai za mu tambaye ku wannan amanar da kiwon idan an ce ki faɗi inda yake a yanzu ba za ki faɗa ba wannan abun da kuke kun bashi dama da lasisin ƙara lalacewa ne idan yaro ya ɗaƙko" "hanyar kangara jawo shi aje jiki a nuna masa ƙauna da soyayya""" "Miƙewa ta yi tsaye tana share idanunta ""ya zo mini jikinsa duk sara kamar korarre mara iyaye a duniyar" "nan har na yi na gama magana bai tanka wani kuskuren iyaye ke haddasa shi""" Tana kaiwa nan ta fice abin ta inda ta shige Inna Binta da Mama Zaituna na kokawa akan wani ƙanzon "tuwon da aka baza ya bushe sai ya yi gwanin sha'awa tana ɓantara da kaiwa baki ta ce ""eh, kya yi kya gama wannan ƙanzon sai na bawa Mufee ke ni fa akan abinci ba wani kirki gare ni ba, ba zan zauna yunwa ta yi ajalina a gidan nan ba, tunda mai gidan zuciyarsa a mace take bai san fus na hakƙin iyali ba sai auri saki da tare yara kamar ƴaƴan ɓeraye kowanne kana kallonsa yunwa zata fara maka sallama a jikinsa haba me ake da hali na..."" Da sauri ta yi shiru ganin malam tsaye ta yi mamaki da bai tanka mata" ba ya shige. Safiyyerh ta sakko daga saman bene tana yi tana duba wayarta ganin saƙon da Ashraf ya tura mata cewa ya ɗan yi tafiya ba ta yi reply ba ta riƙe wayar. Yaya J ta gani zaune ta juya masa manyan idanunta da suka sake fitowa farare tas ta ce """Office ɗin kenan?""" """Ina ni ina zuwa office banga yadda little sis ta farka daddy's favourite"" ta girgiza kai tana ɗan murmushi" "iya leɓe ta ce ""Yaya J kenan, good morning""" """Kin tashi lafiya sai ina?""" """Office, ina da meeting kuma Yaya J ka yi mini addu'a Please da wannan kyakkyawan harshen naka, zan" "baka labari mai daɗi"" ya ware hannunsa ya ce" """To ina jira ko na kai ki office ɗin?"" Ta girgiza kai ta juya tana nufar sashin daddy dake ƙasa. Fiyya tuni ta" "manta abin da ya faru ta manta wani Mutallab fresh take jin kan ta, tana ƴar waƙarta ta turanci tama" manta ta shigo parlon daddy dake zaune ya zuba mata idanu ta yi saurin rufe ba ki ta ce """Ka yi haƙuri daddy i enjoying when i sing a song, don Allah ka yafe wa Maama""" """Sai an yi magana idan kin yi laifi kina buɗe manyan idanunki kinawa jama'a turancin yaran zamani ke ba" "kowa naki da yake bature""" """To babana babban laccara ne wanda ake alfahari da shi dukkan matasa ke son shi saboda ƙoƙari da" "iyawar shi"" Fiyya ta ce tana zaman ƙasan ƙafafun daddy ""Tiger"" sak ta yi jin sunan da ya kira ta da shi," lallai an taɓa donganta ta sa wannan sunan na Tiger ta share kana ta gai da daddy. Ya amsa cikin kulawa duk motsin da take akan idanunsa Fiyya na da mugun wayo dana da wani "experience da Qualities bata yin abun da za a iya following footsteps ɗin ta, she is a clever girl faɗanta har tsoro yake bashi ga taurin kai da miskilanci har addu'a yake Allah ya sassauta mata sai gashi Ubangiji" ya gyara komai a lokacin da bai zato ba. Ya ɗauke kai yana kallon wani gefen """Aliyu yaushe ka dawo?"" Idanunsa a kan waya yana dannawa, wandon uniform na sojoji ne jikinsa sai" fara t.shirt tas wacce ta kama damtsen hannunsa ya saka p.cap ta sojoji fuskarsa kamar ya ce ya shiga uku can ya ce """Da daddare""" """Dare da yaushe? Aliyu kai kana son shigowar dare kamar mara gaskiya?"" Captain ya ɗan kalli daddy ya" "ce ""Tun 12""" """Kuma baka shigo ba me ya sa?""" """Kawai daddy"" ficewa ya yi yana cilla wayar a aljihu yana jin Fiyya na gaishe shi ko inda take bai kalla ba." """daddy ni ba zan iya ɗaukan wannan halin ba wallahi bai ishe ni kallo ba zan daina ko gaishe shi ina dalili, Safiyyerh Abdu Marafa na da class babu mai ɗaga mini shoulder, duk wannan abun da ya yi aure a waje ne yake soja"" Ranta duk a ɓace ta miƙe tana cewa daddy ta tafi ya ce ""Allah Ya tsare Manager ya shirya safiyyerh Abdu Marafa"". Kasancewar sauri take yi ta saka ta yi driving kamar zata tashi saman bata wasa idan tana kan titi, tana isa ta buɗe office ta shiga fahimtar da sabuwar envelope a table ɗin ya saka ta sa hannu ta ɗauka tare da buɗewa taƙaitaccen rubutu ne mai ɗauke da jan biro wanda ke nuna rayuwarta" na cikin matsala. A hankali ta fara duba consent ɗin da takardar ke ɗauke da shi tana ajjiye waya. "“Jarumtarki bai kai ki tsaya bincike akan FS WORLD INVESTMENT COMPANY ba, kina iya ɗaukan rubutun" matsayin wasa amma gargaɗi ne da jan kunne ga yara masu rawar kai irin ki. Ki tsaya da binciken da kike you're nothing but a manager” Ta dinga juya takardar a hannu tana jin confidence nata na ƙara hakan kamar wata dama ce aka haska "mata na nuna cewa lallai akwai ƙullalliyya a wannan kamfanin, kuma ta shirya buɗe faifai ko da za su yi zubaibai ƙwarya ne, ko da gaskiyar da take ƙoƙarin bayyanawa zai yi silar barin ta numfashinta daga ƙirjinta. Ta yi Addison na cikin abubuwan da take ƙarawa a binciken za ta yi komai ko hakan na nufin fito na fito da surukinta ne. Zama ta yi ta fara duba files na sabbin kayan da aka kawo can ta saka aka kira" mata accouter bayan ya shigo ba tare data kalle shi ba ta ce """Accouter kana buƙatar wani abu ne?""" """Allah Ya taimaki manager kamarya fa?"" Still bata kalle shi ba ta yi baya tana duba maganar da aka turo" "mata yanzu a waya ta ce ""kawai kuɗi idan kana so na buƙatun rayuwa""" """Ina jiran lokacin albashi ya yi ai nasan za a sallame mu da wuri"" ta ɗago idanunta masu sanyi ta zuba a" "kan shi sai ta cillo masa ƙaramin file ta ce ""na saka hannu ka yi signature as a accouter ka cire 1m a" "asusun kamfani na baka"" da mamaki ya ce" """Ni kika bawa kuɗin?""" """E, ko baka so?""" """To na ga ban yi wani aikin da na cancanci 1m ba kin sa na fara jin tsoro ba zan iya cin abin da ba haƙƙina" "ba"" ta ɗan yi murmushi ta janyo files ɗin ta yaga ta ce ""meye cikakken sunanka ma?"" Rainin hankalin" "Manager mamaki yake bashi sai kawai ya ce Wazeer"" da hannu ta ce ya je yana fita ta saka aka kira mata MD abin da ta yi wa Accouter shi ta yi wa Md cikin sauri ya ce" """Yanzu kika ɗakko hanya manager da za ki haƙa ramin da za ki iya binne kan ki ciki ai duk sai na raina" "wayonki wallahi da ajin nan naki ko mene a ƙasa ba ruwanki mind your own business rayuwar nan kana kallon wasu abubuwan kake yi kamar baka sani ba, to a haka cibiya ta rai ne mu kuma yanzu hankalin jama'a da yawa na kan siyasa, matasa na neman hanyar karatu, wasu na can suna bautawa ƴan siyasa, wasu sojan baka wasu rayuwar social media wasu bangar siyasa wasu kasuwanci. Safiyyerh da yawa ana yin abin da ya samu ne ko yazo hannu ba wanda kake ganin cancnatar shi ba, ba a duba capacity na abu ko a siyasa kana ji kana ganin wanda ya dace amma kake rufe idanu ka ɗauki baragurbi saboda yana watsa maka hatsi mu ɗin kamar ka ji suka ɗauke mu, think big Fiyya ke macace babu mai ce miki don me," "akwai kuɗin da shi kan shi Alhaji Baihaƙi bai sani""" """Kana son siyasa""" "Md ya yi murmushi ya ce ""Safiyyerh siyasa yanzu ai kusan a jinin kowanne matashi take, kinga muna da" "jam'iyyu uku ɗaya ce mai ƙarfi saboda ita ke riƙe da muƙami ma'ana ƙasar a nan Hon Maɗatai yake neman takarar kujera, sai jam'iyyar su Eng Ali wali sai last jam'iyya wacce mutumin cikin ta ya fi kowanne" "nagarta kuɗi masu dame shi ba, da ƙyar aka taushi zuciyarsa yake muƙamin kusan matashi ne matasa na" son shi amma kasancewar yana cikin jam'iyya ƙarama kusan sabuwa ya sa ba a yin maganar shi ma kuma "da ba musulmi bane"" Safiyyerh ta jinjina masa kai ta ce ""Ka bawa accouter ya yi signature a baka 2m, enjoy yourself MD, but sunan wanda kake bani bayani yanzu?""" "Ya washe bakinsa ba ƙaramin jin daɗi ya yi ba ya ce ""Abraham Denial David, shine ɗan takarar""" """Yana da hannun jari a nan ne?""" """A'a, i don't think zai saka hannun jari a nan gaskiya"" a hankali ta ce ""Me ya sa?""" """Kar ki zurfafa a bar maganar, za mu yi aiki tare"" sallamar shi ta yi tana jin zata yi amfani da Md da" accouter Md zai taimaka wajan sanyawa ta san sirrin kamfanin cikin sauƙi accouter zai taimaka wajan bayyana komai. A gefe guda tana jin kamar ta shiga batun siyasar Abraham ɗin kawai ta ji ya yi mata she just want to help him. **** "Su da kan su sun kwana biyu basu saka shi a idanunsu ba, ba kuma su samu labarin inda yake ba sai" "yanzu da suka ganshi kamar walƙiya kwance a ƙasa idanunsa buɗe yana kallon sama Darma ya ce ""Sai godiya wanda ya ce zai bi sawunka ya wahala, ɗan malam yaƙi halin malam dafinka ƙarinka masifa ne" "idan ka taɓa mutum da shi""" """Darma""" """Ka dake Mai dawa ka jima ka yi lastin irin na dabino, wa kake so a taka a kashe ko a yi masa fiɗa"" Darma" ya ce yana buɗe hannu sama tare da karkatar da baki hannunsa riƙe da ledar pure water ya nannaɗe a "hannu yana kaiwa baki tare da zuƙa. Mutallab ya sake buɗe idanu a sama ya kasa cewa komai tunaninsa ya tafi wani wajan. Goje ya ce ""Sai godiya matsalar goge ce ko wato ka kayan lantarki""" """Zaman gidan yari ba daɗi,amma na ji daɗi""" """Ka ce ka tuna na jakuna nan cinnaku tsakaninmu da su sai ƙarfe ba ma'ana ka tuna na jakin da suka" "haɗa maka kenan""" """Ina jin zafi a ƙirjina farcuna na da suka cire mini sun ƙi fitowa, zan ɗauki fansa Goje""" Kafin su yi magana an yi sallama an ƙarasu cikin sauri Mutallab ya rufe idanunsa jin muryar zabuwa. Goje "ya dinga kallon wacce take tsaye ""Bayin Allah sallama nake muku fa"" Mangal ne ya kalleta sosai ya ce ""Yi batu"" ta ɗan rausayar da kai gefe ta ce ""Amma dai ku musulmai ne amsa sallama wajibi ce""" """To alaiki, mene sagin aiki kike so a yi miki?""" "Kinal ta fito da littafi da biro ta ce ""Sunana Kinal ni mawaƙiya ce, har zan shige na hango ku na ji ina son" tambayarku na ji ina son na yi waƙa akan ku kasan mu da mu da marubuta kusan aikin mu ɗaya muna da "son bin ƙwaƙƙwafi"" Goje ya ce ""To ina ruwan mu? Fece kafin na yi miki lahani""" """Ku ba ƴan shaye-shaye bane? To akan shaye-shayen zan muku tambaya ina yin waƙar zan kawo muku" "ku ji, idan kun yi shaye-shayen me kuke ji mene dalilin daya saka kuka fara shaye-shaye kuma kuke harkar daba""" "Moh na jin su ya juya musu baya zaka ɗauka bacci yake, ransa duk a ɓace saboda jin muryar mace da ya" ji ya san daya juyo zai iya kashe ta tsaf don bashi da wani business da mata. Darma ya ce """Yanzu yadda muke ji za mu faɗa miki kenan?"" Kinal ta yi saurin cewa ""E, wallahi na iya waƙa ina da" "murya sosai babu mamaki idan na yi waƙar na saka a YouTube ta je viral na saka a tiktok ta yi trending"" Darma ya ce ""To ni dai tun daga sanda a gida na yi...,""Da sauri Goje ya tsayar da shi yana cewa ""Kai amma ɗan tsinanniya ne kai, ba haka ake bayani ba""" "Miƙewa ya yi ya ce ""bari na faɗa miki"" wuƙa ya zaro a ƙugunsa Kinal ta zare idanu tana yin baya cikin" "sauri Mangal ya tare bayan jikinta na rawa ta fasa ihu jin yadda Goje ya yanke ta da wuƙa a fuska,ya" danna mata ledan wiwin a baki ta fara zare ido tana ihu. Sai a lokacin Moh ya juyo yana kallon yarinyar ya cije bakinsa tare da juyawa exactly irin ihun da Safiyya ta yi lokacin zata mutu. """Gani ya kore ji, idan kin rero waƙar muna dakon ki a nan sata ƴar munafuka""" "Darma ya dinga tuntsira dariya sosai yana riƙe ciki ""Amma Goje baka da imani kamar fa fitsari ta yi a" "wando gaskiyar kurciyar nan akwai jan ido ga bayani nan kin gani ganin idanunki ai"" ya juya ya kalli Moh ya leƙa ga wata cukurkuɗaɗdiyya takarda yake karantawa shi ba wani karatu ya yi ba ""Wai wannan takardar mece kamar ta asiri kodayaushe tana wajanka, kamar numfashin shaƙa ka faɗa mana ta mece""" cikin sauri ya ɓoye yana damƙe ta a hannu Goje ya ce """Nima sai fakon farar nake na mata karatun makarantar allo, na rasa wacce tsiyar ce a ciki""" """Goje""" """Sai godiya""" """Zan saka maka tsini idan ka taɓa takardar nan ko na saka su tiger cinye ka ɗanye, wallahi zan iya kashe" "ka akan takardar nan""" "Kafin su yi magana an zo da babur an cillo wata takarda da sauri mai babur ɗin ya juya, Mangal ya miƙe" "tsaye ya ɗakko ya buɗe cikin sauri ya kalli Mai dawa dai kuma ya miƙa masa amsa ya yi ya duba, photo" "na gudu biyu ne ɗaya zanen fuskar wata kamar dai mahaukaciya sai kuma photo jira-jirai, photo me mai magana ga wanda yake da cikakken lissafi a gefe an rubuta FS WORLD INVESTMENT COMPANY." **** "Kwana biyu Safiyyerh ta yi busy duk wani family sun zo saboda gobe ne ake ɗaura auren, kamar auren" munafurci ba wata gayya ko shagali ɗaurin aure ne kawai ana yi kuma Ashraf zai ɗauki matarsa su tafi. A daren ranar Safiyyerh ta riga data gama accepting auren Ashraf ta yarda bata da wani miji sai shi zata sawa zuciyarta yadda zata zauna da shi tunda tana son shi ko ba can ba. Waya suka yi da Ashraf ya dinga "tsokanarta ""Har na hango idanun Maama a ɗakin miji, mijin na kuma Ashraf ta yi nasarar samun" "kyakkyawan saurayi"" ta murguɗa masa baki ta ce ""Zan fasa"" ya yi saurin cewa ""Idan ki kaga ba ki auri" "Ashraf to mutuwa na yi ko ke kika mutu, da gaske Fiyya ina son ki Allah shine shaida duk da ina dalilin auren ki ko saka ni akai na yi hakan amma na yi you're my life partner har janna in sha Allah""" """Kamarya? Mene dalilin auren?""" """Ke ba ki da wani favourite words ne sai kamarya, zan faɗa miki komai a daren ranar da kika zama" "halaliyyar Ashraf zan faɗa miki, zan sauƙaƙa miki binciken da kike akan Company"" a ruɗe ta ce ""Ta ya ya kasan ina bincike akan Company""" """Safiyyerh kenan, that's is the difference between man and woman, ina da baƙi sai goben idan na zo" "ganin matata a wannan lokacin dole na rungume ki halal runguma zan miki Safiyyerh"" hankalinta duk a tashe waye Ashraf ne me ya sa daddy ya amince da auren shi? Ta kasa magana har ya kashe kiran sai ya ƙara kiranta video call ƙura mata idanu ya yi taga yana shiri cikin sauri ta ce ""Kuma sai ina?"" ""Inda kika" "aike ni"" ta buɗe idanu" """Kamarya?""" """I miss you Fiyya shine abin da na manta na ce miki, a nan nake jin motsin ki"" ya nuna mata saitin ƙirjinsa," "daga nan ya kashe wayar. Daga ƙarshe ta yi zamanta cikin bedroom Awais har bedroom ya shigo ya dinga mata shira ""Yaya Aiwas ka ɗan yanke mini farce"" ""to ban taɓa ganin amarya irin ba tunda nake a duniya"" ya jawo ƙafar ya fara yanke mata farce ta rufe idanu." "Washegari da sassafe Fiyya na bacci daddy da kan shi ya tashe ta, ta farka da ƙyar saboda kan ta dake" "ciwo mamaki ta yi ganin kusan family a ɗakin ya kalleta ya ce ""Kin dai yi sallah ko?"" Ta ɗaga masa kai ""Daddy lafiya?"" Ya yi shiru ya ce ""Junaid je ku fara yin gaba, Captain an kira shi yanzu daga can headquarter, Ummi ɗakko mini hijabin Maama"" Hijab ya karɓa ya saka mata ya riƙe hannunta Anty Turai ta yi gaba tana zabgawa Fiyya harara har harabar gidan suka je, abin mamaki gidan shiru ta rasa meke faruwa a motar daddy suka shiga yana baya riƙe da ita Awais na jan motar da Ummi. Motar Fiyya kuma da ita Captain ya yi using wajan fita saboda shi bai Fiyya ɗaukan tashi ba. Fiyya ta yi shiru kan ta a ƙasa,har suka ƙarasu cikin babban gidan mai tarin jama'a daidai lokacin aka fito da shi daddy na riƙe da" "hannunta ya ce ""Mamana je ki masa addu'a""" """Addu'a? Daddy waye?"" Ta furta muryarta na rawa ta juya ta kalli makarar da aka ajjiye gabanta ɗauke" "da gawa, ya sake riƙe hannunta da kyau ya jata zuwa gaban makarar ya duƙa tare da yin namijin ƙoƙarin buɗewa. Fiyya numfashinta ta ji ya ɗauke lokacin da idanunta ya yi arba da gawar Ashraf dake kwance cikin makara, jira ya fara ɗaukar gangar jikinta da gaske Ashraf ne kwance ba yau aka ce za a ɗaura musu aure ba shine zai mutu anya gawar Ashraf ce numfashinta ya tsaya cak tana daga tsayen suka ji ta yi" "wani irin ajjiyar zuciya tare da yin baya cikin sauri a tare daddy da J suka tare ta, ta ƙarasa suma a jikinsu." Bayan sallatar gawar Ashraf da binne shi duk ana zaune ana addu'a daddy ya ce yana neman alfarma "don Allah suka ce tame ""Kar a tambayan hujja ko dalili a yanzu ina son a ɗaura auren Safiyyerh da Aliyu""." "*฀for now na san a ranku za ku yi ta wasu wasu, wasu ma su ce ba su gane inda labarin ya nufa ba ku" "dai nutsu tafiyar kura ce mai tsarƙaƙƙiyya har nishaɗi kuke bani idan ana comment tafiyar da hasashe ku lissafi ba zai taɓa kawowa tunanin mutum ba, kar ku ji kun karaya domin na san dole a gaba zaku buƙaci" "labarin, har yanzu shimfiɗa muke yi iya shafi 8 mukai*" Littafin MUTALLAB na kuɗi ne kuma za a ke yin posting kullum. An fara biya yau domin shiga paid group na MUTALLAB. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. A tura shaidar biya ta nan 08164069385 ku yi ku biya a sati uku mu kammala ฀ Domin gyaran nono ❤🔥🔥💃 Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 9 *Bright pens..2nd batch* """Bani da wani zaɓi sai na hakan, haɗa auren Aliyu da Safiyyerh kar ku tambayan dalili kar a tambayan" "cikin Safiyyerh da Aliyu waye ba ƙwayar halittata bace ta yi sanadin zuwan shi duniya, hankalina zai fi kwanciya kafin Ashraf ya kwana cikin kabari ya zamana Safiyyerh nada igiyar aure a kan ta"" ajjiyar zuciya Sharfaɗi ya yi idanunsa a kan Prof Abdu Marafa ya ce ""Me kake jin tsoro da kake so dole ka aurar da ita, Allah Ya gani amintar mu ya saka muka yanke hukuncin haɗa yaran nan aure saboda ƙarfafa zumunci, to kana taka Ubangijin talikai na tashi nasa kuma shine gaskiya, Ashraf ya rasu baya duniya ina tunanin ka bar yarinyar nan ta samu nutsuwa ta duba wanda take so yake son ta sai a yi mata aure, kar a ƙuntata" "rayuwar yarinya""" """Sharfaɗi ba zaka fahimta ba, ka yi mini wannan alfarma ka wakilci Aliyu ni zan wakilci Safiyyerh ga" "jama'a su shaida Please sai a haɗa a yi addu'a har ta Ashraf"" J zufa har yanko masa take yi na tsananin mamaki mene haɗin Captain da Safiyyerh da za a yi musu aure? Baya son zuciyarsa ta gasgata abin da yake jin tsoro ko wassafo shi cikin kan shi, Safiyyerh fa and Aliyu? Ya Allah! Shi dai Awais kan shi a ƙasa" Dr Hash daman baya wajan yana can duba Fiyya tunda ta faɗi wajan ya yi shiru can daddy ya ce """Kawai alfarma nake nema zan ji daɗin hakan idan ka yi mini""" """To shikenan, waye maɗaurin auren?""" "Daddy ya nuna wani abokinsa, Sharfaɗi ya ciro kuɗi mai yawa a cikin aljihu ya dire ya ce ""Ni Sharfaɗi ina" "nemawa ɗana Aliyu Abdu Marafa auren Safiyyerh Abdu Marafa a wajan waliyi na wannan yarinya"" daddy ya saka hannu ya ɗauki kuɗin ya ce ""Ni Abdu Marafa uba a wajan Safiyyerh Abdu Marafa na bawa Aliyu Abdu Marafa auren yarinyar wajena Allah Ya sanya musu albarka"" addu'a aka yi nan take kuma aka" ɗaura auren a gaban shaidu ma ɗaurin ya ce """Aure ya ɗauro a kan sadakin da Sharfaɗi ya bawa dubu ɗari biyu, Allah Ya sanya albarka tsakanin Aliyu" "da Safiyyerh ya kuma kaɗe fitinar da kan iya wanzuwa a tsakaninsu"" duk aka amsa da amin. Daddy ya" "lumshe idanunsa yana sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya nutsuwar ta saukar masa, bashi da sauran fargaba a yanzu Safiyyerh ta zama matar wani." "Kasancewar rasuwar ɗan babban mutum ce kamar Sharfaɗi ya saka manyan mutane zuwa gaisuwa, ƴan" "kasuwa da ƴan siyasa da wanda dai suke jin kansu wasu ne a garin. Kallo kallo aka shiga yi tsakanin Hon Maɗatai da Eng Ali wali dukkan su cikin shiga ta alfarma, ga mutane da take musu baya kowanne da tarin ƴan jagaliya da ƴan daba gudun kota kwana. Hon Maɗatai ya yi murmushi yana miƙawa Ali wali" hannu ya ce """Kwana da yawa Ali wali?"" Ali wali ya ɗauke hannu sai kuma ya juya ya ce" """Ba yanzu ba ka jira na wani lokaci komai zai haska, za a yi tsawa walƙiya ta bayyana munafukan da suke" "ɓoye cikin duhun ciyayi"" murmushi Hon Maɗatai ya yi kawai yana furta ""Allah Ya nuna mana"" gaisuwa duk sukai sai dai daddy tsakaninsu kawai addu'a ya miƙewa daga wajan. Bayan yin ta'aziyya Hon Maɗatai ya ce ""Allah Ya yi wa Ashraf Rahama, ya taƙaita iya kan shi"" Sharfaɗi ya juya ya kalli Hon Maɗatai kana ya kalli Eng Ali wali sai kuma ya ce ""Amin, yanzu ba gashi ba gwanin sha'awa a dinga siyasa bada gaba ba sai an fi samun nutsuwar zuciya data ƙwaƙwalwa duk wanda zai samu wannan kujerar Ubangiji ya gama rubutawa kawai dai lalube ake yi cikin duhu ku haɗa kai da hannu kowa ya yi kamfel nasa babban jin" "daɗin ba jam'iyyarku ɗaya ba""" Cikin jinjina kai Hon Maɗatai ya yi murmushi daman shi bashi da wata matsala da Eng Ali wali shi yake "haukan shi hankalinsa na kan wanda ya yi shiru, shirun nasa kuma yana nufin babbar barazana a gare shi ""Siyasa ai ba zata haɗa musulmi irina faɗa da wani ba, munga jiya mun ga yau muna da tabbacin za muga gobe mai kyau, ni fatana na samu gurbin saka hannun jari a kamfaninka idan aka bani dama an yi" "mini komai Sharfaɗi"" daddy na jin su can aka kira shi waya da sauri ya miƙe tsaye yana neman uzurin" tafiya Eng Ali wali ya bisa da idanu. "Cikin dare Fiyya ta farka da wani irin ciwon kai na ɓari guda, ta kasa buɗe idanunta a hankali ta saka" "hannu ta dafe kan ta duk da halin cewa bai hanata yin addu'a ya yi tashi a baccin ba domin tabbatarwa da kanta ba a cikin kabari ta farka ba. ""Sannu Maama"" shine abin da Ummi ta iya cewa tana hamdala a ranta domin shirun ya yi yawa ta damƙe hannunta sosai" """Ummi kai na ciwo, ciwo nake ji a gefen kaina"" jikinta har rawa yake na tsananin ciwo Ummi ta ce" """Maama zai daina in sha Allah, bari a kira likita""" """Ummi daddy fa?""" """Yanzu ya fita, ki yi ta addu'a komai ya yi farko yana da ƙarshe, wannan ciwon kan zai daina miki" "watarana buɗe idon ki kalle ni"" a hankali ta buɗe idanun ganin yadda idanun ya yi jajir ya saka Ummi cewa ""Subuhanallahi wannan jan kuma na magani da mene?""" """Ummi jimawar da ta yi a kwance da ciwon kan shine ya saka idanun ja yanzu daddy zai shigo Fiyya zata" "ji sauƙi ki kwantar da hankali"" daidai nan daddy ya buɗe ƙofa ya shigo J na bin shi a baya da Dr Hash, ganinsu kuma ya saka komai ya dawo tunanin Fiyya ta runtse idanunta tana jin fargaba na saukar mata. ""Da gaske Ashraf ya mutu daddy? Da gaske an binne Ashraf babu Ashraf ya mutu yanzu haka yana kwance cikin kabari mijin da zan aura ranar ɗaurin aurena ya mutu daddy na shiga uku"" daddy ya kama" hannun Fiyya cikin nutsuwa ya ce """Laa, sam ba ki shiga uku ba tana iya yiyuwa ya shige iyakar shi ne, kuma mutuwa a hannun Ubangiji" "take idan lokacin ya yi kota wacce siga ce dole wannan rai ya koma wajan wanda ya samar dashi, Maama da gaske mijin da za ki aura mutu ki sawa ranki haƙuri ki yi masa addu'a ki saka salama ki ɗauka bashi ne zaɓinki ko alheri gare ki ba, Ubangiji na yin komai a lokacin ya yi niyya babu mai tuhumarsa hujjar hakan domin shi ishasshe ne ki yi addu'a Safiyyerh Ashraf is no longer alive pray for him"" juyawa Fiyya ta yi ta zubawa daddy manyan idanunta wanda yake cike da hawaye da ƙyar ta ce ""Ashraf ya mutu ya bar ni cikin zullumi daddy, inama tuntuni aka ɗaura mini aure da shi, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wayyo ni" "Safiyyerh""" """Zullumi na me kuma Safiyyerh kin ga abubuwa da yawa a rayuwa sai mutuwar Ashraf zai tsaya miki? Ba" "za ki yi addu'a ki sawa zuciyarki sallama, kuma wani hanin ga Allah baiwa ne kamar yadda aka sanar yau ɗaurin auren ki da Ashraf Allah bai yi ba, haka kuma alƙawarin Allah gaskiya ne igiyar auren wani ta hau kan ki Maama"" ta yi shiru don ta tabbatar daddy ba zai fahimce ta ba, ba zai gane me take nufi ba, ta yi missed Ashraf tun ba'a je ko'ina ba ta ji inama ita Ubangiji ya ɗauki rayuwarta ya bar Ashraf ko da bai aure ta ba, babu mamaki ta dalilinsa wani ya san abin da yake ɓoye gashi ta mutu ya barta da wani irin" damuwa ba tare daya bar mata ƙofa ko ɗaya da zata gane ba komai ba. """Daddy me ya sa ka haɗa aure na da Ashraf tun fari?"" Daddy ya kalli Fiyya cikin kwantar da hankali" """Saboda ya cancanta kuma ya dace Maama ki yi shiru da wannan maganganun duk zafin ciwo ne yake sawa kike furta su kamar saukar ruwan sama ki yi addu'a"" ta jinjina masa kai a hankali ta zare hannunta daga cikin nasa idanunta rufe sai sauke numfashi take yi ba tare da ta ce komai ba ta juya ta kwanta maganganun Ashraf na dawo ba, a ranta ta dinga masa addu'a ita bata taɓa sanin bashi da lafiya ba, he" never told her he was sick innalillahi. Dr ne ya shigo zai yi magana daddy ya yi saurin girgiza masa kai alamar kada ya ce wani abu serious Dr "ɗin ya zubawa Safiyyerh idanu ya ce ""za'a sallame ta yau kamar yadda ka buƙaci baka son kwana zan" "mata allura amma before""" """Thank you Dr""" "Dr Hash ya miƙe ya ce ""daddy zan je asibiti ina da aikin dare Awais zai yi dropping nawa bana jin daɗi""" "Ummi ta ce ""Kuma baka jin daɗin zaka tafi kamar dole ka yi kwanan tsaye ba'a ɗaukan uzuri ne"" ya ɗan yi murmushi kawai ya ce ""Ummi ai ba zai yiwu na amshi kuɗi na ƙi aiki ba, sai Ubangiji ya kama ni da" "wannan hakƙin ki yi addu'a zan iya"" ta ce ""To Allah ya sauwaƙe ya bada sa'a ya kuma kare""" """Amin Ummi""" "Dr ɗin ya yi wa Fiyya allura ta samu bacci mai nauyi, Ummi dai kallon daddy take jin ya kira Aliyu ya zo ya" "ɗauki Fiyya nan da 20 minutes shi zai tafi tare da Ummi har lokacin Aliyu bai san da batun auren ba kamar yadda Fiyya bata ɗauki maganar daddy serious ba. Ya gyara mata kwanciya ya miƙe Ummi ta miƙe tana shafa kan Safiyyerh a haka suka fita. Har wajan ƙarfe 1:30 Fiyya na kwance tana bacci lokaci zuwa lokaci wata nurse ke shigowa duba ta. Yana tsaye hannunsa biyu zube cikin aljihu ba zai ce ga abin da yake tunani ba, amma fuskarta kawai yake kallo ganin yadda a bacci ma take ɓata rai ta sauke ajjiyar" "zuciya, ƙofa aka buɗe ya yi saurin yin baya yana kame fuska sosai." "Dr ya kalli Captain ya ce ""Sai yanzu na ɗauka ma ko a nan zata kwana"" Aliyu dai ya yi shiru ya zaro waya" "ya fara dannawa ""ga maganganun nata wannan za a yi amfani da shi lokacin...,"" ""Ka kira su, sai ka musu bayani"" shi daya tsaya tunanin yadda zai tashe ta yake ga daddy sai kiran shi yake banda haka da ba zai zo bama, ya saka ƙafa ya fara zungurun gadon dr ya ce ""Allurar da aka yi mata nada ƙarfi sai dai ka ɗauke ta"" siririn tsaki ya yi ""to ɗauke ta kai"" ganin fuskar Aliyu cikin serious ya sa dr ya nufi Fiyya zai ɗauke ta zuwa waje kafin ya ƙarasa kawai yaga Captain ya saka hannu da drip ɗin da mayafin nata ya ɗaga sama ta zabura ta yi saurin riƙe shi Idan ba kuskuren ji ya yi ba ya ji kamar ta ce ""TAHHB"" ya sata gaban mota" ya kwantar da kujera kamar wanda ake bi haka yake jan motar. **** Yana durƙushe ya tsattsare mutumin da jajayen idanunsa wanda suka shige ciki alamar a buge hannunsa riƙe da askira gefe kuma jibgegen karan shi Tiger ne da duk a cikin karnukan ya fi son shi. Ya saka askira ɗin a cinyar mutumin ya nutsa jini ya fara fita sosai yana ihu da kururuwa cikin tsakiyar daren ga duhu ko'ina ya ce """Wai me ya sa baka da imani ne, zaka raba mini cinya biyu""" "Duk da cewa a buge yake amma tar ya buɗe idanunsa, cikin muryarsa da kana ji ka san shi ba ma'abocin" magana bane da wani kalar sautin mai kama da gurnanin zaki ya ce """Ka gane ni yanzu?"" Ya jinjina kai yana wani irin nishi da kakari kamar na mutuwa ya ce ""Na gane na" "gane, wallahi na gane ka""" """Good"" ya sake nutsa askirar ya yi feshi kunama ta faɗo ta shige cikin wandon birnin ya ce ""Sanda aka yi" "mini baru ma'ana aure, da nazo kai na ganin bakin ƙofar gidana, haka ne?"" Ya sake faɗa yana ƙara cilla masa wata kunamar baƙa ƙirin ta sake shigewa cikin wandon mutumin, Darma da Goje sun tale shi" kowanne ya take hannu ɗaya mutumin ya yi shiru hakan kuma ya sake fusata Moh ainun """Idan aka bani ciwon kai hauka nake yi ba zaka ka ji daɗi ba, a yunwa ce nake, yi batu"" kamar zai mutu" "cikin kakarin mutuwa ya ce ""Zan yi, zan yi magana"" suka sake shi suna kallon shi." """Mutane kala biyu ne suka shigo a wannan daren da aka kawo ta, na farko sun bani kuɗi fuskar su a rufe" "take na biyun ma sun sake bani kuɗi suma fuskar su a rufe take amma sun bani saƙo na baka tun a wannan lokacin, bayan an kama ka na rasa wa zan bawa na dinga bulayi kawai na haƙura, daga baya kuma aka zo aka sake cewa na bada wannan saƙon na ce a'a sai sukai mini tagoma shi da kuɗi har miliyan ɗaya kawai na basu ai kan ƙasar nan yadda muke fama da babu da yunwa ga iyalai ina dasu" "kawai na amsa na bashi""" "Darma ya ce ""ka ji kimini ƴan yankin nan ba za ku gama da duniya lafiya ba, da ƙyar kusha ruwan" "alkausara"" Moh ya zubawa mutumin jajayen idanunsa sai kuma ya miƙe tsaye magana yake son yi amma ta maƙale a harshen shi da ƙyar ya ce ""Ku yi masa ɓalli-ɓalli"" yana cewa haka ya juya." """Baka ji ba, ai na haddace abin da aka rubuta harafi uku ne a jiki. A.M.A, sai wani suna nada ban kamar" "sunan asibiti kamar sunan unguwa idan na tuna zan zo na faɗa maka amma don Allah kar ku yi mini komai a tausaya mini sabuwar amarya ce dani""" """Ni tawa matar ko kwana ban yi ɗakinta ba, duk irin gwagwarmayar dana sha, uhmmm"" ya yi shiru a" lokacin sautin muryarta yake ji na kakarin mutuwa a kunnensa can ya miƙe kawai ya yi gaba. Goje ya ce """Zan dinga zuwa lokaci lokaci domin kana cikin taskar Moh""" "Da sauri suka bi bayansa ganin har ya yi nisa sosai ""Mai dawa daman ka iya yaran nasara na ji ka ce" "Good""" """Na yi kala da wanda iya turanci ko mota ko amfani da waya ne?"" Kallon tsaf sukai masa Darma ya ce" """Ciki ne kai yasin sai fama kake da kan ka ba wannan maganar a basar kawai ya maganar ɗawan nan?""" "Kamar zai yi shiru sai ya ce ""Bana son sabga da mace zan iya kashe ta kamar yadda itama ɗayar na kashe ta""" "Darma ya fashe da dariya sosai yana kaɗa kan shi ya ce ""ba wannan ba wallahi wata figigiya da ita, suma" "dai basu da man kai wai ita ce manja"" Goje ya ce ""matsalar kai daƙiƙi ne ajawo sam ciki ne kai, manager ake cewa dake mayen garau garau ne kai wai manja ai uwar manja gaja kawai"" Darma dai bai kuma Goje ba ya ce ""Maganar gaskiya wannan za a iya karya mata ƙugu a wajan ɗakko ta ma sille kenan, Mai dawa ko kai baka ganta bane"" Ya yi musu shiru yana jinsu dai ""Sai godiya, ina magana baka ganta ba wata ƴar" "shila da ita?""" """Ita wa?""" """Manja ɗin""" """Idan ka ƙara ce mana manja a wajan nan za kaga manja ganin idanunka, ɗan wahalar yaro kawai""" "Mutallab dai idanunsa a lumshe tunanin da yake yi daban, kalmomin da mutumin ya faɗa masa nata yawo a cikin kan shi. A.M.A Ya kasa fahimtar kowanne harafi me yake nufi sai kawai ya taune bakinsa ƙirjinsa na buɗewa duk jikinsa tsami yake masa ya buɗe idanunsa ya kalli sama yana ganin yadda" gajimare ke gudu yana haɗewa tare da warewa muryarsa bata wani fito sosai can ƙasa ya furta kalmar. """her eyes look alike, tiger""." Washegari misalin 12 na rana Safiyyerh na saman bene cikin ɗakinta ta dinga kallon Kinal bata da "nutsuwa sosai da babu abin da zai hanata yin dariya. Kinal ta share hawayenta tana ɓata fuska cikin sanyin murya ta ce ""Kalli yadda sukai mini da fuska daga tambaya na ɗauka za su faɗa mini ashe ƴan" "wahala, ni bada wata munufar na je wajan su ba wallahi kawai su bani amsa na ƙara gaba""" """To ga amsar nan ai""" """Maama fuska ita ce kyan mace fa, yanzu idan tawa ta lalace waye zai aure ni haka? Sun kusa tsaga mini" "baki gashi yanzu ina da aiki a ƙasa sosai har Hon Maɗatai zan yi wa waƙa"" Safiyyerh ta yi shiru tana tunani so take ta fice daga cikin gidan secretly amma no way ""wai ina magana kina ji ba zan shariyar nan naki damuna yake, na zo ɗebe miki damuwa da kewa na rashin Ashraf kamar yadda Ummi ta buƙata duk" "da ciwon da bakina yake mini ina da zuba ke kina ignoring nawa for God sake""" """Idan ba ƙi auro ba sai ki auri ɗan daban kawai"" Kinal ta yi tsaki ta ce ""Kuma zan iya, mene a ciki""" """Shi auren ɗan daban?"" Fiyya ta buƙaci amsa tana kallon Kinal. Kinal ta ce ""Deal, nama yi miki alƙawarin" "in dai ina da numfashi wallahi wallahi sai na auri ɗaya daga cikin ƴan daban nan, kamar ni mawaƙiya za" "su yi wa haka? Uhm"" Fiyya ta lumshe idanu ta buɗe deep down ƙirjinta na bugawa sai ta ce" """You most like them ma, ƴan daban ai sun iya soyayya""" """Ke ta ya kika san sun iya?"" Shoulders kawai Fiyya ta ɗaga ba tare da ta ce komai can ta sauke numfashi" tana kallon Kinal ta ce """Kinal Ashraf ya rasu, mijin da zan aura ya bar ni Kinal ina cikin damuwa ina jin da old Safiyyerh ce ba zan" "ce ina cikin damuwa ba, gwara ta kashe ni haka nake ji"" Kinal ta jinjina kai ""Fiyya something is over doesn't mean your life is over, ki yi haƙuri mu ɗauki ƙaddara ki yi wa Ashraf addu'a Please kar ki saka damuwa wani abun ya zo yana damun ki daman ke idan kika birki ce kamar mai ƴar mero a ka, ƙaddararmu zata zama mai kyau muna tare da addu'ar iyaye ai"" sun jima tare da Kinal har yamma kana" ta tafi gida tana jin dole ta sake komawa wajan ƴan kodin ɗin nan. "Da ƙyar da daddare Fiyya ta sakko ƙasa bayan tayi sallar issha tana sanye da hijabi har ƙasa, fuskarsa" looking ok ba yabo ba fallasa sai dai ta faɗa idanunta ya fito akwai damuwa a tattare da ita. Inda ta yangi "su J ta nufa ta shiga tsakiyar ƴan mazan ta zauna a nutse ta ce ""Sannun ku"" Awais ya ɗago ya kalleta ya" "ce ""Yawwa Manager ya ƙarin haƙuri?"" Idanunta ya juya ta cije baki ta ce" """Allahamdulilah,thank you"" daddy dake kallon ta cike da tausayi ya ce ""tashi a nan wajan Safiyyerh""" """Daddy me ya sa?""" """Ki dai tashi na ce ko?""" "A sanyaye ta miƙe sai kawai ta yi sama ya bita da idanu a hankali ta ce ""Sai yaushe zaka faɗa mata batun" "auren?"" Daddy ya ce ""Da sai an kammala Visa ɗin ta, na san wacce take da ita a baya ta yi expired, to Safiyyerh stubborn girl ce da na yi maganar visa zata kalli cikin idanuna ta fara mini turanci wayonta tsoro yake bani, kuma yanzu i feel very comfortable da Aliyu matsayin mijinta duk da basa shiri amma ba" "zai ɗaga mata ƙafa bana son dai ta yi rayuwa a wajan shi kamar Prisoner, za ta yi shakkar yi masa abu""" """Kana ganin zata amince da auren?"" Ya miƙe tsaye yana haurawa sama ya ce ""In sha Allah"" daman daga" sallah ya dawo shine ya zauna. J dai baya uhm baya uhm'uhm abubuwa da yawa ke yawo a ƙasa wanda baya rasa nasaba da tunanin wace Safiyyerh waye Aliyu? "Ummi ta kalli yadda ya shigo ba wanda ya kula kamar bai ga kowa ba ta ce ""Aliyu tun safe ina ka je ne?""" "Ya buɗe ido ya yi shiru ta ce ""Kuma ka ci abinci ne? Kodayake ba'a tambayar soja ko ya ci abu da za'a buɗe cikin ka duk ganye ne"" kallon Ummi kawai yake kuma ya yi shiru" """Yaushe zaka tafi goben?""" """A'a, night Ummi"" ya ce yana shigewa cikin ɗakin shi dake part ɗin mazan." Fiyya ta ci kuka a ɗaki kamar rai da sauri ta buɗe system ɗinta taga saƙo a e-mail nata tun sanda sukai last called da Ashraf bayan hakan ta minti ashirin da wajan biyar. Maganar daya tura mata ya saka ta buɗe idanu sosai. "_Safiyyerh daddy ya zo ya fita yanzu, ko ma dai menene ki tabbatar ba ki bawa wani damar mallakar FS" "WORLD INVESTMENT COMPANY ba Fiyya mutane biyar sune mamallakan wannan kamfanin mutane masu haɗari ko ni ban san su ba, da ina da yadda zan yi a yanzu zan faɗa miki komai domin sauƙaƙa miki," "ki fara nemo ma'anar FS shine key ɗin binciken, don't cry when you miss me i love you""_" "Safiyyerh was shocked, thinking me ya saka Ashraf ya yi mentioned sunan daddy a lokacin, meke shirin" "faruwa ne gabaɗaya kan ta ya ɗauki zafi da gaske ta yi rashin Ashraf sai yanzu ne take jin gudun zuciyarta na ruɓanya aikinta a kan Ashraf ɗin. Ta kwanta tana rufe idanunta ƙarar notification na wayarta ta saka ta buɗe idanu tana janyo wayar a hankali, rubutu a taƙaice mai ɗauke da azanci da ɓoye manufar abin" da ake so a bayyana. _“laifi akan laifi again? Kodayake shi laifi tudu ne Safiyyerh ke inuwar wani ce ki yi ƙoƙari kar a saka ki shiga wuta”_ "A gigice ta ce ""Na shiga uku ni Safiyyerh""" **** Cikin dare ne wajan biyu da arba'in motarsa na gefen titi cikin duhun daren ya saka facemask ya rufe "fuskarsa tsoro da fargaba ya gaba gitta masa zuciya a hankali ya zuge glasses ɗin motar babu mai cewa shine a ciki, yana buɗewa ya faɗo cikin motar ya ce ""Kira cikin dare? Ban fiya son ina tsaka da wani aikin" "kuma ana kira na wani ba, ya akai?""" Photo ya fito masa da shi na wani kyakkyawan yaro fari tas da shi idanunsa buɗe ya shagwaɓe fuska tare "da miƙa hannu alamar a bashi wani abu, yana sanye cikin wasu ƙananun kaya baƙaƙe. ""Na gani photon" "waye? Wannan yaron fa?""" """Ɗan gidan Safiyyerh ne"" ya furta yana lumshe idanu tare da yin baya ya jingina da kujerar zuciyarsa na" "buɗewa sosai tsoro da fargaba na cika shi ""What! Safiyyerh yaronta kuma?""" """E, idan kaga Safiyyerh ka gan shi kamar an yi kaki ban san ko ta san da yaron ba a tabbatar an gano mini" "inda sa Safiyyerh take""" "Kwanakin wajan biyar da rasuwar Ashraf daddy bai faɗawa Fiyya batun auren ba, haka ma Aliyu Fiyya" "kullum sai ta fita wajan aiki ba kuma ta dawowa da wuri. Yamma wajan magariba take driving a gajiye take sosai fahimtar ana bin bayanta ya saka ta ƙarawa motar giyar da sauri ta ɗakko waya number J ta fara kira amma bai ɗauka ba, ta shiga kiran ta daddy amma a kashe duk wanda take tunanin kiran" "number shi a gidan ta kira bata samu ba," "ta kalli madubin taga har yanzu motar na biye da ita, tare da wasu babura biyu bata iya hango fuskar" "mutanen amma kallo guda ta yi musu ta san ƴan daba ne, ko dai masu satar mota ne ko satar waya ta shiga uku. Baburan guda biyu suka cimma ta ɗaya ya saka hannu ya daki glasses motar nata, ta yi gefe tare da ƙarawa motar gudu suma suka take mata baya a lokacin tsoron da ya yi mata yawa ya saka ta fara gani dishi dishi kan motar na neman kwace mata, cikin sauri tana ƙanƙame steering ta shiga lalubar numbersa bata da tabbacin ko tana da ita cikin sa'a ta gani ta danna kiran sai da ta yi kiran biyar bai" "ɗauka ba, gashi hanya babu mutane a kira na shida ya ɗaga cikin ɗaga murya da fitar hayyaci ta ce" """Yaya na shiga uku Captain wasu ne""" "Ya yi mata shiru can ya ce ""Who are you?""" """Yaya Safiyyerh ce wasu ƴan daba suka biyo ni gashi titi babu kowa, Captain suna da yawa wasu a babur" wasu a mota na kira number kowa a gida basu ɗauka ba gashi ciwon kaina kamar zai tashi bana ganin "hanya sosai kan motar ƙwace mini yake"" ta cikin wayar Captain ya yin siririn tsaki can ya ce" """Ina ruwana?""" """Captain kashe ni fa za su yi innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!""" """Allah Ya ji ƙan ki""" littafin MUTALLAB Na kuɗi ne we're still on free pages. Ka biya a yi adding naka a paid book before mu yi cutting free pages ɗin. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. A tura shaidar biya ta nan 08164069385 "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 10 *Bright pens..2nd batch* """Kamarya Allah Ya ji ƙai na, Captain ina faɗa maka biyo ni ake yi za'a kashe ni, kana cewa Allah Ya ji ƙai" "na, i called you saboda na rasa wanda zan kira Please help me"" ta cikin wayar Captain ya yi tsaki ya ce" """Kee, ina ruwana idan sun kashe ki who cares about your life, zan kira daddy a ɗauki gawarki ok"" kashe" wayar ya yi. Safiyyerh wani irin zafi ta ji a zuciyarta da raɗaɗi bata san ma wanne gurbi zata saka Aliyu ciki ba idanunta ya kawo hawaye baƙin cikin kiran da ta yi masa tana zargin kanta da laifinta ne. Ta cikin madubin motar take sake kallon motar dake bib bayanta da kuma sauran baburan ta runtse idanunta a "fili ta ce ""Ya Allahu Ya Rahmanu ka dubi Safiyyerh ka kawo mata ɗauki..Daddy!""" Ta kira sunan daddy a gigice tana sakin steering motar bata sake sanin abin da ya faru bayan nan ba. Yana tsaye fitowar shi daga motar kenan ya dubi yadda ta yi flat kwance a ƙasa gefen kanta da jini ya "kalli sauran jami'an tsaron da suke wajan ""Is she ok? Tana numfashi?""" """She is, buguwa ne kuma Allah Ya rufa asiri motar ta tsaya da kanta, ba'a yi nasarar kama ko mutum" "ɗaya ba, yarinyar ce dai bamu san wace ita ba za mu duba id card nata sai a kira iyayenta a shaida musu ko asibiti ne a tafi da ita"" ya yi maganar cikin girmama kan shi a ƙasa, wanda ke tambayar ko Fiyya na raye ya yi baya rungume da hannunsa can ya duba a gogo sai bai ce komai ba ""Sir meeting ɗin naka? Ina tunanin ka je kawai za mu kula da komai tunda shugaban jam'iyya da secretary na jam'iyya na jiran zuwan naka"" kafin ya yi magana cikin sauri wata mota ta ƙarasu wajan kamar zata tashi sama ko gama daidaita tsaiwar motar bai yi ba ya fito idanunsa a kan Safiyyerh, mutumin ya dubi fuskarta shima a" hankali kuma ya ce. """Easy Captain, ka kira ni sanda muke kan titin da take ta kuɓuta Allahamdulilah"" jinjina kai Aliyu ya yi" "cikin girmamawa ya ce ""thank you""" """Anything for you Aliyu, amma ku kula tana da harshe zuciyar nan tata irin take ce, Allah Ya bata lafiya""" "Aliyu dai na tsaye idanunsa akan fuskarta ya kasa magana har mutumin ya shiga motarsa driver ya ja, jami'an tsaron suma suka shiga motar suka marasa masa baya cikin tafiyar sirri. Ya jima yana kallon ta hannunsa riƙe da wayarsa tunanin yadda zai yi da ita, ƴar mitsitsiyar yarinya ta fito da shi, banda darajar daddy da babu abin da ya yi masa zafi sanin cewa idan Fiyya ta mutu hakan na nufin tsayawar numfashi daddy ya saka ya lallashi zuciyarsa. Cak ya ɗauke ta ya saka ta a gaban mota yana yin baya da kujerar a" "ransa ya ji ba zai zama drivernta ba, ya ɗauki wayarta ya rufe motar yana shiga ya tare da zama ya sake" juyawa ya kalle ta da kyau sosai jinin ke fita a goshin nata ya taɓe bakinsa kawai a hankali kuma yana ɗora mata tissue ya furta “Fitinanniyya... Safiii” "Farar safiya ce gari ya yi shiru amma shi idanunsa biyu, yadda ya ga dare haka ya ga rana idanunsa tarwai" "a sararin subuhana yana kallon sama da abubuwan da Ubangiji ya wanzar a cikinta, a hankali ya juya ya kalli Darma da Goje sai kuma Mangal dake can gefe guda ya sha ta gaya masa babu daɗi sai lilo yake da ƙafarsa a sama. Mangal ne ya buɗe idanunsa da sauri ya miƙe zaune yana murza idanunsa alamar bai" gama wastsakewa ba. """Jeji naka dawa taka ka huta mai dawa, ba dai gaba da gaba ko ta baya ƙaryar mutum dan uwatar ya aka" "yi ba ka yi kasa bane ka raya daren da gadin mu?"" Moh ya yi shiru ƙirjinsa sai ɗagawa yake. ""Ina tsoron shirun nan naka don ba zai haifar da ɗa mai ido ba, ka tara dafi a cikinka jira kake ka samu inda zaka sauke ƙarin dake damun jikinka ka sarara a kaiwa mai duka lillahi kukan kawai"" sai a lokacin ya juyo da gajiyayyun idanunsa da suka shige ciki duk girman da suke da shi, sun yi wani bala'in ja ya zubawa" Mangal ido """Talk da turanci kenan da hausa na goga maka yi magana sarkin jeji""" """Mangal""" """Yes inji masu jajayen kunnuwa bi ma'ana na'am"" muryar Moh bata fita sosai a lokacin duk wanda ya" "nutsu zai hango wani irin sanyin murya da yake da shi da sauti maraya hayaniya. ""Wacce cuta aka taɓa yi maka a rayuwa wacce ba zaka iya yafewa ba?""" """Kan uban nan, ni ai ka sani a kusurwa kaina ya kulle wanda sukai mini kuma tuni sun girbe abin da suka" "shuka bana yafiya bana cuta bana bari a cutan"" cije baki kawai Moh ya yi yana lumshe idanunsa da sauri ya buɗe su tar saboda yadda yake jin kakari da numfashin fitar ranta yana yi masa amo a kunne, ya mirgina kaɗan ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora akan ɗaya yana girgiza wa ya zubawa zara-zaran yatsun" ƙafarsa idanu tare da rungume hannayensa a ƙirji. """Wai what happened Mai dawa?""" """Ka dai na yi mini turanci don uwarka""" """Ɗan tsinanniya ba, ba uban da ya iya kuma ya san ai duk bama ji shima a Legas ya koya"" cewar Goje" "yana farkawa tare da zama dukkan su babu wanda yake da niyyar miƙewa domin yin sallah. Goje ya kalli Mutallab ya ce ""Yaushe za a kwalo berewar nan ne? Ka yi shiru karfa ka jiƙa masa aiki""" Da sauri Mutallab ya kalli Goje jin sunan daya kira na barewa ya lumshe idanu ya buɗe zuciyarsa na "bugawa sosai sai bai ce komai ba can dai ya miƙe zaune a hankali kuma ya tashi tsaye ya zaga bayan katanga ya daɗe kafin ya dawo wajan Darma ya kalli hannun Mai dawa ya buɗe idanu ya ce ""Bura... Wannan ƙwayar ka shanye to kwarankwasa ka shirya zama mahaukaci, ƙwayar doki ce fa? Wai kashe kanka za ka yi akan wasu ƴanƴan jakuna ka fito musu gaba da gaba mana, a yi komai duk abin da zai faru" "ya jima bai faru ba, ƙarshe dai gidan ɗan kande ne kuma mu ba wai baƙin ta bane""" Mutallab ya tsaya cak a tsakiyar wajan naman jikinsa na motsawa musamman kakkauran ƙirjinsa mai "faɗi sai kawai ya shagiɗe bakinsa gefe kamar zai yi murmushi da sauri ya tsuke fuska zuciyarsa na tuna masa shekarun da suka shige a fusge ya furta ""Sai godiya"" gabaɗaya suka miƙe tsaye suna maimaita" """Sai godiya""" Basu fargaba sai ganin tarin wasu ƴan daba suka gani suna fitowa daga wasu lunguna a ƙalla sun fi su "ashirin ɗauke da gorori wasu wuƙaƙe. ""Dara ta ci gida lallai an raina mu, mu wasu daƙiƙai zasu kawowa" "farmaki har lukanmu?"" Cewar Darma Mangal ya kalle su ya ce ""Kuma suwaye ku yara?""" "Wani daga cikin su ya fito ya tsaya a gaba ya ce ""Sanin sunana ko waye ni bashi da wata fa'ida a gare ka," "da zaka tambayi wanne kalar kisa zan maka zai fi maka, amma saboda gudun tilawa ko tafiya ƙiyama da tunanin wanda ya kashe ka lallai zan goga maka sunan nawa"". Ya zaro wuƙa daga cikin ƙugunsa idanunsa akan Moh da bai ma kalle su ba sama kawai yake kallo yana jin yanayin na yi masa daɗi ya ɗora da ""Uban ƴan daba nake maganin ƙananun yara masu ɓoyewa a saƙo, to cut you short sunana Lauje, ban duƙo dan na saka muku makami ba, na zo na tafi da uban gidan naku salin alin akasin hakan wajan bijire mini zai" "saka an samu kwacewar lissafi dar kenan"" wanda ke kusa da Lauje mai suna Modara ya ce" """Ka saɓo shi a wuya mana sai ka tsaya ɓata yawun da Ubangiji ya halitta a bakinka Oga?""" """Ban zo don rigima ba, bisa umarnin Hon na zo wannan shine""" "Darma ya matsa gefe yana nuna musu Mai dawa Moh kenan ya ce ""Bisimillah gashi nan kuje da shi kuna" "da hannu na san"" Moh ya sake juya musu baya maganganunsu da gaske ciwon kai da zafin zuciya suke" ƙara masa hannunsa kawai yake dunƙulewa yana hura iska sama ko yaushe ya zama sa'annin yara irin su Lauje? """Ji mana""" "Mutallab ya juyo yana gyara tsaiwa idanunsa a birkice Lauje ya dinga kallon Mai dawa, shi bai ya yi" tunanin haka yake ba yaji ana Mai dawa da Mutallab sai ya ji sunan Mutallab kamar na ƙananun yaran "ganin Mutallab cikakken namiji a tsaye mai kakkauran hannu da buɗaɗɗan ƙirji gabaɗaya jikinsa a murɗe yake musamman damtsen hannun ya basar ya ce ""Shige muje""" "Da hannu Mutallab ya yi masa alama da ya zo ya tafi dashi, Lauje ya nufi wajan Mutallab ba tare da sanin" "cewa akwai shafin hannu a jikinsa ba ganin ba wani makamani hannunsa ya saka ya nufe shi. Yana miƙa hannu da sunan kama shi Mutallab ya yi masa wani naushi a gefen ƙirji, nan take Lauje ya fara fari da idanu ƙashin gefen ƙirjinsa ya yi ƙara ya sulale a wajan ba numfashi. Ganin hakan ya saka su Modara ja" baya a tsora ce ya ce """Kut ya bazar dashi ba, wannan mahaukaci ne""" """Bai mutu ba tafiyar zango ƙalilan ya yi kawai ya samu karaya a ƙirji, kar dai ku manta da Mai dawa kuke" "magana masu jeji da namomin jejin da kansu matsalar gajanci kenan kun tari mutumin dake da shafi a hannunsa duka ɗaya ka sume gwara ya saka maka kaifi daya saka hannu, ya zame muku hadda. Yi batu" "waye ya aiko ku?""" """Hon Maɗatai""" """Wani abu ne haka? Me za a yi masa?""" "Modara ya ce ""Bamu sani ba, ya ce yana buƙatar ganinsa shi kaɗai kuma a sirrince""" """To ba zan zo ba""" "Cewar Moh yana cije bakinsa hannunsa har yanzu rawa yake baya son yin kisa, idan ya riƙe wuƙa bai san" "me zai iya yi ba kuma sam. Da mamaki Modara ya ce ""Kasan waye hon Maɗatai kowa? Wallahi taimako" "zai baka shine kawai yake jin tausayin ƴan daba irin mu""" """Ɗan daba irin ka dai, shi Malam Abdullahi ne balle ya yi mini baki, ko Malam Abdullahi can ta matse" "masa"" Modara ya buɗe baki da nufin sake magana ""Kana kira mini sunansa sai na yi maka sabuwar kaciya"" ba shiri ya tsuke bakinsa suka ja Lauje tare da barin wajan cike da takaici." "Safiyyerh na kwance tana bacci tun bayan sallar asuba da ta yi, Dr Hash ya sake ɗaura mata ruwa a" "hankali kuma ya ji tana surutai ƙasa-ƙasa ya kasa kunne da kyau ko zai ji mene take cewa ""Ashraf ka taimaka ka dawo ka faɗa mini ma'anar FS, ka faɗa mini suwaye mutane biyar ɗin da kake magana akai, Ashraf the company is belong to your father,ko a mafarki ne ka faɗa mini ko a fatalwa ne ka zo mini bazan ji tsoro ba, Ashraf i really really need your help, don ka dawo"" Dr Hash ya juya ya kalli daddy da ya" yi ƙasa da kan shi """Daddy akwai damuwa fa, meke faruwa da Fiyya ne? Me take buƙata wajan matacce ne Ashraf zai fito" "daga kabarinsa kuma ya yi mata, daddy Ashraf ya rasu fa ranar da za a ɗaura musu aure da Fiyya me ya sa ba za ta yi tawakakkali ba, me ya sa wai?""" """She loves him so much, tana son Ashraf ne shi ne dalili"" cewar daddy yana sake matsawa tare da zama" "a bakin gadon ya kama hannun Fiyya ya riƙe cikin nasa da kyau ""wannan zafin hannun fa? Her temperature is too high, bana son zazzaɓi a jikin Maama ka yi wani abu Dr Hashim"" Dr Hash ya ce ""Ciwon kanta da bugawar ne ya saka mata zazzaɓi, na yi mata allura zuwa anjima zai sauka ai""" "Maimakon Fiyya ta yi shiru sai ta cigaba da surutan sosai tana furta ""Ni ba Tiger ba ce Tahhb, why are" "you decided to call me Tiger?"" Kamar a gaske kamar kuma yanzu ne ta ji saukar muryarsa a tsakiyar kanta, sautin ya sauka a ƙirjinta ""Saboda ke matar Moh ce Tiger, zama matar Moh is not easy we most fight together halinki irin na tiger ne, matar Moh"" tar da buɗe idanunta a gigice a kuma sauti na ruɗani" "ta ce ""Motar Moh""" Daddy da Dr Hash suka kalli juna jin abin da ta furta kafin su yi magana Safiyyerh ta juyo ta kalli daddy sai "ta yi murmushi mai kyau wanda suka jima basu gani a saman fuskarta ba, ainahin murmushi da kyawun Safiyyerh daya shuɗe ya dawo fil ta riƙe hannun daddy a nutse ta ce ""His voice daddy, muryarsa ce""" """Shi wa?""" """Tahhb"" daddy ya yi murmushi yana shafa sumar kanta ya ce ""ai kuwa na ji nima, ki yi bacci Maama za ki" "samu sauƙi in sha Allah"" ta jinjina masa kai tana riƙe da hannunsa har lokacin ta ce ""In sha Allah daddy," "in sha Allah daddy"" jikinta ya saki ta koma bacci daddy ya sauke numfashi ko samun sukunin karyawa bai yi ba, ya dubi Dr Hash ya sake duban Fiyya ya ce ""Ka yi mata allura kafin ta farka""" """Daddy ka duba Maama tana cikin damuwa ba, baka jin allurar zai saka ta dawo da ɗabi'unta na baya" "daddy yin allurar ba mafita ba musamman ga lafiyarta, tsayin shekaru na daddy har yaushe ne ka duba Safiyyerh don Allah"" miƙewa tsaye daddy ya yi ya ce ""Ka yi hakan Dr Hashim Abdu Marafa, completely tsayin rayuwa haka nake son ganin Safiyyerh"" jinjina kai Dr Hash ya yi sai ya haɗa allurar har guda biyu ya juya bayanta ya caka mata cikin sauri ta ƙanƙame jikinta wani irin azaba da raɗaɗi take ji a duk sanda aka yi mata allurar. Yana yi mata ya fice ba tare daya sake kallon daddy ba. Ya zubawa photonta idanu" yana juya mata baya a hankali ya ce """Ki yafe mini Safiyyerh ki fahimce ni ki fahimci mahaifinki, i am sorry Safiyyerh"" fita ya yi ya rufo ƙofar ya" nufi parlonsa a zaune ya tarar da Ummi tana kallon shi ta ce """Ya jikin nata? Ta farka ne?"" Ya zauna yana numfasawa ""Ta sake yin bacci, ina Aliyu?"" ""Kasan sai ya yi" "niyya yake shigowa"" daddy ya ɗauki wayarsa ya kira number Aliyu yana ɗagawa ya ce Aliyu zo mana ya ajjiye ya kalli Ummi cikin kulawa ya ce" """Ina jin kamar haɗa auren Aliyu da Safiyyerh na yi kuskure ina jin kuma hakan shine mafita, ina jin tsoron" "tambayar da dukkan su za su yi mini wacce bani da amsar su, da gaske bani da wannan amsar tasu Ummi," ba komai Safiyyerh take ganewa tana jin ta isa ta yankewa kanta hukunci ita ba kowa face yarinya mai "wayon gaske da tunani Safiyyerh bata san komai ba ita kawai yarinya ce""" """Ka san dole zaka jira amsar wannan tambayar da kake tsoro, amma sanar dasu auren shine zai fi maka a" "raina ina jin Maama ba zata yi maka gardama ba"" kafin ya ce wani abu Aliyu ya buɗe ƙofar ya shigo da izinin daddy kamar kodayaushe wandon sojoji ne a jijinsa da farar riga tas ya ɗora hula p.cap a kan shi ya zauna kansa a ƙasa yana furta ""barkan ku da safiya""" """Aliyu ya aiki, baka san Maama ba lafiya bane naga baka shigo ba?""" """Na sani"" ya ce kawai a taƙaice yana danna wayarsa ""Ka sani kuma? Shine ba ka yi mata sannu ba me ya" "sa kake haka ne Gadanga, me ya sa kai zuciyarka bata motsawa sai akan Maama meke damun tunaninka baka ɗaukan responsibility ɗinka as a brother""" """Idan bai ɗauki responsibility nasa matsayin yaya ba, yanzu zan ɗauki responsibility Safiyyerh a matsayin" "mijinta"" da wani irin yanayi Aliyu ya juya ya kalli daddy yana son sake tabbatar da abin da ya faɗa masa a" "zuciyarsa wani irin fargaba ne ya wanzu ciki a fili kuma ko gezau ya dai zubawa daddy idanu can ya ce ""kamarya?""" """Da kai da Safiyyerh baku da wata kalma da za ku replying mutum ko responding maganarsa sai kamarya?" "To kamarya dai yadda ka ji ai aikin da ka yi na soja bai saka ka daina jin Hausa ba, har gwara Safiyyerh" "ma"" daddy ya gyara zama Aliyu dai kallon mahaifin nasa kawai yake da wani irin yanayi mai ɗauke da zallar mamaki." """Aliyu ni ban isa na saka dole ba, ban kuma isa na tilasta rayuwarka yin abin da ka yi niyya ko baka so ba," "Aliyu ni dai mahaifinka ne ka saka hakan a zuciyarka. Bani da wanda zai mini wannan rufin asirin kaf family, ka manta da batun Junaid da Awais da kuma Dr, kar ka tambayi mai ya saka na zaɓe ka na ji a raina zaka kula da Safiyyerh ko bayan bana numfashi ko bayan ƙasa ta rufe mini idanu na zaɓi aura maka ita saboda dalili mai ƙarfi, na yarda da ingancinka"" Ya yi shiru Ummi kuma Aliyun take kallo shi kuma yana kallon daddy da duk nutsuwarsa. ""Ranar da Ashraf ya rasu a ranar aka ɗaura maka aure da Safiyyerh, don Allah don girman Allah karka tambayan tsakaninka da Safiyyerh waye ba jinina ba, wannan tambayar shine abu mafi girman laifi a gare ni, ka taimaka ka yi mini alfarma ka riƙe Maama ka" "amshe ta matsayin matarka""" "Captain ya kasa motsi balle magana bai ma san mene zai ce ba. Daddy ya matsa hannunsa ""Don Allah" "Aliyu""" """Ita ta sani?""" """A'a, kai na fara sanarwa Safiyyerh bata da wata matsala ga umarni na"" Aliyu ya sake yin shiru idanunsa" "a ƙasa har ya juya baya ya sake juyawa ya kalli daddy a hankali ya ce ""tell her first, ko bana son ta zan yi ƙoƙarin ganin na fara son Safii in sha Allah""" """Ba zan tambaye ka ni ne ba ɗanka ba ko ita, zan bar tambayar a raina har sanda ka shirya faɗa mana" "gaskiya ni da ita, zan rayuwa da fargabar sanin amsa, da gaske daddy zan so Safii iya tsayin numfashi tunda kai ka zaɓa mini ita""" Daga Ummi har daddy kallon Aliyu suke musamman daddy bai yi tunanin jin wannan amsar ba ya dinga "kallon Aliyu ba ko ƙiftawa ""da gaske zaka so Safiyyerh? Ka san Safiyyan da nake nufi Aliyu?"" Aliyu ya" buɗe idanunsa wanda hula ta ɗan rufe masa su """Safiyyerh Abdu Marafa ko ba ita ba?""" """Ita, zaka so ta ka ce?"" Daddy ya sake faɗa da mamaki" """Bata da Qualities ɗin da za a sota ne?""" """Haka ne tana da shi, na shirya tafiyar ku za ku bar ƙasar nan nan da kwana biyu bana buƙatar ku" "gabaɗaya a yanzu domin nutsuwar zuciya"" Aliyu ya sake duban daddy ya ce" """Kuma? Ka bar tafiyar nan daddy"" sai kuma ya juya gabaɗaya ya kalli Ummi da daddy" """Aliyu soja ne, so i will be with her always""" Yana cewa haka ya fita da ƙyar ya yi jarumtar kai kansa ɗaki ya cire p.cap ɗin kansa ya shiru ba auran ke "damun shi ba, tunani ya fara wa daddy ya haifa tsakanin shi da Safii?" Da yamma Safiyyerh ta ɗakko ƙasa bayan tafiyar Kinal daga ita sai duguwar rigar bacci kanta ba hula "sosai ƙuruciyar nan tata ya bayyana, ta zauna saman kujera ta lumshe idanunta ta zama wata ira tun bayan tashin ta daga bacci jikinta ba ƙwari. I dake kallonta ya ce ""Sannu Manager, ya jikin yanzu?""" """Bayana ke mini ciwo Yaya J, ina jin Dr Hash ya mini allura, bana son allurar nan Yaya J bana jin daɗin ta" "watarana zata kashe ni don Allah ka cewa daddy ya daina sawa Dr ya yi mini"" idanunta ya shiga kawo" "ruwa ta yi lamo da kanta saman hannun kujera. Daman yana bakin ƙofa jin abin da take cewa sai kawai ya juya shi kuma Yaya J ya ce ""Ki yi haƙuri Maama za a daina miki in sha Allah"" ta yi shiru kawai." Dr Hash na zaune a lambun gidan yana waya kasancewar baya da wani aiki a asibiti hutawa yake kashe "wayar ya yi ganin Captain tsaye a kan shi. ""Babban yaya barka da fitowa"" kamar ba zai zauna ba sai kuma" "ya nemi waje ya zauna fuskarsa kamar kodayaushe babu walwala ya jima a haka kana ya ɗaga kai ya kalli Dr Hash ""Akwai wani abu da kake son faɗa ne Captain?""" """Ka daina yi mata allurar da kake mata""" """Me ya sa?""" """Haka dai na ce, idan kuma ka yi zaka sha mamaki"" Dr Hash ya ce ""Wannan kam ai daddy zaka faɗawa" "shine ke bada umarni""" """Wa kake da suna, ka da ka sake ka kuma yi mata idan ba haka ba kuma wallahi zaka kwana ɗakin duhu""" yana cewa haka ya miƙe tare da barin wajan. ***** Hon Maɗatai na zaune gabansa zube da fastocinsa yana magana da wani yaronsa wajan keɓantacce ne kamar lambu haka yake bai san da zuwan mutum ba sai huci da ya ji ta bayansa ya juya da sauri sau kuma ya buɗe idanu waje kafin ya ce """Ya zaka faɗo mini kamar ɓarawo?""" """Da ɗan siyasa da ɓarawo uwa ɗaya ta haife su, waye kai?""" """Baka san waye ni ba a garin kake nufi?""" """Ba'a haife ni da na sanka ba, ka aika akawo ni ina fatan saƙona ya iske ka?""" "Hon Maɗatai ya kalli mutumin gabansa da wani ya ce ""Waƙa ta yi, da ita za'a fara fita yawon kamfel a" "biya a dinga sawa a gidajen rediyo"" ya ciro kuɗi miliyan biyu ya bawa mawaƙin ya ce ""Ga sadakin ka, ina fatan waƙar gaba tafi wannan akwai wata zabiya wai ita Kinal A Awaya"" cikin jin daɗi mawaƙin ya amshi kuɗin ya ce ""Na san Kinal ai ta iya waƙa, ba dai ta shahara sosai bane""" """To sai mu saka ta shahara na ji ta yi Ali wali waƙa, ta yi sosai ta zuba kalamai na fikira harshen nata" "akwai zaƙi dani kuma kawai ya dace a nemo mini ita"" ""zan kawo ta in sha Allah hon, ka yi ka gama ka karya kujerar dambu mai hawa uku Allah Ya kare ka ɗan Majilisa kai ne da nasara Hon"" ""zaka iya tafiya sai na jika""" """Akwai taliya da atamfa da su Omo suger, a tabbata duk local government ɗin da aka je kamfel an basu," "a kuma ɗauki photo da bidiyo za a bawa ƴan social media su baza shi ko'ina. Sai sauran magana na siyan ƙuri'u za ku yi da p.a you can leave Musbah"" Musbah ya miƙe tsaye ya fice sai a lokacin ya juya ya kalli" Moh dake tsaye fuskarsa duk rauni """Nan ai ba jeji bane, ni kuma ba naman jeji bane ba have a seat""" """Bana zama""" """Saboda me?""" """Tsaro, yi magana""" """Shi wanda kakewa aikin baya kula da lafiyarka ne dubi fuskarka Mutallab""" """Ka kira ni da Moh ko Mai dawa sai mu yi magana"" Hon Maɗatai ya jinjina kai ya ce ""Ina son sanar maka" "na haɗa hannu da Dr Abraham, ta yiyuwa ya janye muƙamin da yake nema ƙarƙashin jam'iyyarsa idan haka ta gaske zamu kai Ali wali ƙasa ne, ka haɗa hannu dani lallai za ka ji daɗi""" """Me ka shirya yi wa matasa idan kaci zaɓen?"" Hon Maɗatai ya ɗaga kai ya kalli Moh sai kuma ya yi" murmushi ya ce """Inganta ilimin su, rage musu kuɗin makaranta samar musu da ayyukan yi cusa musu ra'ayin noma da" "muhimmanci yinta""" """Su kuma ƴan daba fa? Wanda kuke anfani da su wajan cimma burikan ku, bayan yaran ku na keɓe kuna" "tattalin tarbiyar su ba ruwansu da sabgar siyasa sai mu ƴaƴan talakawa ƴan wahala kuma ƴan daba mashaya mune ƴan bangar siyasar ku a yau, a gobe a manta damu jibi kuma a neme mu shine ko?"" Hon Maɗatai ya yi murmushi ya ce ""Mutallab kenan, duk wata nasara da muka samu ai daku zamu rabata ni mulki da siyasa tamkar don su ne aka haifan, ina da kyakkyawan tanadi akan ku ba za a bar rayuwarku" "haka ba""" """Me kake buƙata""" """An saka ka kamo Manager ta kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY ko?""" """Wanne kiminin ya faɗa maka?"" Hon Maɗatai ya miƙe tsaye yana zagayawa ya ɗauki fasta ɗinsa ya dinga" "kallon kansa ta ciki can ya ce ""kai yin aikin ne a gabanka, mu ƴan siyasa da idanu ɗaya muke bacci mun" "raba kunnuwanmu ko'ina, ka dai sani a siyasa babu masoyi na dindin haka ma maƙiyi, iya ruwa je fidda kai kowa ya iya allonsa ya ce wanke kuma ni da Ali wali ai sahun qiwa ne ya take na raƙumi kowa da abin" "da yake buƙata, idan ka yi kidnaping yarinyar ka tilasata maka ta saka mini hannu domin na saka hannun" "jari a wannan kamfanin shine abin da nake buƙata"" Jin Mutallab ya yi shiru ya saka ya ce ""Ko baka ji ba?""" """Na ji""" """Mene alaƙar ka da makarantar FGC?""" """Ban sani ba, maganar kuɗin aikinka sai na yi aikin zai sanar. Sai godiya"" yana cewa haka ya bar wajan." Kasancewar Monday ce Safiyyerh ta shirya da wuri zuwa office har yanzu jikinta bai warware ba dole "amma ya zama sai taje. Ba jimawa Md ya shigo bayan sun gaisa fuskarta dai a kame ya shafa kai ya ce ""Manager gari ya ci wuta fa"" idanunta akan wani ducoment tana juya kujera a hankali kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce ""Nawa kake buƙata Md?""" """Ko dubu ɗari biyar ne zan yi maleji""" """Zan saka accouter ya baka miliyan ɗaya"" ya dinga mata godiya sosai ta yi murmushi kawai ta ce ""Mene" "ma'anar FS ni kam Md?"" Tsam ya yi da ransa sai kuma ya ce ""Ba zan iya ba ki wannan amsar ba Safiyyerh, zan dai faɗa miki abin da ba ki sani ba"" ta sake juya kujerar hannunta a haɓarta tana murmushi mai kyau" """Ina ji Md""" """Yatsun da kika gani kwanaki gaskiya ne, ana siyar da ƙodar mutane a wannan kanfanin tare da jarirai," "ana kuma dillacin ƙwayoyi, sauran abun ki yi bincike da kan ki za ki iya dacewa"" yana cewa haka ya fita. Kasa motsi Safiyyerh ta yi numfashinta ya tsaya cak da ƙyar ta miƙe ta ɗauki ruwa ta sha ta dawo saman duguwar kujera ta zauna zufa ta dinga yanko mata a hankali ta ware rolling na kanta ta rufe idanu tana" "kiran sunan Allah. Knocking aka yi da ƙyar ta ce ""In""" "Ta buɗe idanu da mamakin ganin wanda ya shigo, ya ƙarasu cikin office ɗin ""Ba dole ki buɗe idanu ba" "Safiyyerh, idanunki kenan?"" Ta yi murmushi tana gyara zamanta" """I. Qasim kai ne""" """Ni ne Safiyyerh""" "Ya nemi waje ya gaisa ta ce ""Yaushe gari kuma?"" Ya yi murmushi ya ce ""Zama likita a garin nan is not" "easy Fiyya, ya batun ciwon kan ki kowa?"" Ta ce" """Yana nan""" """Ayya sorry, akwai maganganu da zan ba ki in sha Allah da allura, gudun kar ki dinga sha ba daidai ba zan" "dinga zuwa dasu kina sha a gabana na yi miki allurar, za ki samu sauƙi in sha Allah""" """Thank you I. Qasim na gode sosai"" wayarsa aka kira ya kalleta sai kuma ya miƙe tsaye tare da yi mata" alama da yana zuwa. Ta bishi da idanu har ya fita. ***** "Safiyyerh ta dinga kallon daddy kamar mahaukaciya saboda rashin fahimta ta ce ""Daddy, aure da Yaya" "Aliyu ka ce dani kuma Safiyyerh, mu duka ƴaƴanka ne fa"" hawaye ya fara suntiri a saman fuskarta ta saka hannunta ta toshe kunnuwata tana girgiza kanta gabaɗaya ta jiƙa hijabin da ta yi sallah da shi da hawaye ""ruɗanin da kake sani a kullum yana shirin haukatar dani daddy, ba auren ne ban yi na'am da shi ba na" "kasa fahimta ne dani da Captain waye wanda ka haifa waye ba ɗanka ba""" """Ku duka yarana ne Maama, idan har kin yarda ni uba ne a gare ki kuma kina so na da ƙaunar farincikina" "ki amince da auren Maama, ba zan taɓa cutar dake ba ni ubana ne, uban ƙwarai kuma yana zaɓawa yaransa abun ƙwarai ne ki yi mini biyayya Safiyyerh, kin ji ko?""" """Na amince daddy zan amince da abin da ya fi wannan ma, Allah Ya sa shine mafi alheri a gare ni"" ta faɗa" "tana rushewa da kuka da sauri kuma ta yi waje ta nufi ɗakinta ta faɗa saman gado ta dinga wani irin kunjin kukan kamar ranta zai fita wai wanne irin abu ne haka? Ta shiga uku meke faruwa aure fa, auren ma da Captain innalillahi wa'inna ilaihirraji'un addu'a take Allah ya yafe mata komai ta fahimta da ƙyar" bacci ya ɗauke ta ko abinci bata ci ba. Cikin dare ta farka ganinta ta yi rufe da bargo ta yi saurin buɗe ido don bata san kwanciya a duhu gashi an kashe mata hasken ɗakin babu mamaki Yaya J ne. Gani ta yi "wajan ɗaya da rabi ta miƙe ta ɗauki ɗan makullin mota da wayarta ta saka hijabi har ƙasa, ƙofa ta buɗe ta sauka downstairs ba kowa ta buɗe ƙofa ta fita mota ta shiga mai gadi ya buɗe mata cikin sauri ta nufi kamfani gari shiru sai hasken fitilo na titi ta dinga duban hanya ba wanda ke biye da ita a haka ta isa kamfanin ta ajjiye motar a waje, ciki ta shiga wajan mai gadi sun jima suna magana ya ce ""Ana shigo da mata cikin dare ana kuma fita da su, na yi bincike abin da ya saka ke iya ɓangaren abinci kika sani to" "akwai asibiti a cikin wannan kamfanin"" ta ce ""Ka ɗauki number motar ko haddacewa?""" """A'a ranki ya daɗe""" """To shikenan na gode Baba, ga wannan"" ta ɗauki kuɗi ta bashi a cikin aljihun rigarta. Tana ƙoƙarin buɗe" "gate ɗin kamfanin ta fita kawai ta ji ƙarar dingowar mutane, ta juya da sauri suka haɗa idanu da Darma" da kuma Goje da Mangal wani irin mummunan faduwar gaba ne ya sameta lokacin da idanunta ya shige cikin nasa shi bai kai ga dingowar ba yana zaune saman katangar shima ɗin ita yake kallo babu ƙiftawa... MUTALLAB PAID BOOK ne a jerin littafan bright pens. We're still on free pages kar ki bari a yi bake. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 via WhatsApp only. DOMIN INGANTA NONO Assalama alaikum Hajiya muna da ingantaccen maganin gyaran nono wadda ya amsa sunansa magani Maganinmu ingantaccen maganine da yake tada jijiyon nonon da suka saki y'ar uwa breast dinki ko yakai silifas saboda kwanciya kikai amfani dashi in sha Allah zakiga amfaninshi acikin 1week maganinmu powder ne yana ciko da breast y gyarasu bashi da illa ajikin mutum munyi amfani da saiwoyi da magunguna gargajiya domin gyaran breast 08063114606 ina garin kano karki sanya y'ar uwa nono yana karawa mace martaba a gurin mai gida maganinmu kowa zai iya sha wadda zatai yaye ko gyara budurwa duk zasu iya sha breast dinki ya ciko yayi bull -bull "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 11 *Bright pens.. 2nd batch* "Ya ƙura mata idanu yana daga zaune saman katangar a hankali yake girgiza ƙafarsa, fuskarsa rufe da" "baƙin ƙyalle a lokacin duniyar ya ji tana masa daɗi yana jinsa kamar a cikin jirgi ana juyawa dashi, shi ya sa yaƙi sakkowa ƙasa daga katangar, shi kansa bai san wacce irin ƙwaya Mangal ya kawo masa ba. Fiyya ma shi take kallo ganin shi kaɗai ne ya rufe fuskarsa Goje da Darma da Mangal suka zagaye ta, ta juya ta" kalli securityn da yake on duty ranar ta nuna masa Goje """Su kuma waɗannan fa security?"" Kai tsaye ya bata amsa da ""Ban san su ba, amma Hajiya akwai hatsari" "bamu san me suka zo nema ba"" Goje ya matsa kusa da ita yana kallon ta" """Mai dawa wannan ce ƙuruciyar? A hotun kamar bata kai haka girma ba, ƴar firit da ita kamar benu, nan" "kuma an ci kuɗin jama'a an sha madara da milo an yi ɓulɓul"" sai ƙarewa Fiyya kallo yake ita kuma ta yi tsaye tana jin yadda warin wiwi ke dukan hancinta kamar za ta yi amai amma taƙi matasa saboda taurin kai irin na Safiyyerh Abdu Marafa da rashin tsoro. Tsaki ta yi kawai ƙasan zuciyarta kuma tsoro ne fal ga" ƙirjinta dake bugawa kamar zai fito waje sai buɗe manyan idanu waje take yi. """And what is my business with you? Me kuke nema a wannan kamfanin kun zo sai warin ganye kuke" "mini"" Mutallab ya sake buɗe manyan idanunsa jin sautin muryarta zaƙwai a cikin kansa ya kalli bakinta dake motsawa cike da masifa duhun dare ne amma kamfanin haske tar tar ko'ina. Mangal ya lailayo ashar ya dannawa Safiyyerh ""ke dan ƙaniyarki mune muke warin ganyen, su waye sila idan baku ba, ƴar" "wahalar yarinya idan ban bawa tiger namanki ɗanye ya cinye ba""" "Safiyyerh ta juya ta kalli tiger daya hauro ya zauna kusa da Moh, yana zaro harshe waje ta nuna karan da" "hannu ta ce ""abin da ya fi namana ɗanye, banda rainin hankali jikin nawa zaka ɗauka ka bawa shegen karan naku, idan kuɗi kuke buƙata na baku don nasa na yin caji kuke nema, stupid"" Goje ya juya ya kalli" "Mai dawa ya ce ""ba zamu rage wa yarinyar nan tsayin harshe ba kuwa? Kauɗinta ya yi over, ka je ka" "zauna matsalar idan ka sha wannan ƙwayar baka gane komai yanzu babu mamaki jinka kake a saudia""" Moh ya lumshe idanunsa ya sake buɗe su a kan Fiyya duk motsin da take yi a kan idanunsa sai dai ba "wani fahimta yake ba muryarsa a cunkushe mai ban tsoro ya shafa kan tiger ya ce ""shiit""" Tiger ya diro shima ya diro ya tsaya a kan ƙafafuwansa hannunsa ɗaya yana murza gashin kansa wanda ya zama wani iri ba kyan gani na shegun shahararrun ƴan daba ɗin nan. """Mai jeji ƙirit ka ankare ba lokaci ka ɗaƙkota a kafaɗa mu fece kafin kwalawa su kawo kai dan akwai" "kimini a nan wancan mai fararen kayan"" ya nuna securityn wajan wanda shi kaɗai ne kawai ya rage. Safiyyerh ta ja baya tana juya idanunta ta ce ""ban gane ya saɓo ni kafaɗa ba kamar wata ƴar iska ko mara gata, kai naga alamar kai ne shugabansu ko? To wallahi ba wuƙa ba ko bindiga ce bana tsoro kana taɓa ni sai na raba ai an ce ba wani ƙwari ne daku ba"" ta ƙare maganar tana kallon cikin idanun Mutallab" wanda tun ɗazo shi take kallo shi kuma yaƙi furta komai. """Ki iya harshenki ƴar kanzagi ko na fitar miki da jini yanzu na shata miki bille a wannan fuskar kamar" "gwada"" juyawa ta yi ta ce ""Baba wai where are the securities? Where are the rest ka kira su yanzu"" kafin" "baban ya motsa Mangal ya saka ƙafa ya kwarfe shi zuwa ƙasa, ya sake saka ƙafa ya danne masa baki. Darma ya zaro wuƙa ya ce ""Ke fitsararriya ce ko? Ba wata uwar muke nema ba ke muka zo ɗauka, don ke muka cikin wannan kamfanin ke za mu yi kidnaping yanzu kin fahimta kin gane ko, ki shige salin alin ko" "na ɗauke ki yanzu na haura dake wallahi""" Fiyya ta buɗe idanu tana kallon wuƙar dashi kansa Darma ɗin ta yi murmushi zuciyarta kuma bugawa "tsoro ya shige ta, ƙoƙarin danna recoding take a wayarta hannunta ya shiga rawa ta dake a ƙasan zuciyarta tana kiran sunan Allah da ƙyar ta furta ""kidnaping kuma ni, ni Safiyyerh Abdu Marafa za ku sace," "ni Safiyyerh matar soja guda kuna hauka ne ko kuna tunanin mijina zai bari hakan ta kasance?""" "Jin furucin Safiyyerh ya saka Moh sake kallonta da sauri yana hana zuciyarsa abin da yake ji, haka kawai" "ya dinga jin tafasar zuciya ya nufi wajan Safiyyerh jikinsa na rawa idanunsa suka fito waje kamar zasu faɗo da muryar mai ban tsoro mafi muni ba muryar ba ita kanta fuskarsa abar tsoro ce tsaf mutum zai dinga mafarkin ta. Hannunsa riƙe da wuƙa yana kallon cikin idanunta da kyau dab da ita ya ce ""Ba mijinki ba ko ubanki Abdu Marafa aka bani umarnin daƙƙowa ko kashewa sai na yi balle ke"" ya cije bakinsa ya feshi ya cilla mata ƙatuwar baƙar kunama ta shige ƙirjinta kai tsaye, zufa ta dinga yanko mata saboda" "tsananin azaba ta kasa ihu ko kuka ga warin da yake yi yana neman kashe ta, idanunta ya juye ya yi ja ta" "zuba masa idanu tana kallon fuskarsa data yaye,ta miƙa hannu da nufin shafo fuskarsa ta ji ya caka mata" "wuƙar a gefen cikinta ta yi wata ƙara tana buɗe idanu duk yadda jikinta ke rawa ga jini na zuba mai hanata sake kai hannunta ta shafo fuskarsa ba, daidai nan ya yunƙura zai saɓata a kafaɗa suka ji shigowar motoci na jami'an tsaro, bai niyyar barinta ba yadda Goje ke jan shi da ƙarfi ya saka kawai ya" sake ta a wajan yana furta “Mutallab” Ɗaya bayan ɗaya suka kama katangar suka haure daman kuma kaf kamfanin ita ce ƙaramar katanga wacce babu kwalabe jikinta. Securities kala biyu ne dana fararen kaya da masu uniform sai shi da yake sanye da wando three qauter "da farin takalmi da riga baƙa ko p.cap ɗin kansa babu, ya nufe ta sauran suka nufi wajan baba suka fara ɗaukan statement ""Baba kwantar da hankalinka babu abin da zai sameka in sha Allah, bayan waɗannan ƴan daban da suka zo, an bamu tabbacin a daidai yanzu Scorpion ma yana wajan nan ko kuma ya zo"" a hankali Aliyu ya juya ya kalli baban jin tambayar da ake masa, sai kuma ya ɗauke kai ya saka hannu ya ɗauki Fiyya zuwa cikin mota bayan ya kwantar da ita ya tsaya yana kallon wanda ke ɗaya motar a tsaye" "da yake ce masa ""Ya akai kuka barta ta fito cikin dare haka? Macace ita fa""" """Sir ƙuruciya, thanks for the call""" """Anything for you Captain Aliyu"" suka shiga mota duk suka bar wajan ya rage sai jami'an F.i.d kawai da" suke tambayar baba. "Su Goje cikin kwalabati suka shige suka ɓoye suna zare idanu da muzurai a hankali ya ce ""Akwai matsala" "jami'an tsaro ne fal yasin, baka dai bar sheda ba kuma me ya saka ka caka mata wuƙa idan ta mutu fa?""" Moh ya yi shiru can ya ce """Ba zata mutu ba""" """A ciki ka soka mata wuƙar fa? Baka kalli yadda jini ke zuba bane da zaka ce wai ba zata mutu ba?"" Kai" "tsaye Moh ya ce ""ba zata mutu ba""" """A buge kake shi ya sa, askira ka caka mata fa na ɗauka tsoratar da ita kawai za ta yi""" "A firgice ya kalli Goje idanunsa kamar za su faɗo ""Goje, idan ka sake maimaita mini cewa na saka mata" "wuƙa zan maka jahilci yanzu wallahi zan iya kashe ka""" """Kashe ni mana daman ai daba babu wata amana a ciki dole na faɗa, ɗaƙkota aka ce kawai ka yi ba kashe" "ta ba"" Mutallab ya wani juya cikin zafin nama ya damƙo wuyan Goje cikin sauri Darma ya shiga tsakiya ya ce ""Sai godiya kar a yi haka akwai amana, kai Goje ka iya bakinka idan ba farkawa kake so ka yi ka ganka a ƙiyama ba"" Moh ya cije bakinsa kansa na wani irin sara masa yana girgiza kansa ya kalli sama ""duk sanda na sake ganinta sai na kashe ta don uwarka"" duk sukai masa shiru sun daɗe a wajan kafin jami'an tsaron su bar wajan suka fito tare da barin wajan suma kallo ɗaya za ka yi wa Moh ka ɗauke kai saboda" yadda yake huci ya fiddo da ƙarin jikinsa neman inda zai sauke kawai yake. The following days. "I. Qasim ya ce ""Tunda ta bar I.c.u ai Allahamdulilah, she will soon recovering""" """Dr Qasim ba dai abin ku kuke mana na likitoci ba, ya jikin Maama don Allah ita ce kawai last hope ɗina""" "Dr Qasim ya yi murmushi ya ce ""Safiyyerh zata ji sauƙi in sha Allah, ba'a caka mata wuƙar inda za ta yi" "mata illa ba ta zubar da jini sosai ne sai kuma zuriyarta data ninka gudun da take yi, ka yi mata addu'a""" """Shikenan Allah Ya bawa Maama lafiya,zan iya shiga ai kwana biyu ba'a barin mu shiga sai na ji kamar" "har yanzu bata dawo hayyacinta ba"" I. Qasim ya girgiza kai ya ce ""Daddy kana son Safiyyerh da yawa, shiga ka ganta"" har bakin room ɗin da take ciki ya shiga ya shiga sanye da kayan daya dace a shiga aga mara lafiya. I. Qasim ya juya ya fita daddy ya zubawa Safiyyerh idanu tana ƙwace ta sake yin fari a barka da farar mace ta ɗan faɗa an ja mata rigar marasa lafiya zuwa saman ƙirjinta duk da baya kaya a jikin sai iya rigar an buɗe wajan ciwon da akai mata aiki a wajan ya zuba mata idanu ya matsa a hankali yana kama hannunta addu'a ya shiga yi mata sosai ta samu sauƙi zuciyarsa duk babu daɗi idan ya rasa Maama" bai san yaya zai yi ba kuma. """Allah Ya baki lafiya Maama, don Allah ki rage wa kan ki fitina da zaƙewa cikin wasu al'amuran kalli" "yadda za ki saka rayuwarki ta lalace, Safiyyerh ban shirya ba ban shirya ba Safiyyerh"" ya damƙe hannunta" yaga bakinta na motsawa amma sam baya jin me take cewa. Ta shi ya yi ya fita yana sake yi mata addu'a a ransa na samun sauƙi da rangwame. "Bayan ya fito waya ya saka ya kira Aliyu yana ɗagawa ya ce ""Aliyu kana ina ne, an fito ita daga i.c.u amma" "babu kai a wajan bana son haka fa, da baya da yanzu ba ɗaya bane matsayin Safiyyerh ya jima da sauyawa""" """Allah Ya sauwaƙe""" Kawai Aliyu ya furta ta cikin wayar daga nan ya yi shiru ran daddy ya sake ɓaci yana jin kamar ya yi "kuskure na aurawa Aliyu Safiyyerh na damƙa masa dukkan ragamar rayuwarta da tunanin zai kula da lamarin Safiyyerh amma ba lallai hakan ta kasance ba, sosai abubuwa da yawa ke damun zuciyarsa yana hana shi sukuni tare da rashin isasshen bacci, idan Safiyyerh ta tare a gidan mijinta dole ne ya amshi" responsibility da Ubangiji ya ɗora masa na mijinta. "Ummi na kallon daddy da jajayen idanunta ta ce ""Ina ta zuba idanu rayuwar yarinyarta na neman" "lalacewa, ka yi abubuwa da yawa Professor na ja baki na yi shiru da tunanin duk abin da ka yi daidai ne, zuciyata ba zata ɗauka ba Safiyyerh gabaɗaya nawa take ni kawai ta haƙura da aikin wannan Companyn da bana gane masa ai shekarunta bai kai ya kawo ba, ban shirya rasata ba"" daddy ya yi shiru yana kallon" yadda Ummi ke kuka. """Ki tashi muje dare na yi"" da sauri ta kalle shi tana share hawaye ta ce" """Kuma ban gane muje ba zuwa ina?""" """Ai kin san majinyata basa kwana a wannan hospital ɗin, patient ne kawai yake da alhakin kwana"" tun" "kafin ya kammala magana take girgiza masa kai ""i don't think zan iya barin wannan asibitin da Safiyyerh ita kaɗai, ni bana ma ganewa irin haka ka yi musu magana ko a nan zan iya kwana I'll manage"" Daddy ya" "yi gaba yana furta ""Kar na sake maimaita miki"" dole ta miƙe bayan ta sake leƙa Fiyya ta yi waje." "Kafin a rufe shigowar masu ziyara Yaya J ya daɗe zaune gaban Fiyya yana kallon fuskarta, da kwanakin" "baya ne zai riƙe hannunta cikin nasa yana ta mata sannu da addu'a yanzu kallon ta kawai ya kasa koda yin addu'ar ma, can ya miƙe ya fice haka Awais da Dr Hash duk suka shigo basu da tabbacin bacci take ko farkowa ne ba ta yi ba. Wajajen 2 na dare ya buɗe ƙofar ya shigo bayan I. Qasim ya bashi damar hakan daman aikin kwana zai yi idanunsa a kanta har ya shigo ya rufe ƙofar a hankali ya tsaya gabanta" hannunsa biyun zube cikin aljihu ya ɗauki minti a ƙalla ashirin kafin ya ƙarasa ya zauna bakin gadon har yanzu bacci take ya dubi hannun da ruwa yake shiga ya dubi ɗaya hannun da jini ke shiga a hankali ya kama hannun drip ɗin da yake ɗan mitsi-mitsi ya riƙe cikin nasa a hankali yake murza yatsunta can ya ji ta riƙe hannunsa ya ɗaga kai yaga tana jujjuya kanta sai a lokacin ya lura da sauyin ƙarar da na'urar ke yi. Safiyyerh tana buɗe idanu ta rufe saboda wani fau ɗin haske daya shige mata ciki sai kuma hawaye ya "fara bin idanunta ya ɗan sunkuya yana kallon fuskarta. Ta sake buɗe ido ta kalle shi ta dudduba taga ba kowa ta rufe idon still ta buɗe har lokacin jujjuya kanta take yi ""Yaya"" ya yi mata shiru ya sake cewa" """Me na yi musu?"" Still shiru ya yi mata ta buɗe idanu ta kalle sai ta fashe da kuka sosai ƙirjinta na" ɗagawa ya damƙe hannunta """Yaya""" """Safii..."" Ya kira sunanta a hankali ta ce ""Kai na zai cire ƙirjina ciwo cikina ciwo yaya mutuwa zan yi""" """Allah Ya yi miki Rahma"" sai kuma ya matsa dab da kan nata ta saka hannu ta riƙe nashi ta yi shiru a" "hankali ta sake cewa ""Captain""" """Manager""" """Na ce musu mijina soja ne, wai ko sojan zasu kashe balle ni"" ta yi shiru ta sake cewa ""Ka riƙe mini kai na" "ciwo yake mini sosai na shiga uku daddy wayyo"" maimakon ya riƙe kan nata sai ya ɗora goshinsa saman" "nata, ta buɗe idanu ta kalli fuskar Captain kamar zau haɗe da data a nutse ya ce ""sun kashe kin?"" Ta girgiza kai" """Me ya sa?""" """Ban sani ba"" ya ɗan murza mata goshinsa yana kallon cikin idanunta ya ce" """Saboda ke matar soja ce"" ta yi shiru kawai tana kallon shi can ya matsa yana sauka ya zauna saman" kujera. "Washegari da sassafe ƴan sanda suka shigo room ɗin lokacin tana zaune ta ɗan jingina da jikin gado," statement na abin da ya faru suke tambaya. Sp Ghali ya kalli Safiyyerh data sunkuyar da kanta ƙasa ya ce """Da suka zo sun faɗa miki abin da suke buƙata?"" Ta girgiza musu kai." """Za ki iya gane wani daga cikin su? Suna ko kammani?"" Ta ɗago ta kalli Sp Ghali dake tsaye ta ce ""Idan na" "gane kamannin sai me za'a yi to?"" ""Zamu kira a zana mana fuskar wanda kika gane ne""" """To ban gane ba""" "Duk suka tsora mata idanu musamman daddy ta buɗe idanunta itama ta ce ""Kamarya? To na gane ne?""" "Daddy ya ce ""Maama wa kija ji ya ce wani abu?""" Sp Ghali ya dinga kallon Safiyyerh yana jin wani irin abu a ransa na motsa masa sai ya yi murmushi ya ce """dear kin ce basu nemi komai ba, ba wanda kika gane ba suna amma haka kawai sai su caka miki wuƙa" "think Safiyyerh"" sarai Safiyyerh ta tuna sunan da ta ji ya ambata na Mutallab sai ta yi shiru a hankali kuma ta ce" """Sp kasan matsalar da ƙasar nan take ciki musamman Jiharmu akan ƙwacan waya, wayata zasu ƙwace ni" "kuma na hana saboda ina da abubuwa a ciki shine sukai mini haka"" ya jinjina kai ya ce ""Haka ne dear za mu yi bincike zan gano kowaye za mu hukunta shi ƙarƙashin hukuma bisa kundin da aka wanzar, get well soon dear"" ya sake faɗa yana murmushi kan ta dai a ƙasa yake. Sallama sukai dasu daddy suka tafi." Captain na zaune ko tari bai yi ba wayarsa kawai yake dannawa can ya miƙe ya fita daddy ya bisa da kallo haka Yaya J ganin ko sannu bai yi Fiyya ba daman bai jima da zuwa ba. Eng Ali wali ya dinga kaiwa yana kawowa ransa duka a ɓace ya kalli Mai dawa ya ce """Yanzu daka kashe ta fa? Wai me kake nufi da wannan abin da ka yi ne Mutallab?""" """Ka dai na yi mini ihu kamar Malam Abdullahi"" Ali wali ya jinjina kai kawai ya ce ""Kasan ka raina ya ɓaci" "kake cewa haka? Ya zan aike ka ka yi sato yarinya kuma ka caka mata wuƙa salon ka ɓata mini aiki da sanyin safe ake kama fara ba mai dawa""" """To na fasa""" "Ali wali ya buɗe idanu ya ce ""Meka fasa ɗin? Ba dai ɗakko yarinyar ba kake nufi?"" A taƙaice ya ce ""Shi""" """Haba uban mafarauta, kai baka san wasa ba kai kamar ɗa kake a wajena fa"" sai a lokacin Moh ya buɗe" "idanu ya kalli Ali wali yanzu dai normal yake ba'a buge ba ""baka haifan ba, san da aka haifan baka da labari"" ya yi fito yana miƙar da ƙafa ya ce ""To ka kira ɗan naka ya yi maka aikin, mu fa kuke sawa a wahala har a yi zaɓe aci a cinye ka hau kujerar ba lallai yaranka suna ƙasar ba, ba'a rainawa Moh hankali" "ka bar mu matsayin ƴan daban kawai"" Ali wali ya ce" """Ya batun yarinyar?""" """Na ji"" ya ce yana miƙewa tsaye har zai shige ya dawo ya ɗauki bandir ɗin kuɗi ƴan dubu-dubu ya watsa" "cikin aljihu. Sautin daya ji kamar gurnani kamar kuka kuma ya sa ya nufi ƙofar da yaje jin hakan ya murɗa handle zai buɗe cikin sauri Eng Ali wali ya riga shi ya ce ""Haba Mutallab idan iyalina ne a ciki fa?"" Moh ya zubawa Ali wali ido ya kalli ƙofar sai kawai ya fice yabar wajan. ""Ɗan wahalar yaro ɗan jaraba Allah Ya" "nufa na lashe kujerar ganina sai ya yi maka wahala""" "Hon Maɗatai yana zaune ya kalli Sp Ghali ya ce ""Ka lemo record ɗin nasa?""" """Na samu Hon amma cin dai amana ne irin namu na jami'an tsaro amma fidda record ɗin wani criminal" "ya saɓawa kudin tsarin ƙasa"" Hon Maɗatai ya ce ""Waye Mutallab?"" Sp Ghali ya ce ""Nothing serious about him hon, shekaru uku da suka shige an kama shi da laifin kashe matarsa ranar da aka kai masa ita matsayin amarya, kafin nan yana da record na zama gidan yari na watanni sai kuma taɓa guduwa Legas," "a baya kuma kafin hakan shi mafarauci ne ma'abocin shiga jeji ya yi farauta""" """Hon akwai matsala ne? Na ga ka yi shiru?""" """Batun Scorpion ba, case ɗin yarinyar nan Manager a ranar ance shima Scorpion ya je wajan"" Sp Ghali ya" "ce ""Hon Scorpion da ƴan siyasa irin ku yake da matsala fa, ko mutumin daya kashe last yana da za hujjar kisan mune dai bamu sani ba, waye Scorpion ba wanda ya sani jami'an mu na neman shi haka F.i.d Federal investigation department wallahi suna kama shi wannan kisa ne nan take ko su yi masa allurar hauka"" ""Al'amarin Scorpion ya yi kama da ɗaukan fansa fa, za mu zuba ido ya kashe mu ne? Ku hanzarta" "nemo ko waye Sp Ghali""" """In sha Allah Hon""" "Aliyu na zaune saman kujera daddy ya ce ""Kaji ai ko?"" Ya jinjina kai kawai ""Zuwa dare sai ka ɗauke ta ku" "tafi can part ɗin dake gidan daman tuni an zuba komai empty dai yake to ɗazo an kaiwa Safiyyerh kayanta, Aliyu Safiyyerh amana ce idan ka ci amana ba zan yafe maka ba, na yi haƙuri na rabu da kai amma na so kun bar ƙasar gabaɗaya"" addu'a daddy ya yi musu sosai duk da Fiyya bata wajan. Aliyu ya tashi ya fita. A daren ranar ƴan jarida suka shigo saboda hirar da za su da daddy. Sosai aka yi hirar inda yake cewa. ""har kullum ni Professor Abdu Marafa bana goyan mutumin da bashi da wata nagarta wanda baya duba rayuwar yaranmu matsa wanda kuma zuwa gaba sune zasu gaje mu, duk wanda ya buƙaci ku zaɓe shi ku fara duba nagartar shi waye shi, bane background na rayuwarsa waye shi tun farko? kar a yi amfani da talauci da rashin iliminku a saka ku yi zaɓan tumun dare a wannan lokacin matasa yana da kyau ku yi gangami ku magana da murya ku saka iyaye na gida ƙanne da yan'uwa su zaɓi cancanta, wannan masu gamu taliya gishiri ko masu siyan ƙuri'ar mu basu ne wanda suka dace ba, ƙuri'armu ita ce ƴa'cinmu kana siyarwa baka da damar yin zaɓe ku kalli yadda ake mayar da ƙananan yaran ƴan daba masu bangar siyasa ana basu ƙwaya suna aikata zunubi suna kai kansu inda za'a kashe su, ku faɗa mini ko sau kun taɓa ganin ɗan wani daga cikin ƴan takarkarun nan? no! Sai yaran talakawa wanda basu da ilimi ko basu da sana'a sai a yi amfani da wannan damar a janyo su a kurɓata musu rayuwa a ƙarshe kuma ko gidan yari yaro ya tafi wallahi sai dai iyayensa su yi fafutuka duk da cewa har da laifin wasu iyayen a lalacewar yaran, matasa ku haɗa ƙungiya da za ku dinga taimakon juna kar ku yadda da mulkin" "kama karya kuna kallon shekaru huɗu da suka shige yadda zaɓe ya kasance""" """Professor Abdu Marafa kenan a yayin da yake bawa matasa shawara akan su miƙe tsaye domin" "ƙwatuwa jiha ƴan'cinta. Professor mai ya sa duk maganar da zaka yi akan matasa ne? Da batun shaye- shaye ko daba?"" Daddy ya rantse idanunsa yana jin zuciyarsa na yi masa zafi can ya ce" """Ɗan jarida kenan baki abin magana, saboda matasa sune yau, sune gobe haka jibi matasa sune cigaban" "ƙasan idan har aka tsaya musu aka fitar da iri mai kyau, shaye-shaye kuma. ,"" sai kawai ya yi shiru." "Yakasai ya ce ""Gabaɗaya abin da zamu iya naɗa kenan a wannan satin, zamu cigaba da bibiyar professor" Abdu Marafa domin ganin haƙar tasa zata cimma ruwa ko yaya ne? Ni Khalid A Yakasai nake cewa a huta "lafiya""" **** Numfashi Mutallab ke fitarwa a hankali jikinsa duk yanka saboda faɗan da suka yi da ƴan cikin gari bai "san adadin mutanen daya sara ya fitarwa da jini ba, bashi da tabbacin ko bai yi kisa bama rabin fuskarsa duk yanka ne wani wajan har ya zame masa tabo. Goje shima cikinsa rauni ne da ƙyar yake fidda numfashi a hankali ya ce ""Sun kashe Darma fa, ni ban ɗauka haka zuwa kamfel ɗin yake ba, wallahi sun" "kashe Darma na yi ƙoƙarin kai masa ɗauki amma ta kai nake""" """Goje""" """Na'am, Sarki""" """Nemi maɓoya"" ya ce ""Idan na ɓoye kai fa? Naga ba zaka iya tashi ba gwara ni ma kai ma da tuni sun kai" "ka kushewa, gashi wannan ɗan jakar Mangal ban san inda yake ba, balle a jira Ali wali a faɗa masa koda taimakon da zai mana""" """Wai baka jina idan ba ƙiyama kake shirin zuwa ba ka tashi ka face Goje"" da sauri Goje ya miƙe ya yi" "kwana saboda ƙarar motar kwalawa da ya ji, Moh ya saka hannunsa a aljihu ya danna laya tuni ya ɓace a wajan." Abbasa ta dinga kallon Mutallab kamar baya numfashi ta girgiza kawai ta kalli mai yi masa treatment ɗin "bayan ya gama ya miƙe ta ce ""Sannu da ƙoƙari"" ya jinjina mata kai ya fice kawai. Ta yi shiru tana sake kallon Ɗan'malam." "Kamar yadda daddy ya buƙata Safiyyerh ta tare cikin part guda da yake gidan daga can baya, ita dai da to" "kawai take binsa sai kuma idanu ta yarda ba zai zaɓa mata abin da bai dace da rayuwarta ba, ta amince zata zauna da Captain Aliyu zata koyi son shi. Cikin sauri yake gudanar da komai kamar mai tsoran wani abu. A harabar gidan Aliyu na tsaye yana kallon Awais da yake cewa ""Yaya ban gane tambayar da kake" "mini ba""" """Ya sunanka ma?""" "Da mamaki Awais ya ce ""Ikon Allah Yaya ni fa ƙaninka ne tsayin shekaru baka san sunana ba?"" Aliyu ya" "haɗe fuska ba wasa ya ce ""Kuma dole akai na haddace, seriously bana iya tunawa""" """To kai ne Baba captain Aliyu sai Junaid sai Dr Hash sai ni Awais sai Maama"" ""Ok, shi likitan wanne allura" "ya ke yi mata ban damu na san ba a baya yanzu ina so""" """Wai Dr Hash da ya kewa Fiyya? Ban sani ba gaskiya Yaya why not ka tambaye shi?"" Wata tsawa ya" "dakawa Awais yana cewa ""Get lost mumu"" fita ya yi daga cikin gidan gabaɗaya." Har ɗaya saura Safiyyerh na kwance a bedroom ta yi shiru tana jin ciwon na yi mata zafi ta yi kuka sosai "na rashin sanin dalili har bacci ya ɗauke ta. Cikin bacci ta ji an buɗe ƙofar an shigo ta yi saurin rufe idanu yana sanye da kayan bacci farare ya ƙarasu ya duba magungunan yaga ko ɗaya bata sha ba, ya ƙarasa bakin gadon ya zauna shi gabadaya ya manta cikakken sunanta na gaskiya rashin sanin ne zai ce kawai ya saka hannu ya janyo ƙafafuwanta zuwa ƙasa ta matso dab da shi da sauri ta buɗe idanu, suna haɗa idanu" ta tura baki tana juya fuska """Zan saka bindiga na harbe ki a iska kina juyawa"" ta kalle shi ta ce ""To yaya ciwona ka fama mini"" kallon" "da yake mata ya saka ta miƙe zaune ""kin accepting auren?"" Ta jinjina kai ta ce ""Na yi kamar yadda ka yi na san daddy yana da nasa dalilin damuwata ɗaya na rashin sanin gaskiyar ni ce ƴar daddy ko kai, amma aure tun kafin na zo duniya Allah Ya rubuta wanda zai zamo miji gare ni ina da sani daidai gwargwado" "zan zauna ƙarƙashinka duk da baka so na, ko kana so na?"" Ya girgiza mata kai alamar" """A'a""" """Ni ma,sai mu koyi son juna"" ya kalleta kawai sai ya ce ""Muga ciwon"" ""Yaya a wajan ƙirjina ciwon yake" "fa"" da rashin fahimta ya kalli ƙirjin ya kalleta kuma ya nisa ya ce ""Kuma mene a ƙirjin?"" Ya faɗa yana yaye rigar." WE'LL SOON END OF THE FREE PAGES. Ku hanzarta biyan 500 domin karanta Mutallab posting za mu "babu ɓata lokacin ba lallai ku fahimta a yanzu wanda suka shiga paid group sune da batu ko rabin book 1 babu shiga ba. Tsakiyar labarin akwai muke, mene ya faru a farko me zai faru tsakiya ba zaku taɓa sani" ba ko a sashe. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 12 *Bright pens..2nd batch* "Hannunsa ta cire da sauri ta ce ""ciwon fa a wajan ƙirjin yake yaya"" da mamaki Captain ya kalleta ya kalli" "ƙirjin, da gaske bai san mene matsalarta da hakan ba. Ya ɗauki lokaci kafin ya ce ""kuma mene special a" "ƙirjin?""" """Baka sani ba?"" Fiyya ta buƙaci jin amsa ganin har lokacin kallon ta yake da alama processing" "ƙwaƙwalwarsa take yi shi dai ya san wajan da aka caka mata wuƙar kawai zai gani. Bai sake cewa komai ya miƙe tsaye ya nufi fita, Fiyya ta bisa da idanu tana jinjina rainin wayon Captain yana abu kamar baya fahimta. Ta yi shiru bayan fitar tasa, ta ɗan jingina da jikin gadon thinking me ya sa abubuwa suke juyawa tare da faruwa ne? Ba wani tsanar Captain ne a zuciyarta sosai ba, kawai yadda yake abubuwansa ke ƙular da ita amma kaf yayyanta tana matuƙar so da ƙaunar su. Damuwar bai shige dalilin" "daddy na aura mata Captain ba, bayan shi blood brother ɗinta ne. Yanzu ita ce ba jinin daddy ba ko Aliyu?" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! "Da sauri ta riƙe ƙirjinta jin zuciyarta na harbawa, duk yadda take ƙoƙarin ko a cikin bacci ta sake ganin" "gilmar reflection ɗin shi ta gagara, ko sautin muryar tasa ma ta mata sai kuma tunanin mahaukacin daya" caka mata wuƙa ya faɗo cikin ranta wai shi Mutallab? Who is he? """Who is he?""" "Muryarta ta sauka a tsakar kanta tana nanata mata tambayar da zuciyarta ta yi mata a fili. ""To ya ɗauke" "ni ya yi mini me? Safiyyerh Abdu Marafa ai ba sa'ar yara bace, bata zama teddy ba, the whole manager anya ya san me yake ce mini? Ba sai ya sake ganin ko inuwar fiyya ba balle ya aiwatar da abin da ya yi niyya a kaina, aikin banza aikin wofi don ma dai ban san ya zaro wuƙar bane zuwa gaba Captain zan" "lallaɓa ya ara mini bindigarsa problem solved""" Ita kaɗai take ta yin mita ta zubawa madubi idanu bayan ta miƙe tsaye. Wanka ta yi tare da alwala bayan "ta idar da sallah ta ɗauki skin products mai kyau dake sa fatarta laushi ta yi ta ƙyalli, tana son amfani da kayan Aisha s bayero skin care nd herbal medice, ta ɗauki riga mara nauyi saboda ciwon jikin nata. Kasa bacci ta yi ta ɗauki system ɗinta ta fara dannawa hannunta riƙe da ruwan zafi ta jima suna tattaunawa da Md da Secretary ta email kafin ta rufe system ta yi addu'ar bacci ta kwanta sai dai ciwon ya dameta" da zafi har zazzaɓi ya saka ta. "Washegari da ƙyar ta yi sallar asuba don bata yarda ta shige ta, ta rufe jikinta da duvet ta girgiza kai da" "ƙyar baccin ya sake ɗauke ta. Har 12 bata fito ba, sanin abin da ya faru da ita ya saka ba'a nemi ba'asin rashin zuwan nata kamfani ba." "Wajejen ƙarfe biyu ta buɗe idanunta dalilin ƙamshin da ta ji da kuma goshinta da ake murzawa a hankali," ta juya ta kalle shi taga waya ya ke yi muryarsa ƙasa tana jin yadda yake magana one by one jin ana "kallon shi cikin sauri ya ce ""i will call you later""" "Ya juya suka haɗa ido a hankali ta ce ""Ina yini?"" Ya yi mata shiru yana kallon kanta da sauri itama ta kalla" "sai yanzu ta lura kan nata yana cinyarsa ne shi kuma hannunsa na gefen fuskarta ""ɗaga ni""" """Yaya bani lafiya fa"" ya harareta kawai ya yi shiru shima ya ji zazzaɓin ta juya masa baya tana sauke" kanta idanunta rufe zafin zazzaɓin na ƙaruwa ji tayi ya ɗago ta zaune kamar wacce zai zaunar a cinyarsa "ya faki idanunta ya damƙe gefen cikinta ta yi ƙara tana riƙe shi ""Ki dai na yi mini sauti haka, za ki je" "zaman barrack lazy"" ta haɗe fuska tana ji yana taɓa cikinta yaga wajan ciwon na jini ya saka hannu ya" shafi ciwon ya taɓo jinin da hannu can ya miƙe yana juyawa. """Captain jini wajan yake yi ka fama mini na shiga uku"" idan ba kuskuren ji ta yi ba, muryarsa ta ji ya furta" """Allah Ya ƙara""" Cikin dare ne yana tsaye ya fito daga cikin motarsa sanye da manyan kaya na alfarma da fuskarsa rufe da "facemask ya dubi yaran da suke gabansa ya ce ""Ina buƙatar aiki cikin gaggawa bana son wani mistake" "idan aka samu akasi ina cikin taraddi, kuna kallo abu ya taho lokacin na neman cimmana"" Ya buɗe idanu yana sake dudduba inda yake tsaye gani yake kamar ana ganinsa za kuma a iya gane wanene shi." """Mai gida wanne kalar aiki ne ya fito da kai cikin duhuwar nan, faɗa taka cikawa tamu sai da kai iya wuya" "ba wani shege a baya wallahi"" ya ɗan yi murmushin jin daɗi yana kallon mai maganar da kana ganin shi zaka san a buge yake cikin maye kamar kullum" """Idanun mutane nake so, maza uku mata uku"" ya ce yana kallon wanda yake faɗawa maganar ganin" "yadda ya yi shiru kamar dai ban fahimta ba. ""Aiki ja idanun bama na mutum ɗaya ba? Akwai kuskure fa""" """Yanzu akwai wani aiki da zan iya sakawa ka yi mini da zai fi ƙarfinka? Kai ɗin amintacce nane na kuma" "yarda da ƙwarewarka ina jin daɗin business da kai wallahi"" ya zaro kuɗi masu yawan gaske ya miƙa masa, ya sake zaro wata ƙwaya kala daban-daban masu kyan gaske da tsada kana gani kasan manya ne ke shan irin ta. ""Ka fara riƙe wannan kuɗin nasan kana buƙatar caji a kanka kafi yin aiki yadda ya kamata, idan ka kammala ka sanar mini zan faɗa maka inda zaka ajjiye ko?"". ""Ka yi ƙarko irin na dabino sai da kai wallahi yau zam dani, ko kan mutum ka ce na kawo maka a yadda ƙwayar nan ke buɗe mini tunani kawowa zan, ba ƙaramin ilimi ne dani ba da tuni fa ni zan yi ministan kuɗi nace na fasa, kaf ƙasar waye bai sanni ba don uwar mutum"" sambatu kawai yake na maye ya bugu ƙarshen buguwa, shi mutumin dariya kawai yake basa hakan kuma na yi masa daɗi ainun. Mota ya shiga ya bar wajan shi kuma ya gangara ya shiga lungun titin da suke. Tunda ya tafi ya zauna cikin yan'uwansa mashaya yake tunanin ta ina zai fara? Ina zai samu mutane har ya ƙwaƙwule idanunsu hankali kwance? Ya yi shiru yana kallon sama yana ta furzar" da iska mai ɗauke da warin sholi dana bakin gabaɗaya. ***** Mutallab ya tanƙwashe ƙafafuwansa kamar wani sarki ya kuma ɗora hannunsa saman cinyarsa cikin "kowacce ƙafa, kallon Abbasa yake tun ɗazo take magana yaƙi cewa komai ko tari kuma bai yi ba, raunukan jikinsa ya kame sai saura, ido biyu za ka yi da shi ba zaka ƙara marmarin kallon nasa ba, babu rahama a fuskarsa nan zaka ɗauka tunda Ammo ta kawo shi duniya bai taɓa yin murmushi ba, ko haɗa" hanya da inda fara'a take. """Kalli nan""" "Ya dubi abin da take nuna masa, zanen kamfanin ne da photon jariran sai kuma kalmar A.M.A ""Da fari" "mu fara gano ma'anar kalmar A.M.A, photon jariran kuma mai sauƙi ne ana nuna maka har jarirai da aka haifa yau ana siyar da shi a kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, abu biyu ne wanda dole za ka yi ko kusan ukun, da fari sato ita wannan yarinyar ta yiwu a samu wani haske tattare da ita, na biyu kasan yadda duk ka yi ka mallake wannan kamfanin cikin sauƙi, na uku. ,"" sai kuma ta yi shiru ta dinga" kallon Moh ciki da bai """Waye Mutallab, waye kai, dole ka faɗa mini asalin waye kai kana ji na?""" """To na haƙura""" "Ya miƙe tsaye a hankali a lokacin ras yake sai abubuwan da sukai masa tsaye a zuciya da maƙoshi ""Dole" "na san waye kai, ko ka faɗa mini ko ba ka faɗa ba, abu na uku sai ranar da asalin naka ya zo kunnuwana zan furta maka shi"" bai dai yi magana ba, hannunsa zube cikin alijun kayan da Abbasa ta basa ya sauya da ƙyar yafi ƙarfin minti ashirin a tsayen yana harhaɗa kalmomin abin da zai ce mata ransa duk a jagole." """Lalacewar Moh bai kai ya sato yarinya ba""" """Kuma dole a yi hakan fa""" "Ya yi waje abinsa yana yana ƙoƙarin ficewa daga cikin bukkar ta ce ""Baka da lokaci fa Mutallab, kuma" "baka da ikon taɓa ta a waje idan ba kana shirin komawa gidan yari bane, kasan yadda za ka yi dai wish you all the Mutallab""" "Bai ƙara bi ta kanta ba, ya dinga ɗora ƙafafuwansa a ƙasa kamar mai tsoron taka ƙasa sai haɗe fuska yake" "yana kwaɓewa duniyar ya ji ta yi maza zafi ta ko'ina, ya rasa ina zai je me kuma zai yi sai ɗaga yatsun ƙafarsa yake wanda suke zara-zara matar nan Abbasa ta fara takura masa ko waye ya ce ta yi masa gyaran farce? Yama a ka yi ta samu mai yin aski ya wani kwashe masa suma? Bakin bishiya ya samu ya zauna ya sunkuyar da kansa ƙasa, zufa ta shiga tsattsafo masa ta tsakiyar goshi ya sa yatsa ɗaya yana gogewa ya shafa jikinsa ba kayan garawa ko ɗaya yana buƙatar fita daga yanayin da yake ciki, baya son" tunawa ko da wasa. "_“One day i will leave you, duk son nan da nake maka”_" "Ya ji saukar muryarta a kansa ta sauka har ƙasan zuciyarsa a ɗan lumshe idanunsa da ya yi, ya juya zuwa" "gefe sai yake ganin bidiyon abin da ya faru bayan kammala assembly, at that time yana can baya zaune ya yi shiru yana kallon students bai san da zuwanta ba sai ganinta ya yi ta baya kamar zata shige jikinsa ya fiddo manyan idanunsa waje yana miƙewa tsaye hannunsa ɗaya zube a aljihu ya dinga kallon ta da" "ƙyar ya furta ""And what is this Safiyyerh?""" """Bestie shi ake cewa love mana"" ta langwaɓar da kai gefe yana sake kallon yaluwar fuskarta kamar" "zabiya. ""To iskanci za ki mini?""" """Iskanci kuma bestie? Me ya sa kake haka ne, son ka kawai nake yi fa why are you doing this to me? Kai" "ba'a gane maka sam? Ko murmushin masoya ne ka dinga yi mini mana, bafa ni na ɗorawa kai na son ka ba"" idanunta ya cika da waye tana jin zuciyarta na yi mata zafi bata ganin komai a idanunta sai fuskar Mutallab." """A love? Shine za a yi wa mutum fyaɗe a soyayyar??"" Ta buɗe idanu tana rufe baki jikinta har rawa yake" "tana jin kamar ta idda abin da zuriyarta ke umartar ta ""To ka yi haƙuri idan dai na mutu ka huta, kuma idan baka zo gidanmu yau ba Allah a wajan Ammo zan kwana"" fuskar nan a ɗaure ya ja sirirn tsaki ya shige cikin class kafin ya ƙarasa ya ƙara jiyo ta a bayansa tana sake yunƙurin riƙe shi da sauri ta juya sai" kuma ta ɗauki school bag ɗinta ta fice daga makarantar tana kuka. "*** ""i missed the hug"" ya furta ƙasan zuciyarsa lokacin da bidiyon abin ya ɗauke daga kusa da shi, ya yi" shiru yana tunani har yamma ta yi lis bashi da niyyar tashi daga wajan baya son shiga cikin jama'a yana jin nan ɗin shine daidai da ina ya kamata ya ɓoyewa kwalawa. He feels uncomfortable a cikin jama'a haka nan. Safiyyerh na zaune bayan ta dawo daga kamfani ko ɗaki bata shiga ba idan ta tuna yadda Hon Maɗatai "ya sake matsa mata akan hannun jarin da yake son sawa a FS WORLD INVESTMENT COMPANY sai ranta ya sake ɓaci, duk dukiyar da Ubangiji Ya bashi bai gode Allah ba, mutane nawa ne a wannan duniyar da basa ci, idan anci na safe ana fargabar na rana, idan na rana ya samu dare kuma sai dai a yi salatin Annabi a sha ruwa a kwanta, masifar rayuwa ta yi wa talaka dirar mikiya, yunwa na neman illata su ga lalura ga rashin aikin yi? Amma hon Maɗatai shi dukiya yake nema idanu rufe ƴan siyasa da yawa kansu kawai suka sani suke ginawa, mene amfanin talaka ya je ya yi zaɓen? Gabaɗaya sabgogin dimokuraɗiyya ya lalace son zuciya kowa yake bi. Ta yi tsaki tana jin ko zata rasa kujerar Manager ɗin ba zata taɓa bari" Hon Maɗatai ya saka hannu a kamfanin ba. "Miƙewa ta yi ta nufi bedroom bata ɗauki wani lokaci ba ta fito sanye da wando da riga,wandon iya cinya" "kanta ko ɗan kwali babu da mamaki take kallon Captain ganin ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana danna mata system ga wayarta a hannunsa kafin ta ƙarasu ya kashe system ɗin ya ajjiye har wayar. ""Yaya me kake nema a system ɗita kuma?"" Ya yi mata shiru ta zauna kawai tana buɗewa bata sake kallon shi ba, ta shiga duba dukkan ayyukan da aka fitar yau da sauri ta kira accouter da number da take amfani da shi na" kamfanin tana girgiza ƙafa a hankali cikin faɗa ta ce """Accouter me nake gani a haka? Kuɗi fa kimanin miliyan 500m yanzu sun shigo account na kamfani dana" "gani a bayanai, bayan tafiyata me aka fitar ne shinkafa ko me?"" Faɗa take sosai domin ta iya faɗa ajin" ƙarshe ce a fannin. """Manager nifa kina tunawa accouter ne kawai, bani ke da alhakin saka hannu a fitar kaya ko shigowar su" "ba, kawai ni ke saka hannu a duk wani kuɗi da zai shigo ya fita, i am nothing but a Accounter""" "Miƙewa tsaye ta yi tana riƙe ƙugu ta ce ""Rubbish; ka tura mini ducoment na PDF via email na abin da aka" "siya har miliyan 500m yanzu yanzu accouter""" """Ki yi magana da Md ni kawai kuɗin naga shigowar su babu wani file daya zo officer nawa, trust me" "manager ba zan ɓoye miki, na san dai bayan tafiyarki Professor Abdu Marafa ya shigo kamfanin"" ""daddy!""" "Ta furta da ƙarfi ""E, mahaifinki shi""" """Kamarya to?""" """Shine ban sani ba"" sai kawai ta kashe wayar ta ajjiye waje guda, ta sauke numfashi da ƙyar ta shiga uku" "meke shirin faruwa ya ake ƙoƙarin amfani da ita ba tare data sani ba?""" """Yaya"" bai amsa ba idanunsa a ƙafarta ta ce ""Yaya bacci nake ji"" ""to ina ruwana""" Sai kawai yaga ta ɗora kanta a cinyarsa maimakon ta juya masa baya sai ta juyo wajan cikinsa ta yi shiru "tana kallon ƙirjinsa dake buɗe. Ta yi shiru tana sauke numfashi shi dai bai yi magana ba, bai ɗauka haka take da masifa ba yana jin ƙirjinta na ɗagawa a hankali kuma bacci ya ɗauke ta. Cikin baccin ta ji hucin numfashi ta buɗe idanu kallonsa ta dinga yi yadda ya kifa fuskarsa a tata hannunsa ɗaya tamƙe cikin nata ""Captain"" da sauri ya buɗe idanun ya ƙurawa cikin idanunta ido sai kuma ya ɗauke fuska yana haɗe rai. Fiyya bata ce komai ba ta miƙe zaune shi kuma ya shige cikin part ɗinsa yana taku da sauri sai shafa" kai yake yi. Notification ta gani kamar wancan lokacin saƙo ne ta dm nata. Ta buɗe ba wani magana mai tsayi bane sai dai maganar dab take da rusa tunaninta ta bi saƙon da kallo inda ake cewa. "_“bai ci a ce kin yi mantuwa mai nisan haka ba, ki tuna akwai hakƙin wani kan ki Allah Yana kallon ki" TIGER“_ ta dafe kan ta to hakƙin waye a kanta waye mai wannan saƙon kuma? Tsaki ta yi ta miƙe ta bar parlon. Bata sake ganin Captain ba har dare ta yi kwanciyarta. **** Cikin sauri take tafiya tana yi tana juyawa sauri take ta isa chemist amsar maganin ga dare ya raba mijin "nata ya fita. Kamar daga sama taga mutane sun tsaya gabanta fuska rufe ""Su waye ku? Don Allah ku rufa mini asiri magani zan siyo"" muryarta na rawa ta yi maganar. Haɗa idanu sukai sai suka ɗaga ta sama tare da danna ta cikin napep ɗin basu tsaya ko'ina ba sai wani kango a nan taga wasu mutanen kwance kamar basu da rai, kuka take tana duk addu'ar data zo bakinta ""Don Allah kar ku cutar dani don Allah ku" "rufa mini asiri da yarana da rayuwarsu""" Tana ji tana gani suka danneta tun tana ihu har ta kasa jini kamar an yanka rago babu imani suka cire ƙwayar idanunta duk biyun tare da watsa su cikin aliju da gudu suka fice daga kangon. "Bayan ta dawo daga wajan aiki ta shige gidan Anty Turai saboda kiran da ta yi mata, a parlo ta samu Anty" "Turai da yaranta da kuma wasu ƴan mata zaune. ""Ina yini Anty?""" """Sannu matar Captain Aliyu Marafa?"" Cewar Anty Turai ita dai Safiyyerh idanunta akan waya bata ce" "komai ba Waheeda ta ce ""Mama wai shi Uncle captain ɗin son ta yake yi ne? Ni banga abin so a jikin wannan zabiyar ba sam sam wallahi"" Zahiderh ta yi saurin cewa ""Ina fa? Captain ne zai ce yana son Fiyya" "never wallahi, kawai dai auren dole aka yi masa, wannan fari ko na lalura""" "Safiyyerh dai jinsu take Anty Turai ta ce ""Sannu Safiyyerh, ya kamfanin yanzu ai Aliyun ya bar nan wajan" "Zahiderh ya zo ki dinga haƙuri da shi ya jaddada mini baya buƙatar ki cikin rayuwarsa bai san me zai yi da zabiya ba"" miƙewa Safiyyerh ta yi ta ce ""To Anty a ɗaura masa aure da Zahiderh ni bani da wata matsala, zabiya kuma ina jira ku halitto irin kalar idan da sauƙi, so kuma ba abin da ya yi mini zafi da shi zan zauna da mijina haka tunda zaɓin daddy ne, wallahi babu wanda ya kai level ɗin ɗagawa Fiyya hankali"" Anty Turai ta miƙe tana nuna Fiyya idanunta ya rufe sam bata kula da shigowar shi ba, balle ankarar da ita da" su Waheeda suke ta ɗaga hannu zata mari Fiyya dake tsaye tana juya idanunta ta ji an riƙe hannun. "Tun zuwan shi ta ji ƙamshin turaren nasa, ya tsaya a bayanta Anty Turai ta kalli Aliyu ta kasa cewa komai" "ya saki hannunta yana matsawa bayan Fiyya ya zagaye hannunsa a ƙugunta ya jata jikinsa daga baya yana sake kallon Anty Turai ""Shekararki nawa Anty yaushe na zo gidan naki kuma? And who told you bana son ta?"" Duk a dagule yake maganar yana sake haɗe Fiyya da ƙirjinsa kasancewarta duguwa sosai" "so ma sha Allah. ""Aliyu ni zaka shigo gida ka faɗawa haka?""" Bai kalleta ba sai Fiyya daya kalla wacce take shirin juyawa idanunta cike da hawaye ya yi saurin riƙo "hannunta yana ""Wait"" sai kawai ta kifa kanta a ƙirjinsa tana shassheƙar kukan da bata shirya saboda" "ganin idanunsa ""Anty karki sake mini haka""" """Idan na sake me za ka yi Aliyu na ce me za ka yi?"" Ya girgiza kai ya rungume Fiyya tsam a jikinsa ya ce" """Ban san me zan iya yi ba, kawai dai na faɗa miki, kuma i love my wife"" Fiyya ta yi saurin ɗago kai ta kalle shi ya ɗage mata gira ""Yes, I Iove You Safii"" yana cewa haka ya kama hannunta suka fice." *** Suna zaune a dabarsu ya yi sauri ya miƙe tsaye Goje ya ce """Sai godiya, ina aka nufa don shirwa kake baka jewar banza, ɓauna mai tafiyar ɗaukan rai jeji naka" "dabbobi naka, a lafiya mai dawa"" jikinsa ya ji ya fara kakkarwa tsohon tsuminsa na neman tashi ya yi ƙasa da kansa yana ƙoƙarin hana kansa yin kirari da amsar saƙon Goje, ya bar wannan layin tuni. Da ƙyar yana girgiza kai ya ce" """Goje""" """Sai godiya, wuya a ina wuya a daji kai ne mai dawa da jeji na Malam Abdu shalelen Ammo, ƙanin" "Sa'adah da Bafullatana a lafiya aminin Hamida, ɓauna taka mesa taka ba wani bayanka jan biro maganin daƙiƙin yaro Allah Ya ja da ran mai dawa"" gabaɗaya jikin Mai dawa ɓari yake yana damƙe hannunsa wajan ganin mai ɗaga su sama ba har can cikin kansa yake jin kirarin. Kawai ya juya ya bar wajan ""Wai" "ina zaka ne kasan yanayin da ake ciki fa akwai cinnaku""" """Baka haifan ba balle ka tambayan karka biyo ni"" yana cewa haka ya bar wajan ya jima yana tafiya kafin" ya ƙarasu gidan sai ya saka maƙulli ya buɗe ya shiga. A ɓangaren su Safiyyerh tunda suka bar gidan Anty Turai suka shiga mota basu ce komai ba ya kuma "haɗe fuska itama bata ce komai ba, daidai wani gida a bakin titi taga ya tsaya ya kalle ta ""Kar ki fito jira ni nan"" ta jinjina masa kai. Fita ya yi ta jingina tana ɗaukan waya, abin da ta fara cin karo da shi a X picture ɗin wani kyakkyawan yaro yana murmushi ya rufe idanunsa saboda hasken da ya yi masa yawa kamar ka" "taɓa shi jini ya fito, ta dinga kallon picture ɗin sai kawai ta yi skipping zuwa next tweet." "A hankali ya buɗe ƙofar ya shiga idanunsa zube a saman tafkeken screen ɗin computer dake jikin bango," "gabaɗaya wajan nau'in kayan computer ne kala-kala. Ya ɗan dafa kafaɗar wanda yake zaune akan kujera yana juyawa a hankali, kallo ɗaya zaka yi masa kasan mayen computer ne masanin hakin da duk wani surƙulle. Captain ya ce ""Where are you hiding?"" Ya ɗaga idanunsa a hankali ya kalli Captain bai ce komai ba kuma ya cigaba da danna wayar, Captain ya saka hannu ya dungure masa kai ya nemi waje ya zauna yana taɓa computer shima. Da sauri ya miƙe kuma jin sautin muryarta da yadda take ƙoƙarin buɗe ƙofar ya yi saurin miƙewa ya nufi ƙofar daidai nan Fiyya ta shigo ""Yaya gaskiya yunwa nake ji akwai hadari" "sosai a gari ina tsoron ruwa""" """Muje""" Ya yi saurin faɗa yana kama hannunta tare da rufe ta da jikinsa leƙawa take son yi ya saka hannu ya juyar "da fuskarta ya jata waje, shima ɗin dake zaune ya juyo a nutse ganin sun fita ya saka ya cigaba da abin da yake yi." "Cikin dare Fiyya na bacci ta ji ana buga ƙofar parlon kamar za a cire ta, ta miƙe da sauri riga da wando ne" "jikinta na bacci wandon iya cinya ta saka slipper ta fito, tana mamakin mai ya sa Captain ya kai dare har haka? Ta buɗe ƙofar ""Yaya ka tashe ni daga musulmin bacci da nake..."" Shiru ta yi tana yin baya ganin shi tsaye a bakin ƙofa su Goje da Mangal a bayansa ""Kai ne me ka zo yi mini har gidan mijina, matar aure ce" "ni fa"" banko ƙofar Moh ya yi ya shiga yana ƙarewa parlon kallo" """Mai dawa ɗauke ta mu shige kar a yi ta kwanaki"" ta gudu Fiyya ta juya zuwa part ɗin Captain tana kirin" "sunansa a tsora ce kafin ta ƙarasa Moh ya saka ƙafa ya falleta ta faɗi ƙasan tayal idanunsa ya yi jajur domin ba haka ya zo da su ba, jin ana shirin buɗe ƙofar ɗakin Captain Moh ya kalli Goje da sauri Goje ya laɓe a baya kafin Captain ya fito, cikin sauri ya rufe fuskarsa da ƙyalle." """Safii are you ok? Peanut ihun nan fa wife?"" Yana fitowa Goje ya saka gora ya maka masa a ka" kasancewar Captain bai shirya ba ya faɗi a wajan da sauri kuma Moh ya ce Goje ya ɗauki Fiyya ko me ya tuna sai ya saka hannu ɗaya ya sunkuceta a kafaɗa yana ɗaga wuƙa sama suka fice daga gidan... MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 Zan yi cutting free a shafi na 15 in sha Allah. Wannan shafin ku hanzarta yin payment kafin wannan lokacin yanzu kuma na labarin a rufe yake zuwa gaba za ku ce kun shiga uku ashe haka abin yake ina ƙara tuna muku ba fa farkon labarin muke a tsakiya muke waya san mene ya faru a farkon? Me kuma zai faru a gaba? Just pay 500 naira only. "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*" Page 13 *Bright pens..2nd batch* "Safiyyerh na durƙushe a ɗan ƙaramin ɗakin da suka ajjiye ta ciki, warin sigari ya cika ɗakin sai yunƙurin" "amai take yi ta kasa, ta shiga tashin hankali da tunanin suwaye waɗannan da suka je har gidan mijinta suka dake shi tare da yin kidnapped ɗinta? Me suke buƙata a wajanta waya saka su yin hakan? Da alama ba kuɗi suke nema ba wani muradi ne a ran su da suke son cikawa manufar da bata san ta mece ce ba. Ta ɗago kanta da ƙyar tana buɗe kumburarrun idanunta saboda kukan da ta yi da hanzari ta fara buga" ƙofar da hannunta tana girgizawa tare da faɗin. """Wai baku da imani ne me na yi muku idan kuɗi kuke buƙata ku bani waya na kira daddyna zai biya duk" "abin da kuka buƙata na fansa ta, macace ni fa a gidan mijina kuka je har gabansa kuka sato ni, don Allah ku buɗe mini wallahi wari zai kashe ni babu iska a ɗakin ku tausaya mini"" abin da take faɗa tana dukan ƙofar da hannu, amma ko tari ba ta ji sun yi ba, kuma tana da tabbacin suna jinta ta sake ɗaga murya ta" ce """For the sake of Allah, da girman iyayenku ku mayar dani gida gaban iyayena me na yi da za a yi garkuwa" "dani,ku barni da raina kar ku kashe ni zan muku kwatancen gidanmu ku je wajan daddyna a baku dukkan kuɗin da kuke buƙata, idan ba ku yarda ba ku a cikin kuɗina zan baku wallahi mahaifina ya ji abin da ya same ni mutuwa zai yi, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un me na yi muku ne kukai garkuwa dani na shiga uku ni Safiyyerh Allah ka kawo mini ɗauki"" ta sake durƙushewa a bakin ƙofar ta tura kanta cikin cinyoyinta saboda warin sholi daya gama hautsina mata ciki kamar kayan cikinta zai fito haka Safiyyerh ke ji, duk girman idanunta sai da ya yi mitsi-mitsi abin ka da zabiya da ƙyar take buɗe idanun nan, ba sunan wanda bata kira ba hadda Anty Turai akan su kawo mata ɗauki Yaya J ya sha kira. Ta sauke ajjiyar zuciya tana karanta addu'ar neman tsari da kuɓuta daga magauta ta yi zumbur ta miƙe saboda fitsarin" dake mintsinin mararta. "A can wajan ɗakin a cikin gidan da su Goje basu san da shi ba, duk suna zaune suna busa kayan shaye-" "shayensu hayaƙi ya cika wajan, wani na shan sigari wani na shan sholi wani wiwi sun hautsina sai surutai suke yi. Moh na gefe ɗaya ƙwance ƙafarsa ya ɗora akan ɗaya idan yana acting ka ɗauka jinin sarauta ne ko wanda yake da aljanu sarakai a kansa, duk ihun da Fiyya take yi da surutai yana jinta. Goje ya kalle shi" "ya ce ""Wannan yarinyar tafa dame mu wallahi, ka kira ka faɗa masa tunjiya mun ɗakko ta ya san abin yi""" Shiru ya yi yana sake kaɗa ƙafarsa a hankali har lokacin idanunsa a rufe yake. Goje ya kalli ƙofar ɗakin da "Fiyya ke ciki ya sake kallon Moh kafin ya miƙe tsaye ya ce ""Ina da matsala da jin kuka gaskiya, ko dai a" "rufe mata bakin ko a ɓara bakin biyu yanzu da askira""" """Mangal""" "Da sauri Mangal ya kalli Moh jin ya kira shi domin tunjiya da suka ɗakko Fiyya ko tari bai sake yi ba, bai" "runtsa ba har gari ya hawaye ba wanda kuma ya kula a cikin su. ""Ankar sarki, faɗa taka cikawa tamu" "akwai wani sagi a ƙasa ne?""" """Bana son hayaƙin nan"" lokaci guda suka kalle shi a take suka cillar da sigarin tare da saka ƙafa suka" "murje ""Angama sai mene na gaba?"" Bai magana ba ya juya musu baya a hankali ya buɗe idanunsa ya zaro takardar da yake faman ajjiya kamar rai, kusan kullum yana karantawa sama da sau wajan biyar a rana abu ɗaya ne amma sai ya ji baya fahimta,baya kuma ganewa, ya zubawa rubutun idanu Goje shima ya leƙo kai yana kallo ganin ya ninke ya ɓoye ya saka ya yi siririn tsaki ""Na ji takaicin rashin makarantar" "da ban, shi ilimi ko yaya yana da rana""" """Ina zargin wannan takardar bata tsafi bace, kamar ita ce ransa ko iskar dake shaƙa ya manta da komai" "amma banda ita, watarana sai na sace ta yasin"" dariya Goje kawai ya yi ya san Mangal faɗa kawai yake yi. ""Mai dawa kasan a yankinmu an sace mutane har biyu, yau da sakaliya anga gawar ɗaya ba idanu"" ya juyo a hankali ya zubawa Goje idanu kamar mai tunani sai kawai ya miƙe yana taku ɗaiɗai ya fice daga" "cikin gidan, suka bisa da idanu ganin yau ya zama wani so silence kamar ba Moh ba." "Safiyyerh ta ji an turo ƙofar da sauri ta miƙe tsaye tare da ja baya, mutum biyu take gani Goje da Mangal" "shi kuwa tunda ya cillar da ita a ɗakin bata ƙara ganin shi ba. Abincin hannunsa ya cilla mata da ledar ruwa pure water ta kalli takeaway ɗin da ruwan, ta ɗauke kai a hankali tana sake ja baya ""Saura ki ƙi ci kamar na ɗazo, idan kuma kika sake yi mana amai a nan sai kin lashe abin ki tas"" ta ƙurawa wajan ido ta ce ""Ba zan iya cin abinci a nan ba, ni bana shan ruwan leda abincin ma ba irin wannan nake so ba, ko" "nama babu akai""" """Kuma a ina kike tunanin ganin nama? Don ma kin samu an kawo miki dar yarinya saboda kina Manager" "kun saba cin mai kyau a sha mai kyau, a saka suttura a shiga mota a kwana cikin a.c ga naru a gida 24/7, a ci shinkafa basmati da ruwan gora dole ki ce haka, ɗiyar ƙaruna""" "Girgiza masa kai ta yi muryarta na rawa ta ce ""Da gaske nake maka, ni kawai a bani ruwan jakar da lemo" "ko snacks"" Goje ya dinga kallon ta ganin she is serious juyawa ya yi zai bar wajan ta yi saurin cewa ""Don" Allah ku bani waya na kira daddy na maka alƙawarin yanzu za a kawo kuɗin da kuke buƙata wajan nan "akwai sauro headache da fever zai kamani"" ta langwaɓar da kai gefe alamar neman alfama." """Ki jira Mai dawa ya zo, sai ki tambaya bani da ikon haka. Da kike maganar kuɗi kin ji mun ce muna" "buƙata ne? Ba kidnapped ɗin ki mukai domin a bamu kuɗin fansa ba, mun sato ki saboda a koyawa asawa hankali a rage masa tsayin harshensa da yake da kauɗi kin gane? Daga yanzu ki cire rai da samun" "ƴanci""" """Daddy?""" "Safiyyerh ta faɗa a gigice tana dafe kan ta idanunta ya cika da hawaye, tausayin kanta dana daddy ya" "cika mata zuciya babu wani wanda take so a duniya sama da daddy da Ummi me za su yi masa rayuwarta suke son kassarawa tabbas idan suka taɓa kimar mahaifinta. ""Me daddy ya yi muki, mene alaƙae sato ni da kukai da mahaifina me kuke nema a wajansa na roƙe ka da girman Allah kar ku cutar da mahaifinsa kar ku illata rayuwarsa, shi ne jin daɗi da farincikin zuciyata, ku duka kuna da iyaye na tabbata ba za ku" "so rasa su a rayuwarku ba ka ji tausayina Please brother""" """Ni ba brother naki bane ni ɗan daba ne sunana Goje kin gane, idan kina buƙatar wani abu kina iya" "bubbuga ƙofar"" kafin Safiyyerh ta yi magana ya yi sauri rufo ƙofar ya fita. Ya je ya samu Moh a wajen gidan zaune ya sake tanƙwashe ƙafafuwansa ya kalle shi sosai kana ya ce" """Scorpion""" """Kana son faɗar sunan, zan manna maka hauka Goje zan ja maka ruwa"". ""Me ya sa baka son na dinga" "faɗa ne? Ai dafinka ma ya fi na kunama ni ina son sunan"" Moh ya yi shiru yana sake harɗe hannayensa duka biyun ya zubawa samaniyya idanu. ""Idan zan nuna maka asalin kalata a Scorpion ba zaka ɗauka ba," "za ka daina haɗa idanuwa dani sauƙin sunan na wajan faɗa ne, ka kalle ni a Moh ko Mai dawa ok""" """Yadda ka ce haka za a yi, ya zamu yi da yarinyar nan yanzu? Kwananta ɗaya da wuni fa, kuma bata cin" "abinci""" Cikin rashin fahimta Moh ke kallon Goje su yake ya tambaye shi wacce yarinyar bakinsa kuma ya yi masa "nauyi ya dinga juya idanunsa akan fuskar Goje, fahimtar hakan ya saka shima Goje cewa" """Manager wacce Ali wali ya saka mu ɗakko yarinyar da muka je gidansu jiya"" haɗe fuska sosai Mai dawa" ya yi idanunsa ya shige ciki haka kawai ɓacin ransa ya sake ninkuwa ya yi shiru ya datse laɓɓansa kamar "zai raba su gida biyu ya yunƙura zai tashi Goje ya ce ""Wannan sauyin na yanzu na mene? Na fara jin daɗi" "a raina kwana biyu baka sha ƙwaya ba, lafiya dai?""" """Mutallab"" still ya yi shiru Goje ya sake kiran sunansa yana leƙa fuskarsa ganin babu alamar zai kula shi" kawai ya miƙe ya fice ya bar wajan. "***Gabaɗaya suna zaune a cikin parlon banda shi dake tsaye, zuwan nasan ake jira amma tunda ya shigo" "bai kalli kowa ba balle ya yi magana, fuskar nan a murtuke kamar kodayaushe. Yaya J, Awais Dr Hash, Anty Turai Waheeda sai Ummi dake zan gefe bata cewa komai sai goge hawayen da yaƙi tsaya mata take yi. Daddy baya uhm baya uhm'uhm kansa a ƙasa zuciyarsa ta bugawa da ƙarfi yama kasa yarda da abin da ake faɗa har lokacin gani yake wasa ake yi masa da hankali da kuma wahalar da zuciyarsa da ake" saboda anga yana ƙaunar Safiyyerh ƙauna mai tarin yawa an fahimci ita ce rauninsa. """Captain Aliyu Abdu Marafa shiru ba naka bane, ba muzo nan da a shiru ba a matsalar kidnapping ba a yi" "mana wasa"" cewar Sp Ghali daya ƙara amsar case ɗin Safiyyerh a karo na biyu ya ɗaga kai ya kalli masu gadin asalin gidan da kuma na part ɗin su Captain sai kuma ya ce ""Heyy you man, mene sunanka da aikin" "da kake yi?"" Cikin rawar murya ya ce ""Sunana Isma'il ni mai gadi ne Yallaɓai""" """Isma'il sanda abin ya faru ƙarfe nawa ne? A daidai lokacin kana ina kuma?"" ""Ban san ƙarfe nawa bane a" "lokacin don ban duba a gogo ba, sanda abin ya faru kuma ina bakin gate ne amma kafin nan na miƙe na" "shiga banɗaki kama ruwa wallahi gaskiya nake faɗa maka Yallaɓai""" """To na ƙaryata ka ne? Kenan Isma'il bashi da sani akan waɗanda suka shigo gidan ko? Da ɗauke" "Safiyyerh?"". ""Duk abin da na ce maka na yi ƙarya abu ɗaya na sani fitowar su ɗauke da ita, hannunsu riƙe" "da makamai ɗaya ya ce na buɗe ko ya ɓola mini ciki na ji tsoro haƙiƙa sai na buɗe ashe sun yi parking mota wata ɓaka mai kyau daga can gefe""" "Murmushi kawai Sp Ghali ya yi yana duban ɗaya ma'aikacin ya ce ""Kai kuma fa? Mene information?"" Shi" "wannan jikinsa har ɓari yake don tsoro ya ce ""Yadda na gansu Allah Ya sa naga Annabin Rahama, misalin biyu da arba'in ne ina zaune na ji ana dirowa ta katanga kafin na yi magana ɗaya ya make ni yana nuna yatsarsa a baki alamun na yi shiru, ni kuwa na yi shirun don wallahi a lokacin na ɗauka mai gida shi sojan kenan daman shi ke kai wa dare a waje saboda yanayin aikin nasa, suka ɗaure ni ina hango sanda suka nufi part ɗin tunda can babu masu gadi daga nan ban san mene ya faru ciki ba sai gani mukai sun fito da" "ita a kafaɗa kamar ma a sume take yadda ta langwaɓar da kai""" "Daddy da Captain suka runtse idanunsu lokaci ɗaya, kowanne tunanin da yake daban a ransa, is he a" "loser? Captain ke tambayar kansa or he is falled as a husband maybe da yana kwana ɗaki ɗaya da Safii da hakan bai faru ba, idanunsa ya ƙara sauya kala. Daddy ma nasa tunanin dabanne, ko dai ya yi gaggawa ne ba yanzu ya dace ba? Ko mistake ya yi daya aurawa Aliyu Safiyyernsa ne? Is he a loser? Daya" kasa tsare rayuwar yarinyarsa mace ɗaya tilo a duniya ko dai da gaske he is falled as a father? "Kafin kowa ya yi magana ta shigo cikin gidan a gigice duk da nutsuwar da take da ita, da sauri kuma" Daddy ya miƙe tsaye cike da tsoro da mamaki hatta Captain sai da ya ji wani abu mai kama da faɗuwar "gaba, who told her? Tun kafin ta yi magana daddy ya yi saurin matsawa kusa da ita ganin yadda take ta zare idanu fararen idanunta fuskar nan nata ya ɗakko rana kamar ta yage don fari ""Zahiyerh""" "Girgizawa daddy kai ta yi a daburce ta ce ""Ina Maama?"" Ya yi shiru yana ƙoƙarin riƙe hannunta ta ƙwace" ta yi baya da ƙarfi kuma ta ce """Ina Maama? Ka bani ita na tafi da ita where is Safiyyerh""" """Safiyyerh has been kidnapped""" """Kidnapped?"" Ta maimaita tana juyawa ta kalli Sp Ghali anya ya san wacece ita da yake furta mata" "maganar anyi garkuwa da Safiyyerh kai tsaye bai tauna harshe ko ya lissafa maganar ba, Safiyyerh fa? Sp Ghali zai yi magana daddy ya girgiza masa kai yana sake kallon Zahiyerh wacce zuciyarsa ke buɗewa a duk sanda ya kalle ta. ""Ummimi please ki kwantar da hankali ki samu nutsuwa tafiyar nesa kikai jirgi kika" "hau""" """To na ji, ka faɗa mini meke faruwa da Safiyyerh?"" Daddy ya sauke numfashi a hankali kuma ya nuna Sp" "Ghali ya ce ""As he said, he told you already Safiyyerh has been kidnapped""" """Uhm""" """Komai zai daidaita Ummimi"" ita dai bata sake magana ba can ta ɗaga kai ta kalli Aliyu da sauri ya zame" "idanunsa ƙasa ta harɗe hannayenta a ƙirji ta tsaya jikin hawa steps ɗin bene. ""Afuwa Sp muje ko?""" """Next question ɗin mu akan Captain ne""" """Ok ka yi mana"" in ji Anty Turai." """Aliyu kafa yi haƙuri kalar aikin ku na sojoji daban, namu daban kowa da nasa iyawa da ƙwarewar a nasa" "ɓangaren ok. Aliyu kai ne zaka faɗa mana abin da ya faru a cikin gidan su waye suka sace maka mata har cikin gidanka a matsayinka na soja wanda kodayaushe zaka iya samun ƙarin matsayi na aiki, ya akai haka ta faru? Su waye?""" """Ban sani ba""" "Kai tsaye Captain ya bada amsa ""Baka sani ba? Har kuma suka ji maka ciwo kada ka saka na fara zarginka" "na yi tunanin sace Safiyyerh set up ne kuma ne ka yi plans ɗin hakan, ka sace matarka?""" "Aliyu ya dinga kallon Sp Ghali a hankali kuma ya ce ""E"". ""kana nufin ka sace matarka Safiyyerh?""" """E"" ya sake cewa" """Aliyu!!"" Daddy ya kira Aliyu da ƙarfi ya miƙe ya ce ""Da gaske ka sace Safiyyerh?"" Kamar idanun Captain" "za su faɗo ƙasa saboda yadda suka fito waje sai kawai ya lumshe ido ya buɗe ya ce ""E, na sace ta daddy""" "yana cewa ya fita daga parlon yana banko ƙofar da ƙarfi kamar ya cire ta. ""Innalillahi wa'inna" "ilaihirraji'un!"" Muryar Ummi ta karaɗe parlon ƴan mazan dai sukai shiru." """Karya yake yi"" Ummimi ta ce har yanzu taƙi zama lokaci zuwa lokaci kuma tana duba wayarta kawai sai" tabi bayan Aliyu. Daddy har jiri yake gani baya so a fitar da maganar ya fiso a yi komai secretly har Safiyyerh ta dawo gare su amma sai yaushe ne?. Only God knows. ****Ammo na zaune ta yi shiru a ɗakinta kamar kodayaushe ta yi nisa a tunaninta bata ma san Malam "ya shigo ba sai muryar Inna Binta da ta ji a sama wajan ƙofar ɗakin tana faɗin ""Yanzu don Allah Ammo da rana ma ba za ki daina kwantar miji kina satar kwana ba, wacce irin jaraba da masifa ce haka ni Bintalo jaraba kala-kala Malam ɗin duk da basir ya cinye shi da rana ma ba za a bar mana miji mu dinga ganinsa duk da ba wata tsiyar yake yi mana ba"" Ammo ta cira kai ta kalli Inna Binta ta juya ta kalli gefe har yanzu" ba taga Malam ba cikin rashin fahimta ta ce """Kamarya?""" """Ohho shafa ki ji mace an girma amma sai shegen munafurci da kissa wato kafin ki gama sallama ɗan" naki wa duniya kafin ya gama zama ɗan ta'adda ya miki aikin mallake malam ko? Shi ya sa kaf gidan nan "kin fi kowa yawan yara"" Ammo ta kasa cewa komai da ƙyar ta buɗe baki ta ce" """To ina Malam ɗin yake yaushe ya shigo mini?"" Ta banka mata harara ta nuna mata malam dake zaune" "ya yi shiru a hankali ta furta ""Ikon Allah ki yi haƙuri ban san ya shigo ba"" Malam ya yi gyaran murya ko" "kallon Inna Binta bai yi ba cikin damuwa ya ce ""Ammo ki nutsu ki ji me zan ce miki babu tabbacin abin" "dai har yanzu, ki yi haƙuri idan har hakan ya kasance gaskiya""" Jin haka ya saka Inna Binta neman waje ta zauna a bakin dakalin ɗakin Ammo ita dai wacce ake maganar "domin ta shiru ta yi tana bin Malam da kallo gabanta na faɗuwa ba wai yanzu ta saba da faɗuwar gaba ba, ta ji wannan ta musamman ce. ""Gawa aka tsinta. ,"" ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Na Ammo?""" "Malam ya ƙura mata idanu bai taɓa zaton tunanin wancan gantalallan yaron mara amfani a duniya zai zo ranta bq, ya girgiza kai kana ya yi shiru caraf Inna Binta ta ce ""Idan shine ai gwara ka faɗa ko kuwa? Kai aka cire masa ko wuƙa ce harsashi ne ko rayata ko babbake shi aka yi kasan haka ake yi wa ƴan daba, wallahi wani da aka rutsa shi ƴan unguwar jahilin duka sukai masa, ashe shima dai irin tsinannen yaron naka ne wuƙa bata huda shi, suka dinga rutsa masa dutse aka ina sai da kan ya ya yi dugu-dugu a nan cikin gari akai abin, da iyayen nasa suka je wajan ƴan sanda cewa sukai su yi haƙuri gawar ba zata ɗakko ba ta yi muni yaron nan dai da yake bashi da rabon rahama ko sallah ba a yi masa ba, yana can za a yi" "gwaje-gwaje da gawar ƴan makaranta daman ƙarshen duk wani ɗan daba kenan""" "Malam ya yi shiru bai yi zaton haka Inna Binta take ba, Ammo rasa kalmar da za ta yi amfani da ita ta yi" "wajan yi wa Inna Binta, ta yi shiru tana sunkuyar da kai." """Malam ka faɗa mata kawai sai ta ɗauki don gana""" """Wallahi tallahi ko""" Mama ta yi caraf ta faɗa ashe itama tana laɓe a jikin taga daga waje. Ya girgiza kai kawai cike da takaici "kana ya ce ""Gawa aka tsinta ta mace an cire mata idanu biyu kuma an cillar da ita bakin hanya, aka kira" "ana tunanin kamar gawar"" haka kawai ya ji yana jin tsoron kalmar da abin da zai biyo baya Ammo ta ƙura" "masa idanu a sanyaye ta ce ""Sa'adah ce ko Bafullatana ko Hameeda?""" """Hameeda""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Astagafirulla Allah mun tuba jama'a an cire idanun Hameeda gatan na" "ammo ta shige jama'ar gida Hameeda ta mutu a kawo mana ɗauki"" a gigice Inna Binta ta zari mayafi tana ficewa zuwa maƙota. Mama kuma ta yi shiru idan haka ne ba ƙaramin gigita mutuwar Hameeda ya saka ta ba. Ammo bata ce komai ba a ranta tana nanata kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Ita kawai ta yi mata saura a cikin baki ""Ba a tabbatar bata, saboda haka ki taso muje a gani ƙila ki fini ganewa sosai"" kafin Ammo ta yi magana Baba uwar mijin Anty Hameeda ta shigo tare da mijin idanunta ya yi ja" cikin sauri Mama ta ce """Yaya lafiya dai Baba?""" """Ina lafiya, Hameeda ce daga fita siyo magani da daddare mun neme ta mun rasa kwana biyu kenan" "wallahi"". ""Shikenan ta tabbata an kashe Hameeda"" kafin ka ce me cikin gidan ya cika Inna Binta sai rusa ihu take yi tana sun shiga uku an kashe musu yarinya. Koda aka kawo gawar Hameeda ba kowa ya iya gani ba kamar dodo har ta fara wari an cire kyakkyawan idanun nan nata. Ammo ta dinga tuna nasihar Hameeda ta ƙarshe da ta yi musu,daga nan bata sake dawowa gidan ba wani abu ya tokare wuyan" Ammo ta kasa magana balle kuka sai kallon gawar take cike da sarewa. ****Kamar kullum yau na Goje ya buɗe ƙofar tana durƙushe duk ta fita daga cikin hayyacinta idanunta ya faɗa ba zaka taɓa cewa Safiyyerh bace. Ya dire mata abincin yau dai pure water ɗin hadda sanyin shi """Kar ki sake buga mana ƙofa domin ba wanda zai buɗe miki""" """Ka ɗauke bana ci""" """Dar kin yi kyan kai ƴar kurciya"" ya juya baya ta faki idanunsa ta zare ƙaramar wayar data gani a jikin" aljihunsa ta yi saurin ɓoyewa. Goje kuma ya dawo cikin harabar gidan Moh ya gani zaune yana sake karanta takardar sai ya yi murmushi yana dafa kafaɗar Moh ya ce """Ni dai na fara gajiya da siyo abinci gaskiya"" banza Moh ya yi yana ninke takardar tun daren da aka kawo" "Safiyyerh bai sake ganin kamarta ba sai sautin kukanta da yake ji kullum yanzu ma kukan take tana buga musu ƙofa da ƙarfi a fusace ya miƙe tsaye ya nufi ƙofar ɗakin Goje ya bisa da kallo can ya miƙe ya bi bayansa. Da ƙafa ya daki ƙofar ta buɗe da sauri Safiyyerh ta miƙe cak kukan nata ya tsaya a maƙoshi ta tattare ta haɗiye ta mayar zuwa cikinta, fitsarin dake mintsinin mararta ya saki kansa ya fara zuba a gefen ƙafarta, dukkan wata gaɓa ta jikinta ɓari take yi. Ashe da bata san waye ba, bata san waye ya yi kidnapping nata ba sai yanzu cikakkiyar siffarsa ta bayyana zubi da tsarin da halittar da Ubangiji ya yi masa mai firgitarwa bata san waye mafi muni a cikin ƴan daba amma ta san wannan tantirin ne ko daga tsaiwar da ya yi, cikakken namiji a tsaye majiyin ƙarfi matashi kuma mai jini a jika da cikakkiyar lafiya shine matsayin ɗan daba tsaye a gabanta gefen fuskarsa wani zabcecen yanka wanda akai masa ɗinki har ya zama tabo. Salati take ƙoƙarin yi ta kasa ta gama jiƙa wajan da fitsari ƙiris ne babu numfashinta ya" yi ƙaura daga ƙirjinta ta yi saurin ƙasa da idanunta. """Ka yi haƙuri kar ka mini komai, don Allah ko nan waje ne ku bar ni na fito kalli skin ɗina zai lalace akwai" "ants a nan waje"" ta tattare hannun rigarta tana nuna masa farar fatarta da ta yi wani irin tabo ritsi-ritsi kamar kwanciyar ji fuskarsa ta kumbura ta yi jaa sai susa take yi saboda ƙaiƙayi. Ta langwaɓar da kai ta ce ""Ka gani ko na sake nuna maka har bayana"" ta juya bayan tana ƙoƙarin ɗaga rigar ta ji ya daki ƙofar da" mahaukacin ƙarfi kafin ta juyo ya bar wajan. Ta sauke ajjiyar zuciya feeling reliver ganin ƙofar a buɗe. "Tana fitowa suka haɗa idanu da shi da sauri ta juya kanta na bugewa da jikin bango, anya tana da hankali" da lissafi kuwa? Fitsari fa a wando sai ya tsuke fuska. Suna zaune Mangal ya shigo yana hakki da sauri Goje ya zare wuƙa sama tiger ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana gurnani Moh kuma kallon Mangal yake yana jiran ya ji suwaye suka biyo shi don yana da yaƙinin ba wanda ya san gidan da suke. """Kai ɗan wahala mene su waye suka biyo ka?""" """Daga layin su Mai jeji naje an yi rasuwa kuma a gidansu Moh aka anyata lahira wallahi"" duk suka juya" suka kalli Moh shima ɗin kallon nasu yake fuskarsa ba wani sauyi kawai ƙarashen maganar yake jiran ji. """Sai aka ce waye ya baza? Iyayen Moh dai akwai sauran rai wannan dar in sha Allah""" """Wai ko Hamida ko Hamda, idanu aka ƙwaƙule mata ashe tana cikin mutanen da aka sace ta"" Moh" "tunani yake yi ina ma ya san mai sunan Hameeda tasa Hameedan ba zata taɓa mutuwa a irin wannan halin ba, sam ba zata mutu ba duk da yanzu ba ruwansa da ita. Bayan wasu shuɗewar daƙiƙo zumbur ya" "miƙe tsaye kansa na sarawa a dagule ya furta ""Amini?""" Da sauri kuma ya yi wani ɗaki suna shiga suka same shi yana cakawa kasan wata sabuwar allura da Ali "wali ya basu da maye, bayan ya zuƙe ruwan a jikinsa ya ƙara ɗakko wata ya sake cakawa kansa sirinjin ana ukun Goje ya yi saurin matsawa ya ce ""Easy Mutallab,zaka haukata kanka a banza kasan wacce irin" "allura ce ko dan baka jin turanci muma bama ji, haukatar da mutane take yi fa?""" "Sakar masa allurar ya yi ya sake ɗakko wata Goje ya sake riƙe wa ya ce ""Wallahi in dai ina nan ba zaka" "sake yi ba"" ya ƙara sakar masa ya ɗakko fenta zai yi Goje ya ƙara riƙe, Moh ya shammaci Goje ya ɗauke shi ya damfara shi da ƙasa ya saka ƙafa ya take hannunsa hannun ya yi ƙara, ganin yana shirin kashe shi ya sa Mangal ya ɗakko abu ya makawa Moh aka, ya ɗauke ƙafarsa ya juya yana kallon Mangal da sauri" Mangal ya zare Goje ya fito da shi daga ɗakin da gudu suka fice daga cikin gidan. **The following days. Buɗe ƙofa Captain ya yi ya shiga ɗakin a hankali wanda ya yi wa Aliyu mugun sani shi zai lura da ramewar da ya yi. Idanunsa akan Ummimi dake zaune gefen gado hannunta tsakanin cinyoyinta ta sunkuyar da kanta ƙasa ya ƙarasa ya duƙa gabanta ya ɗora hannunsa a cinyarta a hankali kuma ya leƙa kansa ta ƙasa ya kalli fuskarta suka haɗa idanu ta zabga masa harara lallausan murmushi ya yi mata a hankali ya ce """Love""" """Aliyu fita""" "Ya girgiza mata kai ya yi shiru sai lokacin ta yi shiru tana ƙare masa kallo ""Ciwo ka yi ne Gadanga?""" """A'a love""" """Kuma yaushe ka damu da Maama har haka ka dame?""" """Love, Safii is my wife"" ta wani buɗe idanunta na rashin fahimta ""Waye Safii?""" """Safiyyerh, your Maama"" da sauri ta miƙe tsaye tana girgiza kai ""Yaushe aka yi haka? Tunanin waye" "hakan decision ɗin waye wannan professor ko?"" Gani take sauri take yi amma sai ta cire ƙafa ɗaya take mayar da ɗaya ta fice daga ɗakin a parlo taga duka mutanen gidan hadda police da team na musamman da suka fara bincike akan sace Safiyyerh Abdu Marafa. ""Ashe daman baka yarda ba professor za ka iya mini haka? Bana baƙin ciki da auren da ka yi musu amma ina da hakƙi na sanin ka haɗa Safiyyerh da Aliyu aure, Professor burinka ya cika ƙudirinka ya tabbata ka aurawa Safiyyerh Aliyu"" masifa Zahiyerh take yi tai Hausa tai turanci ta koma larabci ba wanda ya tanka ta, kan Abba a ƙasa. Da ƙyar Aliyu ya janye ta a ransa ya gode Allah da bata ce a raba auren ba tsaf zata iya. Ta nemi kujira ta zauna sai nishi" take yi na rashin lafiya. """Zo Aliyu"" ya ƙarasa wajanta ta nuna masa kusa da ita ya zauna, sai kawai ta rufe idanu ta kwanta ta yi" shiru a hankali ya fara danna mata kanta Dr Hash shima ya ɗauki ƙafarta data kumbura ya fara danna mata sai a lokacin Daddy ya buɗe idanu ya kalleta ya girgiza kai fatansa kafin ta farka Safiyyerh ta dawo gida. """Sp har yanzu ba wani kira da muka samu akan batun sace Safiyyerh, ina zargin anya issues na" "kidnapping ne?"". ""Za su kira ai sun sauya salo ina mai tabbatar maka cewa za a kira Safiyyerh zata dawo gida"" daddy ya jinjina kai ya yi shiru." Wayar Aliyu ce ta fara ƙara yana dubawa yaga kamar private number har sai share sai ya yi tunanin ko masu sace Safiyyerh ne? Da sauri ya amsa kiran was the first abin da ya ji daya nemi buɗe masa zuciya "sautin kukan Safiyyerh ƙasa ƙasa ya runtse idanu can ya ji ya ce ""Yaya Please help ants za su cinye mini" "fata Yaya za su kashe ni""" """Safiyyerh listen""" "Karo na farko daya kira sunanta ""Take a heart peanut, ke matar soja zama jaruma"". ""Yaya am scared" "wuƙaƙe"" ya buɗe idanu ya ga duk kallonsa suke yi hadda daddy Sp Ghali ya yi masa alama ya saka speaker. ""Kina ji na?"" Kamar tana gabansa ta ɗaga kai ""Be strong Maama, daddy is here for you, Ummi kowa ma hadda ni am here for you ƴan mata, hadda Ummimi"" da wani irin sauri ta ce ""Ummimi?" "Ummimita Yaya?""" """Sure, ki nutsu wanne waje suka kai ki, za ki iya tuna suna ko wanne abu da zai bamu haske?""" """Yaya sun rufe mini idanu ban san komai ba, don Allah ka taimaka mini daddy help me please"" idanun" daddy ya yi jajur already anyi connecting na wayar an fara bincke da ƙoƙarin tracking daga ina wayar ke zuwa. Shima kuma daga can haɗaɗɗan ɗakinsa da suke zube da kayan na'ura kamar hauka ya saka abu a kunne ya ɗora ƙafa yana girgiza kai a hankali yana jin conversation ɗin Safiyyerh da Aliyu yana yi yana duba time da cije leɓe. Abin da Aliyu bai taɓa yi ba kenan ƙoƙarin jan Safiyyerh da hira da ya ji Ummimi zata motsa zai yi saurin "girgiza ƙafarsa ""In sha Allah i will save you Safii, ki yi ƙoƙarin gane wani abu ki yi addu'a"" tana ƙoƙarin sake magana suka ji ihunta da ƙarar buga wayar da ƙasa ""Safiyyerh kina nan kina kan kayi baby?"" Aliyu ya jere tambayar. Kafin sun an kare daddy ya sulale a wajan babu numfashi." "****Tunda su Goje suka fita yake abu ɗaya kamar wanda za'a zarewa rai, sai buge buge yake yana fasa" "komai na gidan kumfa na fita a bakinsa ihun da ya yi da gurnani shi ya saka Safiyyerh sakin ihu tana yin cilli da wayar a gigice ta miƙe har lokacin kayan bacci ne a jikinta, tana fita ta ganshi a tsakar gidan ya yi tumu-tumu wani irin mahaukacin tausayinsa ya ratsa zuciyarta ta duba babu kowa a gidan sai ta yi tunanin wannan opportunity ne da zata bar gidan hankali kwance, bata damu da kayan jikinta ba sai kawai ta nufi ƙofa da gudu tana ƙoƙarin fita ta ji muryarsa cikin mawuyacin hali kamar ana fisgar ransa abin da ta ji ya saka ta tsaya ta yi jim itama kanta na sarawa tana gani bibbiyu ta sake yunƙurin buɗe ƙofar ta ji ya ce ""Safiyyerh. !"" Ya faɗa da ƙarfi a gigice ta juya taga ita yake kallo yana ƙoƙarin tashi ya" kasa yana miƙo mata hannu... *MUTALLAB IS NOT FREE* We'll soon end the free pages. ka yi payment a yi naka a paid group. MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 Ƴan Niger kuma ya gadda tsarin yake. 'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476 "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *This is not a love story,but a love that builds a story, and a love that destroys" the story.* *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 14 *Bright pens...2nd batch* *Author's books* Munafukin miji Moon Mijin malama Tsintacciya Idan ba ke Sirrinmu E.t.c Follow on Arewabooks Follow on telegram Remain 1 free page Jikinta rawa yake ganin ya kafe ta da idanunsa har lokacin kuma kakkarwa nasa jikin yake yana fesar da numfashi. Ina ya san sunanta? Take tambayar kanta. A hankali Moh ya lumshe idanunsa bayan ya janye su daga gare ta yana ɗan ciccije bakinsa. "Safiyyerh ta kasa fita, idan ta bar shi ya mutu alhalin zata iya taimaka masa Ubangiji zai kamata da laifin" "rashin tausayi da imani, ta salwantar da rai ta hanyar ganganci da son zuciyarta." """Safiyyerh taki rayuwar fa? Kashe ki za su suma fa, ya kamata ki bar wajan nan tunda kin samu dama, shi" "kinga kamar mahaukaci ne maybe"" zuciyarta ta bata shawara cike da gamsuwa ta jinjina kai tare da kama handle ɗin zata fice." Haɗa idanu suka sake sanda ta juyo ya dinga kallon ta rinannun idanunsa sai ta saki hannun ƙofar tana ɗaga ƙafa zata nufe shi. """Run Safiyyerh, run away run Safiyyerh""" Ta sautin muryar zuciyarta a cikin kunnenta ta sauka har tsakiyar kanta ƙirjinta ya dinga ɗagawa tana son tafiya bata kuma san meke janta zuwa gare shi ba. Ta girgiza kai """Save him frist"" ta furta a iya harshenta. Yana ganin ta nufo inda yake ya rufe idanu kafin ta ƙaraso ya" juya baya yadda ba zata ga fuskarsa ba. Jikinta a sanyaye ta durƙusa cike da tsoro ta kasa magana can ta yi ƙarfin halin furta """Ina ke maka ciwo?""" "Ya mata shiru ba bacci yake ba, domin tana hango yadda ƙirjinsa ke ɗagawa sosai yana ƙoƙarin ganin ya" "hana kansa yin abin da ƙwaƙwalwarsa ke umarta shi. ""To faɗa mini inda maganin yake na ɗakko maka""" Jin shirun ya yi yawa ta matsa tana leƙa fuskarsa suka haɗa ido ya zaro mata manyan jajeyen ƙwayar "idanun ta yi saurin ɗauke nata idon ""Tab kalli idanunka fa, ko asibiti zaka je?"" Ta yi maganar tana ƙoƙarin kai hannu zata taɓa shi ya mirgina gefe yana haɗe fuska kamar ya ce ya shiga uku, da zata gane to tabbas ita ɗin ce baya son gani ko jin muryarta ta kura masa hakan" yake yi sosai ya tsuke fuska yana rufe idanu Safiyyerh ta miƙe gabaɗaya hopefully ya buɗe ido ko ya bata "amsa ba sarewa ta sake miƙa hannu dukan da ta ji ya kaiwa jikin bango ne ya saka ta yi baya tana zaman ƴan bori,shima ya tashi zaune yana zazzaro idanu daidai lokacin su Goje suka shigo ya kalli Safiyyerh da" take yarfe hannu saboda bugewar da ta yi ya dubi Moh daya miƙe tsaye yana tangaɗi ya shige ɗaki yana "rufo kansa a ciki. ""Ke me kikai masa?""" """Ƙato da shi me zan masa?""" """Abu a duhu na san matan yanzu ba kunya ce da su ba, idanu rufe suke afkawa maza"" da mamaki" "Safiyyerh take kallon Goje zuciyarta babu daɗi ga takaicin rashin guduwa gana wancan da ko inda take bai kalla ba duk maganar da ta yi masa, ta matsa tana takure jikinta waje guda sai yanzu ma take jin kunyar shigar jikinta sosai, ita Safiyyerh yau ita ce take rayuwa a wajan ƴan daba mashaya kuma ƴan ta'adda hawaye ya cika idanunta sosai mutanen da sam basu suwaye su ba, basu san kansu ba basu da" wani amfani a wajan al'umma. """Ke kina ji ko?""" """Safiyyerh sunana""" """Mene ya daman kuma warning zan miki kar ki kuskure ki sake zuwa wajan shi idan kina son tsira da" "ranki ba, ba kema ko Abdu Marafa bane a nan wallahi zai iya ganin bayansa, ki yi abin da ya shafe ki kawai ki tsaya iya matsayin ki na wacce akai garkuwa da ita kuma ɓarayin gwamnati"". ""Shi wa?""" "Ya nuna mata ƙofa ""kin gane ai""" """A'a"" wuƙa ya zaro yana gwalo idanu waje ya ce ""Idan na cire miki yatsa ɗaya za ki gane ai""" """Ni mu yi magana ta fahimta daku, me kuke buƙata zan baku koma mene amma ku rabu dani don Allah" "ina kyakkyawan fata da muradan da nake son cimma a rayuwa naga ku babu inda kuka saka gaba rayukan ku ma sam baku damu dasu, wallahi ina buƙatar rayuwa mai tsayi da zan bar baya mai kyau ba zaku ɓata mini rayuwata ba, kuma warin sigarin nan juya mini kai yake da ƙyar nake shaƙar numfashi, ni macace mai hankali da ilimi wacce iyayena suka bawa tarbiyya daidai gwargwado in da ilimin addini" "saɓanin ku da ba lallai ko ummul kitahhb kun iya ba, ƴan daba ne ko masu laifi rayuwarku a gurɓace take" "ba a yi muku tarbiyya ba"" hatta Moh dake cikin ɗaki idanunsa a sama yana kallon rufin kwano sai da ya" "waro ido yana sauraren maganganun da take cewa, Mangal ya yi mata ƙuri da nasa idanun haka Goje" """Wuyanki ya isa yanka ba laifinki bane za mu yi maganinki""" """To me na ce na ba daidai ba, don Allah ku ba ƴan daba bane ƴan ta'adda kuma ga tantirin can shine" "shugaban naku da alama asalin daƙiƙi ne ajin ƙarshe sai wari dauɗa dana rana ga na shaye-shaye wallahi...,"" saurin haɗiye maganar ta yi ganin shi tsaye a kanta yana huci ta miƙe tsaye hannu ya ɗaga kamar zai kwaɗa mata mari ta kurma ihu tana ƙanƙame jikinta ""Don Allah ka yi haƙuri ƙarya nake yi wayyo daddy wayyo captain"" sai idanunsa suka sake jirkicewa ta buɗe idanu taga ya zuba mata nasa idanun fuskarsa dab da nata sai juya ƙwayar idonsa yake a saman fuskarta kamar mai son tantancewa" wani abu. "Ta tura baki cike da tsiwa ta ce ""Kana kwaɗa mini mari zan rama tunaninka rabuwa zan yi dakai ka ci" "bulus? Bayan an ce duk wani ɗan shaye-shaye bashi da wani ƙarfi hayaƙi ya cinye shi"" Goje ya ce" """Wannan yarinyar ƴar wasa ce bayan kuɗi data iya sarrafawa har rashin kunya ta iya Allah kar ka rabu da" "ita"" Shi dai Moh na tsaye yana kallon ta ita kuma ta kasa jure ganin ƙwayar idanunsa ta yi ƙasa da kanta tana murguɗa masa baki, bata ankara ba ta ji ya cilla mata baƙar kunawa cikin riga ta zumduma ihu a gigice ta yi kansa zata riƙe shi ya yi saurin baya yana ficewa daga gidan Goje yana ta dariya da buga ƙafa" """Kinga aikin Mai jeji gana Scorpion nan""" ****Eng Ali wali yana zaune a gidan wutawarsa yana zantawa da wasu manyan mutane masu taimaka "masa a harkar kamfel ya dubi P.a ya ce ""P.A ina tunanin iya abin da ake buƙata kenan kuma na bada, ka" "sani ba kuɗi yanzu a ƙasa kamfen ya cinye komai, you can manage ko?""" """Ba damuwa amma muna da raguwar list na local government wajan biyar da bamu je ba yanzu haka, ga" "ƴan media sun matsa kasan mutane babu amana gwara a fara watsa musu hatsi tun yanzu fa a yi maganin yunwar data addaba musu"" Ali wali ya yi murmushi yana juya kai kafin ya ce ""Ku je za mu yi" "magana zuwa dare ina da hira da ƴan zuwa dare we'll talk"" P.A ya kalli mutanen ya ce" """Don't make any mistakes idan kun shiga gidan rediyon ku tabbatar kun yi abin da ya dace, kar kuma ku" "nuna wata alaƙa tsakaninmu da ku yadda na faɗa muku haka zaku faɗa"" ""In sha Allah, ai harma da abin" "da baku buƙata ba mu indai za a biya mu ai buƙatar maje hajji sallah zamu farfaɗi ayyukan bogi da ya yi kuma ya yi mana""" """Nice to hear this, you can leave ku je""" Tafiya suka yi suna murnar ƴar dubu biyar biyar ɗin da za a basu akan faɗar abin da ba haka bane. Ali "wali na shirin miƙewa ya ji numfashi a bayansa ya juya da sauri, tsaye ya ga Moh fuskarsa rufe sai ƙwayar" "idanunsa da take a fili ya cake yana muzurai. ""ka bani tsoro amma""" """Mara gaskiya ko a ruwa zufa yake""" """Me na yi na rashin gaskiya?"" Ya yi masa shiru yana wani irin fito ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora saman" "kujera yana zaro kunama ya ajjiye saman kujerar wajan ta fara yawo tana ɗaga ƙari sama ta kumbura sosai. ""Yaushe ka shigo? Na ce ni zan dinga nemanka bawai ka dinga biyo ni duk inda nake ba, bana so a san ina mu'amala da kai""" """Saboda annoba ne ni? Tunda ka jawo ni haka zaka shanye duk abin da na dama, na kwalo yarinyar" "mene next?"" Murmushi Ali wali ya yi ya ce ""Ai na san kun ɗakko ta, tunda CSP ya yi mini magana akan case ɗin kidnaping sannu namijin duniya""" """Zan kawo ta nan""" """Ina? A'a ka bar ta nan wajanku zan baka key ɗin wani gida sai ku tafi can kwafi sararawa ni bani da" "gaske koda zaka dinga huta gajiyarka a wajanta kana rage zafi"" Moh ya ɗaga kai ya kalli Ali wali da kyau." """Wacce gajiyar, sanyi ne a jikinta?""" """Kana abu kamar ba wayayye ba, mu bar maganar ka yi mini aiki na farko and i appreciate it. Sai batun" "Scorpion"" daidai nan kunamar dake yawo a wajan ta shige hannun Moh ya matse ta ya yar waje guda Ali wali ya cigaba da cewa ""Scorpion ba zai bar mu ba, Hon Maɗatai yake hari a yanzu nasan kuma bayan nan ni ne a list, yana neman zame mana masifa yana kawo mana barazana a akan siyasarmu gwara Hon Maɗatai ya samu dukkan abin da yake nema a mulki ya samu nasa rabon ni yaushe na fara? I will never" "let that happen ba zan bari ya yi galaba akai na ba""" """Me za ka yi?""" """Zan tabbatar an nemo shi an ɓatar da shi, don ba haka kawai yake yin abin da yake ba akwai abin da ya" "taka yake taƙama da gadara dashi, ka yi ƙoƙarin nemo mini shi kafin hukumar FID su kama shi zan" "ruɓanya maka abin da duk na yi niyya""" """To kuna da case da shi?"" Ali wali yace ""Pardon? Kamarya kenan""" """Basar""" "Key ɗin gidan ya basa, hadda na mota Moh yaƙi amsa wai he don't know how to drive ya basa kuɗin" abincin Fiyya mai kyau da duk abin da take so. """Kaƙi faɗa mini waye kai dai ban san komai dangane da kai ba Moh, sunanka kawai na sani Mutallab" "without surname and middle name, whatever shikenan dai"" Moh ya ƙara ɗaga ƙafa zai fita Eng Ali wali" yace """One more think Mutallab""" """Ali wali ka kira ni da ɗan daba ko ɗan ta'adda sai mu yi magana"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Sai" "godiya"" ya tsuke fuska Moh." """Professor Abdu Marafa ya mini mummunan tabo a zuciyar matasan jihar nan,ya ɓata mini suna na ji ina" "son ɗanɗana masa kwatankwacin abin da ya yi mini ta hanyar ramuwar gayya wacce ake cewa tafi ta gayya daɗi, kamar yadda ya ɓata ni shima haka nake so a ɓata tarihin tarbiyyar gidansa da sunan da yake taƙama da shi, a dinga masa kallo a matsayin wanda ya gaza"" Ya yi shiru yana sauke numfashi yana duba" wayarsa ganin shugaban jam'iyya na kiran shi ya miƙe tsaye. """Bayan sato budurwar ƴarsa da kuka yi har gida, ina son ka yi Safiyyerh Abdu Marafa fyaɗe, ina son ka yi" "wa Safiyyerh Abdu Marafa ciki kaga tana da auren wani, wani kuma daban ya yi mata ciki wanin ma ɗan daba, ɗan daban da basu san waye shi ba, kaga Safiyyerh zata haifi ɗan zina ko""" """Ɗan zina?""" "Moh ya maimaita a fili Ali wali ya ce ""To ɗan mene? Yayinda da wani wanda ba mijin yarinyar ba ya keɓe" "da yarinya har ta samu ciki wannan cikin ya sunan shi? Cikin shege ba haka lissafin yake, idan na ce wani" "zan bawa wani aikin lissafin Eng Ali wali bai gama cika ɗari over ɗari ba, dole kai zaka aikata haka Mutallab dole kai zaka yi wa Safiyyerh ciki domin dauɗar gora ciki kan shata""" """Wanne zunubi ita yarinyar ta aikata, gyatuminta ne kamar batun nan ba zan ba, shi kuma daman cikin" "yinsa ake yi? Ba kawai girma yake ba?"" ""Au baka san yin ciki ake ba? Shekarar nawa?""" """Koma mene ba za a yi ba"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Dole zaka yi, ka rubuta kuma ka ajjiye sanda za" "ka yi baka sani ba jeka"" bai wani ɗauki maganar Eng Ali wali da muhimmanci ba ya fice daga gidan." "***Safiyyerh ta rufo ƙofar bayan ta gama dubawa ta kalli Goje ta ce ""Kawai ku siyo mini kayan abincin na" "dinga dafawa sai ina san muku?""" """Kin iya wato ne?""" """Mene wato?"" Ya ce ""Shi girkin nake batu"" ta jinjina masa kai ya miƙe tsaye ya ce ""Da kin yi dabara" daman ba ki da wani amfani. Ita mamaki ta yi ganin kitchen hadda tukunya plates da spoons ga risho da sauran tarkace. Babu jimawa Goje ya dawo hannunsa riƙe da Indomie guda biyar da ƙwai guda goma hadda kayan miya da magi ya bata ya ce """Ta yi musulmin daɗi kin ji Manager""" Ta samu kanta da yin murmushi a ranta kuwa dabara take yi ta samu hanyar guduwa. Suna tsaye ya faɗo "cikin gidan sai ya yi turus yana kallon Goje yaƙi yadda ya kalle ta, ta ƙasan idanu ita kuma take binsa da" "idanu mamakin yadda jikinsa yake a murɗe take har ƙasan zuciyarta ta ji tana shakkarsa. ""Barka da antayowa mai jeji ya ƙarin haƙuri"" banza ya yi masa ya shige ciki Safiyyerh ta ce" """Au rashi ma aka yi masa?""" """Yayarsa aka sace sai jiya aka kanta an ƙwaƙwale mata idanu"" Safiyyerh ta zare idanu tana dafe ƙirji sai" "tausayinsa ya kamata a raunace ta ce ""Kuma bai je gida ba? Anya yana son yayar tasa kuma kun tabbatar wannan ba mahaukaci bane?"" Shi dai tuni Goje ya bar wajan. Ta gama dafa Indomie wacce ta ji azabar Attahiru rabon da ta shiga kitchen a rayuwa ta manta fuskarta ta yi jajir da wani irin roɗi-roɗi idanun" sukai micin-micin ta dinga mata ƙaiƙayi fuskar saboda zafin wuta ta nemi kaɗan ta juye musu a faranti. Moh yana kallon yadda ruga lauma kamar mayunwata sai jan yaji suke yi ya kalli Indomien ya kalle su "can ya miƙe ta ce ""Kai baza ka ci ba? Ni ina son yin sallah fa"" duk suka share ta, suna gama ci suka fice tare da rufo ƙofar ya rage sai ita kaɗai ta haɗe kai da qwwia ta dinga kuka kamar ranta zai fita har bacci ya ɗauke ta a wajan." Cikin bacci ta ji an cillo mata abu ta miƙe da buɗe idanu tsaye ta ganshi ya juya baya leda ce ya cillo ta buɗe taga duguwar riga guda biyu da hijabi da takalmi ta yi ta mamakin yadda ya san size ɗinta ta miƙe tsaye yana jin zata zo wajansa ya nufi hanyar fita ta sha gabansa ya yi turus ta dinga kallonsa shima yana kallonta """Wai kai baka yin magana ne, ko ƴar dariya babu kafin na tafi mu ƙulla mu zama abokai"" ta miƙo masa" "hannu ya kalli hannunta mai ɗauke da siririn zobe sai yatsunta zara zara da su ""Am Safiyyerh Abdu Marafa You?"" Ya sake yin shiru ta langwaɓar da kanta gefe guda ta ce ""Ina son zama ƙawarka fa, zan maka labarin daddyna da yadda yake so na, da labarin kamfanin da nake aiki hadda labarin Ashraf wanda zan aura ya mutu aka aura mini captain labarin Ummimi da Kinal ƙawata i will tell you everything," "abota Frist?"" Ta sake miƙa masa hannun a karo na uku. Gefenta ya bi ya shige yana rufe ƙofar gidan ya" bar ta tsaye da hannu a ƙaƙe takaici ya ishe ta shi wannan yana ɗan ta'adda yana jin kansa kamar ɗan gidan ƙaruna saboda faɗin rai ga miskilancin masifa the manager ita Safiyyerh take magana ake sharewa bai san cewa akan dole take yin maganar ba? Ta lumshe idanunta hawaye na cika cikinsu da ƙyar ta yi alwala ta fara jero salloli. Goje ne ya shigo da sauri ya ce """Ke kina ina fito maza taso"" ta miƙe za ta yi masa gaddama kawar Moh ya shigo ya damƙi hannunta ta" kalli baƙin hannunsa da ɗan mitsitsin nata farin hannun ya jata sukai waje mota ta gani bai tsaya jiran komai ba ya dannata a gaba Goje ya shiga baya Mangal dake tsaye ya ce """Waye zai ja motar yanzu? Ni ban iya ba kuma haka?""" Moh dake shirin shiga mazaunin driver ko me ya tuna ya kalli Safiyyerh a karo na farko ta ji muryarsa a "sake ya ce ""Dawo nan"" tsoran shi take ji ta fito ta koma wajan driver ya dawo ita ta tashi, ya cilla mata" "key ɗin motar ""Muje"" bisimillah ta yi ta fara driving ta juya ta kalle shi ta ce ""Ina?"" Ya bata wayar hannunsa wacce yanzu ya shigo da ita ta duba location da ya fara driving cikin sauri har suka bar wajan." Mintuna kaɗan da barin su motoci suka tsaya a ƙofar gidan Captain ya fito jikinsa danye da uniform na "sojoji da suka amshe shi sosai ga ƙatuwar bindiga sauran yaransa suka fito a hankali ya dinga bin wajan da kallo har ya shiga cikin gidan abin da ya fara cin karo da shi ya sanya zuciyarsa bugawa ganin rigar baccin Fiyya yashe a ƙasa ya ɗuka ya ɗauki rigar idanunsa ya sauka akan wani busasshen jini ya dinga kallon gidan a nan ya kalli ƙwayoyi kala-kala da wuƙaƙe da gorori ya lumshe idanunsa ""Where are you" "Wife? Ina suka kai mini mata?""" """Captain kuma ka tabbatar tracking ɗin nan ya nuna?"" Ya jinjina kai don baya jin zai iya magana. ""Sun" "gudu, amma ya akai sukai san an yi tracking location nasu har suka gudu da wuri haka?""" "Captain ya girgiza kai irin bai sani ba ""Ka kwantar da hankalinka matarka zata kuɓuta ko kana tunanin" "sun yi mata wani abu ne?"" Captain ya nuna masa rigar baccin Safiyyerh da jinin dake wajan mutumin ya dafe kai ya ce" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, in sha Allah ba abin da muke zato bane muje"" fita sukai Captain ya ji a" ransa ba zai bar abin haka nan ba. Mutallab wani gida ya kai su madaidaici mai kyau da tsari da yake can bayan gari duk suna zaune "Safiyyerh kanta na ƙasa tana mamakin yawan shiriun bawan Allan nan, idan ya yi shiru shi kaɗai sai ya" saki ajjiyar zuciya ko ya ƙurawa waje guda ido. ***Wajan sati guda babu labari akan batun sace Safiyyerh ba kiran waya babu komai Daddy ya hana a faɗi maganar ko a social media ko a gidan rediyo ya ce a bar ta tsakaninsu. Yana ƙwace hannunsa maƙale "da ruwa muryarsa a hankali ya ce ""Aliyu waye ya saka?""" """She is my wife daddy""" """And? Ɗan sanda ne kai ko soja?""" """Zan iya amfani da uniform ɗina ko babu haka ai she is my responsibilities yanzu na kula da haƙƙina zan" "ji na zama lusari idan ban nemo Safii ba, kar ka dakatar dani daddy police su yi nasu aikin ni na yi nawa""" """Ka cire hannunka a ciki Aliyu""" """Ok zan jire akan wanne dalili?""" """Aliyu yanzu baka tunanin dalilin hakan su yi mata wani abu ne? Baka san su waye mutanen nan ba, duk" "abin da zaka ji a bayan nawa dana Zahiyerh yake kar ka yi kuskuren da za su salwantar da rayuwar Maama na roƙe ka, mutanen ba mutunci ne da su ba kamar komai hannun Sp Ghali"" Aliyu ya miƙe ya nufi ƙofa ""I am sorry daddy idan kaga na tsaya to na mutu ne, idan da numfashi a ƙirjina ba zan gusa ba" "sai na dawo da Safiyyerh cikin rayuwata i am sorry"" yana cewa haka ya bar ɗakin." "Daddy ya rufe idanunsa daya cika da ƙwalla ya wani irin ramewa ko abinci baya ci Ummi ta ce ""Ka san" "halin Aliyu da baka fito masa ta haka ba, gwara ka saka Ummimi yi masa magana"" daddy yaƙi cewa komai. Wayarsa ta fara ƙara number ya gani sai ya yi sauri ya ɗaga yana kaiwa kunne aka ce." """Barka, ina magana da Professor Abdu Marafa na sani ko baka amsa, zan fara da yi maka ya jiki don ina" "da yaƙinin kana nan zuciyarka na ciwo bari na ɗora maka da wata maganar ban sani ba ko zaka iya jure jin abin da zan faɗa. Yarinyar da kake ji da ita ni na saka a sato mini ita Safiyyerh kenan ina son ka lashe aman da ka yi da kanka. Professor ni ɗan siyasa ne lissafin ɗan siyasa daban yake dana Malami, bana barin kota kwana daman mun saba saka jama'a a uku, wallahi ka shiga komata yanzu nine da wasan ka" "fara lissafa ranakun mutuwar yarinyarka daga yanzu"" da sauri Daddy ya ce" """Waye kai?""" """Sarai ka ɗauki ne muryarta professor, kana magana da Eng Ali wali mai neman takarar ɗan majalisa, ka" "hanani bacci yanzu lokaci ne da zaka ji abin da nake ji"". ""Ali wali me kake buƙata me Safiyyerh ta yi maka" "karka cutar mini da yarinyar don girman Allah kar ka taɓa ta""" """E, ba zan taɓa ta ba muddin ka yi abin da nake so""" """Me kake so?""" """Ka dawo jam'iyyata kuma tsagina ka lashe aman da ka yi ka kuma gyara ɓarnar da ka mini na rusa mini" "dukkan shirina, yadda ka ɓata sunana a wajan matasa da al'umma a gidan rediyo da kai da ɗan jaridar da" "yake mara maka baya ku sake sabon lale wajan wanke ni inma kana buƙatar kuɗi zan bayar hakan ba laifi bane ba""" """Uhm Ali wali kenan tun yanzu har ya yi sauri haka? Ni kake cewa idan ina buƙatar kuɗi kaga na yi maka" "kala da mabuƙaci? Kamar dai ka manta waye Professor kana buƙatar tuni na, laaa la la dama sauran lokaci ai. And da kake batun Safiyyerh tunaninka ita ce raunina ko?"" Daddy ya tsige ruwan hannunsa da ake ƙara masa ya sakko daga saman gadonsa daman tuni ya nunawa Ummi ƙofar fita tun kafin ma ya" ɗaga kiran. """Ka yi kuskure sosai, Safiyyerh is nothing to me kuma she never be my headache idan ka so ka saka wuƙa" "ka yankata a yanzu is doesn't matter for me, idan akan Safiyyerh ka kira ka mini warning ka makara Ali wali tunda Safiyyerh ta bar gidan nan ko da dai da rana ban taɓa tunaninta ba siyasa ce kai kuma yaro ne" "mu zuba mu gani""" "A ɓangaren Ali wali dariya shima ya yi ya ce ""Lallai prof ka cika ɗan siyasa, to wallahi ka shirya ganin" "gawar Safiyyerh a wannan daren ku tara ƴan jana'izarta"". ""Idan ka haifo kuma kai cikakken ɗan iska ne idan har ba zina akai ka haifeka ba na roƙeƙa Ali wali don Allah ka kashe Safiyyerh nima fa wani aikin ka rage mini..,"" ƙit Ali wali ya kashe wayar daddy ya saki dariya yana wani irin murmushi wata number ya kira ana ɗagawa ya shige toilet yana saka key, ya jima ciki kafin ya fito ya zauna saman gado Dr Hash ya shigo da Yaya J ganin daddy zaune ya saka dr cewa ""Daddy ya jikin naka?"" Hawaye ya cika idanun daddy ya ce ""ba abin da zai tafi daidai babu Safiyyerh zuciyata zafi take my innocent Fiyya, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ina tsoran halin da Ummimi zata shiga"" ganin hawaye a idon mahaifin nasu ya saka Junaid" ficewa dr ya zauna ya dinga lallaɓa daddy da bashi bakin za a ga Safiyyerh in sha Allah. Aliyu yana zaune a ɗakinsa aka buɗe ƙofa tare da shigowa ya ɗaga kai ya kalleta ya miƙe da sauri duk da "babu fara'a a fuskarsa amma sai da ya saki ajjiyar zuciya. Ta juya idanunta ""Nan ka ɓoye?"" Ya girgiza mata kai" """Ka cigaba da binciken inda Safiyyerh take Aliyu kar ka saurari mahaifinka ka ji ko?"" ""in sha Allah" "Ummimi"" ta zuba masa ido sai ta juya ya ce ""Tafiya za ki yi?""" """Me zan maka?""" """Love, ganin ki nake son yi"" ta haɗe rai tana cewa ""To ɗakko zani na goyaka"" ya buɗe idanunsa ya yi" "wajanta yana rungume ta ya saki ajjiyar zuciya ""I love you Ummimi, and I love Safii too""" "Kan shi ta shafa ta ce ""Kawai ka zaɓa ni ko ita"" ya lumshe idanunsa ya yi mata shiru, rungume shi ta yi a" "jikinta ta yi shiru tunani daban daban a ranta sai kuma ta sake shi ta ce ""Fito waje"" saƙo Aliyu ya samu cikin gaggawa sunansa ya fito a jerin sojojin da za a yi posting nasu wajan aiki ya dinga kallon saƙon yaushe ma ya dawo da za a sake tura shi wani wajan bayan babu shi a sojojin da aka yi list? Sai kawai ya fita da nufin zuwa kiran da ya samu domin bata uzurin yana da wani muhimmin aiki akan nasa iyalin ya" manta da batun a tsarin aikin sojoji babu sauyi idan har a zaɓe ka. ****Mafarki ta yi mai ban tsoro ta farka a gigice tana kiran sunan TAHHB sai haki take yi fitila taga an "kunna an hasko ta ya zuba mata idanu a ransa yana ƙara mamakin wannan hasken nata gefensa zabtareriyar addace saboda tsaro ya miƙe a hankali ya kunna hasken parlon sai a lokacin Fiyya ta lura da Goje dake cikin kwance cikin jini haka Mangal ga wuƙaƙe a gefen su sai numfarfashi suke yi. Ya taka ya je gabanta ya tsaya can ya duƙa dab da ita baki ta buɗe za ta yi ihu ya saka yatsarsa a bakinsa ""Shhhh"" ta yi" tsit ya cake addar """Mene?""" """Ban kira ka ba wallahi"" ya zuba mata idanunsa masu kaifi ta janye nata ""sunan wa kika kira to?""" """Tahhb""" """Sunanki ne? Ko na Abdu Marafa?"" Ta girgiza kai ""Mafarki na yi a mafarkin na ji sunan, amma ban sani" "ba ni na manta komai na mafarkin ma kai na ciwo yake i have a headache""" "Ya ɗaga addar ya cake ta tsakanin ƙafafuwanta sai sheƙi take yi ya ce ""Ko dai ki faɗa mini waye Tahhb ɗin" "da kika dame ni da kiran sunansa yanzu ki na ɓula miki cinya""" """Don Allah ka yi haƙuri wallahi ban san shi ba""" """Ke wace?"" Moh ya tambaya ""Safiyyerh sunana"" ya cije bakinsa sosai ya ce ""Matar soja ko?"" Ta jinjina" masa kai """To ni waye? Kuma ya nake a wajanki?""" """Wallahi ban san ka ba, kai ba kuwa bane a wajane"" idanunsa har ruwa yake ya daka mata tsawa a gigice" "ya ce ""Waye ni? Waye ni waye tell me...." "❤🔥🔥💃1 page remain ba zan taɓa buɗe komai ba shafi 15 is nothing nothing ku biya you'll never regret sai mun yi nutsu za ku fahimci labarin MUTALLAB bai haɗa hanya da kowanne kalar labari ba, idan za ka yi kuka ka fara tun yanzu ba kuma zan taɓa sauya labarina a yadda nake ba, you better shut" up... MUTALLAB. "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476 "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *The story of a thug husband MUTALLAB, as a good parents za ku bada auren" "yarinyarki ga ɗan daba ɗan ta'adda? Ban ce ku fara kuka tun yanzu ba,ban ce ku ji soyayyar ciki kamar a" ƙirjinku ake wanzar da ita ba.* *The story of TIGER and MOH The destiny of CAPTAIN and FIYYA. Finally the eternal love* *between..The love that separate them and back them together❤🔥😭* *❤🔥 MUTALLAB ❤🔥* Page 15 last free episode *Bright pens.. 2nd batch* For more updates follow Mutallab on Arewabooks in sha Allah ❤🔥 "Page 15 shine last free pages na labarin, kar ka yi tunanin ganin wani page ɗin a waje ka yi payment a yi" "naka into paid group akan 500 kacal, love ɗin da kuke showing yanzu ne zai yi aiki฀MUTALLAB." "Book 1, 2 &3" 500 Naira 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar tsarin biyan zai kasance ta *Stock na airtel*. Ku yi wa wannan layin 84506476 magana sai ta ba ku lambar da za ku turo mata stock ɗin. Kafin ɗorawa da inda muka tsaya zamu ɗauki hutun zango na sati ɗaya tal maybe har a yi albashi ko masu mining ta fashe musu. Godiya ga Hajja Aisha Abubakar Khadhfsum data biyawa mutane 8 ga masu business zaku iya badawa a tallata muku idan kun ɗauki nauyin page in sha Allah. Ba zan manta da BESTIE ba I so much love her wish you all the best Aunty Nazeefah Sabo Nashe ta ce HADARIN GABAS yana hanya. Ina son ta sosai Gaisuwa ga haƙarƙarina uwar gidan Viper tunda mun amince Nabila ce amarya Ayushercool masoyiya. My beb Zee kumurya sai tallafe ƙirji muke muna sata a addu'a gashi zata fara yi mana ZAYTOON a watan Nuwamba i love them sosai "Conversation bana ce kuci kanku ba, saboda ina ƙaunarku Sarautar's library Mutallab fans, Nimcy paid" group my ArewaBooks people. Mikiya writers Association Mikiya fans AUTAR MANYA❤🔥 Ubangiji Ya bar ƙauna. Page 15 Last free pages "*What if I tell you, I love you?*" """kar ki ce ba ki sanni ba, kar ki ce haka dole ma tarihin rayuwarki ba zai taɓa cika ba sai da sunana, dole a" "same ni a cikin rayuwarki sai dai idan za ki cire wani sashi na cikin tarihin"" ya furta yana huci da gwame numfashi Safiyyerh was shocked and speechless at the same time ta kasa kallon shi wani irin tsoro shi" take ji mai girma ya ratsa zuciyarta. A hankali ta ɗago kanta zuwa gare shi hawaye na taruwa cikinsu yana sauka akan fuskarta "Ta ƙura masa ido da sauri kuma ta girgiza kai ta ce ""Wallahi da gaske ban san ka ba, ban taɓa ganin ka ba" "sai kwanakin nan, i don't even know your name balle kai,me ya sa zan sanka to?"" za ta sakar masa kuka ya ɗora yatsarsa a baki ya ce" """Shhhh"" ba shiri ta yi shiru tana sauke ajjiyar zuciya shi dai har lokacin fuskarta yake kallo yana murza" "tsinin wuƙar a ƙasa. ""To kai ka sanni ne? Ni ka cire mini wuƙar nan ka ji ɗan baƙi"" ta furta tana juya idanu" ta langwaɓar da kanta gefe guda. """Ki daina kiran sunana daga yau""" """Sai na dinga ce maka me to? Ka faɗa mini ban ma san sunan ba ai"" ƙoƙarin biye mata yake wajan ganin" ya samu abin da yake buƙata amma a duk kalma ɗaya daya furta ko kafin ya furta sai ya fama hautsina kan shi kafin ya san me zai furta mata. Wuƙar ya ɗauke ya cilar gefe guda ya juya ya kalli Goje jira ya ke yi safiya ta yi ya fara tunanin yadda zai samu likita ya ji ta ce """Kai ne ka yanke su ko? Ba kyau wallahi ka mutu a haka wuta zaka tafi babu fashi kana kallo za mu shige" "aljanna muna jiyo ihunka a cikin lazza ko saƙara tunda baka da wani aiki a rayuwarka sai daba da bushe- bushe cikinka ba komai sai ƙwaya da hayaƙi, gabaɗaya gudanawa kake daka zaɓi wannan rayuwar ne ɗan baƙi? Bayan rayuwa akwai mutuwa fa karka bari ka mutu cikin wannan halin ba zaka ji da kyau" "wajan Mala'iku ba""" """Kina da ɗan'uwa mala'ika ne?""" """Subuhanallahi, kai ko wa'azin baka so kamar jinin fir'auna ni tausayinka kawai nake ji tunda baka gani" "shikenan"" ta haɗe fuska irin ta ji haushin nan har ƙasan zuciyarta ita ƙyamar shi take yi rayuwarsa a gurɓace take babu wani abu na birgewa ko ban sha'awa a ciki deep down kuma tausayin rayuwar tasu take ji tana jin da tana da iko tabbas ba zata taɓa gazawa ba wajan ganin ta taimaka musu. Ya rufe idanunsa yana daga zaunen saman kujera ya ɗauki ƙafa ɗaya ya ɗora akan ɗaya ya fara yin fito wanda ya" cika ɗakin a hankali kuma ya zaro sigari zai kunna ta yi saurin cewa. """Matsalar daƙiƙi kenan a rayuwa, shi da kansa bature ya ce tana lalata lafiya dake babu arabi ba boko" "ba'a gane komai ai shikenan, goodness Safiyyerh what exactly wrong with you, that's not your business"" ta faɗa lokaci guda kuma tana miƙewa tsaye sai dai bata kai ga zuwa inda ta yi niyya ba ta gan shi tsaye a gabanta hannunsa riƙe da sigarin yana zuƙa da fesarwa, ta saka zata rufe hancinta ya sa hannu ya tukare jikin bango ya sata a tsakiya sigarin a bakinsa yana binta da jajayen idanu bakinta na rawa ta girgiza kai" "ta ce ""Mene haka wai?"" Ya yi shiru yana duƙawa fuskarsa dab da nata har lokacin ita ɗin da yake kallo" """Iskanci ne wannan matar aure ce ni fa, saboda ƙwaƙwalwarka bata faɗa maka daidai ko? Idan ka sato ni" "a gidan mijina shine yake nufin me? Zan barka ka yi yadda ka so ko ƙazamin jikinka ya taɓa fatar Safiyyerh ba zan taɓa yafewa kai na ba, da babbar murya ina faɗa maka ni Safiyyerh matar aure ce ka ji ko? Kana jin Hausa ai?""" "Ya zare sigari hayaƙin daya zuƙa ta cikin bakinsa ya dinga fesa mata a fuska ta fara tari tana ɗauke kai, ya" "ƙara zuƙar sigarin a baki ya matsa dab da fuskar tata ya sake fesa mata lokacin ta buɗe baki za ta yi magana gabaɗaya ta haɗiye hayaƙin, a gigice ta fara tari tare da kakarin amai ganin da gaske aman za ta yi,ya matsa a wajan tare da shigewa wani ɗakin. Safiyyerh ta durƙusa tana riƙe ciki saboda wani irin ciwo da yake yi mata ga amai dake ƙara hautsina mata kayan ciki ta rasa yadda za ta yi ta kwanta tana riƙe cikin da dinga rusa kuka. Duk abin da ya fara Goje na jinsu kawai yana cikin wani hali ne tsautsayi ya saka su fita a daren sukai karo da ƴan daban cikin gari sun shigo ɗaukar fansar wani faɗa da aka yi can kwanaki shine suka rufar musu, a cikin ƴan daban cikin garin wanda yake jagorantar su me suna Bakin wuta shine ya sare su shi kuma Moh sai da ya sari wajan mutum goma a yaran Bakin wuta wanda kuma shine faɗan su na farko a rayuwa ba wanda ya san wani, a cikin yaran ba sai da aka buɗewa wani ciki" kuma duka aikin Moh ne yana da tabbacin kuma Bakin wuta ba zai bari haka nan a ci bulus akan shi ba. Goje ya juya kaɗan ya kalli Safiyyerh dake kuka sosai kamar ranta zai fita itama yarinyar naci gare ta ga "bakin tsiwa da Moh na taɓa mace da tuni Safiyyerh bata duniya ya san ba zai iya kashe ta ba amma zuwa gaba zata gane bata da wayo idan ta cigaba da kai shi bango. Tana kukan a haka bacci ya ɗauke ta bata ji kiran sallah ba amma tunda ta motsa bakinta ɗauke da addu'a ta san asuba ta yi ta miƙe da ƙyar ta nufi banɗaki ta yi alwala ta jima tana azkar kafin ta yi raka'atul fijr kana ta yi sallar asuba. A hankali ta dinga leƙa shi abin da ya bata mamaki bai shige ganinsa durƙushe a kan qwiwinsa ba yana kallon gabas ba kuma sallah ya yi ba, kan shi a ƙasa ya yi shiru kamar zata shiga sai kuma ta fasa ta tsaya cak ta samu" kanta da yi masa addu'a samun sauƙi da mafita a rayuwarsa da shiriya idan yana da rabo. """Allah Ya shiryarka idan kana da rabo""" "Ya ɗago kan shi ya juya kaɗan suka haɗa ido, ba ƙaramin gigita ta yi da ganin idanunsa a haka ba, ya ƙura" "mata ido a ransa girman nacinta yake ƙara jinjinawa duk da bai yi mamaki bai kuma zama sabon abu ba," "bai fiya son takura ba wani lokacin. Safiyyerh ta harɗe hannayenta a ƙirji ta ce ""Ko yunwa kake ji na daba" "maka abinci? Ko shayi?""" """To na zo na yi maka shira? Ko waƙa?""" """Get out...""" "Ya ce a hankali muryarsa ƙasa ta buɗe ido jin ya yi turanci ta ce ""Wow ashe a ɗan san wani abu, nifa ba" "zan fita ba bakina ciwo yake na rashin magana gaskiya"" kafin ya yi magana ta shiga cikin ɗakin ya yi saurin tashi da ƙyar ya nufi kujera ya kwanta ƙafarsa ɗaya a armchair ɗaya a can saman kujera hannayensa ya harɗe a ƙirji idanunsa rufe. Safiyyerh ta zauna a ƙasa ita kanta bata san me ya sa take son yin magana da shi ba, ta ji kuma tana barin wajansu zata haɗa Kinal da shi ita take son auren ɗan daba a hankali muryarta a nutse ta ce ""Sunana Safiyyerh Abdu Marafa, ni ce auta a gidanmu..."" Ta ɗan yi shiru bata ga alamar yana ma jinta ba kamar bacci yake yi haka yanayinsa ya nuna bata karaya ba ta sake" matsawa ta ɗora da faɗin. """Mahaifina professor ne ya koyar a jami'o'i da yawa a wannan ƙasar cikakken lakcara ne matasa na son" "shi sosai saboda yana taimaka musu da shawarwari. Ina da yayyi huɗu babban yayenmu sunansa Aliyu muna ce masa Captain shi soja ne, bashi da kirki gabaɗaya baya dariya kamar kai ɗin nan amma shi ba baƙi bane fari tas, yana da ilimi he is educated, sai mai bi masa Dr Hash likita shi a ɓangaren kwakwalwa Neurologist, shi rayuwarsa ba sawa ba hanawa sai my favourite Yaya J sunansa Junaid shi aiki biyu yake yi aikin banki da business, ina son shi sosai kamar yadda yake so na, rayuwarsa abar sha'awa ce wallahi. The last one Awais Shi kuma ɓangaren siyasa yake so amma daddy baya so yanzu dai ya ce yana son zama shahararren ɗan kasuwa ne, sai kuma ni Safiyyerh nima na yi karatu ina aiki yanzu matsayin Manager a FS WORLD INVESTMENT COMPANY, ina da saurayina da nake so kuma yake so na Ashraf sunansa ɗan mai kamfanin da nake aiki ne, akwai wasu abubuwa da bana ganewa a kamfanin..."" Shiru ta" yi da sauri kuma ta kalle shi taga har yanzu idanunsa rufe yake bai motsa ba """Kodayake shikenan, saura kwana ɗaya auren mu da Ashraf ya rasu, Ashraf died ya mutu ya bar ni cikin" "tsoro da fargaba, a ranar daya rasu a ranar ne aka aura mini yayana Aliyu, da dai bana jituwa da shi sam" "amma ƙaddara ta haɗa kuma Ubangiji kaɗai ya san dalilin hakan, wannan shine labarin Safiyyerh Abdu" "Marafa""" "Ta leƙa fuskarsa taga idonsa still a rufe ta tura bakinta gaba ""Nima sai ka bani labarinka ai muna zaune" "waje guda bai kamata bamu san juna ba"" miƙewa taga ya yi ya nufi ƙofa kafin ta bi bayansa har ya fice" daga cikin gidan. "****Eng Ali wali ya dinga kallon Moh da yake tsaye kafin ya ce ""Ina wayar daka amsa wajena? Mene" "amfaninta ina kira baka ɗauka wai?""" """Ba gani gabanka ba?"" Moh ya ce yana kame fuskarsa kamar kodayaushe." """Yarinyar nan tana wajanka ko Mutallab?"" Moh ya yi tsaki a fili da ƙarfi kuma ya ce ""Ni a tarihina sau" "ɗaya ake faɗa mini magana na haddace ka yi batu kawai"" ya ƙarasa maganar yana jawo flask ɗin shayi ya tsiyayi ruwan zafi ya saka madara da su milo ya nemi waje ya zauna ya janyo biredi da plate ɗin ƙwai ya" fara ci duk zafinsa da taurin kan shi a nutse yake cin abinci sai dai baya laumar wasa """Daman kai aka kawowa abincin karin Mutallab? Ai shikenan magana nake so mu yi very important akan" "yarinyar nan daka ɗakko"" ya yi shiru can ya ce ""magana nake maka fa ka yi shiru""" """Kunne ke ji""" """Professor ya raina mini hankali wai ko kashe yarinyar nan zan yi ko a jikinsa yana nufin bai damu da ita" "bane ko mene? To wallahi ni Ali wali zan bashi mamaki, yarinyar nan kafin ya ganta sai ikon Allah don haka ka yi yadda na ce a kanta, ka yi mata fyaɗe ka yi yadda ka so da ita har ta samu ciki yadda zamu watsa labaran yarinyar professor Abdu Marafa ta yi cikin shege ya kore ta daga gida ni kuma na ɗauke ta na kula da ita har zuwa haihuwa,kaga daga nan hankalin jama'a zai yi kan Professor Abdu a bar batuna ni kuma na yi amfani da wannan opportunity wajan cin nasara a zaɓen da yake gabatuwa, don this time ba zan taɓa barin Hon Maɗatai ya yi nasara a zaɓe ba zan yi duk abin da zai tabbatar dani ne na ci zaɓe ko a can hukumar zaɓan inec na shirya tsaf ba gudu ba jada baya siyasa sai ɗan siyasa, harkar siyasa da zama wani a harkar ƙasar nan sai ka nuna ba wani shege ka cire tausayi da imani, ba ri ka ji Mutallab duk wani" "ɗan siyasa kan shi kawai ya sani"" ya numfasa yana ɗaukar ruwa ya sha." "Moh dai har lokacin shayin yake sha hankali kwance abin shi. Ali wali ya duƙa ya ce ""Dole ka yi wa" "Safiyyerh fyaɗe dole ne ka yi wa yarinyar nan ciki, samun cikinta shine plan ɗina na farko da zai kai ni matakin hawa kujerar ɗan majalisa""" """To ya ake cikin?""" """Baka san yadda ake yin ciki ba, ciki na haihu fa?""" """E, ban sani ba""" """Mutallab, da ake cewa ka yi aure a ranar an kashe maka matarka da me za ka yi da auren da ka yi""" """Bayan a yi wa mutum girki ya ci ya yi bacci akwai wani abu ne? To ni ban iya yin ciki ba, sara da soka" "kawai na sani a rayuwa da shiga jeji, ka bar batun hakan bani ba ko waye ba za a yi mata wani abu ba""" """Moh""" """Ali wali"" Mutallab ya ce yana yin kyatsa yana miƙewa tsaye kuma. ""Mutallab yadda aka fara aikin nan" "da kai, to da kai za a ɗora kuma a ƙarashe dole zaka yi wa Safiyyerh fyaɗe i am telling you this, za ka ce na faɗa maka""" """To ka fara bani matarka na yi mata ai kana da ita, sai kace Professor ɗinne ya yi mata"" Ali wali ya dinga" "kallon Moh ganin how serious he is da maganar kuma da gaske yake. ""Ni zan shige zan na ji kira idan ka" "shirya bani matar taka tunda yarinyarka Noor bata ƙasar""" """Ina kasan ina da yarinyar Noor?""" """Ali wali kenan""" Hanyar fita ya yi kamar wancan karan ya ƙara jin sauti mai kama da ihu ya dinga kallon ƙofar kafin Ali wali ya ƙarasu har Moh ya buɗe ƙofar ya shiga cak ya tsaya ganin wata mahaukaciya zaune sai ihu take "ita kaɗai gashinta ya rufe mata fuska ya juya ya kalli Ali wali ya ƙara kallon matar bai yi magana ba ya saki ƙofar zai fita Ali wali ya ce ""Ka manta kaga wannan, sirrina ne""" Ko magana Mutallab bai yi ba ya kwashi kuɗi ya yi waje abinsa yana rufe fuskarsa. Bayan ya fita Ali wali "ya ɗauki waya ya yi kira ana ɗauka ya ce ""an samu matsala P.A yau wani yaga ajjiyata, fitar maganar nan daidai yake da zuwana gidan yari"" ta cikin wayar P.A ya ce" """Kafin ka je gidan yarin ka fara tura wanda yaga ajjiyar taka can""" """Mutallab ne""" """Tab, matsala kenan ina ruwan ciwon idanu wannan yana matsala kuna samun akasi za kaga ba daidai" "ba"" Ali wali ya yi murmushi ya ce ""Ina da tsari P.A idan na tabbatar na ci wannan kujerar zan yi tuggun da za a yi wa Mai dawa ɗaurin rai da rai a gidan yari, ka zo mu yi magana wai kasan har batun ƴa ta Noor ya" "sani, uhm sai ka zo dai""" Yana gama wayar ya duba interview ɗin da za a yi da dukkan wani ɗan takarar ɗan majalisa daka mabanbanta jam'iyyu wanda BBC ke shiryawa hakan yana nufin za su haɗu waje guda da Hon Maɗatai da Dr Abraham Denial David yana da buƙatar ya zauna ya rubuta dukkan abin da zai faɗa a wajan. ***Yana zaune ya zubawa yaron idanu gabaɗaya ba zai shige shekaru biyu da watanni ba a duniya ya yi "wayo gwanin sha'awa duk wanda yaga yaron sai ya burge shi akwai shiga rai da ƙyar yake buɗe idanu saboda farin da yake da shi ya sauke ajjiyar zuciya yaushe zai rabu da damuwar ran shi sai yaushe zai ga Safiyyerh ya nuna mata abin da Ubangiji ya bata, daga samun cikin har haihuwar ba wanda ta sani. A fili ya ce ""Come back please Safiyyerh, where are you ina kika shiga haka me ya sa hakan? Jininki fa" "Safiyyerh haba my innocent Mahmah""" """Ka dinga yin addu'a komai zai daidaita ya zama tarihi Ubangiji yana gani kuma yana kallo ba zai bar" "addu'ar ta tashi a banza ba, zata dawo ta damu ɗan ta, zata dawo a faɗa mata gaskiya, mu ma muna da namu laifin""" """I missed Safiyyerh dear, ki bar ni na koka"" ya ƙarasa ya ɗauki babyn ya rungume a jikinsa hatta farinsa" "irin na uwarsa ne sak yaushe zai ga Safiyyerh ne? Wayarsa ya ɗauka ya yi kira ana ɗauka ya ce ""Har yanzu ba wani information akai ko?"" Ya yi shiru can ya ƙara cewa ""Ka san komai ba, ka san yadda na samu na tsira da raina bana sha'awar komawa kuma ni da aikin lauya har abada, komai namu a can muka baro bani da picture ɗin Safiyyerh ko guda wallahi zan yi ƙoƙarin neman ƙwararren mai zane na" "gani ko za a dace thank you""" "Kashe kiran ya yi ya ajjiye wayar yana sake rungume yaron da ko ɗomin jikin uwa bai sani ba, balle ya sha" nono kamar yadda kowacce uwa ke shayar da nata ɗan. "***Safiyyerh na zaune bayan ta gama musu girki Goje yana ci da sauri yana ƙona harshe ta ce ""Kaci a" "hankali mana akwai zafi"" ya yi murmushi ya ce ""Allah dai ya ba ki kada Manager""" """Amin""" "Suka yi shiru can ta ce ""Wai ba ka ce yayar wannan babban naku ce ta mutu ba? Me ya sa yake zaune a" "nan wai, ina yayenku suke"" Goje ya ce ""Babata ta mutu ni haka baba, shi kuma iyayensa suna nan cikin" "Birget Scorpion ai baya son zuwa gida ko unguwarsu baya son zuwa, tun bayan daya dawo daga gidan yari wajan state cid""" """Kai me ya yi haka to? Kwanansa nawa a wajansu""" """Shekara uku""" "Safiyyerh ta jinjina kai har ranta ta ji tana son cin labarinsa waye shi a hankali ta ce ""Ai daman naga baya" "ji shikenan da wuƙa a hannu ya sari wani wacce kalar rayuwa ce haka?""" "Goje ya ce ""Manager kenan, ai yanayi ne ke sanyawa a zama haka babu wanda ke son zama mutumin" "banza fa, ki gane hakan"". ""Son zuciya dai, Ubangiji daya halicci bayinsa an ce baya ɗora musu abin da ba za su iya ba, a tsaftace halicci kowa tun daga cikin uwa mahaifiya, a nan son zuciya ne da rashin" "wadataccen imani a zuciya da kuma yana da ilimi ai ba zai yi hakan ba"" Goje ya ce" """Ko? Kin san shi ne kin san waye shi? To ki maye masa gurbin abin da ya rasa sai kiga ya dawo daidai idan" "an yi sa'a""" """Me ya rasa shi ɗin?""" """Soyayya, ta uwa, ta mahaifi, ta mata""" """Ok nan wai a haka yana da mata?""" """Ta rasu"" Goje ya ce a taƙaice ta yi shiru ""Ki gwada cewa kina son kiga ki ce za ki aure shi"" da sauri" "Safiyyerh ta kalli Goje ta ce ""Kasan me kake cewa ne? Ina da aure fa ai zunubi ne haka""" """Zance kenan, ba ki da wani aure yarinya haka kalar masu auren take kenan?"" Safiyyerh ta yi shiru ita dai" "ko bata aure shi ba kawai za ta yi using opportunityn ɗin nan ya bata labarinsa, ko a lissafin ƙaddarorinta babu batun zama da ɗan daba balle soyayya har ace aure amma idan har zai bata labarinsa lallai za ta yi wani abu. Ta yi murmushi ta ce" """Kana da gaskiya ka gano ni, ai kaf ƙawayena ni ce bani da aure to bana son gori shine fa nake cewa ina" "da aure shi Captain ɗin ai yayana ne don ka ji, amma kana ganin zai so ni? He is such a arrogant, boring person yana da matsala""" """Ki gwada mana""" """Zan ƙoƙarta, ya sunan shi ok ka ce Scorpion ko?""" """Mutallab sunan shi, mantawa na yi""" """Wow a nice name, sunan shi ya fi shi kyau shine kuje ce masa mai jeji? Kai ya sunanka?"" Ya yi mata" shiru kawai sai ta miƙe ta shige ɗaki. "***A karo na biyu Aliyu ya kalli Commander ya ce ""Sir ka yi replacing nawa da wani mana""" """Aliyu me ya sa kake yin haka, na lura kamar aikin soja ya fara fita daga ranka ko? Ka je ka yi tunanin tun" "farko wahalar daka sha kafin zama abin da ka zama, ƙiriƙiri an ƙara maka muƙami amma ka nuna baka son ana kiranka da sunan muƙamin sai Captain? Why?""" """Sir to a ɗan bani sati guda ok?""" """Ba zai yiwu ba, ka je ka fara shiri cikin daren nan da kwana biyu za a poster ku"" rai ɓace Aliyu ya miƙe" "ya fita bai taɓa Jin takaici da kuma dana sanin zama soja ba a rayuwarsa sai wannan lokacin, shekarunsa nawa a duniya sai yaushe zai cigaba da jurewa yaushe zai ta yin haƙuri baya son shiga cikin ko barrack ne balle a nisanta shi da garin, ya samu sauƙi daga matsalar mata ga kuma wannan matsalar he need his" "wife, seriously he need his Safii yana buƙatar Safiyyerh a gefensa." "Daddy ya dinga kallon Aliyu kafin ya ce ""Aliyu mene plan ɗinka akan case ɗin nan wai? Sp Ghali yana" "neman information ka ja baki ka yi shiru na ce ka cire hannunka a wannan matsalar ko, ka san me hakan yake nufi?""" """Daddy Safiyyerh fa matata ce hakƙin kare ta yana wajena so allow me to do daddy ka rabu dani""" """Allow me to do daddy"" daddy ya maimaita ya juya ya kalli Ummimi dake zaune tana kallon Aliyu ya ce" """Kin gani ko Zahiyerh idan Aliyu ya saka na rasa Maama zai yi mamakina"" murmushi kawai ta yi ta ce ""Matarsa ce fa, ta ya ya zai yi wasa da ranta bayan yana buƙatar ta cikin tasa rayuwar, bana son wani magana mai tsayi da bayane babu mai yi wa Safiyyerh kutse a rayuwarta ka sani, su yi nasu binciken" "shima ya yi""" """Aliyu bar wajan nan""" "Fita ya yi rama rasa wanne kalar tunani zai yi, daddy ya lumshe idanunsa a fili ake ganin bugawar" "zuciyarsa bai shirya ba sam, baya jin kuma akwai abin da zai iya kawo masa cikas bai yi maganinsa ba." Daddy ya gargaɗi kowa akan kar a fitar da maganar sace Safiyyerh kwatsam zance ya fita a shafin daddyn "wanda shi kansa bai san yaya aka yi ba, wayarsa kullum na hannunsa balle ya ce wani ya ɗauka ya yi posting cikin yaran, ya tabbatar kuma ba hacking wayar aka yi ba, aka fara kiran wayarsa domin tabbatar" da gaskiyar al'amarin ya rasa ya ya zai yi kawai ya ɗauki wayar ya kashe. ***Mutallab na zaune yana sauraren Goje Safiyyerh ta fito ta saka hijabi har ƙasa bai kalle ta sai haɗe fuska da ya yi ta ce """Abokina Goje barka ya jiki naga an yi maka treatment, ku siyo ka yayyenki na dinga yi muku tunda dai" "dabar ya zama dole na iya ai"" murmushi ya yi" """Na ɗauka lissafin kuɗi kawai kike ai? Ashe likita ce""" "Ta yi murmushi ta ce ""Ina yini?"" Ta faɗa tana kallon Moh ya yi kicin-kicin da fuska bai amsa ba." """Wallahi kyau kake mini idan kana haɗa fuskar nan, na ji ina son ka kuma zan iya aurenka wallahi"" ya" juya ya kalleta da sauri ta kashe masa idanu ɗaya ta ce """What if I tell you, I love you?"" Ta sake cewa" """Idan fa ka amince zan so ka har numfashina na ƙarshe a duniya, kawai dai kar ka wulaƙanta ni""" """Ke bar nan""" "Ya furta a kausashe kamar ya ce ya shiga uku ""Na san saboda na ce maka ina da aure ne, wasa nake yi" "don kar ku yi mini wani abun ne na faɗa fa, trust me i love you kuma na ji zan iya aurenka a yadda kake, zan baka farinciki walwala da jin daɗi ka amince mini ka ji dear"" Moh ya dinga kallon ta wani irin kallo wanda bai ma san yana yi ba,sai dai ba'a tantance kallon na mene yanayin fuskarsa bai bada damar hakan ba, kaifin idanunsa ya saka Safiyyerh ƙasa da nata idanun, duk da shaye-shayen da ya ke yi da ɗaukar wuƙa matsayin abokiyar rayuwa da tarin raunukan da suke fuskar bai hana wani irin tsoro da shakkarsa ta gitta a zuciyar Safiyyerh Abdu Marafa ba, wani kwarjinin take hango wa na musamman a fuskar Mutallab Tahhb haibarsa da kwarjininsa mai ban tsoro ga namiji balle ɗiya mace sai yanzu take ji ta yi tsaurin idanu wajan tunkarar shi da wannan maganar mai kama da tatsuniya a gare shi, gare shi kallon kin raina mini wayo ya kewa Safiyyerh da tunanin ko ta samu matsala da nata tunanin tunanin ne? Idan ba matsala ta samu na gushewar tunani ba abu mamaki ne gare shi da jin furucinta ya yunƙura zai" tashi ta riga shi miƙewa kanta a ƙasa hawaye na zuba a idanunta. """Don darajar da Allah Ya yiwa Manzon Sallallahu alaihi Wasallama ka saurare ni, ba zan taɓa juya maka" "baya ko da nasani b a kasancewa ta da kai, kai musulmi ne nima musulma ce babu haramci idan mace ta ƙaunaci namijin daya kwanta a ƙasan zuciyarta, a kullum na ganka sai na ji zuciyata na kiran Safiyyerh wannan shine ƙaddararki zaɓin da kike jira irin namijin da kike fata, idan zuciyata ta kusanci zuciyarka sai na ji tawa zuciyar ta sake buɗewa da tarin tausayinka, kullum mutuwa nake da farfaɗuwa da soyayyarka ta yan kwanakin nan data rutsa da zuciyar Safiyyerh Abdu Marafa, kullum mutuwa nake da son ka, wallahi...,"" kasa cigaba ta yi saboda kukan daya ƙwace mata da gaske, da ace ita ƴar wasan kwaikwayo ce irin fina finai da ake haskawa sai ta ce a yanzu acting take, duk abin da take faɗa she doesn't mean it, iya laɓɓanta ne kawai ta yi hakanne saboda ta yi kutse cikin rayuwarsa ta san waye shi me ya sa ya zama" "abin da ya zama, tana son jin labarai mai kama da hikaya ko almara ko na soyayya." """Will you love me?"" Ta ce tana marairace masa fuska tare da ɗan turo masa jajayen cute lips ɗinta, ya bi" lips ɗin da kallo ta haɗe hannaye waje guda ta langwaɓar da kai """Please, Safiyyerh loves you a nan a cikin nan ɗina""" Ta nuna masa saitin ƙirjinta wajan zuciya da yatsarta manuniyya sai ƙifta idanu take. Har lokacin bai ce mata komai ba kamar yadda ta lura yawan magana ba ɗabi'arsa bane yana wanzuwa da shiru da tunanin ya fi masa. A duk maganarta ɗaya ƙare haɗe fuska yake yi ya zaro sigari ya kunna ya saka a baki da ƙarfi ya zuƙi hayaƙin yana jin saukar hayaƙin ƙasan ƙirjinsa ya hura kumatu ya matsa dab ya fesa mata a fuska ya yi gaba abin shi yana taku ɗaiɗai irin he don't care. Safiyyerh ta bisa da idanu ta yi shiru ta ji ta damu sosai a ranta tana Astagafirulla data tuna da gaske ita matar aure ce matar Aliyu Abdu Marafa ce ita halaliyyarsa ta jingina da jikin bango tana lumshe idanunta. "Moh bai ƙara dawowa cikin gidan ba, har dare ya nutsa bama shi ɗaya ba kusan dukkan su basa nan ta" "dinga sallah tana addu'a har girki ta yi musu ta ajjiye amma ya yi sanyi. Tana haka ta ji an buɗe gidan da sauri an shigo ta buɗe ƙofa ba tsoro ta fito Mangal sai nishi yake yana kallon ta, da gudu Goje shima ya shigo yana shigowa kuma ya rufe ƙofar ya zube a ƙasa ta kalle su cikin sigar damuwa ta ce ""Ka rufe ƙofar" "shi kuma fa?""" """Bai shigo ba?"" Ta jinjina masa kai ya miƙe tsaye ya ce ""Jagwal kenan, ai kuwa bama tare""" """Innalillahi kamarya like how bakwa tare?""" """Ke bafa wani abu saɓe kawai ki je ki yi kasa ko"". ""A'a don Allah ka je ka nemo shi ka ji ɗan'uwanka ne fa" "idan wani abu ya same shi ai ba za ka ji daɗi ba, shi ma ba zai bari komai ya same ku ba"" ya yi murmushi ta lura yana da fara'a ba kamar sauran ba ""Ubangiji nada kyakkyawan tanadi a rayuwar Mai dawa, ba" "yanzu zai mutu ba kin ji ko?""" """Na kawo muku abinci?""" """Dar daidai kenan kin taimaki ƴan hanjina jagwalo shi nan a ɓatar da shi a rufawa ciki asiri"" abincin ta" "ɗakko ta kawo musu duk yadda taso su wanke hannu ƙi sukai Kodayake haka ogan nasu shima yake. Har bacci ya ɗauke ta bata saka shi a idanunta ba. Sai da asuba ta fito dafa ruwan wanka kamar jiya haka ta ganshi ya yi shiru yana kallon sama, tunanin maganganun da Abbasa ta yi masa yake da abin da Ali wali" ya dinga nanata masa akan Safiyyerh. """Bai kamata gwarzona ya wanzu yana tunanin da zai iya illata masa rayuwarsa da zuciyarsa ba, haba" "mafaraucina"" ya juya ya kalle ta, ta kashe masa idanu ta ce ""Yes, ba farautar dabbobi kawai ka iya ba ka yi dacen farautar zuciyar ƴar Professor Abdu Marafa"" kamar a buge yake haka ta lura da shi musamman yanayin zaman da ya yi, sai a lokacin ta lura da yankan dake damtsen hannunsa ta ƙarasa ta duƙa ta ce ""Subuhanallahi faɗa ka je ka yi haba mai sunan manya, Muhammad Mutallab fa masu sunanku salihan" "banyi ne""" "Ya duƙar da kan shi ƙasa ta je ta ɗakko kayan da Goje ya kawo ta zauna dab da shi, ta kamo hannun nasa" "sarai ya jita amma bai kula ta ba, tunani ne ya addaba masa. Ya shiga hura masa iskar bakinsa ganin" yankan na kumfa data saka magani ta gama yi masa treatment ta kalle shi taga ya rufe idanu miƙewa ta yi zata fita kamar daga sama ta ji ya ce """Cikakken sunanki""" """Safiyyerh Abdu Marafa""" """Cikakke"" ya sake maimaitawa ""Haka sunan yake fa Jarumi""" """Shi Abdu?""" """E, sunan daddy kenan Abdu"" ya buɗe jajayen idanunsa ya watsa mata su ta yi saurin yin ƙasa da nata" "idanun ta fidda ran zai yi magana har zata juya ya ce ""Ƙarya, idan na tuna miki na kwaɗa miki mari ko?"". ""Allah ni dai haka na sani babana ne fa""" """Uhmm"" ganin kamar da magana a bakinsa kuma a buge yake ta matsa ta zauna ta ce ""Jarumi, do you" "want to say something? Say it. Ka ce wani abu Jarumi""" """Faɗi mana Jarumi""" """Tiger"" ya ce a hankali ta ce ""Me ka ce? Ban ji ba""" """Ammm, hmm kika ce ba ki da aure?"" Ta ce ""E, bani da shi like a told you"" ya buɗe ido ya zura mata" "idanu yana ta kallon ta da ƙyar ya iya cewa ""za ki so ni?""" """Zan aure ka na rayu da kai idan ka faɗa mini labarinka waye kai?"" Ya sake yi mata shiru ""Ina ji""" """Zana ba ki labarina idan za ki aure ni""" """Ni Safiyyerh na yi maka wannan alƙawarin zan rayu da kai a duk yadda rayuwa ta yi da kai Jarumi"" ya" "miƙa mata tafin hannunsa a hankali kamar mai jin tsoro ta kalli hannun cike da rashin fahimta, jiran ba'asi take shi kuma ya yi shiru sun ɗauki minti biyar da wasu daƙiƙo a hankali ya sake furta ""Promise"" ta dinga kallon hannun kafin ta yi Astagafirulla da tunanin Ubangiji ya yafe mata saboda igiyar auren wani ce a kanta ta ɗora ɗan ƙaramin hannunta cikin nasa, tana sawa ya damƙe kamar abin da yake jira kenan ya yi shiru ya lumshe idanunsa muryarta na rawa ta ce ""I Promise you Jarumi"" yana riƙe da hannun bai cika ba bai kuma yi magana ba can ya sake ta, ta fara masa magana sai dai ko tari bai kuma yi ba" tunaninta bacci yake yi ta dinga kallon shi tana son hango kyau ko ko muninsa. A daren ranar su Goje basa nan sai shi ɗaya yana busa hayaƙi a sama yake jinsa sosai ya ji an buɗe ƙofa "an shigo, maza ne har su huɗu sun rufe fuskokinsu ya damƙi wuƙarsa kafin ya miƙe ɗaya ya cafki wajan yankan da Safiyyerh ta gyara masa ya janyo hadda naman wajan suka fara kokawa yana buga su da ƙasa, cikin sauri Safiyyerh dake bacci ta farka zata fito daga cikin ɗakin ya yi baya da ƙarfi ya tura ta ciki ya rufe ƙofar ta taga ta leƙo tana kiran shi, taga ya ɗaga wuƙa ya sokawa ɗaya a gefen wuya ya ƙara soka masa a ciki ya watsar da shi can gefe yana kakari, Safiyyerh ta zaro idanu tana rufe baki saboda ihu za ta yi ganin yadda aka yi kisan kai akan idanunta, bata san mene ya faru ba taga ɗaya ya zaro sirinjin allura ya zirarawa Moh a damtsen shi, ya sake zaro wani ya yi masa da azama Moh ya ɗaga wuƙar hannunsa ya sari wanda ya yi masa hakan ya goce ganin sun yi masa allurar suka ja wanda yake kwance kamar gawa" "suka bar gidan, a hankali ya yi baya ya zube saman kujera jini na ɗiga jikinsa" "Ilahirin jikin Safiyyerh rawa yake cikinta ya ƙulle ta shiga uku, kisan kai aka yi akan idanunta haka dabar" "take dama? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Moh kuma minti goma ya yi yawa ya ji zufa na yanko masa jikinsa ya yi sanyi wani irin baƙon al'amarin ya fara ziyartar gangar jikinsa yana sauka a mararsa, abin da bai taɓa tunani ba idanunsa ya shige ciki ya ɗauki ƙwaya ya zura a ƙasan harshen shi da tunanin zai daina ji, amma ina kan shi ya hau ciwo ya miƙe da ƙyar ya nufi ɗaki jin tsigar jikinsa na miƙewa da zubewa sanyi na ratsa shi komai na jikinsa ya bubbuɗe al'amarin buƙatuwar wani abu. Ya kwanta ya yi shiru can ya mirgina ya yi rufda ciki ya lumshe idanunsa ya jiƙe shimfiɗar lokacin ɗaya da zufa da jinin da yake zufa a jikinsa, ya rasa ciwon ciki yake ko mara ko zazzaɓi? Jijiyoyin kan shi sun miƙe raɗau lallai ya ji akwai abin da yake buƙata ya dinga juyi ya shanye sigari kwali wajan biyu amma ba abin da ya sauya ba zai ce" tsautsayi ne ya kai shi ɗakin Safiyyerh ba saboda kawai tsintar kan shi ya yi a ciki. Safiyyerh na bacci ta ji hucin numfashin mutum a fuskarta ta buɗe idanu da sauri ihu za ta yi ganin "fuskarsa kamar zai haɗe da tata ta yunƙura zata tashi ya saka hannu ya mayar da ita kwancan ""Dan Allah" "karka mini komai ka yi haƙuri ba zan sake kula ka ba, innalillahi na shiga uku daddy ka yi na tuba don" "Allah"" bai kulata ba yana daga durƙushen da yake dab da ita ya miƙa hannu ya kashe wutar ɗakin gabaɗaya." LAST FREE PAGES Waye Mutallab? Waye Scorpion? Wace Safiyyerh? Waye Daddy? Mene FS WORLD INVESTMENT COMPANY? Labarin Mutallab da tarihinsa ya fi wannan da muke ciki yanzu ai za ku zo jin wannan soyayyar ta ƙuruciya ba? Mene yake saka a fara daba da shaye-shaye? Wanne ganganci iyaye suke yi akan yara? Mece siyasa da cikakken tarihin dimokuraɗiyya? Za ku su sanin ya ake mulki a ƙasar nan? Har ku yi supporting yaran ku? Soyayya na saka shaye-shaye ne ko daba? Me ya sa Mata har uku suka mutu ta sadanadin MOH me ya sa ya kashe matarsa SAFIYYERH? YAUSHE SAFIYYERH TA HAIFI YARO? maza hanzarta yin payment chat with me on WhatsApp 08164069385 BRIGHT PENS... 2ND BATCH "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: Chapter 16: You're my destiny" "“Don't touch me” Safiyyerh ta ji saukar husky voice ɗinsa cikin kanta, sautin ya ratsa jiyiyon" "ƙwaƙwalwarta ya sauka har tsakiyar ƙahon zuciyarta da take bugawa, ban da ta san bai iya turanci ba tabbas za ta ce the voice is belong to him kai tsaye, tuna cewa shi ɗan daba tantiri ne kuma ɗan ta'adda uwa uba kidnapper ya saka ta tattara shakkunta a kan shi zuwa gebe, hasken ɗakin ta kunna har lokacin jikinta rawa yake ta juya a hankali ta dube shi, duba na tsanaki ya kifa kansa tsakanin ƙafafuwansa tare da tura hannunsa ya matse ƙafafun da kyau, jikinsa na wani irin ɓari domin har naman jikinsa rawa yake ya haɗa uwar zufa dukkan wata jijiya ta jikin nasa sai da ta bayyana tana amsar yanayin da ya shiga." Wani abu mai kama da tsoro ya ruski zuciyar Safiyyerh muryarta na rawa ta dube shi """Baka da lafiya ne Jarumi? Meke damun ka?"" Ta jera masa tambayar amma ko motsi bai yi ba, balle ta" "saka ran amsawa ta matsa kusa da shi tana leƙa fuskarsa amma ko idanunsa bata hango ba sai jijiyar kansa dake harbawa, wani abu ya gilma a ƙirjinta ta ji kamar zuciyarta ta motsa, motsin da bata san na mene ba a raunace ta ce" """Talk, ka faɗa mini meke damunka abinci za ka ci? Ko tea zan haɗa maka?"" Duk ta rikice musamman jinin" dake zuba a jikin nasa wanda ana ɗaukan wani lokaci komai zai iya faruwa ta miƙe cikin sauri ta bar ɗakin ba jimawa ta dawo hannunta riƙe da Frist acid box da Goje ya kawo ta shiga fito da kayan ta matsa dab da shi duk da zuriyarta cike take da tsoro ta saka hannu zata ɗaga rigar jikinsa ta ji ya ce """Shhhh, kar ki taɓa ni""" """Kamarya kar na taɓa ka, salon ka mutu Allah ya kamani da laifin salwantar da rai, i am Safiyyerh the" "whole manager mai sarrafa biliyoyin kuɗi, amma hakan baya nufin bani da imanin da tausayin da har zan zuba maka idanu jininka ya tafi a banza ba, kuma wa zai so rasa jarumi? Kai Jarumi na ne, don haka ka" "tsaya now i am a doctor don't move"" ta yi maganar in a serious tone." """Kar ki taɓa ni"" Moh ya sake tattara dukkan ƙarfinsa wajan sake maimaita furucin da ya yi har lokacin" "kuma bai ɗago kai ba. Safiyyerh mamakin yadda ta ji muryarsa na fita a hankali ta yi, ba rauni a cikin sautin sai zallar buƙatuwa na wani abu sai sake curewa waje guda yake. ""Nifa bana gane ma'anar na rabu da kai, mene a jikin naka banda sara da suka? Haba jarumi ba'a san irin ku da rigima ba, ko kuna rigima ai bakwa yi wa mace"" ya yi shiru bai tanka ta ba, ta san kuma ba lallai ya sake cewa komai ba sun" fi minti goma a haka can ta ji ya ce """Naaa, switch off the lights"" ta juya ta kalli hasken ɗakin ta kalle shi da garjejen jikinsa" """A'a haske ai rahama ne haka kawai na kashe ban san me zai faru ba,daga ni sai kai? Ka bari na dinga" "ganin komai ina yi maka dressing ina kallon rigimammiyar fuskarka"". ""Kee, kika taɓa ni duk mai ne yi miki ko ya biyo baya shikenan"" ya ce yana ɗago kansa, wani irin fitsari ta ji ya ɗaure mata mara yana mintsininta ba ƙaramin tsoro idanunsa suka bata ba, ta karanci psychologist ko ta nutsu lallai zata iya hango hutar feelings ɗin da yake yawo cikin idanunsa ya kaɗa ya yi jawur. Safiyyerh ta yi saurin ja baya tana ɗaga hannunta sama tare da girgiza masa kai ""Laaa la la, nama fasa yi maka treatment ɗin yi bacci" "abin ka""" "A hankali komai na idanunsa yake warware wa daga maye zuwa wani abu nada daban, wanda yake da" "tabbacin ko mene abin da yake ji, lallai yana wajan Safiyyerh, a wajan Fiyya zai samu he just look at into her eyes, ya dinga kallon jikinta daga sama har ƙasa, ba wai relief yake samu ba, wani irin processing ƙwaƙwalwarsa ke yi masa a hankali ta fara masa tunanin wani long term memories daya shuɗe wanda yake zane daram a idanun zuciyarsa yadda take tsaye a gabansa haka wancan lokacin, kamar kuma" yanzu ne take tsayen idanunta cike da hawaye..... "**** “Idan mutum na zama ƙaddarar mutum, lallai kai ne tawa ƙaddarar, you're nothing but my destiny," "a ƙirji nake jin duk zafin abun, a nan nake jin ciwon"" ta nuna masa tsakiyar ƙirjinta inda zuciyarta ke harbawa, hawaye na cigaba da zuba daga cikin idanunta. Yana zaune saman kujera saboda lokacin break ne, gudun haka ya saka ya keɓance kan shi yana avoiding ɗinta. Yana jin kukan nata ya kasa ce mata" komai sai ƙafarsa da yake kaɗawa a hankali yana gyara zaman goron dake damtsen hannunsa. """Zan iya mutuwa, ko sai na mutu ne zaka ji kana so na? Don't let that happen, ka daina wasa da feelings" "ɗina kana wahalar dani har ciwo na yi satin daya shige"" ta ɗan langwaɓar da kai gefe alamar tausaya wa tana tura masa bakinsa gaba. ""Ba kaga na rame ba?""" """Da kin mutu, zan fi jin daɗi"" ta bubbuɗe idanu waje ta juya ganin ba wasu students da sai ta ji kunya" "domin ya gama yarfata. Kafin ta yi magana ya juyo gabaɗaya ido cikin ido yake yake kallon ta muryarsa ba wasa ya ce ""Yama sunanki? Ina ji zan haƙura da cikar burina na bar makarantar nan saboda ke, kin takura rayuwata kin ƙuntata ni kin hanani sukuni, wai so hauka ne? Da za ki gane yadda nake jin zafi a tawa zuciyar a duk sanda kika kalli cikin idanuna kika furta mini wai kina so na, are you crazy? Are you mad? Wai iyayenki daman soyayya suka kawo ki ne ki yi a school ɗin nan ko karatu, babban takaicina kamar ni ƴar ke ki addabe ni da so? Har nawa kike yaushe aka haife ki? Shekararki nawa a duniya? Irin ku" "ne guntattakin yaran nan masu rawar kai, mace har mace ba aji, what a stupidity? Are you not Ashamed?" "Oh irin ku ne wanda last subject teacher ya yi bayani akan yara masu tashen balaga?...""" "Maganar yake yana runtse idanu, har zuciyarsa yake furucin cike da takaici kuma yake zuba mata" "narkakkun idanunsa, ita kuma kan ta a ƙasa hawayen ma ya kasa fita daga cikin idanunta, sai yanzu ta san cewa kuka rahama ne kuma yana cikin abu mafi sauƙi da yake samar da sukuni a zuciya bata farfaɗo daga maganganun da yake gasa mata ba ya ɗora da. ""Laa, ba za ki lalata mini ƙuruciya ban cimma komai a rayuwa ba, ni dai ina roƙan ki saboda iyayenki ki dai na bibiyata kina manne mini kamar kaska, kai ni ba zan taɓa manta tarihin makarantar nan ba, zanen ƙaddarata baya cika daidai sai an saka sunan wannan makarantar oh, bawan Allah Na Ammo"" ya yi maganar very serious, da tunanin ya yi ending tare da solved na problem ɗin shi da ita, ai da sauri ya buɗe manyan idanunsa jin gabaɗaya ta shige jikinsa ta rungume shi numfashinta na wani irin fisga, afa secondary school suke? Ya ilahil alamin, wannan ta zame mishi jarrabwa ya dinga ƙoƙarin rabata da jikinsa, ta yi masa wani irin riƙo a tight hug wanda ya fito daga can ƙasan zuciyarta hakan ya sa ta fara jin sassauci saboda ɗan ƙaramin connection ɗin da suka samu ""Shikenan, zan barka zan haƙura da soyayyarka kafin nan ai na ji an ce kana aiki kai Ɗan'malam ne, na roƙe ƙa da girman Allah ka yi mini aikin da zan manta da kai a rayuwata, zan manta da kamanminka a ko a cikin baccina, ka yi mini wannan alfarmar"" fisgeta ya yi daga jikinsa, saboda ya fara jin developing" "feelings towards opposite sex yana attacking nasa wannan da akai musu magana a matakin Adolescence, bai jira komai ba ya watsa mata yatsu biyar a fuska yana poiting hannunsa zuwa gare ta ""Haka kika ce?" "Za kiga aikin Ɗan'malam za ki manta da ko sunana ne completely a rayuwarki"" a lokacin har students sun" fara bayyana a wajan ta tsuguna a wajan muryarta bata fita sosai ta ce "“I love you beyond words, I love Mutallab”" "***Kau! Kau! Safiyyerh ta ji saukar maruka a fuskarta, bata san yaushe ya miƙe har ya matse ta a jikin" "bango haka ba, sai numfashinsa ta ji mai sauka da warin sholin daya sha, wani abu na bugarta ta kasa magana. Kamar yanzu ne haka yake jin abin abin saboda abubuwa da suka masa yawo a zuciya ya dinga kallon cikin ƙwayar idanunta ƙirjina na buɗewa da ƙyar ya iya gwame numfashi ya furta" "“Good, kin mata ɗin completely?""" """Me ɗin? Ya zaka matse ni a jikin bango kana na manta, amai nake ji zan iya yi maka a jiki"" da ƙyar take" "iya maganar, ta zame idanunta daga nasa ba zata jure kalla ba ko kaɗan ""Wai wanne irin abu ne haka? A karan farko ka caka mini wuƙa, again kazo har gida ka sace ni, yanzu ka mare ni ban yi maka komai ba, ka mayar dani gaban iyayena ka rabu dani duk abin da kake so zan baka, ina da kuɗi a lot of money, na gaji da zama da ƴan ta'adda mashaya, soyayyar ma na fasa allow me to go don girman Allah""" """You builds and destroys everything""" "Kamarya? Ta tambaya a ranta ita sam bata ganewa ""Who are you,waye kai? Me kake nufi""" """Fita"" ya ce da ƙyar da ƙyar yake motsa ko yatsarsa ne, banda cewa shi ne abin ya faɗa masa yana da" "yaƙinin da ita ɗin ce da tuni ta jima da ya yi masa fyaɗe, wani irin zafi yake ji yana keto ruɓu bakwai na farar jikinsa ya buɗe bakinsa kamar zai magana sai kuma ya hura mata warin abin da take gudu da gayya, gabaɗaya kayan cikinta suka hautsi ne, ya kasa motsi balle ya bata hanya idan har ya ɗaga hannunsa lissafin ne zai sauya, Fiyya ta dinga kakarin amai ta saka dukkan ƙarfinta wajan ture shi amma ina, ko motsi baya yi baya ya zai matsa cikin rashin sa'a kuma jiri ya kwashe shi da shi da ita sukai ƙasa, ita ta fara faɗuwa ta fasa ihu shi kuma ya faɗa jikinta azaba ta saka kawai ta saki kuka wani irin ɗaci take ji a ranta ta dinga ture shi, ya yi shiru sai sauke numfashi yake ya fi ƙarfin minti ashirin kafin ya janye jikinsa cikinsa ya miƙe tsaye ya nufi waje idanunsa rufe, Safiyyerh ta dinga kuka ta cure waje guda tana ja masa" Allah Ya isa kafin kuma ta fara sheƙa amai kamar ta mutu. "Yana fita ya ja kwalin sigari ya dinga zuƙa yana fesarwa, komai yake baya jin daɗi bashi da nutsuwa sama" da shekaru uku kenan. Yana ji aka fara kiraye kiraye amma ya kasa motsi zuciyarsa sai magana take yi masa ita kaɗai. ****M. General ya dinga kallon Aliyu da mamaki fuska kuma a haɗe cike da gargadi da takaici da kuma "nuna dole sai ya yi abin da ake so ya ce ""MAJ, domin ba zan iya ce Captain ba gwara na faɗa maka asalin muƙamin da kake da shi a yanzu, da farko ka faɗa mini hujjarka na ɓoye matsayinka a aikika wa danginka da mutanen jiha da ƙasa? A.A MARAFA ko ka manta wahalhalu da ɓata lokacin da ka yi akan uniform ɗinka da aikinka? Gashi yanzu dama ta sameka na ƙarin wani Matsayin kake wasa da wannan" "opportunity ɗin are you okay?""" """Yes, i am""" """Your not serious MAJ, dole ka je fa kama fara shiri tun yanzu ina ɗaga maka ƙafa ne saboda dalilai da" "yawa banda haka uhm"" M.General ya yi shiru yana kallon MAJ Aliyu wanda yake amsa sunan Captain saboda wani dalili." """Sir, ba lallai ku fahimta ba akwai nauyin daya hau kai ne ina buƙatar sauke shi, ka yi mini afuwa a sauya" "sunana""" """Saboda matarka?"" Kai tsaye Aliyu ya ce ""Idan ka ce hakan ba laifi"" Ya jinjina kai can ya ce ""This is serious," "mace ta shigo rayuwar MAJ, idan ka manta bari na tuna maka ka yi karatu a NDA Nigerian Defense Academy, wa'adin shekara biyar ka yi a makarantar lokacin yaye ɗalibai ka fita da igiyar farko zuwa SND LT second Lieutenant matsayi mai tambarin star ɗaya kenan, daga nan ka je course zuwa Taraba state for 6month bayan ka dawo ka samu matsayin Lieutenant LT tambarin star biyu, bayan nan ka yi shekara huɗu ka samu matsayin Captain CPT tambarin star 3, daga nan ka ji shekara huɗu ka yi course da exam ka tsalleke wannan matakin, ka samu matsayin Major MAJ, tambarin tsuntsu ɗaya"" M.General ya yi shiru" yana juya kujera """Matsayin da mahaifinka bai san da shi ba, ka nemi alfarmar ɓoye sunanka shekaru kenan kana a" "matsayin MAJ, yanzu dama ta sameka an yi posting naka zaka je Jaji Military cantonment Kaduna za ka yi course na shekara ɗaya, da zarar kaci ka haye ka samu igiya ta gaba idan baka samu ba ka maimaita, Aliyu matsayin LT COL kake shirin rasawa fa? Ka san matsayin LIEUTENANT COLONEL kowa?""" """Na sani""" Aliyu ya ce fuskarsa ba walwala kamar ya ce ya shiga uku M.General ya buga table ɗin gabansa ya ce """Stupid dole ka je ko ka fuskanci hukunci, wannan sunayen daga wajan Lieutenant General ya fito sun karɓa ta hannun Chief of Army staff ne kuma, wallahi MAJ ka kiyaye kan ka daga sharrin sojoji malam get lost mumu"" Miƙewa Aliyu ya yi rai ɓace ya fice zuciyarsa a cunkushe. Yana fita MG ya kira waya ba" "jimawa aka ɗauka cikin girmamawa ya ce ""Done Sir"" haka kawai ya ce ya kashe wayar ya ajiye." MAJ Aliyu na isa gida a main parlo yaga jama'ar gidan da jami'an tsaro ya ɗan tsaya ya kalli Ummimi ya "kalli daddy da Ummi sai kawai ya nufi part ɗinsa ""Aliyu"" ya ji kiran Daddy hakan ya sa ya tsaya ba tare daya juyo ba cikin takaici Daddy ya ce ""Me kake shiryawa? Aliyu idan ka yi making any mistakes ka saka aka kashe mini yarinya wallahi zan baka mamaki, na ce ka cire hannunka daga wannan maganar kaƙi ko?"". ""Daddy me kake so na yi?"" Kai tsaye ya ce ""Ka cire binciken da kake akan wanda suka sace mini" "Maama, ka bar hukuma su yi aikin su ga Sp Ghali nan zai yi abin da ya kamata, ka ji ko""" """Shittt, ka san ciwon da ka saka mana a zuciya a yan kwanakin nan ni da Safii Daddy? Ka san me muke ji" "a cikin ran mu? Kasan fargaba da zullumin daka saka zuciyoyinmu, ka san halin da ɗayan mu zai shiga iya ya kasance ba kai ne wanda ka haife wani daga cikinmu tsakanin ni da Safii, idan mu duka ranka ne na san na yi ilimi daidai gwargwado babu aure tsakanin sister and brother, idan ba haka bane ni ne ba ɗanka ba ko Safiyyerh? Tell me daddy, ban san komai na ka aura mini Safii without my knowledge na yi" "accepted auren itama ta yi, bamu soyayya a zuƙatanmu muna ƙoƙarin fara ginawa, an zo an ɗauke mini" mata har gida sai na naɗe bakin hannu na yi shiru? bayan inda da damar kuɓutar da ita? Safii daddy my "wife, ashe ma Aliyu bai amsa sunan soja ba, su yi aikin su na yi nawa"" tunda ya dawo gidan da ƙasar, bai yi magana mai tsayin haka ba sai huci yake, idanun Ummi cike da hawaye ta ci kuka ta gode Allah wasa wasa sace Fiyya na neman zama babban abu gashi shiru ba amo ba labari. ""Aliyu ka san ba zan cutar da" "kai ba ko? To ka yi abin da na ce ka basu information na yadda aka sace ta""" """Uhmm""" """Ina magana kana uhm? Aliyu ni, ni ko Aliyu mahaifinka?""" """Daddy zan basu information ɗin kafin nan ka fara amsa mini tambayoyina, Daddy waye ni Aliyu? Wace" "kuma Safiyyerh? Ya akai batun sace Safiyyerh ya fita a wayarka? Mene ya saka aka ga motarka a ranar da aka caka mata wuƙa? Daddy me ya sa kukewa Safiyyerh allura? Wacce kuma allura ce? Daddy ya akai ka aura mini Safiyyerh a ranar da saurayinta wanda zata aura Ashraf ya rasu? kuma me ya saka yanzu kake son na janye hannuna daga binciken sace matata, matar soja ni MAJ A.A MARAFA?"" Daddy ya dinga kallon Aliyu da tarin mamaki musamman jin muƙamin MAJ ya fi komai gigita shi da bashi mamaki. ""Aliyu ina son ka saki Safiyyerh yanzu ba sai anjima ko gobe ba, ina son ka sake ta tunda idda bata hau kan ta" "ba""" """Divorce? Safii zan saka daddy me ya sa?"" Daddy ya ce ""Daman ni na aura maka ita baka sani ba, yanzu" "kuma na sace ka sake ta bisa umarmina ka sakar mini yarinya yanzu now"". ""Over my died body, idan akwai rabuwa to mutuwa ce zata raba ni da matata Safii, idan kuma kana son na sake ta ka bani amsar duk tambayoyin da na yi maka"" yana cewa haka ya juya kamar zai tashi sama, Ummimi ta bisa da idanu tana girgiza kai. A wannan karan Daddy ji ya yi ciwon gaske na neman kama masa zuciya ya yi baya cikin" sauri Dr Hash ya riƙe shi yana zaunar da shi. Sp Ghali ya ce """In sha Allah Safiyyerh zata dawo gida na maka wannan alƙawari, kuma duk wanda muka samu da saka" "hannu wajan sace ta zai girbi hukunci daidai abin da ya aikata, zamu tafi zuwa anjima ko gobe zamu dawo duka ma'aikatan ɓangaren gidan Captain suna hannunmu, babban abin damuwar bincike ya sake nuna mana bayan wanda suka sace Safiyyerh akwai tabbacin zuwan Scorpion wajan lallai ya kasance a" "wajan""" Kasa magana Daddy hakan ya saka Sp Ghali da shi da team ɗinsa barin gidan. Daddy ya juya ya kalli "Ummi dake kuka kamar ranta zai fita kafin ya yi magana ta miƙe ta bar wajan, J ma ya fice daga parlon" "Ummimi ta kalli daddy ta ce ""Professor mene haka? ka tabbatar Safiyyerh ta dawo cikin ƙoshin lafiya"" ta" "miƙe da ƙyar tana haki ta nufi part ɗin Aliyu ta same shi yana haɗa kaya ta nemi waje ta zauna ta san komai zata ce ba zai yi magana ba yana gama haɗa kayan ya ɗauki jakarsa ya kalle ta ya ce ""I will leave""" """Where?""" """Zan dai tafi""" """To ka sakar masa yarinya ka ji ko Gadanga"" ya dinga kallon Ummimi can ya ce ""Ok ni ne ba ɗan shi ba" "kenan?""" """Yaushe na ce haka?"" Bai magana ba kawai ya ɗauki jakarsa ya yi waje tana ta kiran shi ya yi mata banza" "ya yi gaba. A harabar gidan ya ci karo da Dr Hash, dr ya yi murmushi ya ce ""Babban yaya ba dai tafiya ba?"". ""Ka faɗa mini wacce allura kakewa Safiyyerh,kuma akan wanne dalili?"" Dr Hash ya ce ""Na faɗa maka Daddy zaka. "" Wani irin wawan mari Aliyu ya saukewa Dr Hash yana nuna shi ya ce ""Idan na ƙara" "tambayarka ka ce mini haka sai na tabbatar na karya wata gaɓa ta jikinka kafin na sake maimaita maka tambaya, wacce allura kakewa Safiyyerh?"" Dr Hash ya dafe kunci sai ya yi murmushi ya ce ""Akan Safiyyerh kake wannan? Kar kasu sanin dalili domin ina da yaƙinin ka ji hujjar yi mata allura zaka tsane ta ne, tsana mafi muni kuma kafin ka bar gidan nan sai ka tsinke igiyar aurenka da yake kanta, ka bar hakan tunda baka san komai ba daman ita dauɗar gora ciki kan shata, kamar Safiyyerh matsayin new Safiyyerh da take rayuwa a yanzu kar ka buƙaci sanin wacece old Safiyyerh, wallahi ka ji ko wacce sai ka tsinewa" kan ka na amincewa da aurenta... MUTALLAB ❤🔥 Paid book Book 1&3 #500 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S 08164069385 for more updates follow on Arewabooks "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: Chapter 17: Who is Safiyyerh?" Paid book chat this number via WhatsApp to subscribe urs 08164069385 "Dr Hash ya sake dafa kafaɗar MAJ Aliyu ya ce ""One more thing, kar ka nemi jin tarihin Safiyyerh domin" "zai iya tarwatsa maka zuciya, ina faɗa maka hake ne a matsayina na ɗan'uwanka kuma ƙaninka, idan Ubangiji ya rufewa bawa wani abu, yana nufin sanin abun ba alheri bane ga rayuwarsa ina farinciki kuma daya kasance kai ne mijin Safiyyerh ina murna sosai amma kamar komai a yadda yake babban yaya, bana nufin abu ne mara kyau ya shuɗewa komai na rayuwar Ubangiji yana da nufin samuwarsa a kan shi. Ka zauna da Safiyyerh matsayin new Safiyyerh kuma matarka don Allah"" MAJ ALIYU ya dinga kallon ganin nasa cike da shakku da rashin fahimta wani abu kuma ya tukare masa a wuya, kasancewar rauninsa baya" bayyana ya sa za kaga serious face a tattare da shi. """Who is Safiyyerh? Mene ya faru da ita? Kenan an yi using nawa ne wajan aura mata ni? Exactly?"" Ya yi" "furucin da yake nuna how sad he is, idanunsa ya shige ciki Dr Hash ya girgiza kai ya ce ""MAJ ni fa kamar masinja ne a wannan motar, ka nemi driver sai ya yi maka bayani amma komai yana da dalili da kuma hujja, karka manta soyayyar dake tsakanin zuƙata biyu ma'ana iyaye da yaransu, zamani ya sauya MAJ kowa mafitsara yake nema a rayuwa idan zaka iya ka tsaya Safiyyerh domin ba lallai ka sake ganinta a cikin rayuwarka ba, idan ba zaka iya ba ka barwa zakaru fagen ka ɗauki hakan matsayin wata fitila dana baka"" a hankali Dr Hash ya girgiza kai yana yin baya tare da ɗaga hannunsa sama sai kuma ya yi murmushi sosai ya ce ""Naaa, bana nufin za a kashe maka Safiyyerh ka saka idanu a kanta kawai"" yana" cewa haka ya juya ya bar wajan. "MAJ Aliyu ya jima tsaye a wajan, ya jima abu bai bashi mamaki ba bai kuma tsaya masa a rai ba. Mota ya" "shiga bayan ya saka kayansa cikin sauri ya fita daga motar daidai sanda daddy yake fitowa daga cikin gidan shima hannunsa riƙe da maƙulin nasa motar. Tuƙi yake amma ya rarraba tunaninsa har ya isa ɗan ƙaramin gidan ya fita da sauri yana rufe motar, ya jujjuya yaga babu kowa sai ya shiga ya rufe gidan kamar kullum a zaune ya samu matashin saurayin wannan karan ya kifa kansa saman table ɗin gabansa, hannunsa ɗaya ya ɗora a saman keyboard na computer da yake operating nata a hankali Aliyu ya ƙarasa ya zauna ya ɗan juya ya kalle shi a nutse ya ce ""Muhammad"" da ƙyar ya buɗe idanunsa da suke a lumshe looking so sexcy, kana kallonsa za kaga nutsuwar dake tattare da shi a handsome and gentle man Indeed kallo ɗaya ya yi wa Aliyu ya zame idanunsa yana daidaita zaman nasa, Aliyu ya dubi baƙar fuskar" Muhammad sake ɗan sheƙi da manyan idanunsa nutsuwarsa har tsoro take basa. """Muhammad, cikin ne?"" Ya girgiza masa kai ya dubi MAJ Aliyu a hankali kuma ya ce ""Are you stay with" "me?"" Kai tsaye ya ce masa ""No,zan tafi ne""" """Shiiiit got it wrong""" Muhammad ya furta yana dunƙule hannunsa tare ja baya ya cigaba da danna computer can ya nisa ya ce """Last time da kazo da wata mace"" Aliyu ya tsaya da abin da yake alamar yana jin Muhammad ""Na ji muryarta, na taɓa ganinta""" """Safiyyerh ka gani? Yaushe ma ka zama free har ka fita cikin jama'a, fita kake bana nan ashe?"" Sosai" "Muhammad ya yi mamaki kamar ba zai magana ba sai ya ce ""Fita? Why should i? Laaa, na ganta da ciki i" "saw her with a pregnant"" Aliyu ya miƙe tsaye jikinsa duka rawa yake da ɓari idanunsa ya yi jajur ya taune harshe" """Safiyyerh with pregnant? Ina ka ganta yaushe kuma?""" """Shekaru biyu da watanni, ba zan manta muryarta ba, na juya na ganta naga kun tafi"" Ya faɗa cikin ƙasa" "da murya mara hayaniya har zai magana sai kuma ya yi shiru. ""Are you drunk? Muhammad ka sha wani abu ne yau, ka cigaba da shaye-shaye ne? Wannan maganar ba ta yi kama data wanda suke cikin hayyacinsu ba, ba Safiyyerh ka gani ba, Safiyyerh ba zata taɓa samun ciki ba idan ma zata samu to dani ne ƙwayayen haihuwarta na Aliyu ne"" Muhammad dai bai ce komai ba ya miƙe yana zagayawa ya ɗauki wani remote da pencil ya fara showing wani abu zuwa ga Aliyu, MAJ kuma tunda ya ga Muhammad ya miƙe tsaye ya san ya bar maganar kenan ba zai ƙara cewa komai akai ba. Aliyu baya fahimtar komai ya" "miƙe ya zaga wajan Muhammad ya ce ""Za mu yi magana, stay safe ok?""" """Akwai wani mai kama dani ne? Kake tsoron na fita, ba zan taɓa fita ba kar ka damu"" Aliyu ya kalle shi" sai kuma kawai ya juya ya fita. Muhammad ya bi bayan Aliyu da kallo a hankali ya lumshe idanunsa can "ƙasa zuciyarsa ya furta ""SOPHIE""" "***""Aliyu idan wannan ne damuwarka ka ɗauka ta zo ƙarshe, zan bibiyi case ɗin da ƙasa na maka" "al'ƙawarin matarka zata kuɓuta muddin ba hannun Scorpion ta faɗa ba"" Maj Aliyu ya kalli MG da sauri jin sunan Scorpion daya ambata a hankali ya miƙe tsaye ya ce ""Zan je, ba zan dawo sai na yi nasara"" MG ya miƙe da sauri Aliyu ya yi salute nasa cike da girmamawa yana fita kuma ya nufi mota zuwa ya nufi" airport zuwan nasa airport ya yi daidai da cikar lokaci ya shiga ya zauna a kujera ya daɗe a haka kafin ya "buɗe idanu jin ana jan hannunsa ya juya idanunsa ya sauka akan wani kyakkyawan yaro fari tas da ƙyar yake buɗe ido don fari, yaron asalin kyakkyawa ne ga shiga rai, a tsora ce Maj ya dinga kallon baby boy ɗin, daya lumshe idanunsa ya buɗe, kamannin Fiyya yake hangowa a fuskar yaron, har yanayin ƙiriniyarta domin yaron ya kasa zama sai ƙoƙarin hawa cinyar Maj yake, shi kam ya kasa motsi don mamaki ya dinga kallon yaron da wani irin yanayi na shakku da tantama. ""Sorry ya damake Amsh baya ji, ka yi haƙuri"" Wata mata ta furta tana ɗauke Amsh daga jikin Maj, har yanzu idanun Aliyu na kan yaron da ƙyar ya ja numfashi ya sauke a haka jirgin ya ɗaga zuwa sararin samaniya zuciyar Maj Aliyu na Kano" tare da tunanin halin da Fiyya ke ciki gangar jikinsa kawai yake tare da shi a cikin jirgin. ****Da yammacin ranar lahadi Moh na zaune gaban Abbasa ya tanƙwashe ƙafarsa idanunsa kafe a kanta "a hankali ta furta ""Kamar zan iya amince mata"" Abbasa ta ɗago kai ta kalle shi ta yi murmushi ta ce ""Ka santa ne?"" Ya girgiza mata kai alamar bai santa ba ""Yaushe ka fara yadda da mata?""" """Sanda na fara yadda dake"" ya bata amsa ta sake jinjina masa kai ta ce ""Mace za ta yi tasiri a zuciyarka" "kenan? Ka fasa cimma muradin naka? Ka ajjiye dukkan wata manufarka da ɗaukar fansar matarka? Idan gabaɗaya ka haƙura da wannan dole ne ka mallaki kamfanin FS WORLD INVESTMENT. Mutallab ƙaddararka na tattare da wannan kamfanin, har yanzu ne za a dinga amfani daku matasa ƴan siyasa na cimma burukan su a kan ku? Rayuwarku nada amfani, ina buƙatarka ina buƙatar ganin ka cimma" "burinka""" """Ke ɗin wacece da lokacin ɗaya kika kutso kai cikin rayuwarta? Me kike nufi dani? Iyayen da suka haife ni" "yanzu nine a idanunsu wanda suka tsana, jama'ar unguwa sun tsane ni, duk inda na zaga guduna ake yi, maimakon a yi mini addu'a sai a fara tsinewa mini, ɗa na kowa ne, ni ban zaɓi zama ɗan daba ko mashayi ba, sune suka zaɓan a tarihin rayuwa kowa yana da ɓangare mai kyau, da mara kyau ni wannan ɓangaren nawa aka sani MUTALLAB TAHHB ɗan daba ne ɗan shaye-shaye ɗan ta'adda ba kuma zan daina ba, sai idan ƙaddara ce ta yi galaba akai ne, tunda ana tsangwarmu za a gani"" a maganganunsa zaka fuskanci ƙuncin da zuciyarsa take ciki bai taɓa yi mata magana mai tsayin hakan ba a nutse ta ce ""To wanne ɓangare ne naka mai kyau? Tunda mara kyau aka sani? Ko sau ɗaya ka bani labarinka ka bani" "tarihin rayuwarka, wacce ƙaddara ce ta rusa rayuwarka daga dama zuwa hagu? Waye MUTALLAB?""" """Uhm"" ya ce ya miƙe tsaye domin a hankalina yake bai sha komai ba ta dinga kallonsa a tsaya cikakken" "namiji matashi mai jini a jika. ""An kashe mata uku wanda suka shigo rayuwarka,kar ka bari a kashe ta huɗu, kar ka amshi Safiyyerh kar ka bari zuciyarka ta rinjaye ka har ka bata matsayi, na yi bincike kuma ya tabbatar kai ka kashe matarka da hannunka ba zaka taɓa musa mini ba, ka kashe matarka ka nunawa jama'a kamar anci zalinka""" """E, da gaske nina kashe ta shine hukuncin ta, ta cancanci ta mutu""" """Na sani bana saɓa lissafi Mutallab, hujjarka na kashe ta da laifin data aikata maka ne ban sani ba. Abu" "ɗaya zan faɗa maka karka yadda ka amshi Safiyyerh domin ita ɗin matar aure ce, zai fi kyau ka yi amfani da damar da kake da ita a hannu wajan sanin sirrin FS WORLD INVESTMENT COMPANY, Ka rabu da Safiyyerh matar aure ce"". ""Na ji zan rayu domin ta"" da sauri Abbasa ta ce ""Kana cikin hankalinka? Matar" "auren zaka rayu da ita? Matar aure fa""" """Ba zata taɓa zama matar aure ba, idan ya kasance haka zan kashe auren nata,ko na kashe mijin, ita ɗin" "Matar Moh ce"" yana faɗin haka ya fice daga bukkar kamar walƙiya. Bai san mene ya faru ba a hanya yana tafe ana nuna shi duk da rufe fuskarsa da ya yi, hakan ya saka ya zaro wuƙa yana tafe yana buɗawa tare da zazzaro idanunsa ya dinga bin lungu har ya bar cikin duhuwar ciyayin." Safiyyerh na zaune ta ji ya shigo babu ko sallama ta miƙe da sauri haka kawai take jin tsoron shi ya "ƙarasa ya zauna saman kujera yana huci ta tattara nutsuwarta ta ce ""yin sallama wajibi ne Jarumi, kai fa babban suna gare ka ba'a san irin ku da haka ba, idan ka yi sallama ka nemawa mutum aminci ne, idan ya amsa ya nemaka aminci ne, yin sallama wajibi ce haka amsa ta kuma ko ka yi sai an baka damar shigowa"" bai kulata ba ya zaro sigari ya bata hayaƙi kwana biyu dai bai yi faɗa ba. Safiyyerh ta shagwaɓe" "fuska ta ce ""Kuma daka shigo ina saka kaya fa? Sai ka ganni haka?""" "Sai a lokacin ya juya ya kalle ta, to tunaninta mene? Ina ruwansa da ita da kuma jikinta? Mahaukaciyar" "yarinya kawai ""Sai na ji kamar ina rayuwa tare da mijina ne, idan na ji numfashinka a gidan nan har nutsuwa nake samu, ka sato ni ina nufin ka yi kidnapped ɗina maimakon na damu amma a kullum buƙatar kasancewa da kai nake a duk halin da kake ni ban damu ba, ba ruwana da kai ɗan daba ne na ji zan yi fighting akan soyayyarka, i will fight for your love, i will fight idan zan zama wacce zata sama maka farinki, i don't care with your habits, i don't care with my family ka yarda dani ko sau ɗaya ne, ka bani dama irin damar da kowanne namiji yake bawa mace a rayuwa, ina son wannan damar ko sau ɗaya ne" "zan yi amfani da ita wajan dasa maka soyayyata a ƙirjinka, zan kai ka zuwa wajan Professor""" """You can't"" ta ji ya ce can ƙasan maƙoshinsa yana rufe idanu dif dif dif haka zuciyarsa ke harbawa baya" "son ko jin muryarta ta kuma kasa ganewa, ya juya mata baya a hankali ya ji sautin shassheƙar kukanta na sauka cikin kunnensa bai kulata ba ta ce ""Ka tausaya mini wallahi ina son ka"" ta furta fat fat fat haka ta ji tsokar tsakiyar ƙirjinta na motsawa tare da buguwa, ta ji kalmar son a tsakiyar kanta ya sauka a ƙirjin da sauri cikin ranta bayan zuciyarta ta tuna mata da cewa “Safiyyerh what are you doing? Kina matar aure" "kina son wani?” ta girgiza kai ta ce ""Astagafirulla""" Moh ya miƙe tsaye zaune yana kallon ta a mamakance sai kuma ya taune harshe da laɓɓansa ya jima a "haka kafin ya ce ""Kina so na? Ni ko?"" Ya yi poiting hannunsa zuwa ƙirji yana nuna kan shi." """E, haka ne""" """Mijinki wanda kike aure fa?"" Ya cilla mata tambayar yana tsare ta da manyan idanunsa sai cin magani" yake kamar kuma an tilasta masa yin tambayar yadda yake magana da ƙyar. Tunani ta fara da zuciyarta "“Safiyyerh think, idan na ce masa ni matar aure ce ina da aure ba zai saki jiki dani ya bani soyayyar da" "nake buƙata har naji waye shi ba, my husband is no longer with me, wannan da yake gabana ya yi kidnapped nawa is the one who i pray for, zan faɗa masa ina son shi, i will tell him ina son shi, da na ji waye shi zan bar shi na koma wajan my poor husband Aliyu, the one who i love"" gama tunaninta kenan ya saka Safiyyerh girgiza kai ta ce ""Na yi kama da matar aure ne? Bani da aure ko saurayi bani da shi.."" tana faɗin haka ta yi Astagafirulla a ranta. Shiru ya yi mata ita a dole ya amince ta, ta marairace fuska" sosai tace... """Na rantse da Allah, na rantse da Allah, na rantse da Allah bani da aure ni Safiyyerh bani da miji""" Cak taga ya miƙe ya bar wajan ya shige ɗaki bata ƙara ganinsa har dare ya nutsa su Goje suka shigo. Ta "kalli Goje ta ce ""Aboki ba zaka bani labarin jarumi ba?"" Ya ƙura mata na mujiya sai kuma ya ce ""Maganar kisan matarsa ya tashi, iyayen yarinyar sun ƙara ɗaukaka ƙara da nufin basu yarda ba anci zarafinsu ba a ɗauki ran yarinyarsu a banza ba, maganar da ake yanzu sun kama Malam shi mahaifin Mai dawa, wai ya" "san inda yake ba za su sake shi ba sai ya zo hannu""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, to shi kuma me ya yi musu wai? Ba mai laifi ake kamawa ba?""" """Ƴa ƴan daƙiƙai ne, namansu ha halatta aci tsaf aka bani zanci mutanen nan jahilai ne"" Moh suka ga ya" "fito da sauri Goje ya miƙe tsaye ya ce ""Ina zaka?"" A hankali ya ce ""Zan miƙa kai na, a saki mahaifina"" Goje ya ce ""Ba za a yi haka ba, ita shari'a saɓanin hankali ce mu bi komai a sannu"" da rinannu idanunsa ya dinga kallon Goje ya kasa cewa komai sai huci yake fitarwa yana juya idanun nasa ƙirjin nan da harabawa nan da nan ya fara birkicewa ""Ka yi magana da wanda ya saka aka kama Manager, ta fara barin wajanmu" "sai mun yadda za a yi, akwai Jagwal zamanta wajan namu""" "Juyawa ya ya shige ɗakin daya fito, ya ɗauki wata ƙwaya ya tura a bakinsa ya danne a ƙasan harshe ta" "fara narkewa. Suna jiyo yadda yake buge buge hakan ya saka Safiyyerh ƙarasawa bakin ƙofar ta ce ""Ashe da gaske baka da imani? Kai ba cikakken mumini bane? Maimakon ka kira sunan Ubangiji ka yi masa kirari sai ka fara shan abun maye? Ba'a maganin damuwa da damuwa, idan tunani ya gushe hankali ke nemo shi, haba Jarumina, kira sunan mahaliccinka ko sauya ne repeat after me, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, ka yi ta maimaita hakan a ranka"" shiru ta ji hakan ya saka ta zame a hankali ta jingina da jikin ƙofar hawaye na sauka daga cikin idanunta zuwa fuska wani tausayinsa take ji sosai tun bata san waye shi ba, haka kawai ta ji bata fargabar zama kusa da shi “Ya Allah"" sai kuma ta kalli ƙofar ta shafa ta" "ce ""You are not alone, you have Fiyya kana da Maama""" "***Eng Ali wali ne ke kaiwa da komowa a office ɗinsa ya ja tsaki ya ce ""Zai jiƙa mini aiki yaron nan, ina" "son ya kawo mini ƴar gidan Professor Abdu ko bai yi mata fyaɗen ba na saka wani, ni fa akan biyan buƙatata bana tsoro bata shayi kuma a wannan karon sai na hauka kujerar ɗan Majilisa, na tabbatar na sauke Hon Maɗatai akan kujerar da yake iko da ita, har matsayinsa a cikin zauren Majalissa na chief whip" "sai ya dawo hannuna""" """Distinguish, ina ganin ba matsalar yarinyar nan ce a gabanmu ba, baka da labarin Dr Abraham Denial" "David sun haɗa hannu da Hon Maɗatai?"" A gigice Ali wali ya ce ""Ban gane haɗa hannu ba, ina cewa basa ga maciji da juna""" """Uhm, shi maƙiyi ko yaya yake ba'a raina shi a siyasa, Dr Abraham dumped all progressive congras NNY" "for the New people life NPL da shi da mutanensa kaf"" sosai tashin hankali ya bayyana a fuskar Ali wali ya share zufa ya ce ""Kuma ba plan bane ko shirin yin Anti party?"" Secretary ya ce ""Bana jin haka, ka san shi Abraham tsayayyen mutum ne mai magana ɗaya siyasar ma ba damunsa ta yi ba, sun haɗa hannu ne domin su kai ka ƙasa"" ""Hakan na nufin jawo Professor Abdu Marafa jikina ne ta ƙarfin dole, kuma burina" "ba zai cika ba sai da wannan yarinyar gashi ɗan iskan yaron nan ina kiransa yana neman lalata mini aiki""" """Akwai matsala dai gaskiya"" Ali wali ya ce ""Kar ka damu tun a primary elections sun ga irin ƙarfin da nake" "da shi, jeka kawai secretary"" miƙewa Secretary ya yi ya ce ""Distinguish, ka san siyasa kuwa? Siyasa hanya ce ta ɗarewa ko samun hawa madafun iko domin mulkar jama'a a takaice za'a iya cewa ana yin siyasa domin bayyana manufofi tsakanin masu neman kujerar mulki kuma ana yin siyasa ne tsakanin ɓangarori guda biyu ko sama da haka ba'a kowanne nau,in mulki ake gudanar da siyasa ba sai mulkin dimokoraɗiya mulkin farar hula da jama'a suke zaɓar shugaba bisa kundin tsarin mulkin ƙasa. Ana siyasa domin" "hamayya da juna tsakanin jam'iyyu, dole ka sauya taku kasan su waye a tare da kai shawara ce"" yana" kaiwa nan ya fita karo suka ci da Professor Abdu ya dinga kallonsa irin kallon sanin nan na wani abu daban. "Ali wali ya dinga kallon Prof, Daddy ya yi murmushi ya ce ""Eng Ali wali ɗan takarar Majalissar jiha ne ko" "na tarayya? Ga kifi daga sama gasasshe"" Daddy ya ce yana zama kan kujera ya dinga juya kujerar a hankali ya nisa ya ce ""Ka yi mamaki ko, ganin likita na je ba wanda ya sani na biyo ta nan wajanka, naga kamar baka yarda da abin da na ce ba ko? Da gaske ko sassara gangar jikin Safiyyerh za ka yi bai damu Professor Abdu Marafa ba, matsalar dake ta damuna ka yi mini magani babban albashir na yi magana da mai kamfanin FS WORLD INVESTMENT COMPANY an bawa Hon Maɗatai damar saka hannun jari,na buƙaci kuma a bani duka hannun jarin da Safiyyerh ta saka da kason ta dake cikin kamfanin, zan tattara dukkan ducoments da dukiyarta na yi signature su zama halaliyyata, zan kuma rufe bakin matata da yarana da Zahiyerh akan labarin. To Safiyyerh ba ciwon kai na ba ce ba kuma raunina ba ce, sam ƙwaƙwalwarka bata aiki ka tura Safiyyerh ne idan ya dace ka haɗata da abin da ya dace,kuma su biyun zasu same maka ciwon idanu, nama yi mamakin yadda aka baka damar hawa takara baka da tunani sam Eng Ali wali"" ya miƙe ya fice daga officer ɗin. A hanya ya yi wa J waya yana nishi da ƙyar cewa ya kasa" driving mutuwa zai yi idan ba a nemo masa Maama ba. "****Bacci Safiyyerh take ba tare da sanin tana mafarki ba sai fisge fisge take tana zabura ""Kar ka mini" "haka daddy me ya yi maka? kar ka cutar da shi kar ka cutar da shi, shi ɗin wanda zan aura ne bai san komai ba, iyayensa ma basu sani ba, zan bar shi idan ka so bari na har abada, wallahi ni na kai masa kai ne soyayyar da nake masa ce, ina son shi i love Tahhb daddy ina son Tahhb..."" Da sauri ta buɗe idanu a gigice tana maimaita ""Ina son Tahhb daddy"" jikinta duka rawa yake yana tsugune gabanta ganin ta kasa nutsuwa kamar mai shirin taɓa wuta ya damƙi kafaɗunta ya girgiza da ƙarfi ya ce ""Parrot, your Tahhb is here your husband is here"" hannunsa ta damƙa tana rusa kuka ""Kar ka bar ni, kar ka sake barina daddy" zai raba mu ina son ka Tahhb.... You can now read page 16 to 20 on ArewaBooks search the book Na'ima Sulaiman Sarauta Nimcyluv "[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: Chapter 18: Selfishness" Mutallab a paid book chat this number via WhatsApp to subscribe urs 08164069685... For more updates follow on Arewabooks. "Ya zuba mata idanu yana jin tana sake cewa ""Daddy wallahi idan kukai masa wani abu zan gudu daga" "gidan nan, zan bar gidan nan Daddy me ya sa kuka kasa fahimtar cewa zuciyar Safiyyerh zaku tarwatsa? Daddy da hannunka zaka kashe ƴarka me na yi da na cancanci ka kashe ni? Saboda na ce ina son shi, ina son ruwa da dacewa Daddy? So bai san nasaba, cancanta, arziƙi, ko launin fata ba, balle ya yi zuciya hisabi da abin da ya dace, i love him the way he is, idan zaka raba ni da shi,ka fara kashe ni kamar yadda ka yi niyya, ba wani abu bane don uba ya kashe ƴar cikinsa ƴar daya haifa akan buƙatarsa"" Safiyyerh ta cigaba da ihu da fisge-fisge idanunta rufe gani take data buɗe idanunta zata daina mafarkin, zata fita" daga yanayin da take ciki wanda bata fatan ya gushe daga cikin idanunta. A hankali kamar mai tsoron taɓa jikinta ya saka hannu ya matse ƙafafunta yana jinjigata ya kasa yi mata "magana ""Open your eyes Tiger, buɗe idanun"" ta girgiza masa kai idanunta sharkaf da hawaye ta riƙe hannunsa ""Ba zan buɗe ba, ina buɗewa zan ga babu kai a gabana Tahhb, kana kallon su daddy zasu raba ni da kai, za su rabani da mijina me ya sa Daddy baya son ka, don Allah kar ka tafi daga wajena kar ka" "sake guduwa ka bar ni""" """Ina nan, ni dai mijinki i am here just because of you Safiyyerh, buɗe idanu kiga mijinki Mutallab, ke" "matar Moh ce Tiger, ko ƙaddara ba zata sauya hakan ba""" """Da gaske ba zaka sake guduwa ba? You'll love me back? Na dinga jiranka a ranar baka zo ba, ni ko" "Jarumi,ni Safiyyerh ka bari?"" Moh ya kasa magana idanunsa ya yi wani irin jaa ruwa ya taru a cikinsu, da ace yana yin kuka tabbas da a yanzu duk wanda ya kalli ƙwayar idanun Moh zai san hawaye yake, sai dai shi baya jin yana da wani abu daya rage masa a rayuwa balle ya saka shi kuka, ya yi ƙasa da kansa har yanzu yana riƙe da kafaɗunta. Riƙe shi ta yi cikin shassheƙar kuka while she's smiling at the same time ta taɓa cikinta ""Har yanzu wajan da aka cakan wuƙa yana nan, numfashina bai ƙare a duniya ba shi ya sa" "ban mutu ba, ashe rabon ganin mijina ne""" "Rinannun idanunsa ya buɗe yana kallon fuskarta, har yanzu idanun nata a rufe suke still ya kasa furta" "komai, sai kallon ta yake zuciyarsa na wani irin zafi da tafarfasa. A hankali Safiyyerh ta miƙa hannunta ta shafi fuskarsa sai ta yi murmushi tana girgiza kai ta ce ""Ka barni da soyayya, ka sanni da alkunya ka barni cikin jinya ka tafi, haba jarumi"" Ya sake yi mata shiru a hankali kamar mai tsoron ganin abu, slowly slowly ta fara buɗe idanunta daya gama kumbura ganinta ya sauka a saman ɓakar fuskarsa ta zuba masa idanu ta ƙura cikin idanunsa ido, shima ɗin ita yake kallo da sauri kuma ta yi baya daidai lokacin da wani shocking ya gilma ta cikin kanta ta yi saurin saka hannu ta riƙe kan, tana runtse idanunta jikinta duka rawa yake ga wani irin azaba da tsakiyar kanta ke mata, ta dinga kallon Moh kamar mai shirin tuna wani abu, wani irin zillo zuciyarta ke yi mata tana buɗewa ƙirjinta na bugawa tsit, tsit,tsit haka ta ji jijiyoyin" cikin ƙwaƙwalwarta zuba harbawa harbin da take jinsa daidai da bugun ƙirjinta. """Me kake yi a nan?""" Safiyyerh ta ce tana kallon Moh dake durƙushe ya zuba mata idanu ta ɗan dafe kai tana kwaɓe fuska """Bacci na yi, i had a bad dream, na kasa tuna komai ko ka ji me na ce?""" """I got it wrong, baka ji komai ba ai shikenan"" ta sulale a wajan ta zauna ta haɗe kai da qwwia can ta ɗago" ta kalle shi ta ce """Ina jin kamar ina da matsala da brain ɗina, anya ba haukacewa zan yi ba? Innalillahi wa'inna" "ilaihirraji'un, i wish a gida nake dama a gida nake Dr ya yi mini allurar da yake mini""" "Miƙewa ya yi da baya da baya ya fara tafiya cikin sauri kuma ya juya zuwa ɗakin da yake ciki, wanda" "daman daga nan ya fito sanda ya ji tana surutan yana shiga ya rufe ƙofar. Safiyyerh ta jima a wajan da ƙyar ta miƙe tsaye saboda kukan da ta yi da ciwon da kanta ke yi mata, sai ta zama so silence bata da wani kuzari duk iya ƙoƙarin da ta yi wajan ganin ta tuna mafarkin ta kasa, sosai kan ya yi mata nauyi deep down na zuciyarta tana jin kamar akwai abun dake going a tunaninta wanda ba nata ba. Har zata shige sai kuma ta leƙa ta tagar ɗakin ta hango shi ya yi rufda ciki ga tarin kwalayen sigarin daya shanye" ga wata ƙwaya da ya yi wurgi da ita sosai ta ji babu daɗi sai ta juya ta shige cikin nata ɗakin. ***Ammo ta ɗaga kan ta bayan ta amsa sallama da gaisuwar da Sa'adah ke yi mata tana jin Sa'adah ta ce """Yanzu ina aka kai Malam Ammo, daman case ɗin Mutallab ba'a gama shi ba?""" """Sa'adah kenan, bakwa son gaskiya cikin lamuranku kin taɓa ganin ƙarya ta kore gaskiya kin san zunubin" "da ɗan'uwanku ya yi? Sa'adah kun san zafi da raɗaɗin da zuciyata ke yi mini kisan kai fa, ina tsananin takaici daya kasance ni ce wacce na yi cikin Mutallab, na raini cikin na yi naƙidarsa na haifar, na shayar da shi ruwan nonona Sa'adah anya ba sauya mini yaro a ka yi, anya shine Mutallab ɗin da na ji zafin" "naƙudarsa...,""" """Subuhanallahi, me kike cewa haka Ammo kar ki ƙarasa lalata shi da munanan kalamanki, Ammo ko sau" "ɗaya ba ki taɓa bawa Mutallab dama kin ji ta bakinsa ba kar ki yi masa mummunan alkaba'i wallahi har gobe shi jininki ne ba zaki hana jama'a furta Mutallab ɗan Ammo bane, da kin ja shi a jiki a lokacin da abubuwan suka lalace, da kin nuna masa kuskuren abubuwan da yake, da kin yi masa addu'a, da ba ki nuna masa tsangwama ba. Amma kin juya masa baya sanda yara suke lalacewa mu iyaye sai muce a lokacin za mu tsane su don Allah ki yi wa Mutallab addu'a idan yana da rabo zai shiryu"" murmushin" takaici Ammo ta yi tana girgiza kai """Sa'adah kenan, bayan abubuwan baya ki duba a sanadinsa Hameeda ta rasa ranta yaranta sun zama" "marayu, a sanadinsa yanzu mahaifinsa yana wajan hukuma wacce baƙar kadara na haifa a cikina? Ciki mai haife haife sai ya bani yaron da yafi ƙarfina ya fi ƙarfin ubansa ya fi ƙarfin al'umma ya fi ƙarfin jami'an tsaro ina jin kamar na yi masa Allah Ya isa. ,"" a gigice Sa'adah ta rufe bakin Ammo tana rushewa" "da kuka ta ce ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Hasbunallahu wani'imal wakil""" "Ta kasa magana sai ta sunkuyar da kanta tana rushewa da wani irin kuka mai ban tausayi da cin zuciya," "Ammo ajjiyar zuciya kawai take saukewa dole akwai zunubinta na faruwar komai. Da ƙyar Sa'adah ta miƙe ta saka hijabi ta fita Inna Binta na wanke rama zata kwaɗantawa Mufee ta ce ""Iska na wahalar da mai kayan kara, ai tunda kuka haifi ɗan daba abubuwan da za su dinga faruwa kenan ni dai banci nanin ba, nanin ba zata taɓa cina ba na ji da yunwar cikina ma data Mufee, ita kanta Zaituna data fita bulayi" "mamaki take bani yasin""" Sa'adah bata kula Inna Binta ba ta yi waje hankali tashe duk inda take tunanin za'a kai Malam ta je police "stations har babu adadi Inna Binta ta kalli yaran dake tsakar gidan bakunansu a bushe duk yunwa suke ji ta fashe da dariya har tana tuntsirawa ta ce ""Wallahi ubanku ya janyo muku""" "Sa'adah ta kalli Ɗanyaro ta ce ""Kai kuma saboda Malam baya nan wayar ka karɓo haka?""" """Tawa ce ai"" ta buɗe ido ""taka kuma? Ka san kuɗin wayar nan kuwa?"" Ya yi mata murmushi yana jujjuya" "wayar ya ce ""Na sani, ai bani kaɗai nake da ita a wannan makarantar ba, Iro yana da ita haka Muhajeed haka ma Salmanu""" """Sana'ar me kuke yi? Ko dako kuka fara Ɗanyaro""" """A'a kifi daga sama ne ya sauka, idan rabonka ya rantse dole sai ka samu muma haka ne"" ta dinga kallon" fuskar Ɗanyaro da mamaki """Wanne kifin ka samu daga samu kenan Ɗanyaro?""" """Sirri ne"" yana faɗin haka ya miƙe ya bar wajan ta bishi da idanu." "***MAJ Aliyu ya dinga kallon commander cike da mamaki kafin ya ce ""Sir ban fahimce ka ba, pardon" "please?"". Commander ya yi murmushi ya ce ""MAJ Aliyu kenan, na sanka farin sani sarai ka fahimta na san kuma ka gane na ce ka ciro mini Id card ɗinka, Ka cire uniform ɗinka kuma ka bani bindigarka ai ka ji yanzu tunda Hausa na yi""" """Yes sir, ma'anar cire uniform ɗina ne ban fahimta ba, bafa Captain nake ba, A.A MARAFA mai matsayin" "MAJOR MAJ nake kaki mai tambarin tsuntsu, a gaban yarana kake maganar na cire Uniform nawa kuma na baka bindiga laifin mai na yi?"" Aliyu ya furta yana zazzaro idanu waje zuciyarsa ta motsa, daga zuwan shi cikin Barrack ɗin zata tare shi da maganar iska wacce ba zai taɓa lamunta aci zarafin shi ba, ba zai" taɓa yarda a wulaƙanta shi a gaban yaransa ba. Yadda zuciyarsa ke rawa haka sauran gaɓɓan jikinsa. "Brigadier General ya sake yin murmushi ya ce ""Kuma sai mene da rank ɗin Maj? C'mo my friend remove" "the uniform, ka ajjiye bindigar wajanka ok""" """I am sorry sir BG i can't"" Aliyu ya ce yana ƙoƙarin kiran number waya da sauri ya ji an fisge wayarsa" "kafin Aliyu ya juyo Brigadier General ya wanke Aliyu da mari ya sake zabga masa wani marin, idanun Aliyu kamar su faɗo ƙasa saboda ja yaƙi motsawa shi mamaki yake yi wanne laifi ya aikata har haka? Ance an yi posting nasa zuwa wani dajin duk da matsayinsa ya shige haka, daga nan kuma zai yi exam" amma daga zuwa sai reshe ya juye da mujiya? """I said drop the gun Maj Aliyu""" """I can't, a faɗa mini laifina idan na yi na amsa idan ban yi ba na faɗa, haka ake daman daga zuwa a fara" "tarata da wasu abubuwa da ban sani ba"" hannu Brigadier General ta tafa sojoji su kaiwa Aliyu ƙawanya ""Ku ƙwace mini bindigar hannunsa a cire mini rigar jikinsa"" Aliyu ya ja ya ƙame yana jiran yaga waye zai zo idan yake su kansu sojojin tsoron zuwa wajan Maj Aliyu suke domin sun jima da sanin waye shi, kokawa aka fara dashi suka kasa ƙwatar bindigar ta baya aka zo tare da shammatar shi aka danna masa wata Jijiya a wuyansa ya juya da ƙyar idanunsa ya buɗe bai gama ganin kowaye ba, dishi dishi a hankali ya ce ""Daddy"" sai kuma ya sulale a wajan a haka suka ja shi a ƙasa a cikin Barrack ɗin suka nufi wani" gadirom da shi. "***I. Qasim ya gama gwada Daddy kafin ya ce ""Daddy kana hutawa, jikinsa baya motsi jininka ya hau" "gashi ya nuna ka yi tafiya mai ɗan nisa yau ɗin nan, muna buƙatar lafiyarka"". Girgiza kai Daddy ya yi da ƙyar yake iya magana ya ce ""Qasim ta ya zan samu nutsuwa a zuciyata? Ka tuna Safiyyerh bata tare dani, ka dubi lokacin daya shuɗe ba Maama a gidan nan, sannan ka ce na samu nutsuwa?"" I. Qasim ya ce ""Haka ne, amma idan Safiyyerh ta dawo ta sameka a haka ba zata ji daɗi ba ka san yadda take son ka ai," "Please be patient mu cigaba da addu'a duk inda take Ubangiji ya kuɓutar da ita ya kuma kare ta""" """In sha Allah, na saka ana ta addu'a ana sauke alƙawari da sadaƙa""" "Ummimi ta shigo tana daddana waya Daddy ya kalleta ya kasa magana ta ɗan dube shi ta ce ""Ina ta kiran" "Gadanga wayar a kashe, Aliyu baya kashe waya"" Daddy ya yi jim sai kuma ya ce" """Junaid ɗakko mini wayata muga"" miƙewa Junaid ya yi ya ɗakko wayar Daddy ya amsa ya shiga kiran" "number Aliyu amma a kashe, Junaid ya kira, haka Ummi Qasim ma haka hankalinsu duk a tashe. Sai kawai Ummimi ta fashe da kuka ta ce ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Aliyu me ya samu Aliyu kuma, miji da mata lokaci guda"" Daddy ya ce ""Ki daina kuka kin san yanayin aikin nasu, bari na kira MG mu ji"" cikin sauri Daddy ya fara kiran Major General yana ɗagawa Daddy ya yi gyaran murya ya ce ""Ka yi haƙuri na" "kiran ka kwatsam, mun kira wayar Aliyu mun ji shiru""" "MG ya yi shiru Daddy ya ce ""Ina tare da iyayen yaran a free kake""" """Matsalar network ne, babu mamaki sun ƙarasa cikin jejin ne amma mun yi waya da commander dake" "jan ragamar tawagar lafiya lou suke, idan ya samu sukuni zai kira""" """Thank you, na gode sosai """ """Babu damuwa amma kamar bai kamata ku damu ba, Aliyu soja ne kuna iya yin fiye da shekara ba ku ji" "daga gare shi ba"" sallama suka yi gabaɗaya. Ummimi ta sauke ajjiyar zuciya sai yanzu ta samu nutsuwa haka Ummi. Daddy ya kira wayar Sp Ghali yana ɗagawa ya ce ""Ya ake ciki ne?""" """Muna nan muna ta ƙoƙari bincike na tafiya, amma na rasa ta ina muke samun matsala ana ta yi mana" "kutse cikin na'ura da mun samu mun fara tracking location sai a lalata mana komai, kuma duk wanda yake yin hakan ba ƙaramin gwani bane mun kasa ta ina yake"" miƙewa Daddy ya yi a hankali ya nufi Upstarts yana cewa ""Ya akai to Aliyu ai yanzu ba zai zame muku matsala ba"" magana ya cigaba da yi a" "hankali ba'a jin me yake cewa. Ummimi ta lumshe idanunta ta furta ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un""" "Eng Ali wali yana ta masifa idanunsa akan Csp ya ce ""Lamarin yaron nan babu mutunci, ane mu mini shi" duk inda yake da kuma yarinyar da take wajansa dole na kawo ƙarshen komai ba zan yi sagegeduwa ba a "yi mini sakiyar da ba ruwa, takarar ɗan majalissar tarayya ba wasa ba ce wallahi, zan yi duk iya ƙokarina""" "Jafar ya ce ""Distinguish kana wasa da kujerar ne kamar, A matakin gwamnatin tarayya dama matsayin" "uku garemu Shugaban ƙasa, Sanata, Ɗan majalisar tarayya, kuma idan Scorpion yana raye a duniya dukkan ku ba zaku taɓa samun wannan kujerar ba, lokaci baya jira, ni a tunanina ku nemi sulhu da Scorpion ɗin nan ku ji matsalarsa daku, ku hanzarta yin hakan kafin jami'an FID su kama shi, ina tunanin" "Safiyyerh kuma ita Manager ɗin why not kawai a kashe ta""" """Jafar idan na ce ga abin da mu kaiwa Scorpion ɗin nan na yi ƙarya, ni ban ma san shi ba ban san me" "yake buƙata ba. Safiyyerh kuma ba za a kashe ta ba, ina da wani picture nata za a yi editing a fitar tsirara" "na san dawa za a haɗata a picture ɗin karka damu, ni yanzu matsalata biyu ce zuwa uku, waye Mutallab waye Scorpion sai batun Professor Abdu Marafa shi na gane kamar dukiyar yarinyar ya kewa""" """Idan haka ne ku zauna ku daidaita tsakaninku da Hon Maɗatai da Dr Abraham kuna cikin matsala," "matsala kuma ba'a raina ta a siyasa""" "Ali wali ya ce ""Ok shikenan, zan tura maka photon yarinyar zan maka bayanin abin da nake buƙata, a" ƙirƙiri fake account a handles na social media a yaɗa komai na fara gajiya ƙwan ya fashe warin ya damu "kowa""" ***Safiyyerh na dafa Indomie the only abin da ta iya kenan sai tsirarin abubuwa a hankali ya leƙo ta juyo "ta kalle shi ta ce ""Masoyi abin ba sallama?"" Ya jingina da jikin bangon wajan ta kammala ta juye Indomie a faranti ta saka cokali, ta yi waje bayan ya bata hanya ya sake binta har inda take ta ce ""Za ka ci ne?" "Kana ta biyo ni bafa guduwa zan yi ba, ina nan tare da kai har sanda ka yi niyyar mayar dani gida"" hannu ya saka ya janye farantin ya ajjiye cokalin ya saka hannunsa ya kai lauma ta ce ""Say Bisimillah saboda zaranar da shaiɗan da kuma neman albarka a abincin"" bai kalleta ba, ita dai kamar lauma uku ya yi wa" "Indomien ya cinye tas ta zare ido ta ce ""kafa cinye? Ni kuma fa?""" """Ki cinye ni""" "Ta yi murmushi sosai ""kusan halinku ɗaya da Yaya Aliyu, Allah sarki Captain"" ta yi maganar a hankali sai" "kuma ta ce ""Yaushe zaka mayar dani gida, tunda ba zaka so ni ba?""" """Wacce allura ake miki?""" """Nima ban sani ba, kawai dai ana yi mini ita ko na tambaya ba'a faɗa mini ta mece""" """Kin sanni?"" Fuska ba walwala ya yi tambayar ta girgiza kai ta ce ""Ban san ka ba, ina dai fata wannan" "sanin ya zama sanadiyar faruwar abubuwa da yawa""" """Koda hakan zai saka ki sanni mijinki ne?"" Wani rainin hankali da wayo ta ji sai ta yi dariya ta ce ""Kana" "nufin ko hakan zai saka ka aure ni? E, na yarda"" ya yi mata shiru a hankali kuma ya ce ""Zan bar garin nan, kafin nan zan ba ki labarin da ba kowa ya sani ba daga nan ya rage naki wajan tuna baya ko akasin hakan yanzu ba sai anjima ba za ki ji kowaye Mutallab, kuma kema ya zama dole ki bani information akan Kamfanin nan naki ƙila na taimaka miki, kuma ki sani daga yanzu rayuwarki ta zama ba iya taki ba, wannan tsiwar taki ya saka na ji zan faɗa miki sirrina ban ce ki yi mini kuka ko tauysawa mini ba, bana" "buƙatar tambaya""" "A hankali ta jinjina kai ta ce ""Yadda ka ce haka zan yi my love"" ya zamo ƙasa kusa da ita ya jima yana" kallon ta ya fi ƙarfin minti ashirin a tausashe ya ce asalina ya fara da.... Read chapter 19 and 20 on ArewaBooks "[1/7, 9:34 PM] Sis Fauzy: Chapter 19: Where is my son" "Shiru ya yi mata, Safiyyerh ta langwaɓar da kai ta ce ""A haka za ka bani labarin kana ja mini rai da aji? Ba" "shiru ake ba da ka ce asalina sai ka ɗora kawai muje ba jira, ka saka duk na zaƙu wallahi, ni na jima ban ji abin da nake son ji irin labarinka ba Jarumi"" ya zuba mata idanu baya ko ƙiftawa a karan farko ta ji tsigar jikinta ya fara tashi ƙirjinta ya motsa wani abu mai kama da feelings and emotions na kama zuciyar da" "kyau, ta ja baya daga kusa da shi ta yi shiru kanta a ƙasa." """Ke ma za ki iya bada labarin nawa ga wani"" ya ce yana furzar da iska daga cikin bakinsa har lokacin" "kuma ya kafe ta manyan idanunsa wanda yake lumshe su lokaci zuwa lokaci. ""Ni na sanka ne balle na bawa wani labarinka?"" Ta tura masa baki tana murguɗa masa shi kuma ya girgiza kai kawai ya yi mata shiru a hankali ya zaro wayar dake aljihunsa ya fara dannawa da sauri ya ɗago kai ya kalli Safiyyerh ta ganta ke ƙasa, ya sake kallon screen ɗin wayar hannunsa, ba'a tantancewa damuwarsa ko shiga tashin" "hankalinsa, ya saka hannu ya shafi fuskar wayar ya sake kallon Safiyyerh a hankali ya ce" """Kee. You""" "Ta juyo ta kalle shi, ta buɗe masa idanu saboda kallon tuhumar da yake mata, kallo ne irin na why are" "you doing this to me? Kallo ne na what are hiding? Kallo ne da yake nufin you are not alone Safiyyerh! ""Wannan kallon fa? Bashi ko tara ko wani abu na cinye maka ban sani ba""" "Bai kulata ba sai kawai ya miƙe yana hana jikinsa rawar da yake yi, cikin sauri itama ta miƙe ta ce ""Wai" "me ka gani a wayar haka, dama ka ara mini ko game na dinga yi"" gabaɗaya ya juya zuwa gare ta, ta yi saurin jingina da jikin bango banda idanu baya hayaƙi da ta ce hayaƙi idanunsa ke fitarwa, bakinta ya shiga rawa ta kasa furta masa komai, saboda yadda ya takure ta a jikin bangon tare da sata a tsakiya naman ƙirjinsa ya dinga rawa sai zazzaro manyan idanunsa yake waje kafin ta yi magana ya daka mata" "tsawa ya ce ""Ina ɗana? Where is my son?""" """A baby? Ɗanka kuma?""" """Zan kwaɗa miki mari kika sake mini question akan question""" """Ina zan ga ɗanka kuma ni Safiyyerh, kai ɗin ma yaushe na sanka balle na san kana da ɗana, kuma idan" "kana da yaro what is my business a wannan issue ɗin da zan ɗaukar maka yaro""" """Shhhh a liar, ashe kin haihu"" a wannan point ɗin, Safiyyerh ji ta yi kan ta zai buga ya tarwatse, tuni" "hawayen da yanzu baya neman shekararta wajan fita ya shiga sauka akan farar fuskarta, ta dinga girgiza masa kai amma ta kasa magana sai kawai ta fashe da kuka tana yin ƙasa da kan nata, da zai gane daya matsa, da zai gane daya daina kusanta kan shi zuwa gare ta, a duk wata musayar magana da suke yi zunubi ne a gare ta, tana auren wani, tana rayuwa da wani daban a keɓantacce waje a ƙasan zuciyarta ta ce ""Allah ka gani, bada nufi na yi ba, Allah kar ka tuhume ni da cin zarafin igiyar auren Aliyu, na bar" "mijina na zo wajan ɗan daba. Astagafirulla Ya Allah""" """Ban yi tsammanin dani dake duk mun isa samun ciki ba, ina nufin ban yi zaton na isa bawa mace ciki ba" "a wancan lokacin, kema ban yi zaton kin isa ɗaukan ciki ba, har na biye miki muka aikata zunubin dake bibiyar rayuwarmu, daman an ce mace shaiɗaniyya ce kin yi tasiri a rayuwata, lallai kin yi galaba, kin ganni kina nuna kamar ma ba ki taɓa ganin mai kama dani ba a dukiyarki, balle ki tuna ke ce shaiɗaniyyar da kika shigo rayuwata kika rusa komai nawa kika lalata tarbiyyata, kika ƙwace mini ƙuruciyata, me na yi" "miki? Why why why?""" """Why??""" "Ta ji why ɗin ya sauka a ƙirjinta, Safiyyerh couldn't speak tana shassheƙar kuka ta ce ""Ni ce shaiɗaniya?" "Me na yi maka ni Safiyyerh? Na rantse da Allah da Annabi ban taɓa ganinka ba ko dai ka sake yin shaye- shaye ne? Wacce ƙwaya ka sake sha take faɗa maka ba daidai ba?"" Duk ta ruɗe jikinta nata rawa, shi kuma ya kafe ta da rinannun idanunta har mamakin yadda baya gajiya da ƙura mata ido da yake maimakon ya yi faɗa ko ihu wannan karan muryarsa a raunace yana sake matsar da fuskarsa zuwa gare ta ya ce ""You leave me if you want, saboda ke ba kowa bace face muguwa last tambaya da zan miki ina" "yaron da kika haifa yake?""" """Jarumi!""" Safiyyerh ta kira sunansa a tsora ce gani take kamar ya haukace ya ɗage mata duka girarsa biyun tana "kuka ta dube shi ""Ni Safiyyerh ban taɓa tarayya da wani ɗa namiji ba, ta ya zan samu cikin haihuwa tunda ba'a ruwa ake samu ba, how? Na ce how?""" """How? ta yadda dai kika lalata ni a baya haka to""" """Ka samu matsala"" fuskarsa ba walwala sam kuma yana nufin abin da yake magana akai, ta zata iya tuna" "waye shi zata san shi ba ma'abociyar wasa bane, zai iya irga murmushin da ya yi a duniya, gabaɗaya bai ga abin da zai saka shi murmushi a duniyana balle dariya. Ya ɗaga hannu kamar zai ɗauke ta da mari ta" "saka ɗaga nata hannun, ya yi tsaye yana kallon ta ta ce" """Tunaninka me? Zan zauna ka mare ni wallahi kwaɗa maka mari zan yi nima na dawo da kai cikin" "hayyacinka"" sai gabanta ya hau faɗuwa ganin ya sake matseta a bangon ya ce ""Remember??""" """Me""" """I missed the hug, da kike ta bibiyata""" """Ni ɗin? Over my dead body""" "Ya yi kamar zai riƙe ta, ta runtse idanunta tana sakin ƙara a hankali kuma ta ji ya damƙi hannunta ya ɗora" "a ƙirjinsa da yake bugawa ""Labarina ba zai taɓa kammala ba harafin sunanki ba, ko a baya ban taɓa cewa ina son ki ba, balle yanzu kawai kim cutar dani Allah zai saka mini"" yana cewa haka ya sake ta, ta faɗi a wajan yana harhaɗa hanya ya fice daga gidan bayan ya rufe ƙofar Safiyyerh ta sauke ajjiyar zuciya" wannan mutumin ya fara samun matsala da tunaninsa zuwa gaba zai iya haukacewa. Ta yi shiru thinking wanne hali Daddy yake ciki na rashin ta? Allah ya sa dai bai shiga damuwa ba kar "wani abu ya same shi ta shiga uku, he mean the world to her shine inuwarta. Ta lumshe idanunta tunanin Aliyu ya sauka a ƙirjinta mamakin yadda ta yi accepted yayan nata ba wani tashin hankali, kodayake duk abin da Daddy ya zaɓa mata a rayuwa dole zata amsa, ko wuta ya ce ta shiga babu musu zata shiga saɓon Ubangiji ne kawai ba zata yi ba, shima ba zai taɓa cewa ta yi ba, Ummiminta Yaya J, Awais, Dr tuna waɗannan mutanen ya saka ta fashe da kuka zaman gidan ya yi mata ba daɗi wajan" Daddy kawai take son komawa taga a wanne hali yake ciki? Ta haƙura da jin labarin nasa gabaɗaya. "Moh na fita ya nemi wani dakali a gefen gidan ya zauna ya yi, bawai tunani yake ba shi kan shi bai san" dalilin shirun nasa ba. Zuciyarsa yake son bawa dama na tunanin Aby da Ammo amma ya gagara ya ji ya zare su daga cikin zuciyarsa da rayuwarsa kamar yadda suka kyamatar shi. """Mai dawa""" "Ya juya ya kalli Goje sai bai ce komai ba Goje ya ce ""zaman mu a nan wajan akwai hatsari Mai dawa," "yarinyar a san yadda za a yi da ita mu kama gabanmu""" """Wai ina ta magana ka yi shiru, wannan halin naka na tsana kai ba'a abin arziƙi da kai"". A hankali ya furta" """dake ni ba ɗan arziƙi bane shine""" """Kai na ƙasa, tuba nake waye mutum ai ko aljani sai ya shirya. Mai dawa akwai zance a ƙasa, kafin nan" "kunna abar maganarka ka kai gidan sauti ka ji wani yare""" """No"" a ɗan hassale Goje ya ce ""Wai mene matsalarka da gidan rediyo ne? Kai komai baka so kafi gane ka" yi ta zama cikin kunci kana bankawa cikinka hayaƙi kana yi wa kan ka allura da shan mugawayen ƙwayoyi? "Ka dinga sassautawa kan ka""" Moh ya ɗauke ƙafarsa ɗaya ya ɗora saman ɗaya yanayin zamansa kamar na sarakai a hankali ya dinga "girgiza kan shi ""Na tsani redio, da masu gidan redion""" """Saboda suna baza cigiyar kama Scorpion da tukuici ga wanda ya kawo ko information nasa ne?""" """Oh, jeka faɗa if you want"" Goje ya girgiza kai ya ce ""Ba haka nake nufi ba, lalace ta bata haka ba cin" "amanarka ka tuna dani da kai duk abu ɗaya ne, halayya ɗaya muke ɗabi'a ce kawai ta bambanta mu"" ya cije bakinsa, hopping ko zai ji sassauci daga cikin zuciyarsa wanda yake fata ya ɗago rinannun idanunsa masu kaifi da ban tsoro cikin sauri Goje ya yi ƙasa da kansa wani irin shakkar Moh ya ɗar su a zuciyarsa" "ga wani irin kwarjini da ya yi masa a idanu ""Akwai bambanci, duk ta'addancinka baka taɓa kisa ba""" """Kai ma ɗin baka taɓa ba, sai ɗaukan hanya ka daina jawa kanka jarfa ana zaune lafiya yanzu ma ya muka" "kaya""" """Goje""" """Mai dawa, uban mafarauta""" """Kabar mutum idan ka gan shi, ko kai baka san waye ni ba, kabar ni a yadda nake showing kai na gare ku," "idan na yi shiru ka basar ina ɗage maka ne, Moh baya magana, Moh baya son takurawa, Moh baya son surutu redion ce kuma bana ra'ayi Scorpion kuma da ake magana ba zan taɓa bayyana ba sai na gama yi musu illa, ta'adin da na yi bani da tabbacin zan wanye da Ubangiji lafiya"" Goje da ƙyar ya iya ɗago kai ya kalli Moh, ya ga tuni har ya tashi ya bar wajan kamar walƙiya ya kan rasa inda yake zuwa da yawan lokaci ba'a taɓa gane abin da shirunsa yake nufi, ba'a gane sawun tafiyarsa idan ya taka ƙasa sai ya tabbatar bai" bar shaidar yatsun ƙafarsa ba kafin ya ɗora da tafiya. ***Sharfaɗi na zaune a office ɗinsa na FS WORLD INVESTMENT COMPANY matsayin chairman of the "company. Ya ɗan kalli Professor Abdu ya ce ""Kamar baka da ikon amsar dukiyar Safiyyerh daga wannan Companyn Professor Abdu Marafa, saboda dukiya tata ce kuma saka hannunta, idan ya zama dole mutum ya cire hannun jarinsa muna da tsare-tsaren da muke bi, ba kara zube kamfanin yake ba to ina" "mai baka haƙuri akan hakan""" """Sorry for yourself Sharfaɗi"" Sharfaɗi ya ji saukar muryar Professor bawai mamaki ya bashi ba, yana dai" "tunanin yadda ya rufe idanunsa ta doke kuma yake son ƙwace dukiyar Safiyyerh, tunda Safiyyerh take sisi na salary ɗinta matsayin Manager bata taɓa amsa ba, sai ma kawo wani kuɗin da take ta saka tana daga cikin top 5 richers na masu hannun jari a kamfanin, kuma ita ce ma'aikaciya wacce tafi kowanne" ma'aikaci zaƙaƙuranci. """Safiyyerh dai ƴata ce ina da iko da abin da yake mallakinta, kafin a kammala rubuta sunanta dole a" "samu sunan Abdu Marafa a maƙale da nata, ka faɗa mini tsare-tsaren ku zan bi presidua ɗin komai idan hakan yana nufin bani dukiyar Safiyyerh dake wannan kamfanin""" """I am sorry Abdu Marafa, amma ba mai yiyuwa bane hakan""" """Mene zai hana hakan yiyuwa?"" Daddy ya ce yana buga table ɗin gaban Sharfaɗi tare da miƙewa tsaye" """Please a mutunce leave my office, dukiya umarnin mai ita kawai take ji dole sai mun samu saka hannu Safiyyerh a wannan file ɗin"" ya miƙewa Daddy file ɗin yana zagayawa. Daddy ya ɗauki file ɗin ya yi" "murmushi sai kuma ya kalli Sharfaɗi ya ce ""Idan Safiyyerh ta mutu waye zai gaji duk abin da ta mallaka""" """Wanda suka dace mana, ko a kamfanin nan sai wanda ta saka sunansa a matsayin wakilinta""" """You say it all, ni ne wakilin Maama"" murmushi kawai Sharfaɗi ya yi yana ɗaukan key ɗin motarsa ya ce" """Zaka gani""" "Professor ya yi waje, shima Sharfaɗi haka daddy ya nufi motarsa thinking ta ina zai fara neman signature" "na Safiyyerh? A haka ya isa gida ya yi parking motar daidai nan Dr Hash shima ya dawo daga asibiti ya kalli Mahaifin nasa ""Daddy fita ka sake yi jininka ya hau sosai fa, kada wani abu ya sameka"". Daddy ya girgiza kai a hankali ya fara tari yana dafe kan shi nan da nan idanunsa sukai jajur da sauri Dr Hash ya kama Daddy zuwa cikin gidan lokacin Ummimi na zaune fuskarta ba walwala ta cire idanunta zuwa kan su sai bata ce komai ba Ummi kuma ta ce ""Subuhanallahi ba dai jikin bane? Yaushe ya fita na ɗauka yana" "cikin part ɗinsa""" """Na je Companyn da Maama ke aiki, ko zan samu wani bayani amma shiru"" idanunsa kamar za su zubar" "da hawaye ya juya ya kalli frame ɗin picture ɗinta, ta yi murmushi fararen idanun nan nata sai sheƙi suke," "ta tsuke laɓbanta kana ganin bakinta kasan na tsiwa ne lokacin basu jima da dawowa daga Saudia ba," "har Yaya J na tsokanarta Hajiya guda babu haƙorin makka ta murguɗa masa baki ta ce ""Ai don Allah na yi, ba sai an san na je ba""" """Ina kike Maama? Ina kike safiyyerh Allah Ya sa ba su cutar mini da yarinyar ba, Safiyyerh kina lafiya dai" "ko? Na kasa taimakon ki, arziƙina bai yi mini rana ba"" Ya girgiza kai yana dafe saitin zuciyarsa Ummi ta share hawayen da yaƙi tsaya mata ta ce ""Shi ya sa ban amince da dawowar mu ƙasar nan ba, amma kun kasa fahimtata kalli yanzu babu Safiyyerh. Allah ka kare mini yarinyata ka sanya tana hannu na gari, ka dubi wawta da rashin lissafinta ka kiyaye mana ita"" sai kuma ta fashe da wani irin kuka duk duniya yarinyata ɗaya a duniya mace Safiyyerh, da ita take shawara amma yanzu ba Safiyyerh a tare dasu. ""Junaid ka samu Gadanga a waya?"" J ya girgiza mata kai alamar a'a shi tun sanda aka yi auren Safiyyerh da Aliyu ya rasa bakin magana baya fahimtar abubuwa da dama. Da J da Dr Hash suka kama Daddy zuwa" "part ɗinsa dake upstarts bayan sun kwantar da shi J ya juya Dr Hash ya ce ""Daddy""" """Ya aka yi Hisham?""" """About Maama's sick, condition nata ta kusa cinye lokaci ba'a yi mata allura ba, rashin yin allurar ka san" "me yake nufi, mu duka ba zamu iya ba idan hakan ya kasance ka san taurin kan Safiyyerh da kafiya da" "naci, ga ta da ƙulafuci da saka abu a rai, ita bata yadda da gazawa ko kasawa. Ban san me ya saka haka" "ba daddy komai da zai faru Ubangiji ya riga daya rubuta, baka tunanin zuwa gaba halin da za a iya saka" "Aliyu idan gaskiya ta fito, kamar anza zalunce shi ne ka ɗauka ni ne Captain wallahi ko da gida da mota da biliyoyin kuɗi ba zan iya accepting Safiyyerh as my wife ba, ka saka na fara tunanin ko Aliyu ne ba ɗanka ba shi ya sa ka zaɓi laƙaba masa ita? Tunda bai san mene ya faru ba. Laifi tudu ne daddy daga ɗakin asibiti dana bar Safiyyerh kafin na fito ka ɗauke ta kun dawo gida, ko aikin da akai mata bai" "kammala daidai ba, ka rabata da. ,""" """Hisham, out of my room""" """Daddy"" a tsawace ya ce ""na ce ka fita daga ɗakin nan ko?"" Dr Hash ya dinga kallon daddy sai kawai ya" juya ya fita zuciyarsa na zafi da tafarfasa. Bayan fitar Dr Hash daddy ya ɗakko file ɗin da Sharfaɗi ya bashi ya fara dubawa wata iriyar zabura ya yi yana buɗe idanunsa ganin sunan ALIYU ABDU MARAFA da Safiyyerh ta saka matsayin shine next of kin. "***Sa'adah ta dinga kallon Sp Ghali ta ce ""Shifa wanda kuke nema rabon da mu ganshi mun manta," "kuma kun san zaku sake kama shi kuka sake shi tun farko? Wane ya hana a yanke masa hukunci, ita gaskiya fure take bata ƴaƴa kuje ko kama Mutallab bawai mahaifinsa ba"" Sp Ghali ya ce ""Ki iya bakinki a gaban hukuma kike, hukuma sai da rarrashi haka tsarin aikin yake idan ba yaro akwai uban yaro, kun je kun haifi kangararre mara amfani cikin al'umma wanda gwara mutuwarsa da haihuwarsa, gwara ɓarinsa da cikinsa shine kika kwaso ƙafa kina faɗa mana shirme, ki buɗe kunne da kyau kiji kaf jihar Kano da Nigeria baku da wanda ya isa ya kare Scorpion Tahhb daga tuhumar da ake masa, idan kuma akwai" "Bisimillah""" """Gaskiya ne ba ka yi ƙara ba, bamu da gata sai na Allah wanda ya halicce mu, ya samar mata da numfashi" "tun a ciki muna gode masa a yadda ya bar rayuwarmu, mun amshi jarrabwar daya samar a zuri'ar mu, amma ka sani ba wanda yake so ya kasance ɗan iska ko ɗan daba, Ubangiji baya shawara da mutum wajan zamuwarsa talaka ko mai arzƙi, wata shari'ar sai a lahira a gaban Rabbil samawati. Kai ma daka kasance ɗan sanda ba iliminka bane ko dabararka ba wayonka bane ko sahalewarka, kunfa yakun ce ta Ubangiji ta sauka akan ka, shi mahaifinmu da kuka riƙe kuka haɗa shi da mugawayen mutane shaiɗanu iyayen yarinyar ne suka ce ku kama shi?"" Sp Ghali ya yi mata banza don bata ita yake yi ba, ya saka wasu police su fitar da ita idan kuma taƙi a haɗa da ita a ɗaure. Haka Sa'adah ta juya da abincin data zo da shi," wannan dalilin ya saka bata zo da Bafullatana ba domin sai ta musu hauka a cikin state cid ɗin. ***Da yamma bayan ya kammala sallar la'asar ya ci abinci jikinsa sanye da Dag Flight running short red "ɗin riga da black wando iya cinya bai ƙarasa sauka ba, jikinsa duk a murmurɗe sai Bionic hand gloves a da" sauri da sauri yake running akan machine ɗin ya haɗa zufa sosai lokaci lokaci yake share zufar data gama "jiƙa masa six pack ɗinsa slowly slowly kuma ya fara rage gudun har ya kashe gabaɗaya, a sauka a hankali tare da barin training room ɗin ya tafi wajan hutawa bayan ya ɗakko coke a hannunsa mai sanyi, baƙar fatarsa sai sheƙi take da ƙyalli ya tsaya jikin window yana shaƙar iskar dake kaɗawa ya lumshe idanunsa ya buɗe ya kurɓi coke ɗin shi kaɗai sai haɗe rai yake yana ɗan kwaɓe fuska sai kuma ya ɗauki wayarsa ya" duba number har yanzu dai bata shiga “Muhmmad” Saukar muryar da baya taɓa manta sautin ta a kunnensa haka yanzu ma ta sake saukar masa idan komai "nata ya bar shi to banda wannan muryar sai kuma ya haɗe fuska a fili ya ce ""When i catch you Sophie""" sai ya ɗauke tunanin ya ji kamar ya fita waje ya ji ya yanayin garin yake a yanzu gabaɗaya a takure yake. "Ƙarar computer ya dawo da shi daga tunanin cikin sauri ya saka wayara a aljihu yana furta ""Oh no""" "Da yatsunsa biyu ya dinga shafa screen ɗin dake jikin bango, yana shige abubuwa ɗaya hannunsa da" remote control a nutse komai ya fara backup zuwa cikin computer bakinsa ya mayar gefe kamar zai yi murmushi ganin yadda lokaci ɗaya ya yi musu kutse ya rusa komai da suke yana gamawa ya saita zuwa Voa muryar J kallah ya sauka kunnensa. ***Ture farantin abincin Safiyyerh ta yi tana yarfa hannunta saboda wani irin ciwo da mararta take yi "mata da ƙyar ta miƙe ta fito zuwa parlo ta durƙushe ƙasan ƙafafuwanta. Mangal ya dube ta ya ce ""Ƴar" "wahala ashe attajirai ma suna kuka, ɓarayin gwamnati""" """Kana da matsalar tsinannen yaron nan, shegen surutu kamar haihuwar aku""" "Mangal ya yi shiru yana jan sigarin da yake sha Goje ya kalli Moh ya ce ""Kamar bata da lafiya fa"" ya yi" "masa banza ya lumshe idanunsa. Safiyyerh ta kasa daurewa ta fara kuka sosai ta ce ""Wallahi mutuwa zan yi wayyo cikina wayyo daddy wayyo Yaya J,na shiga uku zan mutu Captain""" """Kut dumadu wai ciwo ta kewa kuka nan dai babu Professor balle ki ji motar ambulance""" """Mai dawa"" ya juya a hankali ya dubi Goje ""Bata da lafiya fa""" """Wai kai akan kuwa baka da imani ne?"" Nan ma ya yi shiru kawai Safiyyerh kuka kawai take ta haɗa zufa," "tun tana yi har ta fara sakin ajjiyar zuciya amma Moh ko yatsarsa bai motsa ba, Goje ya gama masifarsa da bala'in sai ya miƙe ya fita daman tuni Mangal ya fice. Ya miƙe zaune yana motsa damtsen hannunsa da baƙar rigar jikinsa ta kama shi, da ƙyar ya yi wanka ya saka shima saboda surutun tsiya data dame shi. Ya buɗe idanu ganin jini a jikinta can ya saka ƙafa ya zungure ta, ta yi masa banza domin bacci ya fara ɗaukan ta ya zamo zuwa gabanta ya duƙa yana kallon ta taƙi ɗago ya leƙa fuskarta suna haɗa idanu ta" "murguɗa masa baki, sai kuma ta fashe da kuka sosai ta ce" """Ba ruwanka dani, ka bar ni na mutu na fasa son ka ba, bana son ka get lost""" """Kina sake matsawa yau a ƙirjina za ki yi bacci"" ta ɗago da sauri ta kalle shi ba zata taɓa cewa shi ya yi" "maganar ba idanunsa na kan wani waje ta zaro idanu ""Mene wannan?"" Ya faɗa yana sauya fuska itama ta kalli jinin wata kunya ta kama ta, sai ta sunkuyar da kai miƙewa ya yi ta fita can ya sake dawowa ya cilla mata leda daga nan bata sake ganinsa ba har zuwa tsakiyar dare tana bacci ta ji warin wiwi da wari mai kama da shisha ta buɗe ido da ƙyar ganinsa ta yi hakinmce a gabanta ya tanƙwashe ƙafa, hannunsa ɗaya riƙe da zabgegiyar wuƙa tana ɗigar da jini ga gefen kansa da wuyansa an yi masa wani lafiyayen" sara ana hango farin ƙashin wajan. """Jarumi faɗa ka sake yi? Wane ya yi maka haka?""" """Abdu Marafa""" "Ta dinga kallonsa na rashin fahimta, shi kuma yatsun hannunta masu tsayi dugwaye dasu yake kallon" "yadda take ƙoƙarin miƙa hannunta tana son taɓa wajan yanka sai kuma ta dunƙule ta fasa kamar tana tsoro. Tana kula ba sai ji ta yi ya miƙa hannunsa keeeee ya janyo ta zuwa gabansa jinin na ɗiga a jikinta, ya damƙe hannunta da kyau kamar yana tsoron a ƙwace ta, ta kasa kallon shi a hankali ya ce ""Idan na kashe babanki Abdu Marafa ƙila ya taimaka wajan kawo ƙarshen komai, kafin nan buɗe kunne ki ji waye MUTALLAB"" ya zauna har lokacin yana damƙe da hannunta a hankali ya sarƙe yatsunsu waje guda yana" kallon fuskarta. KANO/ BIRGET ASALIN LABARIN "Hausawa sukan ce salati baya hana ɗaukan rai, Ubangiji ya halicci kowanne bawansa dake doran duniya" "da keɓantacciyar ƙaddararsa, ƙaddarar kowanne mai rai tamkar inuwa haka bibiyar rayuwarsa, jarrabwar Ubangiji na gudana tamkar jini a jijiyoyin mutum, hakan na faruwa ne cikin farinciki ko akasin hakan, a kowacce rana a kuma wanne shigowar dare da gushewar shi, abubuwa ma bambanta na faruwa a duniyar da muke ciki don gane da rayuwar mu, ita rayuwa tamkar karatun littafi ce, bangon baya nuna me labarin ciki ya ƙunsa, garɗi ne da shi ko ɗaci, ƙarshen shafi baya alamtawa mai karatu abin da kan iya wanzuwa a shafin gaba, hakan kamar saukar numfashi ne a ƙirjin mai rai, idan ka shaƙa babu" lallai ka sake fitarwa ba tare da tabbacin ka yi numfashin ƙarshe a duniya ba. Faruwar komai a cikin tushe da mafarkin ƙaddara ya faro asali ne a ranar Litinin cikin watan May da da misalin ƙarfe 8:25 na safiyar ranar. Tun daga tsakar gidan yake jiyo ihun da take da sautin muryarta da baya fita sosai balle ya ji me take "cewa, ga ƙarar saukar duka ta ko'ina. Ya dubi biredin hannunsa dake cikin ƙaramar baƙar leda safiyar Ranar Litinin ce a cikin watan Mayu. Yana ta tsaye a wajan sai kuma ya ja ƙafa cikin nutsuwa ya ƙarasa bakin ƙofar, ya ɗauki a ƙalla minti ashirin yana runtse idanunsa jikinsa yana rawa amma ƙa'ida ne baya shiga sai an yi masa izinin jin kukan nata na ƙara tsananta sai kawai ya sake yin sallama cikin muryarsa da bata fita. Ledar hannunsa ya saka a gigice ya dubi Aby ganin wata zabgegiyar bulalar darbejiya a hannunsa yana ta lafta mata har bulalar ta karye ya fara dukan ta da hannu ƙafa ya saka zai taka cikinta" da sauri ya ce """Aby karka kashe ta""" "Ture Aby ya fara amma ina ya kasa tana kuka bakinta duka jini ta ce ""Muhammad kar ka zo nan, ban" "hana ka shigowa idan muna tare da mahaifinka ba"" ya girgiza mata kai har lokacin jikinsa rawa yake, ya saka hannu biyu ta toshe kunnensa saboda ihun da take ba zai jure ganin ana dukan mahaifiyarsa haka ba, ya fara ƙoƙarin kunna redio ko zai daina jin kukan nata amma ba rediyon ya dinga dubawa babu. Ya yi kukan kura ya ɗane bayan Aby yana ture shi akan ya daina dukan Ammo Aby ya saki Ammo ya juyo da" "sauri zuwa ga yaron, ya kafe Aby da idanu cikin sauri Aby ya saka hannu ya damƙi hannun yaron" """Ka yi mini komai banda yaro na, kar ka taɓa mini Muhammad don Allah"" kamar tana tunzura shi ya" ɗauki Mutallab kamar zai fita dashi waje kawai daga tsaye ya sake shi tare da buga shi da ƙasa.... Mutallab paid book ne via this number on WhatsApp to subscribe urs 08164069385 ArewaBooks zuwa 10 na dare a jira update "[1/7, 9:34 PM] Sis Fauzy: Chapter 20: The beginning of the beginning" " Paid book," 8164069385. "Taurin zuciya irin na Mutallab bai saka ya haƙura ba, kansa na zubar da jini ya miƙe daga buga shi da ƙasa" "da Aby ya yi, ya nufi wajan Ammo wacce take kwance ta kasa motsi jikinta duk ya farfashe ba ƙaramin duka Aby ya yi mata ba. Aby na huci ya nuna Mutallab ya ce ""Ba zaka bar wajan nan kafin na haɗa maka na jaki? Tukunna gidan ubanwa ka je ma? Kai kaɗai namiji a gida amma ba uban da kake tsinana mini" "don ubanka?""" """Malam don Allah ka yi haƙuri, Muhammad wai nawa yake ne? Yaushe ma ƙarfinsa ya kawo don Allah," "girman jiki ne ba wani abu ba, ka mini komai karka taɓa mini yaro na na roƙe ka"" da ƙyar take furucin" "saboda wani zazzaɓi daya rufe mata jiki, shatin bulalar na mata wani irin raɗaɗi." "Da yatsa ya nuna Mutallab dake tsaye, ya kafe Aby da manyan idanunsa da sukai jajur jijiyoyin kan duk" "sun fito sai kallo mahaifin nasa yake. ""Na bar shi ya lalace ko? Daman ya ɗakko hanyar tuni, baya son karatu zan amshi yaran kuwa amma banda nawa, cikakkiyar fatiha ba lallai ya iya ba, allon karatun shi kullum jiya iya yau, to wallahi ba a wannan gidan nan, Ɗan'malam yake, dole aga jinin malunta a jikinsa" "kun gane ko""" """Don mafalamar gidanku ba zaka kafe ni da firgitattun idanun nan naka na rai ni ba, ɗan banza mai zubin" "inyamurai da shegiyar baƙar fuska na rasa kamar wa ka ɗakko"" shi dai Mutallab bai yi magana, kuma bai ɗauke idanunsa daga kan Aby ba. Ya sunkuya ya ɗauki ledar daya shigo da ita zai shige wajan Ammo Aby ya saka hannu ya ƙwace ledar ya zazzago biredin Aby ya ɗauke yana jujjuyawa a hannunsa ya dubi" Mutallab ya ce """Ina ka samu wannan? Sata ka fara ko wane ya baka?"" Ya daka masa tsawa ya ce ""Ba magana nake maka" "ba, sai na zarara maka wannan dorinar?""" """Ban taɓa sata ba, ba ni zan ci ba ku na samuwa""" """Ka samu? To a ina?"" Mutallab ya kalli Aby ya kalli biredin ya kasa cewa komai ya ɗauki mintuna yana" "sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya kafin ya ce ""Ina da shara na yi, Ammo bata ci abinci ba tun jiya haka Muneeberh""" """To ya fi maka dai, kuma ka shige cikin almajirai yanzu na zo na ji inda ka tsaya a karatun naka"" ya gutsira" biredin gida uku ya ɗauke kaso biyu ya cillawa Ammo ɗaya ya yi waje har ya yi nisa ya jiyo muryar Mutallab ya ce. """Kai ne babana, kamanninka ne""" "Yana faɗin hakan ya shige can cikin ɗakin ya zauna yana sunkuyar da kan shi zuwa ƙasa, gabaɗaya a" "cunkushe yake jin zuciyarsa jin sautin muryar Ammo yake ji na sauka a kunnensa da zarar ya rufe idanunsa, bai san me ya sa Aby yake yawan dukan ta ba, bai san me ta yi masa ba, ko daman haka kowanne uba yake dukan matarsa? A gaban yarenta ya ja numfashi ya sauke ya juya ya kalli ɗakin so" yake ya tambayi Ammo ina Muneeberh? Amma ya rasa yadda zai buɗe bakin nasa. "Ɗakko biredin da ya yi saura ta yi ta raba biyu ta ce ""Karɓi wannan kaci ka sha ruwa sai ka je ka ɗauki" "allonka ya yi maka karatun, don Allah na Ammo ka dinga jin magana don Allah""" """Bana ci, ki bawa Muneeberh""" "Tana girgiza masa kai cikin damuwa ta ce ""Na san baka ci komai ba, ka amsa Muneeberh ƙila ta samu" "abinci a gidan da taje yi musu aike, da nace ta je gidan Hameeda to ashe sun koma Legas da mijin nata, Bafullatana ta yi nisa kuma itama fama take da kanta, babbar damuwata satin da zamu shiga shine satin bikin Sa'adah gashi ba mu yi komai ba, malam zai iya cewa a ɗaga"" duk maganar da take yi kallon ta kawai yake bai ce komai ba, sai lumshe idanunsa yake alamar bacci yake ji, domin jiya sai wajan shabiyu na dare ya shigo gidan yana wajan siyar da rake yana dawowa kuma malam ya tattara kuɗin da jarin da" ribar ya ƙwace. Ganin ba zai yi magana ya saka ta miƙe tsaye da ƙyar ta ce """Ko Sa'adah da Muneeberh sun dawo kar ka kuskura ka yi maganar abin da malam ya yi mini, ina sake" "jaddada maka ka tashi ka je wajansa ya yi maka karatun ka ji dai""" "Juya mata baya ya yi, ƙafarsa da takalmi da komai ya yi rufda ciki a hankali ya saka hannu ya riƙe cikinsa" "saboda ciwon da yake masa, ya lumshe idanunsa tunani ya fara yadda za a yi ya zama mai kuɗi, kuɗin da zai kula da Ammo Aby ya siya mata abinci da safe da rana da dare ya rushe gidansu ya yi musu wani, mai kuɗi yake son zama yana buƙatar zama mai cikakken iko, amma ta ya ya? Iko baya samuwa sai da kuɗi, kuɗi baya taɓa samuwa sai da ilimi, gashi Aby ya rantse ba zai saka shi makarantar boko ba, kenan babu wata hanya da zai iya zama mai kuɗi? Ba zai yi ilimi ba? Ya mirgina kaɗan ganin ba zai iya baccin ba" saboda yunwa ya miƙe ya fito waje. "Mama Zaituna ce ta dinga dariya tana tafa hannayenta ta ce ""Daɗi miji, ki zauna kamar jaka miji yana" "laftarki na yau daban na gobe daban, kamar kuma kaska kin kasa tafiya gidanku wannan maita har ina? A yi dai mu gani idan tusa zata hura wuta dani ake zancen"" Ammo bata kulata ba, ta fara aikin da yake" "gabanta Mutallab bai tanka ba, ya yi waje abin shi yana bada faɗi." "Can nesa da wajan Almajiran ya zauna yana jiyo duk karatun da suke yi, hankalinsa na kan wani waje" "daban jin karatun na takura masa kawai ya miƙe ya sake barin wajan. Tafiya yake tayi shi kaɗai a ƙasa da ƙyar yake ɗaga ƙafarsa har ya kawo bakin titi inda ake gyaran wani waje kamar masana'anta ya jingina ya dinga kallon babban waje ga ma'aikatu da yawa. Can ya ƙarasa ya kalli wani mutumi ya ce ""Assalamu Alaika"" mutumin ya ajjiye abin hannunsa ya kalli Mutallab ya ce ""Wasalamu Alaika, sannu yaro ya aka yi" "wa kake nema?""" """Zan kwashe muku kaya ko ɗaukan bulo a bani kuɗi""" "Ya dinga kallon yaron ya ce ""Ka zaka iya ɗaukan bulo? Yaro wannan aikin manya ne ka ji ko kamata ya yi" "ace kana makaranta baka dinga gararanba a titi ba""" """Na gwada maka ne?""" """Ƙuruciya ga daɗi ga wawta ina kai ina ɗaukan wannan ai aikin mu ne"" Mutallab ya kalli mutumin sai ya" ƙarasa inda aka ajjiye tarin bulan simitinti hannu biyu ya saka ya ɗauki bulo da kowanne hannu cikin "sauri ya ƙarasa tare da ajjiyewa, a haka ya dinga kwasa yana ajjiyewa har ya kammala ya dawo gaban" "mutumin ya tsaya bai ce komai ba. ""Allah Alhakkamu tuwon alkama kake ci ko na dawa? Ko ni da yake" "aikina ba zan iya kwashewa lokaci guda ba"" ya zura hannunsa cikin aljihu ya ɗakko gudar dubu ɗaya ya" "damƙawa Mutallab ya ce ""Jeka maza, sai kuma gobe idan rai ya kaimu"" Ya dinga juya dubu ɗayan yana jin wani iri ƙasan ransa, sai kawai ya tsallaka titi a hankali ya sake juyawa ya zubawa masana'antar idanu wacce ake ƙara faɗaɗa girman cikinta da wajan. A ƙa'ida Mutallab ya kwashe bulan dubu uku ne amma mutumin ya zame dubu biyu ya bashi dubu ɗaya ya dinga murna ya samu lalar dubu biyu da addu'ar" gobe ma Mutallab ya dawo tunda bai san ciwon jikinsa ba yaron. "Da yamma yana zaune saman dakali ya sauro rake da dubu ɗayan ya siyar har yanzu kuma bai karya ba," "ya harɗe hannayensa a ƙirjin tare da danne cikinsa saboda zafin da yake masa, rigunan jikinsa duka a kusan koɗd suke yanzu ma blue riga ce da gajeren wando ya saka iya qwiwa ya zubawa wani gida idanu yana nan zaune ya ji an dafa ƙafafuwansa ya ɗago suka haɗa idanu. Murmushi ya yi, bayan ya zauna ya ce ""Kai baka zuwa makaranta ne? Kullum ina ganinka a nan zaune"". Mutallab bai bashi amsa ba hakan ya" "saka Kimiya cewa ""bari na sha iska a nan, cikin gida akwai takura""" """Ohh ok"" Mutallab ya ce yana kallon littafin da Kimiya ya ɗakko yana duba assignment. Son da ya kewa" "karatu kamar rai ya saka ya dinga kokawa da nauyin bakinsa kafin ya ce ""Kai kana yi""" """E, ina zuwa makaranta, na koya maka ne"" ya jinjinawa kimiya kai, cikin sauri Kimiya ya ajjiye littafin ya" "ce ""To ajjiye mini ina zuwa"" ya ɗin bisa da kallo, baya taɓa ɗaukan abin da ba nasa ba sai ya dinga bin littafin da idanu yana zaune har Kimiya ya ƙarasu ya ajjiye computer hannunsa, da babban plate da gorar ruwa guda biyu, ya buɗe computer ya juya ya kalli Mutallab ya ce ""Ina son computer sosai, komai na" "harkar na'ura ina son shi, sunana Kimiya kai fa?""" """Mutallab""" "ya furta can ƙasa, bayan ya ɗauki sacanni. ""Nice name, mu ci abinci sai na koya maka karatun ko?""" """A'a"" Kimiya ya ce ""To saboda kai na ɗakko ai, Jadda ta matsa na ci, ni kuma I'm full, ka ci Please""" """Allahamdulilah""" "Shine abin da Mutallab ya sake cewa bisa dole Kimiya ya rabu da shi, a nan wajan ya fara koya masa" "yadda ake karatun Hausa kamar wasa duk abin da ya yi masa take yake ɗauka a kan shi tas, suka fara English alphabets sai kuma irin su two latters words daga nan ya fara yi nasa spelling sun jima suna karatu, Mutallab baya tambaya saboda bashi da magana shi ya sa da an yi abu yake ɗauka ko a magana bai son maimaici. Yana sauraren Kimiya lokaci zuwa lokaci yana kallon abincin da lumshe idanunsa saboda aroman na abincin dake shiga hancinsa. Bayan sun kammala magariba na neman yi a hankali ya sakko daga saman tudun yana kaɗe jikinsa ""bari na je gida, gobe kazo nan na yi maka wani karatun"" ya" "jinjina kai idanunsa akan Kimiya so yake yace thank you, bakinsa ya yi masa nauyi." """Karka damu, never mind abokina sai mun haɗu goben""" "Kimiya ya juya ya tafi, shima Mutallab ya nufi gida, kafin ya shiga ya yi alwala ya bi jam'i cikin almajirai." "Yana shiga gida ya tarar Aby sai zabga masifa yake hannunsa riƙe da bulala Mutallab kamar kodayaushe ya yi sallama cikin Hausarsa. Aby ya yo kan shi da bulala ya ce ""Ɗan banza mai zubin kwaɗona, wato kai" "ba ɗan arziƙi bane, duk maganar da na yi maka ya tashi a banza a iska ko?""" "Maimakon Mutallab ya ƙwace kan shi sai ya ce ""Ina yini Aby? Barka da yamma""" """Yini ban gan shi ba, ke ke kina ina fito nan tunda ke kike ɗaure masa gidan"" Ammo ta fito daga cikin" "ɗaki hannunta riƙe da casbaha. ""Malam gani""" """Wato da na ce ya zo karatu ke kika hana shi ko? Ya tafi gantalin dake gantalalle ne shi, kai uban me ka" "sha ne naga idanunka ya yi jawur, wani abun ka fara watsawa"" Sa'adah ta ce ""Malam ina na ammo zai ga san wani afwa, fafutuka kawai yake yi""" """Ungo wannan Sa'ade, na ce riƙe naki, ki zo kiga yadda ya yi to Allah dai ya sa ba wata jarabar ya ɗakko" "mana ba, kuma mene ya hanaka zuwa ɗaukan karatu""" """Aby bana gane karatu, ba shi nake so ba, ka kai ni makarantarsu Kimiya"" Malam ya buɗe idanu ya ce" """Wacce jarabar ce Kimiya kuma? Karatun addinin ne baka ganewa, to buɗe kunne ka ji yadda babu wani yaro a gidan nan daya taɓa zuwa makaranta haka kai ma ba zaka taɓa zuwa ba, karatun allon shi na yi niyya ka yi ka ji ai""" """Ba zan ba, bana fa ganewa, aya kake ja mini mai yawa tun kafin ka gama faɗa na manta me ka ce""" "Malam ya yi sararo sai kuma ya ɗaga dorinar ya dinga zarara masa bayan ya ɗage rigar jikinsa, duk inda" "ya shimfiɗa masa sai fatar wajan ta ɗaga ta kumbura. Ammo ya dinga bawa Aby haƙuri amma sam yaƙi ji," yace idan ta sake magana zai haɗa da ita ya jibga ta dinga kuka haka Muneeberh. Sa'adah ta ga ji ta ce """Malam shi duka baya magani, ka bishi a sannu idan ya kangare a kan dukan nan wahala zaka sha"" ita" "ma idanunta cike da hawaye, dukan da Malam kewa Mutallab bana wasa bane shi kuma ko motsi ya ƙi yi sau huci yake fitarwa yana kumbura. ""Kamar jaki ka yi ta duka amma baya damuwa sai kace jikin rodi, ji nake kamar na tsinewa ɗan nan""" """Idan ka tsine mini Aby ka yi wa kan ka, da gaske Aby idan na lalacewa kai na lalacewa. ,"" kau! Ƙarar" "sautin marin da Ammo ta saukewa Mutallab a fuska tana nuna shi ta ce ""Ashe baka da kunya, mahafinka ne fa, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un""" """To me na ce? Kalamai ne babu daɗi ne?"" Ammo ta kasa cewa komai ta lura da gaske bai san yadda zai" dinga magana bane. Sunansa ta fara kira shi kuma ya juya ya yi waje har ya je bakin ƙofa ya tsaya ya ce """Haka Moh yake magana, ni ɗan Abdullahi ne da Ammo haka tsarin Moh yake"" ya buga ƙofar jikin bango da ƙarfi kamar zai girgiɗeta." """Kinga zunubin da kika aikata ko? Kinga kuskuren abin da nake faɗa miki tun ba yanzu ba? To kinga inda" "son zuciyarki ya janyo miki, kalli zunubinki nan, ga dai shi nan kin fara girba tun yanzu"" ficewa ya yi yana" buga ƙwafa. "Har ƙarfe tara na dare bai shigo ba, Muneeberh ta ce ""Ammo na duba ko'ina fa baya nan, har Almajirai" "sun tashi karatu"" Ammo ta ce ""Me ya sa Muhammad? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wannan yaron"" Sa'adah ta ce ""Wai me ya yi ne? Ammo Mutallab shi kaɗai ne namiji a gidan nan, ya wankewa Malam kaya ya goge gabaɗaya shekarunsa nawa a duniya? Maintain malam ya nemo abin da za muci Mutallab" "yake turawa wai ya je ya nemo kuɗi duk inda suke a yi abinci, daman ciyar da gidan nan hakƙin na Ammo" "ne? Kuma magana ɗaya biyu babu wa'azi ba nasiha sai a hau shi da duka ko mugun baki, wallahi ku" "daina irin maganganun nan suna tasiri akan yara balle Mutallab da yake da baƙar zuciya, ki dube shi duk inda yake ko ruwa bai sha ba, kalli inda idanunsa sukai zuru-zuru wacce kalar rayuwa ce Malam ya zaɓa mana haka? Sai auri saki amma a waje ya dinga faɗar Allah a baki, shi ya sa ake cewa a yadda da faɗar" "Malam banda abin da yake aikatawa, ace gidan malam guda ya kasance haka?" """Sa'adah furucinki suna tsananta akan mahaifinki, Muhammad ai namiji ne zai jure ai namiji ba kamar" "mace bane"" da mamaki Sa'adah ta ce" """Wake sabo da wahala, shekara goma sha huɗu fa tafiya sha biyar yaushe Mutallab ya isa duka wannan" "wai? Ai shikenan""" "Sa'adah ta yi shiru, Muneeberh ta ce ""Ammo cikina ciwo yake ba abinci? Da na je gidan bata nan zama" "kawai na yi"" a firgice Ammo ta ce ""Muni, kina nufin ba ki ci abinci ba, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Muneeberh bakya jure yunwa fa""" """To ban samu ba""" "Wani hawaye ya taro a idanun Ammo, wannan azababbiyar rayuwa ya ya za su da ita ne? Rana zafi" "inuwa ƙona, ina talaka zai saka kan shi ne ya ji daɗi?. Ta miƙe tsaye lokacin Malam a ɗakin Mama Zaituna yake ta ƙarasa bakin ƙofar ta tsaya tana ta sallama ba'a amsa ba. Labulan ta ɗaga Malam ya yi saurin naɗe ledar tsiran da suke ci da Mama Zaituna yana waro idanu ya ce ""Ya ya na ce ya ya?"". ""Malam Muneeberh bata ci komai ba tun safe, kuma kasan ciwonta ba'a son tana zama da yunwa"" cikin faɗa da" hargowa yana cilla raguwar tsiran hannunsa ya ce """Wai ni kaɗai na haifi yarinya mai ciwon sikila ne? Na ga ji ba, ba zan mutu a tsaye saboda wannan" "galababban ciwon ba, yunwa kuma ta zo ta gwaugwayi ƙashin bayana, ina wancan salmamman yaro ya je ya yi fafutuka ya samu wani abu zuwa safiya muma mu samu na karyawa"" Ammo ta kasa magana ta saki labulen ta maƙale a jikin bango taci kuka son ranta gashi dare ya yi ta rasa inda zata saka ranta, can" "ta zari hijabi ta fita neman Mutallab amma goma da wajan rabi tana bulayi babu shi ta dawo a gajiye liƙis," ta tarar Muneeberh ta yi bacci sai Sa'adah dake zaune ta zabga tagumi ta dubi Ammo ta ce """Ammo wahalar ta isa haka, shekara nawa ne kina ɓoye mana garin da aka haife ki? Ba ki da kuwa nan" "ya kamata ki je can ki nemi ɗauki yan'uwanki""" "Kirjin Ammo ya hau bugawa fuskar nan nata babu walwala ta ce ""Sa'adah yaushe zan cigaba da ce miki" "bana buƙatar wannan maganar ko kin fini sanin me nake yi ne? Iye, la la ahir ɗinki kul kar na kuma jin kin" "tunkare ni da wannan banzan maganar"" cikin damuwa itama Sa'adah ta ce ""Ba zan kuma ba ki yi haƙuri" "Ammo""" "Mutallab duk abin da ake yana cikin ɗakin zaure, ciwon ciki ya kama shi ƙirjinsa na masa zafi," "matsananciyar yunwar da yake ji yana jin fitar Ammo ya kasa tashi shi ba zai ce when last rabon da yaci abinci ba. Kuma ba zai taɓa cewa ya ci ba, tun yana cikin wannan halin har bacci ya ɗauke shi mai nauyi." "***Da sauri take sakkowa daga saman benen tana yi tana duba agogon hannunta, ta farka daga bacci" "bata ji motsin mutanen gidan ba, har Ummeyh. Tun jiya da daddare da ta je yi wa daddy goodnight ta dinga jin sauti da sambatu yana fitowa daga cikin bedroom ɗin nasa ya saka ta yi cak, ta kasa shiga ta ƙara ɗaukan ƙafa zata shiga sai ta sake jiyo surutun daddy da Ummeyh wanda bai dace a ce a age ɗinta suna bari tana jin irin haka ba. Ta dubi lokaci a hankali taga wajan 10:15 she just want to say goodnight" to them. "Ta sake lumshe idanunta ta buɗe har a lokacin tana jiyo sautin surutai da sambatun iyayen nata, ta ji" "ƙirjinta ya buɗe tsigar jikinta ya tashi sosai ta ƙanƙame jikinta, ba tare data san sexual sounds da take ji , sounds ɗin iyayen nata take jiyowa ba, ta ji ta kamu da ƙaunar wannan yanayin da suke ciki duk da bata san mene ba, ta ji dama ita ce. Ta yi trying na buɗe ƙofar babu adadi zuciyarta na dankwafarta tana faɗa" mata """Safiyyerh, su daddy da Ummeyh ne ciki kar ki buɗe ƙofar nan""" "wata zuciyar ta ce ""to amma ihun me suke yi haka? Basu da lafiya ne ko mene?""" "A lokacin goodnight ɗin da bata iya ce musu kenan ba ta juya zuwa bedroom ɗinta, sai dai ta kasa yin" "assignment na makaranta ta ajjiye books ɗin gefe guda ta ji bata ma gane karatun hankalinta duka ya karkata zuwa ga wannan ihun da take ji, kuma ba wannan ne karon farko ba, ko a parlo take zaune tare da Ummeyh sai ta ce bari ta je wajan daddy duba abu, daga nan Ummeyh bata sake fitowa sai ta ji sun fara wannan yanayin." "she tried her best to study but was unable to do so, ganin ba zata iya karatun ba, ta kwanta da tunanin" "yin bacci tunda gobe akwai school, tana rufe ido ta ji wannan sautin dai a wannan karan again and again muryar Ummeyh ce." """Innalillahi Safiyyerh meke faruwa dake ne haka?""" "A fili tana ɗan tura bakinta gaba ta ce ""I can't sleep""" """Try, za ki iya akwai makaranta""" "Ta jinjinawa zuciyarta kai, a haka bacci ya ɗauke ta without knowing hankalin da iyayen nata suke ciki da" alamar kamar sun manta ma tana rayuwa a cikin gidan. """Again"" Safiyyerh ta furta a hankali bayan ta gama tuna cewa jiya har ta yi bacci ba taga su daddy ba. Ta" dubi agogo takwas ta kusa ta ɗan marairace tana sake sakkowa jikinta sanye da uniform. """Daddy, daddy, Ummeyh Ummeyh""" Ta dinga jera musu kira daidai lokacin data kammala sakkowa daga saman benen kenan. A hankali aka "buɗe ƙofa Ummeyh ta fito daddy ma ya fito cikin shirin tafiya wajan aiki Safiyyerh ta zuba musu ido lokacin da suka haɗa idanu da Ummeyh ta ɗaga mata hannu tana ƙoƙarin gaida daddy taga ya ja Ummeyh gefensa ya sumbace ta, sumbata mai girma da tsayi wanda ya sanya Safiyyerh saurin lumshe idanunta tana ƙanƙame jikinta da ya yi mata nauyi, wishing and hoping ina ma ita Daddy ya kewa abin da" ya kewa Ummey dama ita ce Ummeyh. """Good morning daddy""" """Morning my dear, har kin shirya You are almost late for school, ten minutes to eight kina can kina bacci" "ko Safiyyerh?""" """Na yi assignment ne""" "Ummeyh ta ce ""Kuma assignment ne sai da gari ya waye? You're not serious Safiyyerh kin yi breakfast?""" "Ta jinjina kai alamar ta yi, kanta kuma har lokacin yana ƙasa saboda daddy bai saki Ummeyh ba. Ta juya" "tana ɗaukan school box ɗinta ta ce ""Ummeyh sai na dawo"" ""Ok, ki kula sosai""" "Safiyyerh na zaune cikin motar daddy ya buɗe ya shigo, ita dai bata ce komai ba, zuriyarta na faɗa mata" "ta tambayi daddy me ya sa suke haka shi da Ummeyh ko basu da lafiya ne? Saboda various sounds ɗin is so annoying to her yana sawa ta dinga jin wani iri ta ji dama ita take yi dama kuma ita ce a shoe ɗin su. Daddy ya fara dropping Safiyyerh a school, koda ta shiga class bata fahimtar komai. Bayan sun fito break class captain ya dinga takura mata ita dai bata kula shi ba assignment ɗin kuma ta samu 0/10 ita da" kanta ta san shirme ta yi sanda ta yi bata ma san me take rubutawa ba seriously. "Safiyyerh na parlo a zaune gidan ya yi mata girma sosai ta juya ta kalli Ummeyh ta ce ""Ummeyh ba kowa" "gidan, shiru babu daɗi""" "Ummeyh ta ƙarasu ta zauna ta ce ""Iyee yau ke kike cewa gidan babu daɗi? Basa nan ne kema ai ba" "fitowa kike ba You are always in your room Safiyyerh""" "Murmushi ta yi wa Ummeyh tana lumshe idanunta ta buɗe ta ce ""Yawwa, Ummeyh idan mutum ya yi" "shekara nawa ne ake masa aure"" sosai ta yi mamakin furucin Safiyyerh at her young age ta dinga kallon" "yarinyarta ta kafin ta numfasa ta ce ""Sai mutum ya yi a ƙalla shekaru ashirin da biyar, ya girma sosai ya" "kammala karatu""" """Lallai sai an kammala karatu Ummeyh? Dole ne?""" """Is like a compulsory""" Safiyyerh ta jinjina kai kawai tana kwanciya saman kujera tare da ɗaukan remote jikinta sanye da baƙin jeans da riga short body kalbar dake kanta ya sauka har zuwa armchair sai kawai channel channel take daga ƙarshe ta bar wata channel inda ake haska tarihin faɗan tutsi and hutu can ta sake sauyawa tasha a haka ta ji sallamar ƙawar Ummeyh Maryam. Safiyyerh ta miƙe zaune bayan ta ajjiye remote ɗin hannunta ta ce """Ina yini Anty?""" """Lafiya lou ɗiyar arziƙi ya makaranta?""" """Good Anty""" "tun kafin Safiyyerh ta tashi Ummeyh ta ce ""Maryam kaya sun yi kyau sosai, na ji daɗin kayan Aisha s" "bayero skin care and herbal medice sosai kin ji yadda mu ka yi da daddy?""" "Maryam ta yi murmushi ta ce ""Oh kayan nan? The best kayan mata sellers kenan indai s bayero ce""" "Maryam ta yi ƙasa da murya ta ce ""Amma bai kamata kina irin maganar a gaban yarinyarki ba, kin san" "yaran zamani kuma ma apart from this bai kamata ba"" Ummeyh ta juya ta kalli Safiyyerh hankalinta na kan t.v ta ce ""Safiyyerh nawa take? Duk me zan ce a gabanta bata sani ba she is just 14yrs going to 15 she is still remain my baby""" """Ah! Lallai a secondary school take fa ki daina ganinta haka""" """A'a ba haka take ba, nawa ma take kar ki ɓata mini rai haka kawai"" Maryam ta yi murmushi ta ce ""Ya yi" "to, wannan da kika gani a waya shine ake using da shi before going to bed, na sex kenan"" hankalin dai Maryam bai kwanta ba sai ta kalli Safiyyerh ta ce ""Safiyyerh je ki kawo mini ruwa"" Safiyyerh ta ajjiye remote ɗin a hankali kuma ta ɗauki wayar Ummeyh ta shige kitchen chrome ta shiga bayan ta kunna data ta fara goggle da sauri ta rubuta “Sex meaning” sai aka watso mata sex na gender ta goge da sauri" tana kallon hanyar waje hannunta na rawa ta sake rubuta “Sex between daddy and Ummeyh..... A yi weekend lafiya Allah ya nuna mana Monday cikin aminci....... "[1/7, 9:34 PM] Sis Fauzy: Chapter 21: thief" "Goggle ya watso mata videos sama da ashirin with different style, Safiyyerh ta bubbuɗe idanu bakinta" "buɗe, she can't believe it ai ita ƴan iska take gani ta girgiza kai cikin siriryar muryarta ta ce" """Oh no, i said with daddy and Ummeyh, wannan ba parents nawa bane goggle""" """Results not found"" suka bata amsa, Safiyyerh ta yi shiru thinking to waɗancan mutanen ai iyayen wasu" "ne, ita daddy da Ummeyh take tambaya jikinta ya yi sanyi sai ƙifta ƴan idanunta take, idan ta yi kamar za ta yi playing videon sai ta fasa, ita ai daddy take nema, sai ta ajjiye wayar hoping wani lokacin za su nuna mata. Drinks ta kwaso a plate da snacks ta gorar ruwa ta ɗauki wayar ta saka cikin jeans ɗin jikinta, a hankali ta fita zuwa parlon Anty Maryam na ganinta ta yi shiru tana murmushi ta ce" """Yawwa Safiyyerh thank you""" Ta yi murmushi sometimes murmushinta tafi iyawa sai ƙifta idanu. Ta juya ta kalli wata farar roba da aka "rubuta S Bayero jiki ga wasu magunguna da aka rubuta, hatsabibiyar gumbar madara data nonon raƙumi, maganin basir dana sanyi sadidan sai maganin hips da breast. Safiyyerh ta miƙe ta je ya zauna can saman kujera tana sake ɗaukan remote bawai t.v take kallo ba hankalinta da tunaninta yana ga maganar da su" Ummeyh ke yi da take cewa """Kin tabbatar maganin nan yana da kyau? Ni bana son kashe kuɗi na siyi abu a banza, i hate it ki yi mini" "confirmation please Maryam"" Anty Maryam ta ce ""Wannan fa testing and trust ne, idan kika sha wannan wallahi da gudu za ki ɗauki waya ki kira Alhaji Abdu, yazo sabga ta samu, ke ba ki yi mamakin yadda kike zaune har yanzu ke kaɗai ba? To ai duk wannan gyaran ne ya saka, wallahi kayan S Bayero na musamman ne ko nono mace ya zube ta sha sai taga abin mamaki, gana ƙarin ni'ima mijinki ya jiki so ma" "sha Allah, ba zai so ki dinga nesa da shi ba sam ina faɗa miki you'll come for more""" """Allah Maryam? Na yarda dake yanzu kin gane ki bani address na S Bayero kawai da number wayarta sai" "mu dinga magana da ita, ba sai na sakaki ɗawainiyya ba ko?"" Anty Maryam ta watsawa Ummeyh harara" "ta ce ""Ji ƴar baƙin ciki, kawai ɗan abin da nake samu na riba zaki rage mini sara nake wajanta fa, matar nan baiwar Allah ce komai lalacewar mace sai ta gyara ta sosai, an yi komai a can a can""" """Na ga alama, bani details nata""" """Kano Kuntau gadon kaya cement kafin a fita ring road take, kina zuwa ki tambayi wace Aisha s bayero" "skin care nd herbal medice the best kayan mata sellers ko kawai ki kira numberta +234 812 149 1609"" Ummeyh ta ce ""Kiran zai fi ko?"" Sun jima suna hira har suka fara yin ƙasa da murya gudun kar Safiyyerh ta ji, Ummeyh ta juya taga ta yi bacci ta dinga zayyanawa Anty Maryam abubuwan da suka faru tsakaninta da daddy, suna ya yi suna buga shewa har Anty Maryam ta tafi. Ummeyh ta dawo parlon ta ɗan leƙa fuskarsa Safiyyerh taga bacci take ta sake taɓa hannunta ta ji ya kwanta sai ta sauke ajjiyar" "zuciya, ta kwashi kayan zuwa bedroom ɗinta." "Ƙyallaro idanu ta yi barin Ummeyh parlon, ta buɗe idanun zuwa sama tare da yin shiru ta dinga tunani a" "ranta, mene kuma ni'ima? Sunan wata friend ɗinta ce a Islamiyya, ko ita zata tambaya? A hankali ta miƙe" "ta nufi upstarts suka ji karo da Ummeyh ta shiga murza idanu Ummeyh ta ce ""Daman ba bacci kike ba dear? Are you awake?""" """Yanzu Ummeyh na tashi""" "Yadda ta ɗan washe fararen haƙoranta tana lumshe idanunta Ummeyh ta gani, ta girgiza kai kawai kafin" "ta ce ""Kar ki sake komawa bacci yanzu, ki je ki yi wanka ki sauya kaya ki dawo ƙasa yanzu kin ji ai?""" """Ok"" kawai Safiyyerh ta ce tana tafiya zuwa bedroom ɗinta. Ta jima tsaye gaban mirrow bayan ta fito" "daga wanka tana kallon kanta, a hankali ta yi baya ta juya ta cikin madubin haka kawai batun hips ɗin da Anty Maryam ta faɗa ya dinga yawo a ranta, ita ai bata da shi? Ko sai ta zama kamar Ummeyh zata samu ne? Ta dubi ƙirjinta daya fara ɗan tasawa sosai saboda cima mai kyau da kwanciyar hankali, sai ta tura bakinta cikin yanayin damuwa a fili ta furta ""Kamar na Ummeyh nake so, ni komai irin na Ummeyhna nake so"" ta yi baya ta kwanta saman gado ta lumshe idanunta, ta samu kanta ta tuna yanayin data samu su daddy nan da nan tsigar jikinta ya fara tashi ta cure waje guda a hankali hawaye ya silalo ta gefen idanunta wani irin ciwo take ji haka kawai, ga mararta ya kumbura ta fara birgima akan lafiyayen gadon" "nata tana kuka a hankali tare da riƙe cikinta, har lokacin kuma sambatun daddy da Ummeyh take ji a" cikin kunnuwanta jikinta ya fara wata kalar kakkarwa da ƙyar take sauke numfashi a hankali kuma bacci "ya ɗauke ta, ta cure waje guda hannayenta tsakanin cinyoyinta a wahale take baccin." "***Tsaye ta ganshi a kanta ta ɗaga idanu suka kalli juna can ta ce ""Muhammad baka da lafiya ne? Ina" "kuma ka shiga jiya na game unguwa da neman ka? Ina ka kwana Muhammad?"" Shiru ya yi mata yana ta kallon ta ya juya ya kalli Muneeberh dake kwance ta yi shiru tana jan numfashi." """Ina magana ka tsaya mini aka, kai ba soja ba kamar ka haɗiye muciya na ammo?""" """Ina kwana?""" "Ya furta da ƙyar, domin kallon da ya yi mata abin da yake son cewa kenan yake tunani ya zame ya zauna" "saman ƙafafuwansa kamar ana masa dolen zama, sai kalle kalle yake yi. ""Lafiya lou, ina ka shiga jiyan" "ne?""" """Ɗakin zaure""" """Ɗakin zaure kuma? Ɗakin da yake cike da tarkace ga sauro baka gudun lafiyarka?"" Ta yi tambayar cike" "da damuwa ya ɗan buɗe fararen idanunsa kamar zai faɗaɗa fuskarsa sai kuma ya haɗe gira ya ce ""Jinin moh lafiya yake, Moh yana da kyakkyawar lafiya""" """Iyeee to kar na sake ganinka a wannan ɗakin ko dabba ka ajjiye ciki ai ka dinga tausaya mata balle ɗan" "kyakkyawan yaro na""" """Ammo, ki daina kar a ji""" """Me zan daina kuma?""" """Moh ba yaro bane, Moh namiji ne, ni ba yaro bane""" "Ta dinga kallon shi da mamaki, a dai haka jikinsa baya nuna shekarun da yake da shi sam, yana da baiwar" "tsayi ƙwarai da jiki mai kyau duk da wahalar da suke sha na fama da yanayin rayuwa, da yawan lokaci" "bata ɓata bakinta wajan faɗar shekarun Mutallab. Ta jinjina masa kai ta ce ""Sannu namiji, ka tashi ka je cikin ɗalibai ka ɗauki karatu don Allah Muhammad""" """In faɗa miki gaskiya?""" "Ya ce yana sake kallon Muneeberh dake kallon shi sosai jininsa ya haɗu da yayar tasa, daga ita sai shi zai" "iya yin komai saboda ita haka yake ji a ƙirjinsa. Ammo ta ce ""Wacce gaskiya kuma na ammo daya shige ka yi abin da mahaifinka ke so, ka yi karatu sosai ka gaje shi"" kamar ta faɗa masa mugun abu ya ɗan runtse idanunsa ya buɗe take suka sauya kala ya ja numfashi ta cikin ƙirjinsa ya fesar zuwa waje. ""Gadon" "allo data wada kenan, ba zan iya ba makarantar su Kimiya nake so don Allah ammo""" """Waye kimiya?""" """Wani, ya iya karatu har turanci don Allah a saka ni""" """Muhammad bani da ikon saka a makarantar da kake so, idan ma ina da shi bani da ƙarfin hakan bani da" "shi ka yi biyayya ga mahaifinka shine fatana, duk wani yaron arziƙi da yake son gamawa da iyaye lafiya dole ya yi musu abin da suke so ciki har biyayya dole ce wannan Muhammad ka yi karatu don Allah, kana kallo yana ganin kamar ni nake sawa kake bijire masa haba na ammo autan ammo namiji babban mutum"" ya sunkuyar da kai sai cin magani yake ya jima kafin ya miƙe ya ƙarasa wajan Muneeberh ya" durƙusa daidai kanta ya ɗuka ka ɗan yana bubbuɗe idanu """Me?""" """Cikina ne"" ta bashi amsa ya saka hannu ya ɗago ta zaune tana ɗan riƙe hannunsa ta yi masa murmushi" "ta ce ""ɗan'uwa in sha za ka ji daɗi watarana,ko ba yanzu ba zaka tuna na faɗa maka""" """Kin karya?""" "Ta girgiza masa kai ya tsora mata idanu da sauri ta ce ""A'a ɗan'uwa"" ya yi shiru har sannan yana riƙe da" "ita a gefen jikinsa Ammo ta ce ""Dame zata karya ba komai a gidan, sile idan ina da ita to ban san da zamanta a ɗakin ba, na je duk inda ya kamata babu wani taimako ya za a yi? Rayuwa ce"" a hankali ya kwantar da Muneeberh ya miƙe tsaye tare da fitowa a tsakar gidan ya ci karo da Aby riƙe da bulala ya shigo ɗaukan allo ya ɗaga bulalar ya zararawa Mutallab, bai tsammaci dukan ba hakan ya saka ya buɗe ido yana shafa wajan hannunsa ya taɓo dan shi wanda yake da tabbacin jini ne ya dubi Aby a hankali ya" ce """Barka da safiya. ,"" a tsawace ya dakatar da shi da faɗin cewa ""Karka ƙarasa ahir ɗinka, ɗan banza mai" "zubin adawa kai wannan da a ƙarnin fir'auna ka zo da ƙyar idan ba'a yaron shi zaka tashi ba, kai gabaɗaya baka da imani da tausayi a zuciyarka Muɗallabi? So kake na faɗi na mutu da wahalar ku? Ba abin da ka iya dai gantali da zaman gida anya kana son wanyewa lafiya? Kana son rabauta duniya lafiya ko sai duniya ta yi maka atishawar tsaki? Ɗan banza yaro da idanu daƙwa-daƙwa kunne wani falau anya da ba ɗan ta'adda za a yi ba aka fasa wasbunallahu"" Mutallab bai ce komai ba ya kafe Aby da idanun da" yake aibatawa yana ƙoƙarin haramtawa jikinsa yin rawa. Mama Zaituna ta ce """Malam dubi yadda ya kafe ka da idanu? Ai na manta jikan su iyalode ne da Adebayo, idan ya ɗauki" "baƙar zuciya da ƙifaɗi kar ka ji mamaki ai haka jinin yarabawa yake gudana, baya tsotsa a nono ba? La shakka sai abin da ka gani kawai malam""" """Aby... Aby... Aby halitta Allah ne ni fa, halittar Ubangiji zaka haɗa ni da fir'auna? Ni ni ko?""" """Kai kai, e kai don gidanku ka wani gyaɗa kai kamar ƙadangare to ba halin fir'auna kake nuna mini ba?" "Gidan nan babu wanda ya saka komai a cikinsa amma ka je ka saka uwarka a gaba, zaka shige ko sai na ɗaura maka mari yanzu yanzu ba sai anjima ba"" Mutallab sai huci yake ya kasa cewa komai, idan ya kalli mahaifin nasa maimakon ya ji zafi sai ya ji wani irin so da ƙaunar Aby na gudana a jikinsa, Ubangiji ya jarabce shi da wata irin soyayya da ƙaunar iyayen nashi. Ya kasa cewa komai ya jinjina kai kawai ya fice daga cikin gidan Aby ya ce ""Da ƙyar ba ɗan ta'adda za a yi a wajan nan ba, jinin yarabawa na yawo a" "jikinka""" Mutallab na jiyo Aby bai magana ya nufi waje yana tafiya a hankali shi kansa baya tuna rabon da ya saka "wani abu a cikinsa. Ya dinga yawo amma ko dakon da yake samu yau babu wani labari, daman kuɗin jiya tuni Aby ya ƙwace bai faɗawa Ammo bane kuma babu mamaki da shine ya siyi wannan tsiren da suka dinga ci da Mama Zaituna. Ya koma wajan ginin masana'antar amma yau aka ce ya yi haƙuri babu, ya dinga bulayi bara a kufai har rana ta take babu ko ruwa a cikinsa. Tunawa ya yi da gidan Alhaji Wada da" yake ɗan unguwar kuma shine mai arziƙi a area ɗin kai tsaye ya tafi gidan ya isa bakin gate mai gadi ya kalle shi ya ce """Ya aka yi? Wa kake nema?""" """Shiga zan""" """Gidan gyatuminka ne da kai tsaye zaka shiga? Bar wajan nan""" """Ka buɗe mini, Aby bai yi maka komai ba ka daina zagin babana, ka daina da gaske ban so""" """Iyee ba shakka to idan kai cikakken mara kunya ne zo ka shige ni ka shiga gidan muga, wani yaro" "baƙiƙƙirin da kai sai buɗaɗɗan ƙirji "" Mutallab bai ƙara kallon mai gadin ba ya nufin cikin gidan, ganin haka ya saka mai gadin saurin babbake hanya shi kuma ya na zuwa ya saka ƙafin kafaɗa ya bangaje mai gadin ya faɗi wanwar a wajan cikin sauri ya shige cikin tafkeken gidan, a nutse ya dinga bin gidan daya gaji da haɗuwa, an saka gwarya a gurbinta komai na gidan sai da ya nuna kan shi cewa da arziƙi aka siye shi, Mutallab bai taɓa tsammanin a rayuwa akwai gida irin wannan ba, kamar ba za a mutu ba. Ya dinga tafiyarsa mai faɗi yana riƙe ƙugu tare da ɗan rarraba idanu har ganinsa ya sauka akan sharar gidan, fal" nama a cikin shekarar su shinkafa kayan abinci mai kyau wanda aka wofitar dasu a cikin dustbin. "Yana kishin giɗe cikin shigar shan iska, ya tumbinsa dake waje yana nasa sha'anin ya saka hannu sai" "shafa ciki yake hannunsa ɗaya riƙe da jarida yana dubawa, ya ɗora ƙafa ɗaya saman kujerar dake gefe yana kaɗawa a hankali ga tarin lunch da aka jere masa gari guda kaɗan yaci ya ture gefe. Hajiya Salmerh dake gefe ta ce" """Alhaji wai yaushe za a buɗe sabon shagon nan naka ne? Ya kamata a ɗauki ko yaran unguwar nan uku" "ne marasa aikin yi su zauna a shagon""" """I don't think so "" Ta ce ""Me ya sa to? At least a rage masu zaman banza, na ga cewa kai ne mai kuɗi a" "wannan unguwar wanda Allah ya azurta kuma akwai yara maza da dama masu buƙatar aiki wanda ba su yi makaranta ba, idan muka jasu a jiki a haƙiƙa mun tallafa ko"" ya ajiye jaridar hannunsa ya kalleta ya ce" """Da Allah ya yi mini arziƙi sai aka ce na saka ƙafa na wofitar da arziƙin ta hanyar jawo yaran talaka jikina?" "Shi ne abin da kike nufi Hajiya Salmerh? Ke da yaran talakawa muke ja a sabgogin da muke kin isa kiga na kawo haka? Haran da babu abin da suka sani sune kike nufi na damƙawa dukiyata ko?"" Ta girgiza masa kai ta ce ""bana nufin haka Alhaji. Idan muka duba su yaran basu da abin yi kasan kuma rashin sana'a ga matasa yana kawo illa ga al'umma, wani daga nan yake rasa nutsuwarsa shi aikin riƙe shago ba lallai sai mutum nada ilimi ba idan har zai iya lissafa kuɗi daga ɗaya zuwa miliyan ya kuma iya Hausa," "apart from this sai me""" """. Uncomfortable thinking""" "Ya ce; kafin ya kalleta ya ce ""Shi talaka a duk sanda kikai mai halarci sai ya miki akasin haka, idan kika ja" "shi inuwa ya kai ki dare at the end, shi ya saka Ubangiji ya yi su a talakawa kuma su ƙare cikin talauci su dauwama a shi, su yi ta bauta mana suna bibiyarmu kamar kare da jela, yadda kika gansu haka just leave them, Allah shi ya san manufar jaki da bai yi shi da ƙaho ba, ni ba zan iya jan talaka jikina ba, ba kuma" "zan zuba idanu ƴaƴana su yi tarayya da yaran talakawa ba, shi talaucin nan masifa ne""" """Alhaji saboda hakƙin zaman tare dana maƙotaka, Ubangiji ya ce da damar wani ya ci gadon wani to" "maƙoci zai ci gadon maƙocinsa, ni dai na fita har ga Allah"" ya yi mata shiru ta juya zata tashi sai a lokacin ta lura da shi dake tsaye ta yi saurin cewa ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, kai lafiya?"" Mutallab ya rufe idanunsa ya buɗe, ji yake kamar ya muzanta bai taɓa ba, ya kasa jurewa ba zai iya zuba idanu yaga Muneeberh cikin jin yunwa da ciwo ba. Da ƙyar ya haɗiye yawon bakinsa ya shige maƙot; kafin ya sake" kallon Hajia Salmerh dake cewa """Me kake so, alamjiri ne kai waya turo ka, ko shara kake ɗaukewa?""" """Abinci na zo a sammini, a sani a makaranta kuma""" "Hajia Salmerh ta kalli Alhaji Wada wanda shi kuma yake kallon Mutallab baki sake ya nanata ""A saka ka a" "makaranta?""" """E"" shi kawai Mutallab ya ce, yana tsastsare Alhaji Wada da firgitattun idanunsa Alhaji Wada ya ce" """Saboda Alhaji Wada ne ubanka ya haifeka ko? Yake da alhakin saka ka, kinga irin abin da nake faɗa miki kinga irin tsaurin idanu na yaran talakawa?"" Hajia Salmerh ta girgiza kai ta ce ""A'a Alhaji ba'a haka, ka" "daina don Allah gobe baka san waye zai ji ƙan ka ba"" ta juya kan Mutallab ta ce ""Ya sunanka?""" """Mutallab, Moh shine sunan"" ya faɗa with full confidence ta ce ""Ma sha Allah sannu Muhammad" "Mutallab, ya kamata ace ai yanzu ka jima da fara makaranta ka daina yawo, yanzu zan baka abinci makaranta kuma idan ka je gida sai ka ce a saka ka"" ya yi mata shiru ta juya ta ɗauki wani baban filas" "zata zuba masa abincin Alhaji Wada ya ce ""Idan kika bashi abincina Allah Ya isa Hajia Salmerh""" """Subuhanallahi, me ya kawo wannan maganar mai ɗaci haka? Ai ka kammalawa cin abincin ƙarshe a" "shara za a zubar ka bari na basa don Allah""" """Kuɗina ne, haƙƙina ne so kar ki bawa wani abincina na faɗa miki sanda na yi wahala na samu basu da" "labari ke hatsi nawa ba zan iya bawa wani talaka ba""" """Wai me ya sa kake haramtawa kan ka aljanna ne Alhaji, kake gaba da dukkan abin da zai saka ka" "rabauta tare da hannun riga da abin da zai kawo cigaba arziƙinka?"" Ya dube ta sheƙeƙe ""haka na yi niyya," "rabauta idan kina badawa layi ya biyo ta kai na ki tsalle ke ni Hajia Salmerh""" """Ka yi haƙuri yaro, ka yi haƙuri bani da iko ka ji""" """Ka hana abincin?""" Har wani huci yake jikinsa na kyarma ganin samu da rashi tsoro da fargabar halin da zai ruski Muneeberh ya dame shi cikin tsawa Alhaji Wada ya ce """Get out from my house, fice mini a gida"" ko gizau kamar bada Mutallab yake ba, ya zubawa abincin" "idanu idanunsa wani irin ruwa ya kwanta, wani abu ke ci masa cikin zuciya zafi da raɗaɗin ya bayyana har cikin idanun a hankali ya dinga tafiya da baya da baya yana sake duban abincin sai da ya je ƙarshe ya tsaya yana zubawa Alhaji Wada narkakkun idanunsa da sukai wani irin rikiɗewa sai kawai ya jinjina kai ya" "fita, ya bar cikin gidan cike da wani irin abu a ransa har ya je compound bai lura ba." "Mutallab kasa komawa gida ya yi, ya dinga yawo ko taro bai samu ba, deep down a zuciyarsa thinking" "mai ya sa masu kuɗi masu da son taimako da ƙaunar talakawa ne? Ko mutum yana zaɓar abin da ya kamata ya zama ne? Kamar juya ya nemi dakali ya zauna ya harɗe ƙafarsa waje guda, shi sam bai iya zama bayan wannan ba, ya dinga kallon mutane zaman shi ke sa wahala Kimiya ya ƙarasu hannunsa riƙe" "da littafi ya yi murmushi ya bawa Mutallab hannu ya ce ""Hi""" """Sannu""" "Mutallab ya ce, ba tare daya miƙa nasa hannun ba, Kimiya ya ɗan sha ƙewa yana kallon wani wajan ya ce" """Zo muje karatun""" "Shiru bai amsa, sai Kimiya ya juyo yaga Mutallab wani wajan yake kalla ya ɗauka bai ji me ya ce ba ya" "sake maimaitawa sai a lokacin ya juyo ya mai da hankalinsa ga Kimiya ya tsare shi da idanun nan nasa masu kaifi. ""Wani abu zan nuna maka, it's very important""" """Shhhh"" ya furta sai ya miƙe tsaye, sosai ya fi Kimiya tsayi da jiki tafiya ya fara Mutallab na baya" "hannunsa ɗaya cikin aljihu fuska a haɗe, ɗayan hannun yana shafa samar kan shi da ta yi cunkus baƙa ƙirin da ita. Duk girman gidan Alhaji Wada sai gidan su Kimiya ya ninka shi sau dubu, shi Mutallab bai ɗauka ma da mutane ba a ciki, ko dan shiga sabgar wasu bai dame shi bane? Ya basar duk da gidan ya yi masa ainun iskar ciki ma ta musamman ce amma sai ya yi kicin-kicin da fuska ba walwala sam. A haka suka dinga kurɗawa gidan kuma tsit kamar babu masu rai a ciki har suka isa part ɗin Kimiya, ya buɗe wani ɗaki tun daga ƙofar ɗakin Mutallab ke jiyo sautin na'urori suna shiga yaga abubuwa kamar zasu" buɗe masa ido. """Welcome to my world MOH""" "Kimiya ya buɗe hannu yana murmushi, ya ja baƙar kujera ya zauna ya nunawa Mutallab ya ce ""Zauna na" "nuna maka yadda ake wasu abubuwa da computer""" "Bai zauna ba, sai duƙawa da ya yi ya zubawa mouse ɗin dake hannun Kimiya idanu, a hankali yake" "recoding duk wani abu da yaga Kimiya ya yi. ""I love engineering, na iya hacking na iya kutse zan iya yin abubuwa da yawa alot abu""" """Ohh"" kawai Mutallab ya ce, can ya zauna yana ta kallon Kimiya can ya miƙe ya isa ya fara nuna masa" "yadda ake taɓa computer su shortcut da sauran su. A hankali ya ɗauki ƙafa ɗaya ya ɗora saman kujera ya harɗe hannu a ƙirji, ba'a yi masa maimaici abu shi ya sa babu wahalar ya haddace sun jima a zaune ya" koyi abubuwa da dama kafin ya miƙe tsaye yana kaɗe jiki kamar wanda ya zauna cikin ƙasa Kimiya ya ce """Ina zuwa, ka jira""" "Not too long ya dawo hannunsa riƙe da sabbin kaya, wayam ya tarar wajan Mutallab ya fece ya yi jim sai" kuma ya yi murmushi yana ɗaga shoulders. """Ya naga ka dawo da kayan? Abokin ya tafi ne?""" """You got it right Jeddah he lefted""" "Ta yi murmushi na manyan mata sosai ta ce ""Kuma dai, first haɗuwar ku he refused to eat the food," "yanzu kuma ya gudu wanne kalar aboki ka samu mana yau kuma Kimiya?""" """Jeddah kawai na ji ina son shi""" "Tana murmushi ta ce ""to Allah ya bar soyayya"" ya yi shiru kawai." ***Mutallab ya yi shiru yana kallon Muneeberh data gama fita daga hayyacinta ya juya ya kalli Ammo "wacce taci kuka har ta gaji idanunta ya yi jaa ya kumbura da ƙyar ta ce ""Baka samu komai ba kai ma ko?"" Ya yi shiru ta girgiza kai ta ce ""Allah mun tuba, Allah ka kawo mana ɗauki saboda Manzon Allah, Allah ka ciyar damu kamar yadda ka ciyar da mutanen Annabi Isah ka sauƙaƙa mana wannan yanayin rayuwar""" "Ya sake miƙewa ya fice a zaure ya ci karo da Aby ya ce ""Sannu Aby"" ya ce ""Yawwa sannu gantalalle"" cak" ya tsaya ya kalli Aby a hankali yana girgiza ya ce """Aby ni fa ɗanka ne""" """Ai na ɗauka sadaƙar ka aka bani, zaka huce ko sai na zarara maka wannan a jiki?""" """To ka mayar dani wajan ubana"" yana cewa haka ya yi waje yana wani irin banko ƙofar gidan ya yi yana" jan ƙwafa a fili. ***Da daddare Safiyyerh na zaune idanunta ya shige ciki kamar mai bacci ta riƙe filo a ƙirjinta ta "rungume tsam sai numfashi take ja tare da saukewa ita bata san meke damunta ba, ta ji kawai yanzu bata san komai har karatun komai ya fice a ranta ta buɗe ido ta kalli Ummeyh ta ce" """Ummeyh"" bayan ta amsa ta ce ""Ummeyh shekarata nawa?""" """You are 14 years old Safiyyerh""" """To za'a iya yi wa mai shekaruna aure suna kwana tare da miji a ɗaki suna maganganu Ummeyh?""" "Bata ɗauki maganar Safiyyerh serious ba, ta ce ""A'a, sai ta girma sosai sai a yi mata aure kiga miji ma har" "goyata zai dinga yi""" """Daddy yana goya ki?"" Cikin mamaki ta juya ta ce ""Like how""" """Ohh no my mouth"" Safiyyerh ta ce tana rufe bakinta da buɗe idanunta sosai. Ummeyh bata sake yin" "magana ba can ta miƙe tana ƙoƙarin shiga kitchen daddy ya shigo daga masallaci, da sauri Ummeyh ta tarɓe shi ta rungume shi, shima ya yi hugging nata back, ta ce ""Wlcm darling"" ya zuba mata idanu sai kuma ya sumbaci lips ɗinta da sauri ita kuma ta fara kissing nasa, Safiyyerh ta buɗe idanu sosai tana kallon yadda iyayen nata ke kiss suna shan laɓɓan juna, ta lumshe ido ta ƙare ƙanƙame filon ƙirjinta a hankali ta zaro harshe ta suɗe laɓɓanta ta ƙura musu idanu tana ɗauke komai cikin ranta, sosai take tunani to mene hakan? Ya sunan abin da suke yi almost 5 minutes kafin daddy ya yi saurin janye" Ummeyh ganin haka ya saka Safiyyerh mazewa ya ɗauke idanunta zuwa gefe """Daddy's angel how are you?""" "Ta yi yaƙe na murmushi, ta kalle shi bata ce komai ba. Ya buɗe ido ya ce ""Mene ya samu idanunki?""" """I think I feel sleepy; daddy""" "Ta miƙe tsaye, daga ita sai three qauter da half vest, daddy ya ce ""kin ci abinci? Kin yi assignment?""" "Kai ta jinjina masa ya ce ""Ok good night dear"" ""Daddy, Ummeyh night"" Ummeyh ta ce ""Ok night""" "Safiyyerh ta yi kamar zata shige ɗakinta sai ta shiga bedroom ɗin Ummeyh ta ɗakko wayarta, idan zata" "iya tunawa a bidiyon ɗazo taga irin abin da su daddy suka yi yanzu. Ta kulle ɗakin nata wanda take kwana ita ɗaya ta ajjiye wayar a gefe, ta ɗauki textbook da notebook za ta yi assignment amma ta kasa, ta ji ta manta komai can dai ta rubuta abin da za ta iya yi ta ajjiye abu ɗaya tunaninta yake tuna mata Daddy kiss Ummeyh, Ummeyh kissing daddy ta juya ta mirgina zuwa gefe har lokaci ya ja, can dai ya" janyo wayar ta sake yin searching. "***Cikin dare Mutallab ya nufi gidan Alhaji Wada ya samu mai gadi na bacci, kamar mai rufa ido haka ya" "haura katangar gidan ya dira jikinsa sai rawa yake, idan ya tuna halin daya baro Muneeberh sai ya ci ko zai rasa ran shi ba zai koma ba sai ya nemo mata abincin. Ta baya ya lallaɓa har ya isa store ɗin gidan ya yi dace a buɗe yake biredi ɗaya ya ɗauka, sai baƙar leda daya buɗe ya zuba garin kwaki daya gani shima kaɗan sai suger, ilahirin jikinsa ɓari yake na rashin sabo, a haka ya fito daga gidan ya sake kama katanga ya dira sai sauke numfashi yake, ya riƙe biredin da yake ɗaya tak a hannu ya ji ya samu nutsuwa Muneeberh zata ci wani abun, a ransa kuma ya ji ai sata ya yi kuma sata haramun ce, amma ai ya je ya tambaye shi ya taimaka masa yaƙi. Cikin sasarafa ya nufi gida ba kowa sawu ya ɗauke saboda tare ya nutsa sosai, ya buɗe ƙofa kamar ɓarawo ya shiga gidan ya sauke ajjiyar zuciya ganin babu Aby a tsakar gidan ya ɗaga labulan ɗakin Ammo ya ce ""Munee ga abinc. "" Kalmar da bai iya ƙarasawa ba kenan" "ganin Ammo na kuka kamar ranta zai fita ga Muneeberh dake bacci an lulluɓe ta da zani, Mama Zaituna zai faɗin Allahu Akbar take ya kasa fahimtar mene ya faru ya kalli biredin hannunsa kafin ya yi magana" kuma ƙarar jiniyar ƴan'sanda ta cika unguwar.... MUTALLAB ❤🔥 "Littafin kudi ne, pay before you read. To subscribe urs chat this number via WhatsApp only" 08164069385 500 naira only ❤🔥 "[1/7, 9:34 PM] Sis Fauzy: Chapter 22: Heartless careless" Paid book ₦500 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. Evidence of payment send via WhatsApp number 08164069385 Read on ArewaBooks Read on telegram "Read on WhatsApp, but pay before." Not edited ❤🔥 Jikinsa ne ya ɗauki rawa bayan tunaninsa ya gama wassafa masa gawar Muneeberh ce kwance a gaban "Ammo, bai san ya ake mutuwa ba, balle ya ji yadda ake jin zafin fitar rai, ya dan san idan mutum ya mutu ana nufin ba zaka sake ganinsa ba, jin muryarsa, ko ganin wani abu nashi sai dai abubuwan da ya mutu ya bari. Biredin dake hannunsu ne ya sulale zuwa ƙasa ya faɗi, ledan garin kwakin ta tarwatse da ƙyar ya iya jan ƙafarsa zuwa cikin ɗakin ya durƙusa daidai inda gawar take ya zufawa saitin ƙirjinta idanu yana" saka ran yaga zuciyarta ta buga ko yaya ne amma tunaninsa ya ƙaryata zaton da zuciyata ke yi masa. "Hannunsa ya cira tare da yaye zanin da aka rufe mata fuskar, ganinsa ya fara sauka akan fuskarta da ta yi" "fari tas an toshe mata hanci da audiga haka kunnuwanta. Har lokacin bai yadda gawarta ce a gabansa ba yafi yadda dai bacci take ya ɗan buɗe manyan idanunsa da suka fara shigewa ciki a hankali ya furta ""Bacci take? Yaushe zata farka to?"" Ya miƙe hannu zai zare audigar hancin Muneeberh." "Cikin sauri Ammo ta riƙe hannunsa tana shassheƙar kuka ta ce ""Muhammad, da gaske ƴar'uwarka bacci" "take irin baccin da kowanne mai rai a duniya zai ɗanɗani ɗacin yinsa, baccin da babi ranar farkawa sai a darul salam, bacci da kowa yake jiran ranar wa'adin da nasa zai yi. Muhammad; kana ji Muneeberh ,""" "wani irin kallo da Mutallab ya yi mata ya saka Ammo yin shiru da bakinta, shi kan shi bai yi zaton zai iya" yi wa Ammo irin wannan kallon ba. """Bata jira na dawo ba? Ba na ce zan dawo ba? Mutallab baya ƙarya alƙawari, Munee wake up na samo" "miki abinci""" """Muhammad, Muneeberh ta koma ga mahaliccinta Allah Ya yi mata rasuwa ka fahimci hakan""" """Rasuwa?"" Maimaicin furucin da ya yi ya jishi a tsakiyar kan shi. Ya kama hannun Muneeberh ya damƙe" "ya tuna kafin ya fita nemo mata abincin yana zaune a ɗakinsa na zaure ya yi shiru, Sa'adah ta shigo ɗakin da gudu tana kiran shi ya miƙe ya bi bayanta yana zuwa yaga Muneeberh a cinyar Ammo tana riƙe cikinta,ya ƙarasa ɗakin ya duƙa gaban Muneeberh." """Ya dai?"" Ba ta yi magana ba, ta zame daga jikin Ammo ta dawo jikin Mutallab ya gyara durƙushen da ya" "yi yana riƙe hannayenta biyun ta juya ta kalle shi sai ta yi masa murmushi da ƙyar ya ce mata ""Ina ke" "ciwo?""" """Ba ko'ina, yunwa dai nake ji ɗan'uwa, Ammo ta fita bata samu abinci ba, komai na ɗakinta ta siyar" "saboda ta ciyar damu, Malam faɗa yake wai ya gaji da ciwona, bai san ni yunwa ce ta yi mini mugun kamo ba...,"" ta yi ta sake numfasawa tana kwantar da kanta a ƙirjinsa, duk da ta girme shi amma ya fita girma tsayi jiki da wani irin faɗi, da yawan lokaci ta kan ce ita ai ta haƙura shine babba, bayan haifuwar Muneeberh Ammo ta haifi Mutallab, wanda kuma shine last born ɗinta kuma ɗa namiji ɗaya tilo da take da shi, akwai soyayya mai girma tsakanin Muneeberh da Mutallab soyayyar da ko Ammo ba zata ce ga adadin da take da shi ba, ko ciwonta ne ya tashi shine yake jinyarta ta yi ta masa kuka, komai ya samu Munee, babu wanda ke gane bashi da lafiya sai ita yana da son jiki idan bashi da lafiya, kuma baya uhm'uhm, kawai dai ya jisa a jikin mutum baya magana mai tsayi da zarar ya yi sai ya saka shirme a ciki," shi yasa ake cewa kakansa yayo. """Tayo; yunwa babu daɗi talauci masifa ne talaka yana cikin jarrabawa, ina jin zafi a nan ɗina"" ta nuna" "masa ƙirjinta da cikinta sai ta yi murmushi ta ce ""Duk tsanani ka nemi abin yi karka bari ka wulaƙanta ka ji Tayo? Za ka yi farinciki duk da akwai ƙalubale gare ka, ko sau ɗaya bayan bana raye ƙasa ta rufe mini idanuna idan kana da rabo na tsayin rayuwa ka hayayyfa kar ka manta da wannan soyayyar dake tsakaninmu, ka daure ka sawa jinka sunana ka cigaba da tuna ƴar'uwarka mai son ka"" sai ta yi murmushi" "ta ɗan harare shi da ƙyar a cikin daren ya riƙe kan shi ya ce ""Bari na samo miki abinci """ """Daka bar shi, daren zai yi maka tsayi Tayo"" har lokacin murmushi take masa, ta san baya son tuna Tayo" "faɗa ake dashi sai taga bai ce mata komai ba. Yana ƙoƙarin sakin ta ta ce ""Ina zaka?""" """Quiet; ki bar idanunki buɗe""" """Ai kowa ba zaka dawo ka saman ba, bacci zan yi mai nauyin gaske na samu sa'ida daga yunwar da nake" "ji har abada""" """Me?"" Ta sake murmushi ta ce ""Wasa nake, idan baka so na yi bacci yau ɗaya ka yi murmushi naga" "yadda murmushi kewa jinin yarabawa kyau, ka ɗan rungume ni ina jin daɗi idan ka riƙe ni""" "Mutallab, ya juyawa su Ammo da Sa'adah baya ita dai Ammo shiru ta yi. Ya kalli Muneeberh dake kallon" "shi a hankali ya ɗage mata girarsa duka biyun, sannu a hankali fuskarsa ke faɗaɗa da wani irin yalwataccen murmushi, sai taga kamar an sauya shi bata taɓa zaton kyan shi ya kai haka ba sai yanzu." """Sai ka rungume ni kuma, ai haka na ce shi ne zan ta jin bugawar ƙirjinka da zuciyarka a tattare dani ko?""" "Ya sake ɗage mata girar har sannan bai magana ba, a hankali ya sata jikinsa ya rungume ta tsam, sai ya dinga jin wani abu mai kama da fargaba na rutsa zuciyarsa, su jima kafin ya sake ta sai ta ce." """Scorpion, da ita ka yi kama na ji a gidan da nake aiki suna kwatance da dafin jikinta da ƙarin dake jikin" "ka dace da Scorpion ka yi ta zama a haka""" """Kar ki baccin""" "Ta jinjina masa kai, ya miƙe tsaye Ammo ta ce ""Ta daren nan ina zaka? Mu bar wa Ubangiji komai mu jira" "zuwa safiya""" """A'a, zan je saboda ita""" """Ka duba lokaci dai, daren ya riga ya nisa ba inda zaka samu abinci yanzu"" bai sake cewa komai ya fice" "daga cikin gidan, Muneeberh ta bisa da kallo tana sake ƙanƙame cikinta dake karta mata." "Mutallab, ya sauke wata ɓoyayyiyar ajiyar zuciya yana sake kallon gawar Muneeberh kafin ya ce ""Ba tace" ba za ta yi bacci ba? Ta koyi ƙarya? Ni ni ko? Ni zata yi wa ƙarya to maza tashe ta Ammo tashe ta ci "abinci""" "Ya yi maganar yana ƙoƙarin ɗaga gawar Muneeberh, daidai lokacin Aby ya shigo ɗakin hankali tashe" yana nuna Mutallab da yatsa ya ce """Ashe ɓarawo na haifa? Mai haura gidan mutane cikin dare sauran ka riƙe mukami kana tare hanya daka" "fita cikin daren nan ashe sata ka fita yi? Allah wadaran naka ya lalace, Allah wadaran hali irin naka Muɗallabi Allah ya yi ɗaiɗai da hali mai kwatankwacin naka, to ban haifa ɗan iska a gida ba, ba zan lamunci haka ba ga ƴan'sanda can tarago guda a waje sun zo kama ka"" zumbur Ammo ta miƙe tsaye ita da Sa'adah ga gawar Muneeberh a ƙasa kwance. Mutallab jin an ambaci ƴan'sanda ya saka ya ji tsoro da shakka, ji yake wanda ya yi kisan kai ake kamawa? Me ya yi to? Biredi ɗaya ya ɗakko gidan Alhaji Wada da garin kwaki, wacce ya sato dominta yana zuwa ya ruski gawarta ta mutu saboda tsananin yunwa, bayan kafin ya je ya yi satar sai da ta fara neman taimako aka hana shi. A hankali ya sulale ya koma" "bayan Ammo, baya son akama shi baya son jin kalmar ƴan'sanda." """Muhammad da gaske ka haura gidan Alhaji Wada ka yi masa sata?"" A hankali ya jinjina mata kai tunda" bai iya ƙarya ba ya ce """E, na haura""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Me ka sato? Me ka ɗakko masa har ya zo unguwar nan cike da" "ƴan'sanda, Mutallab tarbiyyar da na yi maka kenan?""" """Ki yafe mini Ammo, ban sakewa, biredi guda ɗaya na ɗakko da garin kwaki zan kawowa Muneeberh" "dake jin yunwa. ,"" wani irin marin ɓarin makauniyya Ammo ta sauke masa a fuska dama da hagu, ƙarfin" "marin ya saka ya yi baya kamar zai faɗi sai ya ja ya cake a wajan, ya kafe Ammo da jirkitattun idanunsa" "tunani yake bai ya yi mai zafi haka? Bafa kuɗi ya ɗauka ba, inda ya ɗauki abinci suna da wadatar shi." "Wani irin huci yake fitarwa ta hancinsa ƴan'sandan suka shigo ganin haka ya saka Mutallab girgiza kai ya riƙe Ammo, yarabancin da bata san ya iya ba shi ta ji ya fara yi, hakan ya ƙuntata zuciyarta domin duk abin da ya danganci yaruba ta tsane shi, sai ta dinga jin kamar ma shine ya kashe Muneeberh saboda" sakacinsa. """Ba zan sake ba, kar ki bashi su tafi dani, ga biredin can da garin, idan Munee ta tashi zan nemo mata" "wani abun, dukana za su yi""" "Tausayin Mutallab ya cika zuciyar Ammo, ta kalli ɗan'sandan ta ce ""Yallaɓai shi yaro ne mai ƙulafucin" "yan'uwa, ku yi haƙuri ga abin da ya ɗakko nan wacce ya yi dominta ba gawarta ya tarar"" Cikin faɗa Malam ya ce ""Wallahi sai sun tafi dashi gwara su koya masa hankali su saka ya yi ladab, ban haifi wanda zai saka mini hawan jini ba"" kamar Ammo ta yi hauka ta rasa yadda za ta yi, Mutallab ya riƙe ta gam sai girgiza kai yake, idan ya kalli bindigun hannun jami'an tsaron sai ya firgita. Kokawa suka fara da malam Mutallab ya riƙe jikin Ammo cikin zafin rai Malam ya fisgo Mutallab ya hankaɗa shi gefe bisa tsautsayi kan shi ya daki jikin kujerar ƙarfe dake ɗakin, ajjiyar zuciya kawai Mutallab ya saki saboda shigewar da ƙarfen ya yi a gefen kan shi jini ya fara zuba, bai san inda kan shi yake ba ya dinga miƙawa Malam da Ammo hannu amma haka ƴan'sandan suka ɗauke shi kamar babban mutum sukai waje da shi zuwa cikin motar, sai a lokacin kuma Malam ya ji hankalinsa tashi ganin jinin da yake zuba gashi sun ɗauke shi" tamkar bashi da rai. "Ammo ta rasa bakin sai Sa'adah ce kawai take yi, tun a daren akaiwa Muneeberh wanka domin ƙarfe" "bakwai na safe za'a yi mata jana'iza. 6:30 Bafullatana ta shigo gidan a gigice sai ihu da kururuwa take tana buga ƙasa, da ƙyar aka jata ciki saboda masu ɗaukan gawar Muneeberh sun ƙarasu, Ammo na ji na gani aka ɗauki yarinyar da yunwa ta yi sanadin tafiyar ta zuwa lahira, shikenan ta rasa ƴarta? Sanadin" yunwa da talauci innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. "**Safiyyerh na zaune cikin class tana attending subject ɗin da ake yi musu, kallon teacher ɗin kawai take" "da idanunta sai ka ɗauka ji take amma idan aka ɗauki ƙwayar idanunta dake saman board ba zata taɓa iya maimaita abin da malamin ke cewa ba na daga explanation ɗin da yake, kawai dai tana kallon shi ne har ya yi ya kammala ya fita. Ta sunkuyar da kanta ƙasa har bata san sanda aka shigo tare da zama kusa" da ita ba. """Safiyyerh"" ya kira sunan underneath his berth yana kallon ta, ta ɗan ɗago kai ganinsa ya bata mamaki ta" "ɗan buɗe idanunta sosai ya yi mata murmushi ya ce ""Sleepy baby, are you alone?""" """E, how are you?""" """Good, kin san dai me zan tambaye ki ai ko? Kin sani oya bani amsa ta righ now""" """To; she is not around"" ya buɗe ido ya ce ""koyaushe dai the same answer, shikenan ai"" ta yi masa" "murmushi kawai ta ɗauke kan ta ya dubi agogon hannunsa mai tsada ya ce ""Safiyyerh me ya sa kike son keɓance kan ki daga cikin students ne? Ki yi ta zama cikin class it doesn't bother you?""" """It wasn't "" tace tana rufe ido ya jinjina kai ya matsa ya ce ""You looks so beautiful when you are smile," "please keep smiling beb"" ta tura masa baki ta ce ""Ni ka daina ce mini baby kamar ƴar tsana, kana naku ajin kana zuwa nan maza a kama ka"" ya buɗe hannunsa ya watsa ya ce ""And so what? Kuɗi fa babana ya biya ai baza su ƙaunaci asarar Student ko ɗaya ba, private school ba government ba, balle a ƙuntata mu so we have a right a freedom a power mu yi duk abin da muke so"" safiyyerh dai bata ce komai ba, ta yi" ƙasa da kan ta shima gefe ya juyar da kan shi ya zubawa wani waje ido ya ce. """Ya Allah, i really really love her, I love Safiyyerh, I love her smile, her mouth, her eyes, her innocent face" "i love everything about her About Safiyyerh. Ya rabbi help me ka bani Safiyyerh matsayin matata"" sai" "kuma ya juyo ya kalle ta, ta yi saurin sunkuyar da kan ta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta, hannunsa ya miƙa zai kamo nata ta yi saurin janye wa tana tura masa baki. ""My Sophia, kina jin ba zan iya auren ki bane? Ba kiga kowa a school ɗin nan yana da budurwa ba""" """Uhm'uhm ni ban so, Ummeyh ta ce sai mutum ya girma ake masa aure, I'm just 14 years fa?"" "". so?""" "Ya tambaye ta yana sake kallon yatsun hannunta ""Ki yi accepting nawa as a lover, as your love kiga yadda ake abu, sai na tabbatar na goge kunyar idanunki""" "Ta yi sauri ta miƙe tsaye saboda time ɗin tashi ya yi ma, daddy take jira ta ɗauki school bag ɗinta, da" "lunchbox tana ƙoƙarin fita ya saka hannu ya yi saurin janyo baby hijab ɗin ta, trying to hug her kafin ya rungume ta, jikinta har rawa yake wajan ɗaga yatsa ta nuna shi ta ce ""Karka fara Captain kar ka soma" "Please.""" """But... i love you""" """And this is your problem not mine, don Allah ka rabu dani"" ta sake yunƙurin juyawa ya yi saurin riƙo" "hannunta ya jingina ta jikin bango tare da ɗora kan shi a kafaɗarta ya ce ""Ke wai ba kiga kowa sabgar gabansa yake a wannan makarantar ba? No one's care soyayya fa akwai daɗi Safiyyerh"" ta ɗan buɗe ido tana ture shi, by forcing him to raise his head from her shoulder amma ta kasa cikin yanayin Teacher" Basam ya shigo da ƙarfi ya ce """Safiyyerh. !!"" Cikin sauri captain ya sake ta, jikin Safiyyerh na wani irin rawa tuni hawaye ya cika" "idanunta kan ta a ƙasa Teacher Basam ya ce ""Ok ok abin da kike a makarantar kenan? Shi mahaifin naki" "ya turo ki kenan ki yi ba shakka Safiyyerh""" """Wallahi... I am... Sirr"" ta rasa kalaman magana ya daka mata tsawa sosai yana nuna mata ƙota ya ce" """dilla can get lost"" ta fice tana fashewa da wani irin kuka tana jawa Captain Allah Ya isa salon a dinga ce" mata ƴar iska. "Captain na fita abokansa suka dinga masa dariya wani ya ce ""Kai ma duk faɗin school ɗin nan ka rasa" "dawa za ka yi soyayya ka liƙewa sai kwaila? Duk jan ajin nan duk yaran da suke bibiyarka? Yarinyar daba uwar data sani she just in jss 2 amma ka bani kunya da marikar mamaki wallahi"" ya ɗaga kafaɗa ya ce ""Ba zaku gane ba, ina son Safiyyerh saboda idanunta ba buɗe ba, sauran kuma sun san mene duniya idan" "soyayya ce gwara na gina mata soyayyata a zuciyarta i love her sweetness voice , da nutsuwarta""" "Murmushi duk dukai suna duba wayoyin hannunsu, Safiyyerh na jinsu ta yi shiru ta nufi motar da take da" tabbacin ta Daddy ce a ranta tana jinjina kalmar kwailar da suke magana akai. ***SSS State Security Service "Da sauri yake tafiya yana yi yana duba abin hannunsa, jikinsa sanye da baƙaƙen kaya yana ƙarasa" "shigowa harabar wajan sauran jami'an suka miƙe suna sara masa, har ya isa cikin meeting hall ɗin nasu. Ya ja kujera ya zauna gabansa an rubuta DIG JOHAR. ya dinga kallon jami'an wajan da suka kasance jami'an SSS. A hankali ya fara musu magana cike da gargaɗi da fusata ya ce ""Watakila kun manta aikin ku da matsayin da muke ciki a yanzu da lalacewa tsaro, kuma wannan meeting ɗin na sirri ne kuma kai da kai saboda barazanar da muke samu. Idan ba ku manta ba hukumar SSS hukumar jami'an tsaro na fararen kaya, sun samu rashin jami'ansu saboda wani kuskure da suka yi a baya, har hakan ya bashi damar bawa wasu mutane bayanan sirrin SSS wanda a yau ake mana baranza da shi dole mu sauya taku" kuma mu binciku wannan jami'in namu da ya ci amanar aikinsa akan rashin toshe da ma'ana. Babu wasa duk wanda muka samu da laifin da muke nemansa da shi babu sassauci zamu yi masa hukunci daidai da "laifin daya aikata, jami'an SSS basa jiran umarni ba sa kaiwa court, idan hukunci na kisa ne mune muke da iko, idan mutum ba zai mana amfani ba mu haukatar da shi so dole salon aikin mu ya sauya," "understand?""" """Yes sir""" "Suka haɗa baki wajan amsa masa, kowa ka gani a wajan fuskarsa babu walwala da sassauci daidai suke" da aikin nasu a kuma shirye suke tsaf. Dig Johar ya fara zayyana musu bayani don gane da SSS ɗin. Bayan ya gama cike cike ya ɗaga kan shi ya kalli team ɗin ya ce fara da cewa """Kamar yadda kuka sani (SSS) A Jami'ai a matsayin Department of State Services (Dss)ne hukumomin" "tsaro na Najeriya da kuma ɗaya daga uku gaje ƙungiyoyin da National Security Organization (NSO). Hukumar tana karkashin fadar shugaban ƙasa ta Tarayyar Najeriya, kuma tana kai rahoton ayyukanta ga ofishin hukumar NSA. Babban nauyin da ya rataya a wuyanta shi ne a cikin ƙasar kuma ya haɗa da yaƙi da leken asiri, tsaro na cikin gida, yaƙi da ta'addanci, da sa ido da kuma binciken wasu nau'ikan manyan laifuka da ake yiwa jihar. Ana kuma ɗorawa musu alhakin kare manyan jami’an gwamnati, musamman shugaban kasa, mataimakin shugaban kasa, gwamnonin jahohi da shugabannin jihohi da gwamnatocin da suka kai ziyara tare da iyalansu, ya zama dole jami'an tsaron SSS su kula akan haka, kuskure guda muka yi fadar shugaban ƙasa ba zata lamunta, aikin mu na farko kula da rayuwar Minister wacce take" "daf da shiga tsari sauran bayanan za ku ji ok?"" Suka sake cewa ""Yes sir""" "Miƙewa suka yi gabaɗaya tare da fitowa, Dig Johar ya fito ya ruski wata tana da kuka har ya shige sai ya" "dawo ya dube ta ya ce ""Baiwar Allah nan ba wajan tsayawa a yi kuka bane, idan wani kika zo gani ki binciki sashin binciken da suka kama shi, ɗan ta'adda ne? Ko ɗan fashi mai garkuwa da mutane ne wanda kika zo wajan nasa?"" Ta girgiza masa kai ta ce ""A'a babu ɗaya daga cikin abin da kake faɗa, babu abin da ya aikata"" da mamaki Dig Johar ya ce ""Unbelievable; kenan me ya yi da sai a kai shi police station ai"" tana kuka ta ce ""Muma mun yi zaton haka, sunana Hameeda Abdullahi, ƙanina aka kawo nan tun jiya, mun zo an hana mu ganinsa wallahi yallaɓai babu abin da ya aikata ka yarda da na yi yaro ne" "shekarunsa goma sha huɗu kawai jiki Allah ya hure masa""" "Ya buɗe ido, ""shekaru sha huɗu, kuma kika ce babu abin da ya yi?""" """E, tsautsayi ne kawai gidan wani Alhaji Wada dake unguwarmu ya haura ya ɗakko biredi ɗaya da garin" "kwaki zai bawa ƴar'uwarsa, kuma ƙaddara ta riga fata kafin dawowa ta rasu, shine aka zo kama shi ko jana'izar yarinyar bai gani ba, hasali ma an ce biredin daya ɗakko amma sam ƴan'sandan da suka kama shi sunƙi yarda"" Dig Johar ya dinga kallon ta cike da tausayawa kafin ya ce ""Follow me, biyoni"" bayansa tafi har zuwa reception wani jami'i ya sara masa yana ƙamewa ""Jiya an kawo wasu ne?"" ""Yes sir"" ya ce" """Good, duba mini wani kaga me ya yi ammmm mene sunan?""" """Muhammad Abdullahi""" "Suna aka fara dubawa mutumin ya ce ""Yes sir, an kawo mai sunan da laifin shiga fashi har aka kama shi" "da bindiga ƙirar IMI Tavor"" wata zabura Dig Johar ya yi cikin ɗaga murya ya ce ""What bindiga mai girar IMI Tavor? Kasan me hakan yake nufi? Tun daga shekarun baya, daidaitattun bindigogin harin da SSS combat operatives/security protection officers (SPO) ke amfani da su sune IMI Tavor Tar-21 da masana'antun sojoji na Isra'ila suka samar da makamin kariya, shine yanzu zaka ce an samu bindigar a hannunsa? How comes? Ke ba cewa kika ƙaramin yaro bane?"" Jikin Anty Hameeda na rawa ta ce ""Wallahi tallahi Yallaɓai ƙaramin yaro ne ko wuƙa bai taɓa ɗauka ba, tausayi ne da talaucin da muke" "fama da shi don Allah ku yi haƙuri""" """Ba maganar haƙuri bace hajiyata, uhm a statement akwai number wanda ya saka a kama yaron?""" """Akwai sir "" ya ce" """call the number"" da ƙyar aka bar Anty Hameeda ta leƙa ta window ta hango Mutallab, ta ganshi" durƙushe jikinsa babu riga sai wando ko motsi ba ya yi an yi masa jahilin duka ko'ina shatin bulala ne a jikinsa. Kiran duniya da ta yi masa bai amsata ba ya yi shiru idanunsa rufe tana kuka ta bar wajan hankali tashe. Mutallab na zaune idanunsa na hango masa Muneeberh ya ji wasu daga gefe suna maganar fashi da makami wasu garkuwa da mutane wasu batun shugabanni ƴan siyasa. Gabaɗaya bai ci ace kunnuwansa na jiye masa maganganu irin wannan ba ya kalli wani da hannunsa yake riƙe da wata ƙaramar askira a "hankali ya ce ""Ka iya zane?""" """Ya akai?""" """Yi mini za ka yi""" """Me za a zana maka?""" "Ya rufe idanunsa ya buɗe a hankali ya ce ""Scorpion"" ko gezau Mutallab bai yi ba, waje biyu aka zana" "masa Scorpion da ƙirjinsa da bayansa tsananin azaba ya saka jikinsa ya dinga tsuma da rawa da wani irin ɓari da kakkarwa jini na ɗiga ta jikinsa. Ana haka wasu ƙarti sukayo kan shi ya kasa miƙewa kafin ya yunƙura suka afa masa wata ƙwaya a baki suna danne shi ya dinga ihu da kururuwa cikin sauri masu kula da wajan suka shigo daga cikin hadda Dig Johar ya saka aka ɗauke Mutallab zuwa wani ɗakin ya kalle shi ya kalli sauran mutanen can ya ce ""Ku bamu waje"" basu san me suka tattauna ba washegari da safe sai ga Anty Hameeda da Bafullatana suna tsaye aka fito da Mutallab suka riƙe shi daidai kuma Alhaji Abdu" ya shigo wajan abokinsa Sp ya dinga kallon Mutallab. Kwana biyu da dawowarsa wanda ya yi daidai da sadaƙar ukun Muneeberh yana zaune a waje ya saka "riga ya rufe jikinsa dake masa raɗaɗi babu wanda ya fahimci me zanen yake nufi ya ɗan yi shiru yana tunani, wani alamjiri ya ji yana karatu ya juya ya kalli almajirin sai kawai ya girgiza kan shi. Tunawa da wani abu ya saka ya miƙe ya fara tafiya a ƙafa ya shiga cikin duhuwa sosai har gab da magariba Mutallab bai dawo ba hankalin Ammo ya tashi, sai wajan takwas na dare ya shigo hannunsa riƙe da tarkace ya" shige ɗakin zaure ya rufo har gari ya waye idanunsa biyu babu wanda ya san inda ya shiga. "Washegari da safe ya shigo, Ammo ta dinga kallonsa saboda kayan dake jikinsa, rigar binjima ce da hular" "saƙi, sai guru da laya a jikinsa da ya saka a damtsen hannunsa, sai kambu zubin kayan mafarauta. Ta dinga kallonsa kamar an sauya mata ɗa da ƙyar ta ce ""Wannan shigar fa?"" Ya nemi waje ya zauna ya ce ""Ina kwana Ammo?"" Ta ce ""Allahamdulilah,ya daɗin haƙurin ƴar'uwarka? Muhammad don Allah ka cire komai a ranka ka dinga yi mata addu'a naga tunda ka dawo ba ka yi magana akan ta ba, baka ce komai ciwon da kaji a gida ma kaƙi yadda kaje a duba maka, haka tsoron wani ciwon ya shiga ciki? Ni gabaɗaya ɗabi'unka daga dawowa zuwa yau duk sun fara sauyawa mini"" bai ce komai ba ya ja kwanon taliyar data dafa, ƴar murji da ake siyarwar a moƙota ta dafa da manja da ya ji. Ya cire cokalin ciki ya saka yatsun" hannunsa ta ce. """Naga damuna ce zata zo, zan je sharaɗa su dinga bani sarin abin makamashi ayafa ake ce masa, na" "dinga siyarwa ina samun kuɗi idan ya ƙare sai na kai musu na amso wani, akwai wata mata dake bayar da bashin fulawa zan fito da injin taliya na fara yi ina ƙulawa ɗari, ɗari biyu murjajjiya"" shi dai taliyar kawai yake ci, yana gamawa ya ɗauki ruwa ya sha ya yi gyatsa ta ce ""Allahamdulilah, wannan shigar fa?""" """Ba komai, Allah Ya taimaka"" ya ce yana kwanciya kan katifa ya yi rufda ciki ƙafarsa sanye cikin takalmi" "yana ji yana cewa ba kyau rufda ciki ya yi mata shiru, ta kuma tambaye shi Alhaji Wada yafe masa ya yi ne da aka sake shi nan ma ya yi mata shiru. Yana ta kwance Muneeberh na yi masa gizau a idanunsa sai kawai ya miƙe ya fice koda ya fito tsakar gidan Mama Zaituna ta ce ""A'a kaga na jami'an tsaro bada kan ka a sare, kace sata ta yi rana gaba gaba kuma sai abin da Allah ya yi"" Malam ya ce ""kuma ka tabbatar ka" "zauna a makaranta, ɓarawo kawai""" "Inda suka saba haɗuwa suka haɗu da Kimiyya ya yi masa ta'aziyya ya ce ""Friend Jeddah ta ce ka je ku" "gaisa"" Mutallab ya ɗan juya bai magana ba hakan ya saka Kimiyya cewa ""My mother, babata ba kana son shiga makaranta ba, to maybe your wishe is come true, ta shi muje"" kamar yaƙi zuwa sai kuma ya miƙe ya bi bayan Kimiyya""" "***Suna saman dinning na suna dinner, kamar an cillota cikin gidan haka ta faɗo, Ummeyh ta yi saurin" "miƙewa tsaye gabanta na faɗuwa dai addu'a take ta kalli Daddy ta ce ""Sannu Abdu, hankalinka ma a kwance yake ko wato duk maganar da na yi maka jiya a banza ta tafi?"" Ya yi mata shiru, domin ya gama sanin dalilin faɗan nata kuma bata buƙatar maganarsa a yanzu ya dinga kumfar baki ta yi ta gama ta" ɗora da faɗin. """Wannan shine zuwana na biyun ƙarshe, ka bari na yi na ƙarshe kaga abin da zai faru"" ta watsawa" Ummeyh wani mummunan kallo kana ta fice. Safiyyerh dai hannunta riƙe da spoin tana ɗan jujjuya Indomien dake gabanta don ƙin cin komai ta yi. Daddy ya yi murmushi ya ce """Safiyyerh lafiya?""" """Good,dad"" ya ce ""To, ma sha Allah. Guess what?""" """I have no idea, ka faɗa mini kawai"" ya zaro sabuwar waya daga cikin kwali ya ce ""For you Safiyyerh," "daman ai na yi miki alƙawari ko? Gashi ki dinga browsing assignments tun da kin ce system ɗin bakya so""" "ta amshi wayar tana jujjuyawa ta ce ""Daddy but is too big for me, ko Ummeyh ko na isa riƙe waya ne?""" """Yes Safiyyerh, kin isa riƙe waya mana har ma kin shige, kina assignment kina games da sauran wasu" "abubuwan kina gaisawa da friends naki"" Safiyyerh ta girgiza kai sai kuma ta kalli Kikuyu ta kalli daddy ta ce ""Kenan na isa aure tunda aka bani waya?""" """No; aure da saura Safiyyerh ke ƴar boko ce, ki zama wayayyiya karatu shine yanzu ki zama babbar mace" "ko auren kikai kina jan hankalin mijinki da tsarin da Ubangiji ya yi miki, my dear aure akwai daɗi komai kike so Mijin ya yi miki,bakwai caring tsakanin husband and wife"" ta ƙure mahaifinta da idanu, yana magana tana lumshe fararen idanunta ta suka fara sauyawa can ta miƙe da wayar a hannunta ta nufi kujera ta zauna, ta ja filo ta rungume a ƙirjinta. Kowanne a adolescencet stage ɗinsa yana nuna abin da ya fi su, sai dai iyaye suƙi nutsuwa su fahimta, ko a kalaman yaro wajan furuci yana yawan ambaton abin da zuciyarsa ke so. Ta sake rungume filon a ƙirjinta tana kallo daddy ya sakko daga wajan cin abincin haka Ummeyh. Ummeyh ta ce ""Daughter goodnight, ki kashe kallon idan kin gama ki yi bacci da wuri kin ji?"" Ta jinjina musu kai ta kasa cewa ma goodnight ga iyayen nata. Channel ta sauya zuwa zee world suna haska wani series indan film, wajan da aka hasko ya yi matuƙar jan hankalinta taga exactly irin abin da su" Ummeyh suke yi kenan. Ta duba title na film ɗin taga an saka “Married again” """I love this, I love it, how can i get it?"" Wata zuciyar ta ce ""Safiyyerh za ki samu ne, when you have a" "boyfriend, idan kina da saurayi za ki samu Safiyyerh""" """A boyfriend?"" Ta faɗa a fili sai kuma ta jinjina kai, ai kishiyar saurayi miji ne, man, woman, boy, girl," "single, marriage, boyfriend, husband. Miƙewa ta yi bayan an gama episode ɗin, ta kashe ta haura upstarts ta nufi bedroom ɗin Ummeyh ta nufi wajan mirror ta ga duk tarkacan kayan data siya wajan S Bayero suna nan. Ta ɗauki wata zuma da aka saka ya breast ce, ta tuna kwailar da aka ce mata, ta kafa baki ta sha zumbar son ranta, ta ajjiye ta ɗauki wasu sauran tarkacan ta dinga sha tana gamawa ta koma nata bedroom ɗin. Bacci ya gagari idanun Safiyyerh data rufe idanunta sai ta hango bakin daddy yana" "sumbatar Ummeyh sosai moment ɗin ya zauna daram a ranta, ta ajjiye books ɗinta a gefe kawai." "Cikin dare ta farka da ciwon ciki, ya dinga buga ƙofar daddy wacce ta tabbatar Ummeyh na ciki, anjima" "kafin a buɗe mata Ummeyh ta kalleta ta ce ""Daughter ya aka yi?"" ""Ummeyh cikina ke ciwo"" Daddy yana" "daga ciki a ƙwance ya ce ""Dr ki duba ta?""" """Bani da kayan aiki a gida yanzu Prof, mu bari zuwa safiya"" ta kama hannun Safiyyerh suka shigo ɗakin" "aka rufe, ta kwantar da ita saman kujera tana ta yi mata sannu kanta a kan cinyar Ummeyh har bacci ya ɗauke ta. Still cikin daren sautin da ake yi ne ya sake farkar da Safiyyerh daga bacci, sautin da take jiyo shi kullum daga waje yau gata a ɗakin da ake yi, ta ji tana son ganin abin da yake wannan sambatun dake akwai ɗan blue ɗin haske a ɗakin ana iya ganin abu ta juyar da kanta a hankali zuwa direction ɗin da" sexual sounds ɗin ke fitowa.... "[1/7, 9:34 PM] Sis Fauzy: Chapter 23: Diyna's death" Paid book ₦500 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S evidence of payment send via WhatsApp number 08164069385 "Need more updates, chapters? Follow on Arewabooks" "Saurin ɗauke kan ta Safiyyerh ta yi, tana runtse idanunta ƙirjinta na bugawa saboda abin da idanunta" "suka so gani, cikin nutsuwa ta sakko daga kujerar a hankali kuma ta nufi wajan ƙofa ta zare key ta buɗe ta fita ba tare da sun sani ba. Fitar ta da sautin rufe ƙofar ya saka daddy dawowa cikin nutsuwarsa ya miƙe zaune bayan ya koma gefe, ya juya ya kalli Ummeyh ya sake kallon kujerar da bacci ya ɗauke Safiyyerh akai, ya dubi ƙofar daya gama tabbatarwa yanzu aka buɗe tare da fita daga ɗakin." """Subuhanallahi, kin manta cewa daughter na ɗakin nan nawa ne Madam?"" Ummeyh ta ja bargo ta miƙe" "zaune itama tana kallon ƙofar ta ce. ""A'a ban manta ba wani abun ne sir?""" """Har ma kike tambaya? Me muka aikata yanzu? Kin san cewa Safiyyerh na ɗakin nan kika hilace ni?" "Innalillahi me ya sa haka Madam?"". ""Ka kwantar da hankali mana dare ne kar aji muryarka ta ɗauka ka ji""" """Na kwantar da hankali fa kika ce? Me ya sa kike abu kamar dai bakya ganewa, shin ya dace Safiyyerh ta" "ji ko ganin halin da muke ciki? Wallahi har raina na manta tana ciki ɗakin nan, wayewar da na yi ai ba kai na bari taga wannan ɗanyen aikin ba, ƙarar rufe ƙofa ne fa ya dawo ni cikin nutsuwata wane ya san tun yaushe take idanu biyu? Wane ya san irin kallon data gama yi mana kafin ta fita? Wane ya san irin" "maganganun da kunnenta ya jiye mata? Ni ko ke? Wake da tabbacin hakan Madam?""" "Ummeyh ta kwantar da murya ta ce ""Ka haƙurƙurtawa ranka don Allah yallaɓai, Safiyyerh yarinya ce" "guda nawa take? Kamar yanzu ne muka haifeta haka nake ganinta cikin idanuna, ko ka manta ko shekaru goma sha biyar ba ta yi ba? Ita kawai ka bar ta da yin karatunta, ta fi gane karatu fiye da komai kalmar “Love” ma Safiyyerh bata sani ba, balle ga batun auratayya ko ganin mu ta yi ba zata fahimci me muke ba, kar ka damu ka ji"" daddy ya ja numfashi ya sauke har yanzu bai ji ya gamsu ba, ya ji tsoro sosai." Murmushi Ummeyh ta yi tana sauka daga saman gadon ta ce """Ka dai na yi wa Safiyyerh kallon babba, wallahi ƙuruciya ke damun ta ko baka ji tana tambayarka ta isa" "riƙe waya bane? Ni fa da kake gani zan iya ɗaukan Safiyyerh na sata a tsakiyar gadon nan, gani ga ka gata ba wani abu bane""" """Ok"" daddy ya ce yana juya mata baya, sai kuma ya miƙe ya shige toilet ransa duk a ɓace. Ummeyh fita" "ta yi kai tsaye bedroom ɗin Safiyyerh ta nufa, ta buɗe a hankali ganinta ta yi kwance a saman gado ta ja filo ɗaya ta rungume a ƙirjinta ta ƙanƙame sosai, ga wani filon tsakanin cinyoyinta data cusa ta harɗe ƙafa. Ummeyh ta ja mata ƙofar ganin bacci take yi. Tana fita Safiyyerh ta buɗe idanu tare da mirginawa ta zubawa ƙofar idanu, a hankali wasu hawaye masu zafi suka fara biyo gefen idanunta, wani irin abu take ji a cikin zuciyarta kuma yake mata yawo a saman fatarta, duk abin da ta ƙissima a ranta idan ba daddy ta hasaso ba, bata jin abin yana yi mata daɗi. Ta kifa kanta jikin filo ta fashe da wani irin" "matsanancin kuka, data san me take ji wataƙila da ta ji sauƙi a ranta da gangar jikinta." "Jikinta na kakkarwa ta sulale ta sakko ƙasan gado, ta durƙushe wani irin kuka take mara sauti data rufe" "idanunta sai ta hango abin da su daddynta suke yi da Ummeyhta, sun manta tana ɗakin; ta ji kawai burinta ta jita a jikin daddy, itama ya yi kissing ɗin ta, ya sumbace ta kamar yadda ya ke yi wa Ummeyh. Idan har abin da suke yi shine aure, to ita aure take so, kuma ba wanda take son aura sai daddynta shine ya iya irin abin da take gani a cikin idanunta, za ta tambayi daddy yaushe zai aure ta kawai idan ya yi wa" Ummeyh itama ya yi mata abin. "Da ƙyar bacci ya ɗauke ta a ƙasan carpet ɗin, har bata san asuba ta yi gari ya fara haske ba sai ji ta yi ana" "kiran sunanta ta buɗe idanunta da ƙyar ta zuba akan fuskar daddy, ta ja idanun ta lumshe. Daddy ya kalli yadda idanunta sukai jawur ya ce ""Ke lafiya kike? Me ya samu Idanunki haka?"" Ta lumshe idanunta, ta sake buɗe su akan daddy ta yi shiru bayan ta ƙurawa laɓɓansa idanu. ""Kin yi sallah?""" "Ta girgiza masa kai, ya ce ""Kuma kike zaune har yanzu Safiyyerh? Ga lokacin makaranta Ummeyhnki har" "ta tafi asibiti dutyn safe gare ta""" """Yanzu zan yi""" "Ta ce a hankali sai kuma ta miƙe ta nufi toilet ba tare data sake kallon daddy ba, wani irin rawa zuciyarta" "ke yi mata a duk sanda ta kalle shi, abubuwan da suke mata yawo a rai da zuciya daban suke kuma tana" jin daidai ne. Bayan ta yi wanka tare da alwala taƙi fitowa daga toilet ɗin. Jin shiru ya sa ya buɗe ƙofar "toilet ɗin ta leƙo da kai a hankali, a zaune taga daddy gefen gado yana dudduba littafan makarantarta, ta" buɗe idanu sai kuma ta yi saurin komawa cikin toilet ɗin. "Jin shiru ya saka ya fara kiranta cikin faɗa ""Safiyyerh... Safiyyerh""" """Daddy"" ta ce bayan ta fito ta saka hijabin dake banɗakin, ya kalleta ya kalli littafin hannunta ya ce" """Mene wannan?"" Ta fara ƙifta ƴan idanunta, ya daka mata tsawa ya ce ""Ina magana mene wannan nake" "gani kamar jan biro a notebook ɗin ki haka?""" """Daddy, I did.... ban ci assignment ɗin ba, shine. ,"" ya sake daka mata tsawa ya cilla mata littafin yana" "nuna mata ya ce ""Har kike da ƙarfin quiwwar kallan cikin idanuna ki ce mini wai ba kici assignment ba?" "Daga class work har assignment duka zero, gabaɗaya cancelled me kike tunani? Karatun ne bakya ganewa ko kuma mene?""" "Kuka ta fashe da shi, ta kasa magana ita bata san meke damunta ba bata gane karatun gabaɗaya yanzu," "ko me aka yi bata fahimta ta dinga kuka kamar ranta zai fita da ƙyar ta iya cewa ""Ka yi haƙuri daddy ba" "zan sake ba, don Allah ,"" sai kuma ta yi shiru ta zubawa jajayen laɓɓansa idanu da yake juya su yana surfa mata faɗa, ta ja idanu ta rufe tana ƙanƙame jikinta waje guda har ya yi faɗan ya gama bata sake fahimtar abin da yake cewa ba. Ta ja jikinta zuwa gefen gado bayan ta ɗauki littafinta, kwana biyu bata" cin komai a assignment a cikin goma ta ci ɗaya ko zero ta dinga buɗe littafin tana share hawaye. "***Mutallab na zaune ya harɗe ƙafafuwansa waje guda, a nutse yake yin zanen wani haɗaɗɗan gida a" "wata farar takadda, zubin gidan ya yi sosai har yake ganin kamar ma ya fi gidansu Kimiyya kyau. Ammo ta kalle shi ta ce ""Ina amfanin wannan zanen da kake yi tun ɗazo? Kana ji yana nanata idan baka je" "ɗaukan karatu ba yadda zai yi maka""" """Muhammad ina magana kana ji wai wanne ɗabi'u ka sauya marasa amfani haka? Ka fi so dai a yi ta" "maka magana ɗaya? Ka yi kunnen uwar sheƙu da mutane?""" """Gidan ya yi ko?""" "Ya ce, yana miƙa mata zanen gidan ta amsa kai tsaye ta yaga zanen gida biyu, ya yi sauri ya runtse" "idanunsa yana jin kamar zuciyarsa ta yaga, ya zuba mata hargitsastsun idanunsa cikin faɗa ta fara cewa ""Ba zan lamunci wannan yanayin ba, ba zan ɗauki rashin albarka da darajar da kake ba, na kasa gane ina ka dosa me kake nufi tunda ka dawo daga wajan waɗancan mutanen na rasa gane kan ka, ka wata shiga daka tsiri yi kamar jikin mafarauci "" miƙewa kawai ya yi ba tare ya ce mata uffan ba ya nufi waje. Cikin" "rashin sani ta ji bakinta ya furta ""Mara amfani, kamar ba jinjina ba""" "Bata kula da shi ba, sai gani ta yi ya dawo ya tsaya ƙerere a kanta ya yi kicin-kicin da fuska ya saka hannu" ya doka jikin ƙofar ya ce """To kawai ku nemo mini iyayena, a nemo mini wanda suka haife ni"" ya faɗa yana wani irin huci tare da" "zazzaro idanunsa waje jikinsa ya ɗauki mazari. Ta ce ""Ni kake cewa na nemo maka iyayenka?""" """To ni na ce ku yi cikina ku haifan ne? Na ce a samu cikin Mutallab ne? Ko kun yi shawara dani sanda za" "ku haifan ne eh, idan ba zaku taya ni riƙe ƙaddararta ba, sai ku tattara ni a mayar dani cikin, ko a kai ni wajan wanda kuke tunanin sune iyayena, a daina ƙuntata ni haka nan""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"" shine abin da Ammo ta samu zarafin ta saki baki tana kallonsa ya girgiza" "kai yana runtse idanunsa cikin huci da zafin zuciya ya ce ""A'a kar mu fara haka dake Ammo, ki dai na yin salati kina y kamar ba ki gane ba, sai ki faɗawa Malam Abdullahi ya nemo mini uba, kafin na lalace na ja muku aiki"" Yana kaiwa nan ya fice daga cikin gidan kamar walƙiya, zuciyarsa a cunkushe. Sa'adah ta girgiza kai ta ce ""Ammo Ku daina irin haka fa, za ku sa ya dinga jin kamar ba kune kuka haife shi ba wallahi, da kika fahimci sauyi a tare dashi ai jan shi za ki yi a jiki ki tambaye shi ko lafiya, amma ki dubi" "me kika ce fisabilillahi namiji ɗa ku kasa riƙe shi, rayuwarsa daga wannan sai wannan?""" """Sa'adah me na yi? Me na ce daga cewa mara amfani shi ɗin yana abu kamar ba jinina ba?""" """To ai bai kamata ki ce masa haka ba, ta ya zai zama mara amfani a gare ki, kin fi kowa sanin ke kika" "haife shi me ya sa za ki ce kamar ba jininka ba, maganganunku za su dinga tasiri ne a zuciyarsa suna yaɗo ku saka masa maragurbin tunani cikin zuciyarsa, ko ni aka faɗawa zan ji babu daɗi na dinga ganin kamar ba kune kuka haifan ba. Ammo Mutallab shine zai fita nemo abincin da za a ci a gidan nan maimakon" "Malam, ya yi wankin kayan Malam ya goge ki duba gidan nan raya daga ƙashi sai fata babu mamaki zuwa" "gaba kiji yana cewa zai ƙara aure. Allah ke riƙe da tarbiyyar yaran gidan nan kawai, ki duba fa kamata mace ba aiki ba, ba komai ba idan gari ya waye sai Malam yace mini wai na je na nemi kuɗi, to iskanci zan yi ko me? Jikina zan rabawa maza suna bani kuɗi ina siyan abinci ina ci?"" Tana shassheƙar kuka sosai" ta ce """Wallahi ko mutuwar Munee Allah sanadi sakacin Malam sanadi, tun da ya tara zuri'a dole ne ya fita ya" "nema, da ƙarfinsa da lafiyarsa babu ta inda Allah ya rage shi, amma ya saka ƙafa ya shure dukkan wani nauyin uba daya rayata a wuyansa, ta ya ya Mutallab zai iya kula da gidan nan? Haba don Allah wallahi kun dinga sauƙaƙawa ranku akan yaron nan, Malam na yi masa alkaba'i kema za ki fara ba ki san yadda bakin iyaye ke yin tasiri a kan yara ba? Ki zauna ki fahimci ɗanki ki gane wane kalar sauyi ya yi amma kin" "kasa ko? Ai shikenan"" Ammo ta kalli Sa'adah kana ta ce" """To banda lalacewa ta fara samun shi ya zauna yana zanen gidan da ko a mafarki ba zai tsinci kan shi a" "ciki ba? Dubi shigar da ya yi kamar ɗan mahaukaciya? Lalataccen yaro kawai, ba zai bar ni da ƙuncin da" "nake ji a cikin zuciyata ba""" """Tab, Allah mun tuba""" "Sa'adah ta ce tana miƙewa zuwa waje domin ba zata iya cigaba da zaman takaici ba, sai ta ɗauki hijab" ɗinta ta saka ta nufi gidan Anty Hameeda daman ta zo mutuwar Munee tana nan basu koma Legas ɗin ba. "Washegari da safe misalin shaɗaya Mutallab na zaune gaban Aby, cikin tarin almajirin da suke wajan" "suna ɗaukan karatu hannu kowanne ɗauke da allo, shi banda ihu da yake ji a tsakiyar kan shi baya fahimtar komai, aya ɗaya aka ruhuta masa a jikin allon amma ko wasali bai riƙe ba. Idan ya juya ya kalli" zabgegiyar bulalar dake hannun Malam sai ya durƙusar da kan shi. "Tunaninsa ya barranta ya dire allon hannun nasa ya dubi Aby tun safe yau bai furta komai ba sai yanzu," yana kame fuska ya ce """Duka ne dai ka daka Aby, ba zan iya karatun nan ba, ka dake ni ina da shiga dawa yau, zan kamo ɓauna," "bulala ɗari ce ko dubu ɗaya?"" Aby ya ce ""Ba za ka yi karatun ba ka ce?"" Ya jinjina kai tare da yin shiru," "wannan maganar da ya yi mai tsayi ma Allah ne ya nufa zai yi, ban da haka sai dai Aby yaga ya bar wajan" bayan ya dire masa allon. """Muɗallabi, karatun allon ne ba za ka yi ba?"" Aby ya koma magana cikin tausasawa." "Kai tsaye Mutallab ya ce ""E, kawai bane ganewa ne, kuma daga yau sunana MAI DAWA""" Da idanu Aby ya yi wa gardawa nuni suka kame shi nan take ya ɗaura masa mari. Kafin ya saka masa "marin anci uwar dambe da shi, ya dinga buga mutanen da ƙasa saboda ƙarfine da shi jikinsa ya ƙara buɗewa da murɗewa kamar rodi. Aby ya saka suka ɗauke shi aka sa shi a wani ɗan mitsitsiyar ɗaki dake gidan ya saka kwaɗo bayan ya rufo ƙofar. Aby ya fito yana surfa bala'i jin babu wanda ya kula shi daga Ammo har Mama Zaituna ya saka ya kalli yaran da suke tsakar gidan suna rarraba idanu ya daka musu tsawa yana zararawa ɗaya daga ciki bulala ya ce ""Yaran iska kawai ƴan banza da kunnuwa kowanne daidai dana irin uwarsa"" ya leƙa ɗakin Ammo ya kalleta sai kuma ya shiga ya nemi waje ya zauna ya ce ""Idan kina son zamana dake ya wanye lafiya kuma ya ɗore na ɗaga miki ƙafa har zuwa aljanna, ya zama dole ki zame hannunki daga kan tsinannen yaron nan Muɗallabi"" ƙullin taliyar da take yi ne ya suɓuce daga hannunta, ƙirjinta ya duka da ƙarfi wani irin zafi ya fara mamaye saman fatarta kallon da take masa ya juye daga na biyayya zuwa na tuhuma ta ce ""Malam ko baka ji furucin da ka yi bane? Kana nufin ka tsinewa na Ammo?"". ""Ba kafe ni za ki yi da idanu ba, ni ban ce na tsine masa ba; amma ina gab da yin" "hakan inda ki kaga gulando haka nake jin zuciyata akan Muɗallabi""" """To ko dai da gaske ba kai ka haife shi ba?"" Malam ya girgiza kai ya ce ""Idan kin amince kin taɓa aikata" "zina da wani to sai na ce a cikin yarana akwai wanda ba nawa ba, a yaran kuma Muɗallabi ne wanda kikai zina kika haifa, idan kuma kin san ba ki taɓa aikata komai ba a rayuwar duniya da wani ɗa namijin face ni Malam Abdullahi to sai na ce Muɗallabi jinina ne, kuma halak ɗina"" ya sake jinjina kai ya dubi Ammo da kyau ya ce ""Zunubinki ya ja aka samu yaron nan mai zubin adawa da samudawa, Zunubinki ne ya ja aka haifi wannan jinin yarabawan, ba zan fasa cewa son rai da son zuciyar da kika nuna ya haifar da duk wannan ba, to ni ban haifi ɗan da zai fi ƙarfina ba, ya saka mini hawan jini ba gaira ba dalili, wallahi tallahi ki cire hannunki daga kan shi, kar na kuma jin kin tofa uffan taki idan kuma kin ƙi yanzu ki ɗauki hanyar. ,"" da sauri Ammo ta girgiza kai ta ce ""Ya isa shikenan, Allah Ya raya shi ya tsare shi"" tana cewa" "haka ta cigaba da abin da take yi shi kuma ya tashi ya fita. Sa'adah dake zaune ta ce ""Yanzu Ammo kin amince rayuwar Mutallab ta lalace? Wacce irin rayuwa ce wata mahaifiyar na rabuwa da miji domin kula" "da yaranta ke kina sadaukar da naki wa duniya? Ba za ki haƙura da zaman gidan Malam ki koma""" """Sa'adah ya ishe ni fita"" sai kuma ta fara zubar da hawaye ta ce ""Sa'adah wacce uwa kike tunanin zata" "zuba idanu rayuwar yaranta su lalace? Na yi imani da Allah ko mahaukaciya ta san daɗin ɗa, ta kuma san wahalar data sha kafin ta same shi, mani da zaɓi Sa'adah bani da wata mafita wacce ta shige zaman" "gidan ubanku da daɗi babu, ki tayani riƙe wannan ƙaddarar bayan wancan kuma a bar maganar iya haka" "nan"" miƙewa ta yi jiki a saɓule ta nufi waje Sa'adah ta bita da idanu." "Mutallab yana cikin ɗakin zaune ya yi shiru, can ya buɗe ido saboda wani irin ciwo da kan shi ya fara yi ya" "saka hannu ya dafe wajan ciwon da ya ji, abu kamar wasa sai ya fara girgiza kan da ƙarfi yana zabura kamar zai tashi baya ganin komai balle ganewa duhu ne kawai a cikin idanunsa, ya ji kamar ana buga masa guduma a tsakiyar kan shi, wani irin ya kurma wanda ya saka Ammo zabura daidai lokacin kuma Uncle ne Mutallab mai suna Ade ya yi sallama ya shigo, da Ade da Ammo suka kasa tsere wajan nufar ɗakin da Aby ya rufe Mutallab a ciki tare da sanya masa mari. Duka ɗaya Ade ya yi wa ƙofar ta buɗe ya" "fara shiga ciki, durƙushe ya tarar da Mutallab ya daddafe kan shi jini na zuba, a hankali ya ce" """Tayo"" ya ɗago ya kafe Ade da idanunsa da sukai wani mahaukacin jaa, ya fara zazaare musu manyan" "idanunsa a firgice ya ce ""Su waye ku? Ku su waye?""" """Tayo, ni ne Ade Uncle ɗinka mai zuwa ganinka tun kana zanin goyo. Wannan kuma mahaifiyarka ce" "Ammo ka gane mu yanzu?"" Ya yi shiru bai ce komai ba, sai jikinsa da yake rawa ga jini na cigaba da zuba. Da zarar Ade ya nufo wajan Mutallab zai hau bubbuɗe masa idanu da yunƙuri kamar zai kai masa cafka, Ammo ta fashe da kuka Ade ya ce ""Akwai matsala ba, sai ka ce mai taɓin ƙwaƙwalwa? Ko dai Tayo ya haukace ne?"" Ammo ta ce ""Wallahi lafiya ƙalau yake ba mahaukaci bane, ba hauka yake ba"" Ade ya" girgiza kai """Alamun hauka nake gani a tattare da shi, Allah Ya sa kada hakan ya tabbata ki fita waje ki nemo mana" "mutane su kama mini shi zuwa cikin motata"" jin an ce a kama shi ya saka Mutallab miƙewa tsaye, har lokacin zazaare idanu yake ga jirin dake ɗibarsa amma yana tsaye saman ƙafafuwansa, ana haka wasu maza su huɗu suka shigo yana ganinsu ya fara dunƙule hannayensa kamar za a yi dambe, yadda Ade ya tsammata haka ne kokawa aka dinga yi da Mutallab duk wanda ya matsa kusa da shi sai ya saka hannu ya buge, daya damƙi hannun wani sai daya karya ya saki da ƙyar aka kama shi tare da sanya shi a mota" suka nufi asibiti unguwar ta ɗan cika saboda abu kaɗan yanzu ake jira a samu abin zuzutawa. "****Neurologist Dr ne ya amshi Mutallab, bayan an yi masa allura bacci ya ɗauke shi, bayan shi hadda" "sauran likitoci scanning aka yi masa da sauran gwaje-gwajen daya kamata. A hankali ya sauke numfashi ya kalli Ade ya ce ""Kai ne mahaifin Muhammad Mutallab Abdullahi?""" """Kusan haka, ni Uncle ɗin shi ne yayan mahaifiyarsa""" """Ok good. Daman ya taɓa jin ciwo a kan shi ne? Bayan hakan ya je asibiti ko yaya ne?"" Ade ya ce" """Mahaifiyarsa ta yi mini bayani, ubansa ne ya ture shi ya faɗi kansa ya daki jikin kujera a nan ya ji ciwon, kuma daga nan bai kwana gida ba saboda ƴan'sanda da suka kama shi a taƙaice dai Mutallab bai je asibiti ba, bayan ya dawo kuma ya shashantar da abin"" Likitan ya kalli Ade sosai yana ta mamaki a ran shi kamar basu san girman kuskuren da sukai ba? Ya numfasha ya ce ""Kuma bai ce kuma kan na yi mishi" "ciwo ba? Ko wasu sauyin ɗabi'u da kuka fara gani a tattare da shi?""" "Jim ya yi sai ya girgiza kai ya ce ""bani da amsar wannan, domin ba a tare nake da su ba"" Dr ya miƙawa" "Ade scanned copy na result ɗin, Ade ya amsa amsa tare da x-ray ɗin brain ɗin Mutallab da aka yi. ""I am sorry, Mutallab ya samu matsala da ƙwaƙwalwarsa sanadin bugawar da ya yi a kan shi"" jikin Ade har rawa yake wajan furta ""Subuhana, matsala kuma? Kamarya Dr""" """Matsalar ƙwaƙwalwa hauka kenan, shi mahaukaci kuma baya yadda shi mahaukaci ne, bani da yaƙinin" "ko zai warke ko a'a, amma komai ya zo ransa a daidai zai ɗauke shi, kuma zai iya aikata shi, ban sani ba ko haukan zai zamana na duka ko shiru-shiru sai munga farkawarsa, ƙwaƙwalwarsa ta ruɓanya aikinta a kashi 70/100 zafin zuciyarsa zai iya ninkuwa, na taƙaice maka Muhammad Mutallab Abdullahi ya samu taɓin hankali"" Ade ya dinga salati cikin Hausarsa da bata fita sosai, tausayin Mutallab ya sake kama shi sosai. Yana zaune Dr ya cigaba da yi masa bayani da irin magana da za su ɗora shi akai, za a yi masa transfer zuwa dawanau ya dinga ganin likita a can. Kwanan Mutallab biyu a asibiti aka sallame shi, kuma tunda ya farka yaƙi yadda ya buɗe idanunsa ko tari baya yi ya zama wani so silence miskilancinsa ya ƙaro" fiye da kima. Duk hirar da suke yana ji har sanda Ade yake cewa. """A shawarce a yi masa aure, yadda matarsa zata dinga kulawa da shi idan ya samu kulawar mace" wataƙila abin ya zo mana da sauƙi tunda na lura har rashin ƴar'uwarwa Muneeberh ke damunsa. """Aure fa Yaya? Wa kake tunanin zai bawa Mutallab auren ƴar'sa, ana ganin kamar ya haukace? Babu mai" "bawa mahaukaci auren ƴar'sa gaskiya Yaya""" """Ni ne mahaukacin? Ni ne kike cewa mahaukaci?"" Ya faɗa yana buɗe rinannun idanunsa ya shigar da su" "ciki, saboda yadda ya yunƙura cikin sauri Ade ya ce ""Kuma wane ya isa ya cewa Tayo mahaukaci ban yi shari'a da shi ba? Ba da kai ake ba"" Ya jinjina kansa sai kuma ya miƙe ya fita, shi dai ya san ras yake ba abin da yake damunsa." """Kinga ni ba'a san ina zuwa wajanki ba, da an sani da an ɗauki mataki a kaina, a don haka ki cigaba da" "haƙuri da jurewa watarana sai labari a yanzu dai baki da wani gida daya shige na Malam Abdullahi, Tayo kuma zan yi magana da mahaifinsa"" godiya ta dinga jera masa har ya miƙe ya ɗakko kuɗi ya bata ya fita waje ya samu Malam sun jima suna tattaunawa da malam kafin ya nemi Mutallab amma maganar" duniya ya yi wa Mutallab ya yi masa shiru bama zaka ɗauka da shi yake maganar ba. "**Kimiyya ya dinga kallon Jeddah kafin ya ce ""Don Allah Jeddah ba sai kin jira Papi ya dawo ba, ki daure" "haba my love"" ta cilla masa harara bata ce komai ba, ya dawo kusa da ita ya kama hannunta ya ce ""Allah fa da kansa yana mai son mai taimako, ka taimaki mabuƙaci baka san ta inda Ubangiji zai taimaka maka ba""" """Kimiyya da ka sani lauya ka karanta, shine zai fi dacewa da kai wallahi anya ba sa a sauya maka tsari ba" "tun kafin lokaci ya yi?""" "Ya ce ""Kuma kin san zan iya tsara mutane da kalamai na, surutuna bai tashi a banza ba, ba ƴan ƙarairayi" "ake yi ba sai a yi winning shari'a?""" "Ta ce ""In ji ka kenan? Ita shari'a domin mai gaskiya ake yi, a kuma bi bayan mai gaskiya ka gane, da kake" "maganar na taimaki wani kai sai ka taimaki wanda bashi da ƙarfin ɗaukan lauya, musamman case ɗin" "fyaɗe, garkuwa da mutane when it comes to your hand ka tabbatar ka tsayawa mai gaskiya Kimiyya, zan sauya maka layin karatunka""" """Burina fa? Kin san nawa burin Jeddah""." """Sai mu yi replacing naka da abokin naka, problem solved """ """Kenan za ki saka shi a makarantar tamu Jeddah?"" Ta jinjina masa kai tana murmushi ta ce ""In sha Allah," "zan gana da principal ɗin naku, ka yi conversing ɗin abokin naka ya zo na ganshi, tunda kaga wancan karan kafin na fito palro ya gudu""" """Shi fa kamar yana da issues da mata ne, ya ce wai baya son kallo"" Jeddah ta ɗauki wayarta tana kiran" "principal ɗin ta ce ""Har wani haɗaɗɗe ne shi haka? Ko iyayi dai naku na yaran yanzu"" tana jin principal" "ɗin ya ɗauka ta miƙe tana cewa ""Assalamu Alaika"". Kimiyya ya bi bayan Jeddah da kallo sai ya miƙe ya" yi waje da sauri yana jin daɗi a ransa. "***Da daddare Aby ya shigo ɗakin zauren da Mutallab ke ciki, abubuwa ya dinga gani na ban mamaki sai" "bai ɗauki abin serious ba ya ce ""Ka je gidan Malam Ayuba wajan ƴarsa Diyna ku tattauna, ita za a aura" "maka zuwa nan da sati guda ba zan iya zama da mahaukaci a cikin gidana ba""" "Mutallab ya yi shiru ya cigaba da abin da ya ke yi hannunsa riƙe da fafaren goro manya ""Ka ji ko baka ji" "ba?"". ""Na ji"" ya ce a daƙile Aby ya juya ya fita. Kamar yadda ya ce ya nufi gidansu Diyna jikinsa sanye da kayan mafarauta ya cake a ƙofar gidan har Diyna ta fito, ta kusa sakin fitsari saboda tsananin tsoro ta" "dinga kallon shi, kyakkyawa da shi tubarakallah ita baƙinsa ya yi mata a irin tsarin mijin da take so." """Kai ne Mutallab ɗin?""" "Ya yi shiru, ta yi murmushi ta ce ""Yadda ka cake kamar a tsakiyar jeji na san kai ne Mai dawa ɗin, sunana" "Diyna babana ya ce za a aura mini kai"" nan ma ya yi shiru, ya ɗakko ɗan kuttu ya yana busa hayaƙin ƙarfe, Diyna ta dinga kallon yadda yake busa hayaƙin kafin ta ce" """Miskilancin sai ya ƙarawa mijina na gobe kyau, zuciyata ta kamo da son mafarauci"" tana ta surutu bai ce" komai sai da ya gama abin da yake ya yi gyaran murya """Ehmn hmm, da farko ni ba ki yi mini kala da mata ba, na biyu cutar ki za a yi za'a aura miki mahaukaci," "ina da taɓin ƙwaƙwalwa, na uku ni mafarauci ne, na huɗu ni ban san mene auren ba, zanta jibgarki kenan a banza kuma ba abin da zai faru ina da shaidar taɓin hankali a dawanau...,"" ya jim maganar ta yi masa tsayi don dai ba yadda za a yi ya haɗe ta a jumla ɗaya ne, ya karka tar da hular saƙin dake kan shi ya ce ""Ki faɗawa babanki Malam Ayuba, ya faɗawa babana Malam Abdullahi kin ce ba kya son" "mahaukaci, ya nema miki wani zaujin a yanki""" """Ni ai ina son ka, wallahi haka zan ce musu ina son ka kai ma ka amince"" Diyana ta faɗa tuni idanunta ya" "kawo ruwa, lokaci ɗaya Allah ya ɗarsa mata son Mutallab a zuciyarta, itama yarinya ce kamar shi," "babanta ya rasu a wajan babanta take zaune. Ta koma cikin gida tana rusa kuka kamar almara ta ce ita wallahi Mutallab Mai dawa take so, ɗan gidan Ammo da Malam Abdullahi." "Hankalin Malam Ayuba ya tashi, ganin har gari ya hawaye Diyna bata fito a ɗaki ba sai kuka take a aura" "mata Mutallab. Mai dawa kam ya manta da batun wata Diyna ya shige ɗakin zaure inda yake gudanar da sabgoginsa ciki, ƴan gidan sai da suga mota ta faka an shiga zaure kuma an fita sai basu damu ba. Shi kuma Aby ya daina takurawa Mutallab akan karatu saboda babban almajirinsa ya ce ɓata lokaci fa yake akan Mutallab yana wahalar da shi, kullum Mutallab sai ya ɗauki karatu a wajansa, shi yana jin daɗin" "yadda kake ɓaɓatu akan sai ya yi karatun, shi kuma boko ne a gabansa, amma Mutallab ya yi karatu" "sosai fiye da yadda malam ke horar da ɗalibansa, bayan karatu har fassara ya juya yana haddacewa." "Gefen Safiyyerh damuwarta ta ninku bata da walwala da farinciki idan ba muryar Daddy ta ji ba, ko" "fuskarsa ta gani sai ta ji ta samu nutsuwa a ranta ta dinga cewa daddyna mijina, tattara sabgar karatu ta zubar a gefe makarantar ma ta dame ta ta ji dama kawai a cire ta. Baya iya bacci sai ta rungume filo a ƙirjinta, kullum sai ta kwashi kayan Ummeyh na S Bayero ta sha, lokaci ɗaya jikinta ya fara buɗewa ƙirjinta ya cicciko fatar jikinta ta sake sheƙi hips ɗinta ya buɗe, sai ta fara saka hijabi hakan ya saka Ummeyh ba ta yi noticing komai ba, ba kuma ta taɓa tambayar Safiyyerh daliln saka hijabin ba, bata" tsaya da lura da kayan matan nata ba. Bata ɗauki zancen Safiyyerh na aure da take yawan yi mata ba. ***Mai dawa na ƙofar gidan tsaye da Kimiyya da zuwansa kenan Malam Ayuba ya ƙarasu wajan da sauri "yana kuka tare da cewa ""Me muka yi maka, daga maganar aure shi ne zaka kashe mini ƴata kazo kaga" "halin da take ciki""" "Mutallab ya dinga kallon Malam Ayuba, kuma ya yi burus Kimiyya ne ya ja hannun Mutallab suka rufawa" "Malam Ayuba baya, tun kafin su isa suka tarar an cika ƙofar gidan ga wani hayaƙi na tashi kamar gobara," da sauri ya faɗa ciki yana shiga ya jiyo muryar Diyna na cewa """Zai kashe ni, Mutallab ne wallahi shine ina son shi ina son shi"" sosai wuta ke ci a ɗakin da take ciki, gashi" "ƙofar ta manne taƙi buɗewa, duk wani ƙokari da Mutallab zai yi but he couldn't save Diyna's life, yana jiyo ihunta ta cikin wutar tana babbakewa ya kasa ceton rayuwar Diyna, tun tana ihu har ta daina ta mutu a cikin wutar gobara tana ambaton sunansa wanda duk wanda ya zo sai ya gasgta cewa shine ya" kashe Diyna. Back to story. "Ya ja numfashi mai tsayi ta cikin bakinsa ya fesar, kansa na juyawa kamar yanzu ne yake jiyo ihun Diyna a" "kunnensa. Ya buɗe jajayen idanunsa ya kalli Safiyyerh dasu, ta yi saurin ɗauke kai wani irin tsoran shi da shakkarsa take ji, magana yake son yi mata amma ya kasa." "Safiyyerh ta yi ƙarfin halin cewa ""shikenan Diyna ta rasu?"" Ya ɗage mata girarsa biyun, almar e;." """Allah sarki. Allah Ya ji ƙan ta"" sai kuma ta fara kuka ƙasa ƙasa, tuna cewa yanzu fa shi mahaukaci ne" yana da taɓin ƙwaƙwalwa? Ta dinga rusa masa kuka wanda shi kuma ya yi ko gezau kamar ma kukan "nishaɗi yake saka shi, sai dai duk wani motsin Fiyya akan idanunsa yake ya dinga jin kan shi na sara masa," "ya saka ƙata ya zungure ta, taƙi daina kukan ya sake zungurinta nan ma ta yi masa banza, ya saki wuƙar" "hannunsa wacce jinin jiki ya fara bushewa amma sarar da aka yi masa shi har yanzu yana nan, ya matsa" "dab da iya ya duƙa tare da saka hannu ya tallafo haɓarta ta runtse idanunta tana faɗin Astagafirulla a zuciyarta, duk abin nan bai saka ta manta ita matar aure ce ba." """Shhhh, Quiet""" Ta kasa daina kukan ta cigaba da kallonsa kuma ya yi ƙasa da murya yana sake duƙar da fuskarsa dab da "tata, yafi minti uku yana kallon fuskarta kamar mai son tantance abu, sautin muryarsa daga ƙirjinta take fitowa ya ce ""Shiru, ko na yi miki abin da nake ta riƙe da shi tsayin shekaru"" ta dinga shassheƙar kuka a hankali ya saka yatsarsa, manuniyya ya fara kewaye lips ɗinta da ita, cikin wata murya ya ce ""Duk macen da tace tana so na, sai a wayi gari ta mutu, Diyna ita ce first, mata uku suna mutuwa saboda ni, ana cewa ni na kashe su, daga cikin har matata wacce na aura, gawar data zama gawa ta ƙarshe ita ce gawarki" "Safiyyerh"" ya yi shiru yana cigaba da zagaye lips ɗinta da yatsarsa." "[1/7, 9:34 PM] Sis Fauzy: Chapter 24: If he is your husband, who am i?""" "Safiyyerh ta zame fuskarta, cikin kuka ta ce ""da gaske kana da taɓin ƙwaƙwalwa? Mahaukaci ne kai, don" "Allah ka ƙaryata zuciyata, ka ce mini lafiya ƙalau tunaninka da ƙwaƙwalwarka suke"" kuka take sosai" "kamar wacce aka cewa Professor Abdu Marafa ya mutu, da ƙyar take jan numfashi ta kalle shi taga yana nan durƙushe gabanta ita kuma yake kallo." """Jarumi"" ya ɗage mata girarsa biyun, ta ce ""Karka raunata zuciyata da jinkimarka, kar ka saka mini" "soyayyarka ta dole, domin hakan ba ƙaramar jarrabawa bace a wajena, ka yi mini komai amma kar ka bari na kamu da tsananin son ka, wannan zuciyar dake cikin ƙirjina. ,"" ta yi shiru tana nuna masa ƙirjinta" "da yatsa, ya kalli ƙirjin sau ɗaya ya mayar da idanunsa zuwa kan fuskarta musamman idanunta." """Ba zata jure ba, ka faɗa mini wanda ya saka ka sato ni, kuma ka ƙarasa bani labarinka, ba zan jure" "zaman a nan ba""" """Hmm""" """Na ji tausayin Muneeberh na jima ban ji mutuwar data tsaya mini irin wannan ba, ban ɗauka akwai" "wanda suke cikin halin na yunwa da rashi har haka ba sai a cikin labarinka. Sannan Aby bai..,""" "Ta yi shiru tana sunkuyar da kanta zuwa ƙasa, domin ba zata jure kallon cikin idanunsa ba; for a while." """Mugu ne"" Moh ya yi furucin numfashinsa na sauka a fuskarta, ta girgiza kai a hankali ta ce ""A'a ni ban ce""" """Ce"" ya ce, yana miƙar da hannunsa saboda jinin dake zuba inda aka yanke shi. Safiyyerh ta girgiza kai" "tare da yin shiru, har ƙasan zuciyarta take tsananin jin tausayin talaka,idan baka da kuɗi a rayuwa shikenan kai ba mutum bane. ""Don Allah ka matsa daga kusa dani, wallahi tsoro kake bani kuma mun yi kusa da juna sosai"" shi dai bai ce mata komai ba, sai idanunsa masu kaifi daya kafeta da su kamar mai" "son fahimtar wani abu, yana kallon ta yana motsa bakinsa." """Jarumi"" Moh ya dube ta, cikin raunin murya da sabon tashin hankalin daya mamaye fuskarta ta ce" """Bayan daba da shaye-shaye da kuma bangar siyasa da ka yi amma baka taɓa yin..."" Ta yi shiru, ya buɗe mata ido." """Kee"" ya kira ta cikin dakakkiyar muryarsa ya yi kiran, ta ji mararta ta kumbura kamar za ta yi fitsari, ta" "fara inda-inda sai kuma ta ce ""Uhm amm ba komai""" """Ƙarya kina, talk"" domin da yawan lokaci a furucinsa zaka fahimci yana da alaƙa da jinin yarabawa. Ya" "fara juya wuƙar hannunsa ta ce ""Me za ka yi da wuƙa yanzu? Ba dai faɗa ba?""" """Ke zan yanka, ba'a rainawa Moh hankali, zan fara nuna miki da gaske ina da taɓin hankali"" kamar ta saki" "fitsari haka Safiyyerh ta ji ta ce ""Haba Jarumi, me ya kawo maganar nan kuma? Wai ba'a wasa da kai ne?"" Bai kulata ba, ya cigaba da juya wuƙar ya ɗaga tare da nufar gefen cikinta, ta yi zumbur zata tashi ya miƙa hannunsa ya damƙi gefen cikin nata ya miƙe tsaye da ita a hannunsa, ta haɗiye wani irin yawu da ƙyar sai ƙifta masa idanu take, banda kiran sunayen Allah guda ɗari babu ɗaya da take babu abin da" take a ranta. """Allah Ya baka haƙuri Jarumi""" """Ce...!"" Ta ce ""Amma baka taɓa aikata zina ba, bayan abubuwan da ka yi ko?"" Ita kan ta bata san ta yi" "maganar ba, kawai abinne ke ci mata zuciya ba tare da sanin dalili ba. Mai dawa, ya kafe ta da idanu musamman ɗan siririn zanen S ɗin dake wuyanta wanda aka yi da baƙin abu, ya haska fatar wuyan sosai" a barka da zabiya. """Baka taɓa aikata zina ba ko? Ka faɗa mini baka taɓa aikata zina ba don Allah Jarumi, don Allah ka" "taimaki Safiyyerh da zuciyarta""" """Mece zina?"" Ya tambaye ta. Ta ce ""Baka sani ba?"" Ya mata shiru, ta ce ""A yi abin auratayya ba aure"" ya" "shagiɗar da bakinsa zuwa gefe ya ɗaga idanunsa ya kalli sama ya jima a haka fuskarsa nan ba walwala kamar kodayaushe, ya sakko da idanunsa ya sake zubawa wuyanta ido." """Yi yadda zan gane""" """To a yi iskanci ba tare da aure ba""" """Shhhh, idan wanne ne na taɓa, da kuma ke na yi iskancin har mun samu sakamakon hakan, ɗa kenan" "ko?""" "Dum! Haka Safiyyerh ta ji a tsakiyar kan ta, wasu abu kamar jonin wutar lantarki suka fara yi mata" "tarnatsi a cikin kan nata, ta yi saurin dafe kai jikinta na rawa ta yi baya kamar zata faɗi, amma bawan Allan ko motsi bai yi ba, balle ya tare ta. Cikin rashin fahimta ta ce ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Ka taɓa zina? Na shiga uku ni Safiyyerh wai me ya sa baka da ɓoye abu ko da ka aikata? Ka san tabon da ka ajjiye mini a zuciyata kuwa? Har na mutu ba zan manta wannan kalmar ba, saboda kaga ina son ka na damu da kai? Shine bari ka nemo hanyar ƙuntatawa zuciyata?"" Ta fashe da wani irin raunataccen kuka, a lokacin mantawa ta yi da igiyar auren Maj Aliyu uku da yake kan ta, wani irin tiriri da zafi take ji," "zuciyarta a matse take a takure cikin ƙuntataccen ƙirjinta, ta ji iskar wajan ta yi mata kaɗan." "Miƙewa Safiyyerh ta yi cikin sauri ta nufi hanyar fita cikin daren idanunta rufe ko ganin gabanta ba ta yi," bayan ta buɗe ƙofar tana ƙoƙarin fita ta ji ya saka hannunsa ya damƙo ƙugunta ya haɗo da wanda dake "jikinta a jerin kayan daya kawo mata, a gigice ta juyo saboda wani irin miƙewa da gargasar jikinta ta yi" "cikin faɗa ta ce ""Wanne irin iskanci wannan zaka riƙe mini ƙugu, ko sha fara kaga aljan ɗin ka watsa eh?""" """Iskanci?"" Ya buƙata? Don shi bai ga abin iskanci ba. Ba ki Safiyyerh ta buɗe da nufin cewa ""Ka sake ni," "ina da aure ina miji so, Maj Aliyu ina da auren wani a kai na haramun ne ko jin muryarta balle taɓa wani sashi daga jikina"" sai ta yi shiru, tuna cewa ai bai san tana aure ba taga duk wani bayani da za ta yi masa ba zai fahimta ba ta kwantar da murya ta ce ""Abin da kake ba kyau, ka cika ni"" a hankali ya sake ta, yana" "ta kallon ta da zai iya kuma ya jure zai tambaye ta akan mene iskanci yake nufi, a tsakanin lokacin nan ya" "furta masa kalmar iskanci sai wajan uku. ""Ka yi haƙuri don Allah"" ya sake mata shiru kawai." """Bai kamata a ce ina zaƙewa tare da kutsa kai cikin rayuwarka har haka ba, na ni kawai zan rayuwa da kai" "don Allah ka bani wannan damar""" """Ki dinga ce mini ɗan iska?""" """Baka haka nake nufi ba, kalmar zina ta mini tsauri da yawa wallahi i can't take it from you""" """Uhm"" ya ce ya juya yana tangaɗi sosai ya fita daga cikin gidan tare da rufe ƙofar da ƙarfi." """Ka yafe mini Captain, Ka yafe mini Aliyu naci amanar aurenka da yake kaina, na wulaƙanta igiyar aure," "na rusa yadda da amincin da Daddy ya yi mini, na saka ƙafa na rushe wannan ni'imar na yi tarayya da waninka, wanin da bai dace ba, wanin da bashi da cancanta ko rabin nagartar da kake da shi. Ni shaiɗaniyya ce kamar yadda yake faɗa, na sake ribatarsa, da wanne ido zan kalli mahaliccina wajan yi masa bayanin da aurena na kula wani namajin daban?"" Safiyyerh kuka take sosai, jikinta na wani irin ɓari ta takure waje guda ta cusa kan ta tsakiyar ƙafafuwanta. ""I am sorry Aliyu, ka yafe mini Ka yafe mini" "na wulaƙanta aurenka"" shiru ta yi saboda ganinsa da ta yi tsaye a kanta, sai muzurai yake yi mata da ƙyar ta ce ""Don Allah Mutallab"" sai ta yi shiru jin sunan nasa ya yi mata wani irin kwarjini ""Ka mayar dani gidanmu, da ka yi garkuwa dani idan wani abu kake buƙata ka kira iyayena za su baka koma mene, saɓon" "Ubangiji ba kyau""" """Idan shi mijinki ne, ni waye?""" "Rawar jikinta ya tsananta ta girgiza kai laɓɓanta na rawa ""Kamarya?"" Safiyyerh ta kasa fahimtar tun kafin" "faruwar komai da fitar Mutallab, taɓin hankalinsa ya motsa musamman yanzu da yake tsaye yana zazzaro manyan idanunsa waje, jikinsa na rawa ya ɗuka gabanta kai ya ɗago za ta yi magana, ta ji ya shaƙe mata wuya ya fara kifa mata mari a fuska idanunsa sun tara ruwa, wata azaba yake ji a cikin kan nasa, Safiyyerh ta fara kakari shatin yatsunsa suka zauna a fuskarta, gashi da iya ƙarfinsa ya shaƙe ta idanunta suka ƙaƙƙafe numfashinta ya fara tsayawa a ƙirji ta saka hannu ta damƙe ƙirjinsa tana shura" ƙafa. "Goje na shigo cikin tashin hankali, ganin Moh ya shaƙe Safiyyerh zai kashe ta ya sana ya nufi wajan su da" "sauri ya ce ""Mai dawa""" """Ya dai? Me ta yi maka ka sake musu ƴa wallahi"" sai a lokacin ya lura tamkar Moh baya cikin hayyacinsa," "ya fara ƙoƙarin ture shi amma ya kasa, daya matsa sai yaga ya fara kawo masa damƙa da ƙarfi yake cewa" """kar ka zo nan""" "Goje ya rasa yadda zai yi Safiyyerh har fitsari ta yi saboda wahala, ta ƙanƙame ƙirjinsa da hannunta biyu" "har tana taɓo kwantattun gashin da suke wajan, cikin sauri Goje ya faki idanun Moh ya danna masa wata jijiya dake bayan wuyansa, nan take ya saki Safiyyerh ya dafe wuyansa a hankali ya sulale a wajan ba numfashi, Safiyyerh ba ta faɗo jikinsa a sume. Mangal daya shigo yanzu yana haƙi ya buɗe ido ya ce ""Yaƙi" "suka yi ne? Wai ragas kenan yarinyar nan tana raye kuwa?""" """Kai baka faɗar alheri ne?""" "Mangal ya ce ""Daga tambaya? Faɗa suka yi ne ko mene?"". ""India ne da Pakistan ɗan wahala ɓace daga" "nan"" ko a jikinsa ya nemi waje ya zauna, shima Goje ya zauna. Goje bai damu da duk wasu kayan maye ba hakan ya saka zaka ganshi a ɗan nutse." "Da safe Mutallab ne ya fara buɗe idanunsa da ƙyar yana dafe kan shi da yake sarawa tare da juyawa, ya" "dinga mamakin abin da ya saka shi kwanciya a nan wajan, ya dafe kai a hankali yana ɗan haɗe fuska. Nauyin da ya ji a ƙirjinsa da numfashi da ya ji yana ɗauka ya saka ya ɗan yunƙura zaune ya zubewa fuskarta idanu, ganin yadda ta yi jawur ga yatsun ƙwance a fuskar, ya kalli wuyanta shatin farata ya gani duk an ƙwarzane mata wuya, ya rufe ido ya buɗe tas komai ya dawo kansa ya dinga kallon ta, ya miƙa hannu kamar zai taɓa ta sai ya fasa saboda zafin zazzaɓin da ya ji, ya ture kan ta miƙe tsaye ya nufi ɗaya" ɗakin tare da rufo ƙofa. "Yadda ta sume da kanta, haka ma yanzu ta farfaɗo tana jan numfashin wahala ta ja jiki ta miƙe, ta dinga" "kallon ita ke ƙwance a ƙasa, ita Manager guda? Safiyyerh, Fiyyar daddy a wajan ƴan daba kuma a ƙwance a nan ta dinga kuka sai da ta yi mai isarta ta yi shiru. Goje ya dube ta ya ce ""Zan buɗe miki ƙofa ki gudu, domin za ki iya rasa rayuwarki a nan wajan a hannunsa, ni fatana da burina bai huce rayuwarsa ta gyaru" "kamar kowanne mutum ba, mun san cewa akwai ƙaddarorin da babu yadda muka iya da su, dole mu yi" "haƙuri mu zuba idanu har lokacin da Ubangiji ya so, ki tashi ki je zan faɗa masa ban san yadda aka yi kika" "fita ba""" "Safiyyerh ta yi shiru sai ta ce ""Zan gane hanya?"" Ya ce ""E, ta shi""" "Ta miƙe jikinta na yi mata tsami ta saka abayar dake wajan, ta zura takalmi kan ta ko ɗan kwali babu ta" "nufi ƙofar fita, Goje ya bita da kallo. Tsayawa ta yi ya ce ""Fece mana"" Safiyyerh ta girgiza kai ta ce ""Ba" "komai idan na tafi?""" """Ban gane ba komai ba?""" """Wallahi ba zan iya barinsa ba, ba zan iya tafiya ba ka yi mini afuwa"" da mamaki Goje ya ce ""Ubanki ne" "shi da ba za ki iya barinsa ba? Shi babu abin da sai same shi sai ikon Allah, ke kuma a banza zai kashe ki wallahi"" sulalewa ta yi a wajan ta zauna, tana fashewa da kuka sosai ta ce ""Wallahi zan zauna da shi, ba zan iya tafiya ba ka yi mini uzuri"" wani siririn tsaki Goje ya ja ya miƙe tare da barin gidan, tana nan zaune ita kaɗai kamar mayya ta ji ya buɗe ƙofa ya fito, ta takure ya kalle ta ya share, ya zaro sigari ya kunna ya" farawa busawa yana sha yana lumshe idanunsa da kaɗa ƙafa kamar yana enjoying moment ɗin. "Yana yi yana kallon ta, amma ba za a taɓa cewa kallon nata ya ke yi ba, sai daya shanye kara goma ya" "miƙe zuwa ɗaki bai jima ba, ya fito ya dawo gabanta ya durƙusa. Ta fara ja baya tana takurewa tare da girgiza kan ta, so yake ya ce mata sorry amma the last abin da zai iya kenan a rayuwarsa bada haƙuri, Safiyyerh ta miƙe zata tashi a kumbure yana cika da batsewa ya ce ""Koma""" """Ka yi haƙuri, ba zan iya zama inda kake ba"" ya miƙa hannu zai taɓa wajan yatsun dake fuskarta ta ta" "zana ta fasa ihu tana ganin kamar sake shaƙeta zai yi, shi kuma ya riƙe ta gama suka fara dambe duk ta fita hayyacinta ya matse ta a ƙirjinta ya rufe ta da hannunsa cikin muryar gargaɗi a raunace ya ce." """Finally i accept that, I'm always the wrong person in everyone's story, everyone's life"" ya yi maganar a" "hankali kamar mai raɗa, can ya cika ta, ta matsa gefe guda tana jin wani iri lallai akwai wani abu a tattare da shi wanda yake jan ta zuwa gare shi." """Bana bada haƙuri, zahirina kika gani just take it"" ya jingina da jikin kujera ya zuba mata idanu a hankali" kuma ya ɗora da bata labarin domin haka tafi fahimtar hakan sosai. ***After Diyna's death "Duk inda aka zaga sai a ce Mutallab ɗan gidan Malam Abdullahi mai allo ya kashe Diyna, saboda tun" "kafin wutar ta kama take kuka tana kiran sunan Mutallab, al'amarin da ya yi wa Malam zafi a cikin ransa," "ganin yadda ake laƙaba sunansa a jikin na Mutallab ransa ya ɓaci ainun, yana jin haka kawai yaro ba zai" "ɓata masa suna a gari ba, aure kuma dole sai ya yi masa naganin kangara da lalacewa kenan." Yana cikin tarin almajiran ya shigo cikin gidan yana sabaɓi ya tarar da Mama Zaituna ta yi zauna saboda "ki karyawa ba ta yi ba, Ammo hankalinta na kan kuka da take ɗaurawa saboda ta mayar da hankalinta a kan sana'a sosai kodan bikin Sa'adah da za a yi. ""ina wannan gangararren yaron yake ina ya shiga?"" Ta yi masa shiru ya ɗaga hannu ya zarara mata bulala, ya ce ""Ina magana domin iskanci kina mini shiru? Ina makashin yake mai ɗakkowa jama'a magana ba gaira ba dalili, yanzu ya tabbata ya kashe musu yarinya a banza? Sai ya maɗiɗi ake dani a gari shi ya sa na ji ba fara zuƙewa? Shegen yaro ya ɗakko jinin masifa da shegiyar zuciya kafiya da naci kamar na kafuran farko, anya ba lalatacce bane ba?"" Ammo ta yi ƙasa da kai tana shafa inda Malam ya zabga mata bulalar Mama Zaituna ban da dariya babu abin da take yi kafin" ta ankara itama ya cauɗa mata bulalar. Zumbur ta miƙe ta yi ɗaki. Malam ya hau faɗa yana kumfar baki. "Mutallab da shigowarsa kenan ya tsaya cak a bakin ƙofar Malam ya ce ""Yawwa yawwa ɗan asara" "haihuwar asara, da gaske ka kashe Diyna ka kashe musu yarin""" """E, na kashe ta""" """Innalillahi ka kashe ta fa kace?"" Ya yi shiru, Malam ya dinga aibata Mutallab alkaba'i kala-kala ya ce" """Kuma aure ba fashi, idan kaga dama itama yarinyar ka kashe ta"" ya jinjina kai bai ce komai ba. ""Ka je" "wajan abokina Malam Umaru, akwai yarinya tana nan wajansa marainiyya ce ka je ku gana cikin satin nan za a ɗaura muku aure""" Gabaɗaya naman jikinsa rawa yake yi da wani irin ɓari zuciyarsa na tafasa. Tun bayan faɗan da ake yi "masa bai ɗago ba, balle ya tofa tasa ""Ina jin kamar na haifawa kaina matsala"" cewar Ammo." "Ya ɗago rinannun idanunsa wani irin ruwa ne kwance a cikinsu, jijiyoyin kansa sun yi ɗoɗar tare da" jerewa suna harba masa. """Mutallab"" ya ji zuciyarsa ta kirayen shi, kiran da sai daya ja numfashi ya haɗiye abinsa zuwa ciki ba tare" "daya fesar ba, yana jin hucin zuciyarsa na keto ruɓin fata bakwai da Ubangiji ya halitta a jikinsa, me ya sa suke son yi wa rayuwarsa iyaka da jin daɗi ne? shahara tare da daular da yake mafarki suke son yi masa" "farraƙo da ita? Da gaske arziƙi yake so, iko yake buƙata, lalle suna son tauye rayuwarsa." "A hargitse ya furta ""Kar ka yi mini baki, Aby da kun sani da ba ku yi cikina ba, da kun sani da baku yarda" "kun haifan ba, karku ƙuntata rayuwata ba zan ɗauka ba"" Kuka Ammo take sosai ya saka ƙafa ya buga jikan ƙyauren nan take ya faɗo, ya dinga dunƙule hannunsa jini na zuba rezar dake cikin tafin hannun" nasa na shigewa ciki hannun. """Idan na lalace ku na lalacewa domin zama zan yi mu raba hisabin tare"" Ya faɗa yana zaro ƙatuwar mesa" daga cikin aljihunsa ya rataya a wuyansa. """Me kake so?""" "Kai tsaye ya ce ""KUƊI, IKO!""" """To kai da kuɗi sai dai idan ana yi a lahira, tagayyararran yaro kawai, ɗan banza mai irin zuciyar abu" "lahab"" wani irin abu ne ya kama zuciyar Mutallab mai kama da rauni, zuciyarsa ta dinga rawa tana masa motsi a ƙirji ya matsa kusa da Malam ya durƙusa akan ƙafafuwansa kan shi a ƙasa ya dafa ƙafafuwan Malam ya ce ""Aby Abu Lahab ɗin da aka ambata a cikin Alqur'ani, cikin suratul Masad kake haɗawa jininka da shi, wanda ya yi Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama tawaye shi kake dongana shi dani? Me na yi da zafi haka? Ni Aby ni ni ko? Na roƙe ka daka daina kar abin ya wa Mutallab yawa, ba zan jure ba ka yi mini aikin gafara Aby, ka mini addu'a ka nema mini shiriya idan kuskure nake"" Aby ya" saka ƙafa ya hankaɗe Mutallab ya nuna shi da yatsa ya ce """To me haihuwarka ta tsinana mini? Dame ka ƙare ni da shi banda tashin hankali, nikam da nasan cewa" "abin da aka haifa kenan gwara a zubar da kai tun kana ciki ma ya istigigari, ban hango ta inda zaka iya taimaka mini ba a rayuwa"" ya yi ƙwafa ya fice daga cikin gidan, har ya yi nisa ya dawo ya ce ""Saura na samu labarin ka je kaga yarinyar can ba, wama take da suna? Jaanah"" Mutallab ya yi ta zama a wajan ya miƙe ya isa inda Ammo take ya ce ""Barka da yamma"" ta yi masa shiru ya yi ta tsaiwa can ya ce ""Zan" "ɗaura miki"" sai kawai yaga ta miƙe ta bar wajan shima ta fita zuciyarsa a raunace." "***Kimiyya ya shigo parlo yana murmushi ya kalli Jeddah dake zauna tana duba abubuwa, shigar alfama" ce a jikinta kana ganinta ka san ba sai an yi magana ba irin manyan hajiyoyi ne wanda suka gama ganin "dukiya da arziƙi kala-kala. Ya ce ""Can ki Jeddah """ """No idea, ba zai shige maganar abokinka ba"" Kimiyya ya zauna yana shafa kai ya ce ""So, he is finally" "here"" ya yi maganar yana nuna mata Mutallab da ya yi ƙiƙam a bakin ƙofar shigowa parlon. Jeddah ta" "ɗaga kai ta kalle shi, taga ai ya kerewa kimiyya a tsayi da jiki da komai, ta dubi shigar mafarautar dake jikinsa ya cake fuska ba yabo ba fallasa." """Kai ba so ka ba, mene ya haɗaka da tsaiwa kuma? Come in; shigo ciki""" "Kimiyya ya yi murmushi wanda baya barin fuskarsa ya ce ""Bashi da yadda ne Jeddah"" ""Ok"" kawai ta ce" "tana sake kallon Mutallab ɗin, a hankali ya shigo yana tafiya ɗaiɗai shi idan aka ce ya zauna tamkar an haɗa shi da aiki ne ya durƙusa ya ce ""kina lafiya?""" """Allahamdulilah, shekararka nawa ne? Ni naga jikinka bai nuna mini shekarun da Kimiyya ke faɗa ba," "kalle ka kamar ka goya shi?""" """Sai dai na tambayo""" """Baka sani ba? Where is your birth certificate?"" Ya buɗe ido, Kimiyya ya ce ""Takaddar haihuwa wai take" "nufi"" Ya girgiza kai alamar babu, Jeddah ta ce ""Ok, irin takaddar allurar da akewa yara suna jarirai?"" Nan ma ya yi ta ce ""Allah Alhakkamu, Kimiyya zai baka uniform, mun kammala komai, a makarantar za a ƙarasa abin da ba mu yi ba, the fee payable per annum is N300,000 per student, so har ka gama makarantar ba wani damuwa, ina fatan kuma ba za a yi asarar kuɗin tara ba ko?"" Shi dai bai ce komai ba, yana kallon ƙasa banda yanayinsa ya fara sauyawa masifar girmamawa ta Mutallab ko haɗa ido ba zai da" "ita ba. ""Jeddah shi fa kamar robot eh ne, yana da basira da gane abu""" """To ya batun exchange ɗin da za ku yi?"" Ya ce ""Na faɗa masa, Allah Jeddah idan ki kaga abubuwan da ya" "sani akan computer yanzu you'll be surprise za ki yi mamaki sosai"" Ta jinjina kai ta ce ""I like surprises, ina son abin mamaki""" "Mutallab ya yi da ƙyar wajan faɗin ""Na gode, Allah Ya amfana zuri'a""" """Yi wa kai ne ai""" "Yin duniya ta ce ya tsaya bless ta Kammala abinci amma yaƙi, suka nufi part ɗin Kimiyya a tare suka" "dinga abubuwa Mutallab ya ɗauki abu ya saka a kunne ya yi shiru kamar daga sama cikin mamaki ya ji ya kutsa kai cikin wayar wasu da suke yi, ya janyo kujerar ya ɗauki abu ya sakawa Kimiyya, mamaki ya cika Kimiyya ya dinga kallon Mutallab sukai shiru kuma suna jin conversation ɗin mutanen wanda kamar" "haɗaka suka yi, da tsantsar mamaki Kimiyya ya ce ""Mu faɗawa Jeddah""" """No, ka yi saving recording""" "Kimiyya ya fara saving kamar yadda Mutallab ya ce, sukai shiru shi Mutallab ko a jikinsa, Kimiyya kuma" gabaɗaya hankalinsa a tashe yake. "Da daddare Mutallab ya shirya cikin kayan da suka zame masa kamar suttura a yanzu, daman tuni iyaye" "sun fara jawa yaransu kunne a kan su fita sabgar Ɗan'malam, dama shi ba abokai ne da shi ba rayuwarsa kawai yake, abokinsa ɗaya TARIQ. Bayan ya isa ya yi tsaye a ƙofar gidansu Jaanah, ta fito ta tsaya bai kalleta ba, a yanayinta kawai ya san cewa bata cancanta da zama matar Moh ba, ba za a taɓa ganin Matar Moh haka ba. ""Ina yini?"" Ya yi mata shiru ta ce ""Bawan Allah na fito an ce mini zance kazo wajena," "na yi sallama shiru, na gaisheta shima shiru"" idan gini ya motsa Mutallab ya yi magana." "Ta yi murmushi ta ce ""Mazan fama kenan, su TAHHB manya""" """Tahhb?"" Ya maimaita sunan a ran shi, ta ce ""Ka mini kyau da suna Tahhb, na ji kuma na amince zan yi" "rayuwa da kai"" bai sai mene ya ja ra'ayinsa da Jaanah ba ya juya kamar zai kalleta ya fasa. ""Ta ce Sunana Fatymerh, amma ana kira na da Jaanah ,"" ta fashi rayuwarta gabaɗaya abin ta manta ne kawai bata" "faɗa ba, Jaanah akwai shiga rai tana da surutu kamar taci naman aku ta kalle shi ta ce ""Tahhb""" """Tahhab"" ta sake kiran sunan shi a karo na biyu, bai amsa ta ce ""An ce wai ka kashe Diyna, idan na" "amince da auren naka nima kashe ni za ka yi? Zan mutu?""" "Ya juyo sosai, fara ce ita tas tana matsagaicin jiki kana ganinta ka san bata da kwanciyar hankali saboda" "kayan da suke jikinta. Ta yi murmushi sai kuma ta gyalgyale da dariya sosai har tana saka ta dafa shi, a lokacin hannunta zafi zau ta ɗauke hannunta ta ce ""Afuwan, zazzaɓi nake yi ka ji hannuna zafi ko?""" """Tahhab, ni dai ko zan mutu ba komai, balle ba zaka kashe Jaanah ba, zan rayuwa tare da kai, kaima" "babanka ya mutu? Babarka ta mutu ne ko?"" Bata tsammata ba, ta ga ya girgiza mata kai ta ce ""Ayya na ɗauka baka da Mama da Papa, Tahhab zan aure ka"" ya miƙe tsaye ya miƙa mata ledar hannunsa, ta amsa ta leƙa taga gurasa ce da nama ta saka hannu ta ɗauki naman za ta kai bakinta ya ce ""Kamata"" ta ɗago kai, taga wani waje yake kalla daban ta sake yin dariya ta saka naman a baki ta ji ya ce ""Naman Gafiya" "ne. , ki shiga ciki Mutallab ya amince da auren ki""" "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 25: Jaanah" "Jaanah ta ce ""Da gaske ka amince zaka aure ni Tahhb? Kuma ba zan mutu kamar wacce zaka aura ta" "farko Diyna?"" Ta yi furucin cikin roƙo da tausayawa, bai juya ya kalleta ba, sai ta ɗauka ko ya fasa ne? Cewa za'a yi mata aure, at her young age ya zama maɓudin tashin hankalinta, bayyana mata wanda zata aura, ma'ana Mutallab Ɗan'malam ya zama tambaya a cikin zuciyar Jaanah, ganin Mutallab tsaye gabanta matsayin wanda zai aure ta ya zame mata dukkan amsarta, ya share mata shakku da kokwanto.""Idan ni zan wa kai na aure ba zan aure ki ba"" ya yi shiru, ya kalleta da kyau kallo na daƙiƙo ""Idan kuma yi mini za'a yi, Mutallab baya da wani zaɓi ok"" ""Na gane, na gode hakan ma"" Jaanah ta ce tare da yin murmushi ta jingina da katangar dake gidansu, with different thinking running on her mind. Har ya shigewa ganinta bata bar wajan ba, kamar mai using magic haka ta ji zuciyarta tattara tare da tafiya wajan Mutallab, ta ji koma mene zata amince da shi. Bayan Jaanah ta shiga cikin gidan ta cigaba da aikin da take yi, Malam Umaru ya ce ""Ya kuka yi dashi kuma?"" Ta ce ""Ya ce na faɗa maka ya amince da auren"" Malam Umaru ya jinjina kai cikin jin daɗi ya ce ""Madallah, gwara duka mu aurar daku ai ko" "hankalinmu zai yi ɗaya""" """Baba baka son ganina har haka ne? Ai aure bar Ubangiji ne haka malaminmu yake faɗa mana"" Jaanah ta" "faɗa hankalinta kwance, shi kuma Baba ya ce ""Ba shakka Jaanah ni kike faɗawa haka? Daman auren kike jira a yi miki kenan?"" Ta ajjiye abin da take yi tare da yin jigum sai kuma ta ce" """Baba kai kace za ka yi mini auren nan, idan ban yi maka biyaya a duniya wa zan yi wa? Dole na yi maka" "idan ina son wanyewa da duniya lafiya, shine iya abin da zan yi na rabauta da lahira ta""" """Kenan murna kike za a yi miki aure? Daman abin da kike so kenan Fatymerh?""" """E, baba domin kai ma kana murna, ni na ji Tahhb ya yi mini"" Jannah ta ce, tana lumshe idanunta ji ta yi" "kamar rana ɗaya ta zame mata shekara guda da sanin Mutallab, ta ji ta damuw da shi, ko idanunta ta rufe tsaiwar shi take gani cikin duhuwar idanunta, idan abin da ake kira shine so; tana matuƙar son Tahhb, soyayya mara adadi. ""Anya Jaanah? Kina ta kuka bakya son auren har bulala na saka miki a jiki shine za ki ce haka?"" Janaah ta fidda fararen idanunta waje sai kuma ta yi murmushi ta ce ""Ya zan yi da ƙaddarar Jaanah? Labarin Jaanah ba zai cika ba sai da Mutallab Ɗan'malam"" tana cewa haka ta miƙe ta" shige ɗakin da take ƙwance zuciyarta ta fara haiƙo mata kanta a matsayin matar Mutallab. "Mutallab ne ya shigo cikin gidan bayan gari ya waye hantsi ya yi, Malam na kishingiɗe yana gyanyaɗi sai" "Ammo dake aikin sana'arta, Mama Zaituna ta yi jigum da hannu a haɓa. Sarai ta ji sallamar da ya yi" "amma ta share shi ya dire baƙar ledar hannunsa Malam ya buɗe idanunsa ganin baƙar leda ya saka ya miƙe zaune ya ce ""Meye a cikin baƙar leda?""" """Ina kwana?"" Mutallab ya ce yana durƙushewa a saman ƙafarsa, yana duban Malam ɗin, Malam ya ce" """Ban kwana ba, mene a leda na ce maka wai? Kasan bana shiri da irin ledojin nan""" "Ya dinga kallon Aby, yana jin inama ya ce Mutallab Allah Ya yi maka albarka,inama ya ce Mutallab meke" "damunka? Ko sau ɗaya ne ya bashi rana irin ranar da kowanne ke farinciki da iyayensa, ya yi hira da shi ƙila abin da yake danƙare a zuciyarsa ya wareware ya samu sukuni ko yaya ne, ya numfasa ya ce ""Nama ne da kayan miyya"". ""Ko kai fa, idan kana haka ai lafiya lou zamu zauna da kai wallahi, ke ɗauki a sarrafa mana shi yanzu kin ji ko, sai ka basa kuɗi a siyo biredi"" ya zame ya zura hannunsa cikin aljihu ya ɗakko" "dubu biyu ya bawa Malam. Yana washe bakinsa ya ce ""Iyee farare har biyu?""" """Batun yarinyar Aby""" """Ka je ka ganta ko?"" Sai ya jinjina masa kai, ya miƙe tsaye kafin ya ce ""Ina da matsala, kar na dinga dukar" "musu yarinya""" "Aby ya ce ""Idan ka yi niya ka kashe ta kamar yadda ka kashe Diyna, ai na jima da sanin ɗan ta'adda na" "haifa, makami ne kawai baka fara ɗauka ba, ɗan'uwansa fir'auna yaro da zuciya a ƙeƙashe anya zaka" "wanye lafiya Muɗallabi?""" """Aby abin farinciki ne ka haifi ɗan'uwan fir'auna, ka yi mini duk bakin da za ka yi mini wallahi ko tsinewa" "Mutallab ka yi ba zan damu ba, duk masifar dana ɗakko tare zamu raba, idan ba ku yi cikina ba sai ku faɗa mini wanda suka, domin baku cancanta da zama iyayen Mutallab ba"" Ammo ta juyo ta kalle shi, idanunta ya wani irin sauyawa, Mutallab ya kafe Aby da idanu yana jiran jin me zai ce, gwara ya faɗa musu sai su ɗanɗani irin ɗacin da yake ji a ƙasan zuciyarsa. Baki a sake Aby ya ce ""Mu kake faɗawa" "wannan muna nan maganganun?""" """Nima ni kake faɗawa ɗan'uwan fir'auna ne ni, Aby kar ka fara sawa ina dana sanin zama a cikin Ammo," "na ji daman tun ina ciki na sauya mahaifa zuwa na wata uwa daban...,"" kafin ya ƙarasa Ammo ta ɗauke shi da mari, ganin yaƙi matsawa ta ɗakko itace ta fara maka masa, ta mance da raunin kan shi, shi kuma ko motsi bai yi ba, ganin jini na zuba a kan nasa ya saka ta ajjiye itacen ta shige ɗaki tana goge hawayen idanunta, ganin yadda yake muzurai da manyan idanunsa ya saka Aby ya ƙi tankawa ya yi masa shiru ya ce ""Ke Zaituna ɗauki ki dafa naman nan, yanzu zan fita nemo biredi"" ta ce ""To Malam"" ya juya ya kalli yaran da suke zaune sun kafe shi da idanu ya ce ""Zaku tashi daga nan ko sai na cicci gidanku?"" jikinsu na" "rawa suka tarwatse daga taskar gidan, ya fice yana yin sababi kamar zai ari baki." "Mutallab yana zaune tsakar gidan, jinin kansa har ya gaji da ɗiga ya fara bushewa, aka gama dafa naman" "da komai aka rarraba yaran sai murna suke yaushe rabon da suci nama? Mama Zaituna kamar zata cire yatsun hannu haka ta dinga yi. Malam ya kammala ci ya yi gyatsa ya kalli MUTALLAB kan shi ke a ƙasa kamar wani basarake ya ce ""Nama ya yi daɗi, ga zaƙi madalla ina ka samu nama haka da yawa?"" Aby ya" "ce ""Muɗallabi magana nake kana kunnen uwar shegu dani?""" """Point of correction Aby, Mai dawa sunana, nama kuma a dawa na samu shi"" ya ce yana murza hular" "saƙin dake kan shi, hannunsa ɗaya riƙe da kokara. Aby was shocked, ya ce ""Wacce dawar? Ba naman" "kasuwa bane?""" "Mai dawa ya jinjina kai yana miƙewa tsaye tare da cakewa ya ɗaɗɗage girarsa biyun ya ce ""Naman maciji," "da Gafiya ne"" yana faɗin hakan ya fice ya bar musu gidan, Aby ya juya ya kalli Mama Zaituna itama ta" "kalla shi, a kusan tare suka ruga da gudu zuwa bakin rariya, suka dinga sheƙa amai kamar zasu fitar da" "kayan cikinsu, tun suna yi da ƙarfinsu har jikinsu ya yi sanyi. Sa'adah data fito daga ɗaki domin yin wanka" "ta kalli yadda Malam da Mama Zaituna suna zube a ƙasa suna mayar da numfashi, Sa'adah ta juya ta kalli ƙanwarta Ikram ta ce ""Ikram mene ya same su?""" """Na'am da Mutallab ya kawo ne ya ce musu na maciji ne da Gafiya""" """Auzubillahi...,"" sai kuma Sa'adah ta fashe da dariya, ta durƙusa tana riƙe ciki tare da yarfe hannunta" "tana faɗin ""wayyo Allah cikina, daga cin naman sai amai kenan? Ke Ikram naman ba daɗi ne?""" """Akwai daɗi sosai, laaa kinga Malam yana gudawa"" Ikram ta ce tana nuna Aby da yatsa, Sa'adah ta juya," "exactly; kamar yadda Ikram ta ce gudawa ce ta kwacewa Aby ya numfasa da ƙyar ya ce ""Zo zo nan" "Sa'adah taimake ni, zayo yana bina naman maciji azzalumin yaron nan ya bamu, ban yaf. ,"" Sa'adah ta yi saurin cewa ""A'a Malam, irin bakin da kake yi masa ne ya fara tasiri gashi nan ka fara gani, don Allah ka yi haƙuri kar ka furta wata magana bayan wannan"" ta taimaka masa ya tashi,ya nufi banɗaki yana shiga Sa'adah ta kwanta har da birgima saboda da dariya Ikram ma ta dinga dariya tana buga bokici Sa'adah data juya ta kalli Mama Zaituna a ƙasa tana numfashi sai ta sake fashewa da dariya ta ce" """Naman maciji, gudawa wayyo ni Sa'adah""." "Yammacin ranar Mutallab ya ji zuciyarsa na jan shi zuwa gare ta, kawai dai surutun yake son ji a cikin" "kunnuwansa. Ya juya ya kalli Kimiyya ya ɗan yi gyaran murya, Kimiyya ya ce ""Maza suna ganin miskilancinsa a wajanka, ina ga mace Please?""" """Kamarya?"" Mutallab ya ce yana sakkowa daga kan tudun da suke zaune, yana ɗan ya motsa fuska yana" "jin shi duk a takure kwana biyu ya ɗan saba da shiga dawa cikin jeji. Kimiyya ma ya sakko ya ce ""Kamar" "yadda ka ji, kana da ɗabi'ar shari'a da jijji da kai, a yi magana sai ka yi kamar baka ji ba"" yana ɗan bubbuɗe idanu tare da ja da baya ya ce ""Ni? Ni ɗin?""" """You, You ɗin. Ka sani ai idan ma haka ne ko akasin hakan""" """Lallai"" Mutallab ya ce, yana jinjina kansa, da gaske bai ga wani shari'a ba bai san ya ake yin ta ba." "Juyawa sukai suka fara tafiya kimiyyar ya ce""Akwai wata sister ta, Allah ya ɗora son wani bawan Allah to irin halinku ɗaya ne, yana da miskilanci,tana shan wahala sosai kasan ance miskilin mutum yafi mahaukaci ban haushi, itama kuma ta nace ka san halin soyayya ai"" da rashin fahimta ya ce ""A'a""" "Mutallab ya ce kimiyya ya yi dariya ya ce ""Lokaci zaka santa ai"" sun yi nisa a tafiya Mutallab nata tunanin" "abin da zai cewa Kimiyya, a hankali ya furzar da iska daga cikin bakinsa ta fidda hucin zafi a nutse ya ce ""Aure take so su yi kenan?"". ""E mana, he loves him so much. Ba irin nacin da ba'a yi ma da faɗa amma ta" "nace daga nan fahimci soyayya ƙaddara ce, halitta ce a zuciya sai aka barta""" """Sunansa fa"" Mutallab ya buƙata yana saka yatsa ɗaya a tsakiyar goshinsa a hankali yake murzawa ya" "zubawa gefe guda ido, suna cigaba da tafiya a haka. Kimiyya was so confuse, ya ce ""Me za ka yi da sunan kuma Moh?""" """To bar shi""" "Ya girgiza kai, ya zaro wayarsa a aljihu kiran farko ta ɗaga Kimiyya ya ce ""My dear how are you, ya kike" "ne?"" A can ɓangaren ta amsa shi, ya ɗora da cewa ""Yama sunan wannan ɗan wahalar? Saurayin naki?"" Ya tambaya tare da sauraren ta a fili ya ce ""Haysam"" sai kuma ya kashe wayar ya juya ya kalli Mutallab ya ce ""Wai Haysam sunansa ta ce, akwai wani abu ne Moh?"" Mutallab ya juya da rinannun idanunsa da lokaci ɗaya sukai ja, ya kalli Kimiyya dasu, sai bai ce masa komai ba. ""Ina faɗa maka sunan nasa fa, wai Haysam kamar wani sunan tsuntsu"" Mutallab ya sake juyawa ya kalli Kimiyya idanunsa a birkice ya ƙara yi masa shiru. Kimiyya ya cigaba da surutu, can yaga Moh ya dafe kansa yana furzar da iska ""Friend lafiya" "kake ne? Ko akwai wani abu?""" """Ƙalau"" Moh ya ce, sai kuma ya sanya hanyar inda za shi ya yi nisa da Kimiyya ya ce ""Mu haɗu dare ko" "safe ok?""" "Bai jira me Kimiyya zai ce ba ya yi tafiyarsa, Kimiyya ya girgiza kawai kawai yana jinjina miskilanci irin na" Mutallab ɗin. "***Baba Umaru na zaune a tsakar gida shi da matarsa suna tattaunawa, Jaanah na ɗaki ta yi shiru,tana" "tunanin ko dai ya fasa auren nata ne? Shi ya sa bai ƙara zuwa inda take ba? A hankali ta miƙe zaune saboda kiran da aka yi mata, kanta ko ɗan kwali babu ta fito ta ce ""Gani Baba?"" Baba ya dube ta ya ce ""Ya ake ciki ne?"" A hankali ta ce ""To bai sake zuciya ba"" Baba ya numfasa ya ce ""Ko ke za ki gidan nasu kin ji lafiya?"" Ta yi saurin girgiza kai, Allah Ya yi wa Jaanah kunya ta kasa cewa komai. Baba na shirin magana yaga inuwar mutum tsaye a kan shi bata ko motsi, ya ɗan razana ya juyawa yana salati sai kuma" ya hangame bakinsa ganin wanda yake tsaye. Jaanah ta juya suka haɗa ido dashi ya yi tsaye a tsakar gidan hannunsa ɗaya riƙe da leda ɗayan kuma ba "komai sai zura shi da ya yi a cikin aljihun rigar ya kafe Jaanah da ido, gashinta sai motsi yake kasancewar tana da yalwar suma har gaban goshi, sun jima suna kallon juna kafin ta yi ƙoƙarin zame idanunta ba dan zuciyarta ta gaji da ganin idanunsa ba, ta ji nutsuwa ta saukar mata sai kuma kunya ta lulluɓe ta. Baba Umaru ya ce ""Ikon Allah, to haka ake zuwa gidan mutane ba ko sallama?"" Ya ce yana miƙewa tsaye tare" "da kallon Jaanah ya ce ""Shige ɗaki Jaanah""" """To"" ta miƙe ta nufi hanyar ɗakin gani ta yi Mutallab ya biyo bayanta ta ɗan tsaya shima ya tsaya cikin" "faɗa Baba ya ce ""Ya zaka bita ɗaki? Waje zaka koma""" "Mutallab, ya juya gabaɗaya zuwa inda baba yake suka kalli juna sai ya zame idanunsa ya kalli Jaanah" "dake wasa da yatsun hannunta ya ce ""Sai na yi me a waje? Wajanta na zo ai"". ""Daka zo wajanta sai ka bita ɗaki saboda hauka ake yi? Ko haukan naka ne ya motsa iyee? Ai na ji labarin dalilin haukan ake so a yi maka aure, kawai ka faɗo mini gida babu ko sallama, kuma ka bi yarinya cikin ɗaki bayan tsakanin mace da namiji na uku shaiɗan ne, idan ya zance kazo ka tsaya a waje yanzu zata fito"" ya ƙare maganar" cikin faɗa. """Wani abu ne zai faru idan na bita ɗakin? To ta fito wajan haka""" """Baka san mene zai iya faruwa ba kenan idan ka bita ɗakin, Jaanah ai ba namiji bace haka kawai zuciya ta" "ribace ka a kan ɗiyata? Ka je wajan yanzu zata fito""" "Mutallab ya ce ""Sai na yi me idan ta ribacen? Muje"" ya kalli Jaanah yana faɗin haka. ""Bari na sako hijabi" "to"" ya kafe ta da idanu, ta yi saurin juyar da kanta gefe ya koma gefe ya tsaya baba ya yi cikin ɗaki ganin Mutallab bai da niyyar fita daga cikin gidan nasa. Hijabin ta sako ta dawo tsakar gidan tana murmushi ta tsaya sai kuma ta durƙusa ta ce ""Ina yini?"" Ya yi shiru, ya dinga kallon ta bai ce komai ba. Ta ce ""Ganina kazo yi? Nima da tunaninka na kwana a zuciyata Tahhb, ina fata ba sauya ra'ayinka ka yi a kan Jaanah ba ko?"" Hannunsa mai ɗauke da ledar ya miƙa mata ta saka hannu biyu ta amsa ta buɗe ciki, kamar wancan karan nama ne da gurasa amma wannan ta fasa mene kamar tsuntsu ne haka aka gashe shi ga fika" fikinsa nan. """Jaanah ƴar gatan mijinta, duk ni ɗaya ne Tahhb?"" Jin ya mata shiru ta sake cewa ""Ka zauna muci ko?"" Ta" "ce tana juyawa ta ɗakko faranti ta dawo tare da jan kujera ta zauna, ta juye gurasar a ciki da naman ta ce ""Ka zauna mu yi hira mana, daman tun safe ina ɗaki"" ya yi ƙiƙam sai kuma ya durƙusa daidai inda take," "har yana jiyo numfashinsa ta tura masa farantin naman ta ce ""Ci, ka rage mini"" ba shiri ta ɗauka ta fara ci" ta lumshe idanunta ta buɗe """Naman mene yau aka samu a dawa? Wannan bana gafiya bane""" """Ƴar shila"" ya ce yana duban yatsun ƙafarta duba na tsanaki, wanda data san me yake kallo data gudu" ɗaki ko ɓoye ƙafarta. Ya miƙe ya juya ya nufi hanyar waje """Tahhb, Tahhb ,"" Jaanah ta ce tana biyo shi da ɗan gudu ya tsaya ta ce ""To baka ce komai ba"" ya dube" ta sai kawai ya fice daga cikin gidan ya nufi hanyar nasu gidan wanda yake jin kamar ana masa farraƙu da zaman gidan iyayen nasa. "A tsakar gida ya samu Sa'adah ya zaune shima bayan ya ɗan kaɗe wajan ta ce ""Na Ammo daga ina" "haka?"" Bai kalle ta ba ya ce ""Kin aike ni ne Yaya?"" Ta ce ""Ah ah, na dai damu ne ban ganka ba, babu Bafullatana ba Anty Hameeda ba Muneeberh gidan ya yi mini faɗi, kai kuma ba'a hirar abin arziƙi da kai ko zaman gidan ba ka yi"" ya mata shiru ta ce ""Abin da ka yi baka kyauta ba, Na Ammo iyaye ba abin wasa bane kullum albarkar su muke nema, ba zamu taɓa biyansu abin da suka yi mana a gidan duniya ba, ko zaka goya Ammo ko Malam a baya tun daga nan garin Kano, unguwar Birget ka kai shi Makka a ƙasa wallahi baka biya ladan haihuwar da suka yi maka ba, rayuwa na tattare da ƙalubale mu yi musu uzuri" "don Allah""" """To, wa'azi kike mini kenan Yaya?"" Ya ce yana naɗe ƙafa tare da yin zaman da ya saba na tanƙwashe" "ƙafafuwansa waje guda ya ɗora hannunsa a saman cinyoyi. Sa'adah ta ce ""Wace ni tinatarwa ce kawai na yi maka ita""" """Uhmm""." """Ka je ka basu haƙuri har Mama Zaituna, a dinga sanyaya ruwan sanyi ana shan ragowar ruwan alwalar" "sallar asar Tayo"" ya yi kicin-kicin da fuska can ya miƙe ya nufi wajan Malam ya ɗaga balulen ya hango Aby ƙwance sai ya shiga ya durƙusa,ya jima a zaune kafin ya ce ""Aby"" malam ya ɗago kai ganin Mutallab ya saka ya yi shiru. ""Na yi laifi ka yafe mini Aby, ka daina aibata ƙuruciyata baka san ya girmana zai kasance ba, ka yafe mini"" Malam ya yunƙura ya ce ""Ni wai? Na yafe maka na shiga banɗaki ba adadi, Allah Ya isa Allah Ya isa abin da ka yi mini zaka gani"" Mutallab ya miƙe ya fita rai ɓace yana zuwa ƙofar" gida yaga Kimiyya tsaye. Sai kuma ya juya zuwa ɗakin zaure. "Kimiyya ya dinga kallon ɗakin da Mutallab ke rayuwa ya miƙa hannu zai taɓa wani buzu ya ji ya ce ""A'a," "ba ruwana""" """Gani to, amma wannan ɗakin na lafiya ne haka Mutallab? Waɗannan abubuwan fa? Wancan ɓangaren" "dana kayan fulani kala-kala fa shi na mene?""" """Quiet, sunan ma?""" """Haysam""" """To yana da aure ai, har ma da raya wallahi""." "Da mamaki Kimiyya ya kalli Mutallab kafin ya ce ""Tab, bangane ma'anar yana da aure ba? Ya aka yi ka" "sani?"" Banza Mutallab ya yi masa yana cigaba da abin da yake yi. Kafin ya ce ""Za ta yi auren nasa, ita ƴar" "uwar taka"". ""Ka ce yana da aure har da yara kuma ka ce zata iya auren nasa ban fahimta ba""" """E, akwai rabo a tsakani da kuma ƙalubale haka alƙalumma suka nuna"" Kimiyya ya numfasa ya ji ya fara" "tsoron Mutallab a ran shi, amma soyayyarsa ƙara yawa take a zuciyarsa ""Tsafi kake yi kenan Mutallab, ba" "kyau fa""" """Jini ka gani ko jarirai""" """Bokanci kenan? Kimiyya ya faɗa a raunace cike da damuwa don bai ji daɗin hakan ba. ""Zan baka sirri" "daga cikin Alkur'ani ka bata ta yi da zuciya ɗaya, sirrin jefa soyayya a zuciyar wanda kake tsananin so, wallahi wallahi ko waye a duniya muddin ka yi masa sai ya ji babu wanda yake so a duniya sai kai, amma kar a yi domin cutar da wani, Mutallab bai lamunta ba, wannan sirrin ga wanda suke cikin jarrabawar" "soyayya ne ok"" Kimiyya ya jinjina kai ya ce ""To zan faɗa mata""" """Mene sirrin?"" Kimiyya da ya buƙata, har lokacin kuma Mutallab bai haɗa idanu da Kimiyya ba tun" shigowarsu ɗakin. """cikin dare zata tashi ta yi lafila raka'a biyu, ta yi miftahul amàl, sai ta karanci ummul kitahhb, fatiha" "keman ƙafa 113, ana fara aikin ranar Lahadi, Litinin, Talata, kwana uku ake yi. Bayan ta yi sallah tana kallon alƙabila za ta yi karatun, sai kuma ta yi woridin Ya-ƙahharu ƙafa 113 shima sai salatin fatih 113 shima, shine abin da za ta yi washegari da safe ta yi sadaƙa ta wainar gero""" "Kimiyya kallon Mutallab kawai yake yi kana ya ce ""To mene sadaƙar?"". ""Ka jira ta yi""" """Amma ba kyau""" """Na sani, ai ba'a shiga dawa don ƙarya ka kalli komai ka yi shiru. Me ya sa kake wasa da sallah?""" """Ni kuma?""" """E, kai ɗin sallah bata dame ka ba, zan yi faɗa abubuwa da yawa game da kai sallar ce mai muhimmaci ka" "gyara ka ji"" yana cewa haka ya miƙe ya fita daga cikin ɗakin, kunya ta kama Kimiyya da gaske bai damu da yin sallah a kan lokaci ba. Bayan sun fito sun waje ya ce ""Monday ne zaka fara zuwa makaranta, are you ready?"" Mutallab ya jinjina kai, suka koma can waje guda suka zaune Kimiyya kaɗai ke yi masa shiri shi dai jinjina kai kawai yake domin ji ya yi bakinsa na yi masa ciwo. Yana daga inda suke ya hango Sa'adah na zance ganin tana ta murmushi saurayin na dariya kamar ba namiji ba ya ji ransa ya ɓaci sosai," yana kuma nan ya hango wasu masa biyu da Malam Umaru da Aby ya taɓe bakinsa. Jaanah. "Sanda ta biyo bayan Mutallab tana faɗin ""Tahhb, Tahhb "" Ta faɗa ne a lokacin ba tare da tunanin zai" "tsaya ɗin ba, ita kuma zuriyarta ba zata jure ba, ta sauke ajjiyar zuciya tana dafe ƙirji ganin ya tsaya, ta ji kamar ta ƙarasa gabansa ta kama hannunsa ta ɗora a ƙirjinta ko hakan zai saka ya ji yadda zuciyarta ke bugawa, tana bugawa saboda shi, tana bugawa saboda soyayyarsa, tana bugawa ne saboda yadda ya yi tsaye a gabanta. Ta langwaɓar da kan ta ta ce ""To baka ce komai ba?"" Yadda ya juyo ya duba ta, sai ya ji zuciyarta na tarwatsewa ƙirjinta na buɗewa, ta yi waiting to hear from him sai kawai taga ya fice. Jaanah ta fi bayan Mutallab da kallo, ta sulale ƙasa a nan inda take, ta jima kafin ta shiga gida da tunanin" Mutallab maƙale a zuriyarta. "Duk motsin da take yi shi take ji yana mata yawo a tsokar ƙirjinta. ""Jaanah"" Baba ya kira sunanta ta amsa" "tana miƙewa zaune ya ce ""An saka ranar ɗaurin auren ku, gobe da maraice a kawo kuɗin sadaki yanzu mahaifin Muɗallabi""" """To Baba"" ta ce a raunace hawaye na bin idanunta ya ce ""kukan na mene kuma Zarah?""" """Baba me ya sa kake son aurar dani ne?""" "Zama ya yi yana kwantar da muryarsa ya ce ""Ba komai Jaanah, rayuwa ce ta yi tsada tun bayan rasuwar" "iyayenki nake ta fama yanzu ƙarfina ya ƙare idan na aurar dake wani nauyin zai sauka a kaina"" tana kuka ta ce ""Shekaruna 14 baba, aurar dani shine mafita? Shikenan na amince amma ina dukiyar da aka mutu aka bar mini?"" Jikin Baba na rawa ya ce ""Wacce dukiya? Waya faɗa miki na sake jin wannan maganar sai ranki ya yi mugun ɓaci Jaanah"" fashewa ta yi da kuka sosai, tabi Baba da kallo har ya fita waje. Ta yi kuka" son ranta a lokacin an yi sallar magariba ta saka hijabi ta saka takalmi ta nufi inda zata samu Mutallab. "Yana zaune a waje kamar koyaushe shi kaɗai ya hango ta, ya yi ta kallon ta yana mamakin ina zata? Sai" "yaga ta nufo shi, tana zuwa ta durƙushewa a gefen ƙafafuwansa ta fashe da kuka mai raunata zuciya. Ya yi shiru don bai san me zai ce mata ba, ganin kukan ba mai ƙarewa bane ya saka ƙafa ya zungure ta, yana miƙewa tsaye ta miƙe tana kare fuskarta ya dinga kallon ko'ina yaga ba mutane ya yi ƙasa da murya ya ce" """Mee?""" """Baba ya ce an kawo sadakin auren mu ɗazo"" sai ta kuma fashe masa da kuka jikinta har rawa yake, ya" "bubbuɗe idanunsa yana dire kokarar hannunsa a ƙasa, bunjimar rigar farautar dake jikinsa na kaɗawa." """To, shi ne na kuka?""" """Na tuna abin da malam ya ce ne, idan an yi musamman ƙanan yara masu ƙarancin shekaru wai ana" "samun yoyon fitsari idan akai tarayya tunda shekarun basu kai ba, kuma idan yarinya ta samu ciki zata iya mutuwa, kaga shekaruna 14 fa""" "Ya bubbuɗe manyan idanunsa da tsoro shima ya ce ""To! Mun shiga uku, kar mu yi yoyon fitsari to"" ya" faɗa cikin nutsuwa da alamun gaskiya cikin maganarsa. """To ai kai namiji ne, ni ce zan samu cikin ai kuma ni ce ƙarama""" "Ya ce ""Ni kuma nine mai yin cikin ai, shekaruna 14 nima""" """Innalillahi yaya za mu yi, ashe da gaske malamin ƙawa'idi yake?"" Ta sake fashewa da kuka tana girgiza" "kai, ya matsa dab da ita ganin kamar zata fita hayyacinta ga dare ya yi, ya duƙa fuskarsa daidai tata ya ce" """Jaaa. """ "Ya kira sunan nata, ta ce ""Jaanah ne sunan ai"" ""Oh... Da gaske ban isa bawa mace ciki ba, ni tsoro nake ji" "kije gida ba abin da zai faru ko?""" """To ba za ka yi mini cikin ba? Ƙawayena sun ce idan aka biya sadaki wai amarya na biya""" "Ya dinga kallon ta, da gaske suka su biyun shekarunsu sha huɗu, amma ƙuruciyar Jaanah ta girmama. Ya" "numfasha ya ce ""To za ki biya ni sadakin kenan yanzu?"" Taƙi magana ta dinga kuka tana diddire masa ƙafa ya sake matsawa kamar zai kama hannunta sai ya fasa, bai tsammata ba yaga ta ɗora kanta a gefen ƙirjinsa ta fashe da wani irin raunataccen kuka, bai ce mata uffan ba ta dinga kuka hawayenta na jiƙa masa riga, da gaske yana son ce mata wani abu amma ba zai iya ba. Ta janye kanta a hankali ta ce ""Zan" "je gida""" """Hmmm"" ya ce tana kallonsa sai ta juya tana share hawayen idanunta shima ya juya mata baya zai tafi" "gida, ƙarar sautin muryarta ya ji a kunnensa, tana kiran sunansa, ya ji kiran ya sauka har ƙasan zuciyarsa," "da sauri ya juyo wani irin sandarewa Mutallab ya yi ganin yadda Jaanah ke salati tare da ihu wuta na cin jikinta, cin bana wasa ba, wuta ce wacce kamar gas ya kama haka take ci a jikin Jaanah." "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 26: Who are you" Paid book #500 Pay before you read 08164069385 Follow on Arewabooks Not edited "Jaanah was screaming, tana ihu da salati lokaci guda tare da kiran sunan Mutallab,wutar na ƙara cin" "naman jikinta. Mutallab ya yi cak idan akwai abin da ya tsayar da tunaninsa waje guda, ƙwaƙwalwata ta daina moving ƙirjinsa ta daina bugawa shine ganin Jaaanah na ci a cikin wutar, and he can't do anything to help her. Wani irin mazari jikinsa yake kamar ana kaɗa masa ƙahon gangi cikin azama ya ƙarasa wajanta daidai lokacin ya daina jin sautin fitar muryarta, yana ƙoƙarin cikin wutar ya bata kariya da gangar jikinsa ya ji an yi saurin janye shi. ""Ina zaka? Cikin wutar zaka shiga? Kar a kwashi gawa biyu domin ita kam ta riga data rasu sai haƙuri"" Mutallab ya juya ya zubawa Kimiyya idanunsa da suka koma launin rawa-rawa kamar bana mutum ba, yadda ƙirjinsa ke rawa haka haka gangara jikinsa ya kasa furta komai a lokacin mutane har sun fara taruwa, maganar ta isa kunnen Baba Umaru sai gashi da sauri yana" kururuwa. """Ya kashe mini yarinya, ya kashe ta jama'a a taimaka mini kaico, wayyo Zaraha'una wayyo Jaanah"" kuka" "yake da ƙarfinsa mutane suna riƙe shi, lokacin wutar ta mutu dalilin ruwan da aka sheƙa mata, sai dai Jaanah rai ya yi halinsa, she died with smile on her. Baba ya ƙanƙame gawar Jaanah da jini ke zuba wajan wutar da ta ci ""Allah Ya ɗaiɗaitaka in sha Allah a rayuwa ba zakaga daidai ba, ba zaka taɓa yin farinciki ba, ka kashe mini marainiyyar Allah"" ya girgiza kai sai ya kuma rushewa da kuka ya ce ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, wanne irin zalunci ne wannan? Wanne irin rashin imani ne, lafiyar Allah yarinya ta fito ashe wajanka ta zo shine ka kashe ta kamar yadda ka kashe matar da za'a aura maka ta farko? Kenan yanzu" "duk ƴan'matan unguwar nan sai ka kashe su?""" """A'a baba bafa shi ya kashe ta ba, tsautsayi ne kuma lokacinta ne ya yi kamar kowanne mumuni"" Kimiyya" "ya faɗa a raunace idanunsa kuma akan Mutallab ganin jikinsa har yanzu rawa yake yi, ya kafe gawar Jaanah da idanunsa." """Kenan ƙarya zan yi masa? Kowa yana da labarin Diyna yadda ta babbake a cikin wuta a ranar da yaje" "wajanta, gashi yanzu ma a ranar da aka kawo kuɗin sadakin aurensa shi da Jaanah itama ta babbake a wuta, ya kashe har mata biyu daga cewa za'a aura masa su waye ya san gawarar gaba? Wallahi ran Jaanah ba zai taɓa tafiya a banza ba"" Ya sake rushewa da kuka ya ce ""Ashe shi ya sa ɗazo da yammaci ya je mana har cikin gida yana ƙoƙarin bin bayanta zuwa cikin ɗaki, bamu sani ba yana shirya yadda zai kashe ta ne, Malam Abdullahi ya yi haihuwar asara ya haifi tsinanne"". Ran kimiyya a ɓace ya ce ""Malam ko ƴan'sanda zaka kira dole sai bincike ya nuna musu shaidar gisan da ya yi wa Jaanah, kuma they find" "nothing, actually nothing, mu ɗauki ƙaddara""" """Dame yake taƙama da zai dinga kashe rayukan raya mata daka ance za'a aura masa su? Allah ya isa na" "wallahi"" cewar Baba Umaru." "Mutallab ƙafafuwansa na rawa ya durƙushe dab da inda Baba Umaru yake zaune, ya saka hannuna yana" "shirin riƙe hannun Jaanah Baba Umaru ya ce ""Karka sake ka taɓa mini gawar yarinya bayan ka kashe ta"" Moh, ya ɗaga idanuna ya kalli Baba Umaru dasu cikin sauri Baba Umaru ya ɗauke kai ya kasa cewa komai," "Mutallab ya damƙe hannun Jaanah muryarsa na rawa tana fita da ƙyar ya furta ""Na faɗa kada a aura mini ke, ni ina da taɓin hankali ina da matsalar ciwon hauka. ,"" ya yi shiru ya sauke ɓoyayyiyar ajiyar" "zuciya ta cikin ƙirjinsa ""Da gaske ni na kashe ta ban sani ba, sai dai ba zan iya kashe Jannaa ba, ki yafe mini na kasa ceton ki na kasa, na kasa kamar ɗayar"" ya kasa cigaba da kukan lokacin Aby ya zo hankali tashe, ya dinga ɗauke Mutallab da maruka babu adadi babu kalar zagin da bai yi masa ba sai wanda ya" manta. """Ko shakku ba zan yi ba kai ne ka kashe musu ƴa, irin mutuwa ɗaya Jaanah da Diyna suka yi, ni dai ka" "zame mini masifa a cikin rayuwata ka cutar da zuciyata ka saka mini rauni da giɓin da ba zai taɓa gogewa ba"" sai kuma ya fashe da kuka jin yadda ake cewa Mutallab Ɗan'malam ya kashe Jaanah da Diyna. Har aka ɗauke gawar Jaanah Mutallab ya kasa motsawa, Kimiyya nata bashi haƙuri da ban baki. Suna nan sai kuma jiniyar motar ƴan'sanda ta karaɗe wajan. A ruɗe kimiyya ya ce ""Mutallab tashi ka gudu, police ne ka tafi kar su kama ka"" amma ko gezau bai ba har suka ƙarasu wajan suka zagaye su a gun. "" Heee, Who" "is Mutallab?""" """Gani"" Mutallab ya ce." """Arrest him officer""" """Wallahi bai kashe kuwa ba, kar ku tafi da shi don Allah, Please let go of him, wallahi bai kashe ta ba ina" "da wajan sanda abin ya faru he is innocent"" ko ta kan kimiyya basu bi ba, su kama Mutallab zuwa cikin mota, tare da jan motar da gudu." "Shi ba zai iya cewa ga adadin lokacin daya shafe cikin wajan da aka saka shi ba, yana takure ya yi shiru" "tare da tunani fal a cikin ransa, mutuwar Jaanah ta tsaya masa a zuciya, tun ihun da ta yi na farko tare da sautin daya fito da kiran sunansa ya ji wani abu ya tokare masa maƙoshi, ya tsaya masa a ƙirji ya haɗu da ciwon dake wajan na rasuwar Muneeberh suka tattaro tare da zame masa wani tabo, tabon daya gino a zuciyar kamar ɗigar dalma a fata wanda ba zai taɓa gogewa ba da wannan raɗaɗin da ɗacin zai wanzu a duniya. Ya ji tsoro da shakkar sake haɗa idanu da kowacce ɗiya mace a duniya. Yana durƙushen aka buɗe" "ƙofa, bai ɗago ba kuma motsa ba wani ya ce ""Sir wannan shine wanda ake tuhuma""" """Wanda ya kashe ƴan'mata har biyu? Me suka yi masa? A wajan bada statement me aka ce?"" Officer ya" "ce ""Sir, yarinyar daya kashe ta farko sunanta Diyna, ita ce yarinyar da mahaifinsa ya bashi umarni ya je ya gano ta idan ta yi masa a ɗaura musu aure, a ranar da ya je gidansu Diyna a ranar ta mutu cikin dare ta mutu tana ihu tare da kiran sunan Mutallab, wanda yake bada tabbacin shine ya kashe ta. Yarinya ta biyu kuma ita ce Jaanah, bayan rasuwar Diyna mahaifin Mutallab ya sake bashi umarni ya je ya gano ƴar wajan Malam Umaru mai suna Jaanah, ya je har ya ce ya amince da auren, a ranar da aka kai sadakin auren Jaanah ta fito daga gidansu cikin dare zuwa wajan Mutallab a can inda yake zama, ba'a san abin da ya faru sai gani akai wuta tana ci a jikin Jaanah shi kuma Mutallab ɗin na tsaye a wajan yaƙi taimakon ta," "duk da irin kiran sunansa da yarinyar take yi matsayin ya zo ya taimaka mata""" "Dig Johar ya jinjina kai ya ce ""Ya kashe mata biyu kenan? A lokacin da ake shirin aura masa su, baya son" "auren ne ko wani laifi suka yi masa wanda suka cancanci ya kashe su? Hakan yana cewa duk macen da akai yunƙurin aura masa zai kashe ta ne kafin auren?"" Dig Johar ya ƙare maganar cikin ɗacin zuciya musamman idan ya sake kallon Mutallab sai ya ji kamar duniyarsa zata jirkice ne. Officer ɗin ya rusuna" "cike da girmamawa ya ce ""Sir, a record ma kamar an taɓa kawo shi cikin wajan na""" """Na sani"" cewar Dig Johar. Kana ya numfasa ya ja kujera ya zauna idanunsa akan Mutallab da yaƙi ɗago" "kansa, balle ya kalle su Dig Johar ya ce ""Kuma lafiya yake baya shaye-shaye? An tabbatar?"" Officer ya ce ""Binciken da muka yi ya nuna baya shaye-shaye, kawai dai shi mafauri ne yana shiga jeji ya yi abin da zai ya kamo naman dawa"". ""Good, lafiyar ƙwaƙwalwa fa?"" Officer ya ce ""Sir ban sani ba"" Dig Johar ya ɗan yi murmushi iya laɓɓansa kana ya ce" """Mutallab"" a hankali Mutallab ya ɗago kai ya kalli Dig Johar, kallo ɗaya ya ɗauke kai. ""Mene matsalarka" "da matan da kake kashewa?"". Mutallab ya yi shiru, domin bashi da abin faɗa da gaske ""Yin shiru ba shine mafita ba, ka bani haɗin kai mu yi magana kai yaro ne shi ya saka nake tauysawa ƙuruciyarka""" """Bani da matsala"" Dig Johar, ya ji muryar Mutallab ta sauka a cikin kunnuwansa a kumbure cikin rashin" "tsoro kafin ya yi magana ya sake ji ya ce ""Idan maganar kisa ne, e da gaske na kashe su a shirya kashe ni domin sauƙaƙa mini zaman wajan nan, Moh ya kashe Diyna da Jaanah tabbas"" baki buɗe Dig Johar ya ce ""Kana cikin hankalinka kuwa? Ka kashe su kace fa?"" Mutallab ya ɗago rinannun idanunsa kamar za su zazzago waje ya ce ""Gaskiyar kenan, ko gobe aka nema maƙala mini wata macen za'a wayi gari babu ita a" "duniya""" """Ko yana da matsalar ƙwaƙwalwa ne?"" Dig Johar ya buƙata yana juyawa tare da kallon officer." """Sir, sai dai a yi bincike a family nasa, akwai wata ƴar'uwarsa a nan waje""" """A binciko yanzu, immediately""" "Bayan fitar Officer, Dig Johar ya yi shiru yana ta kallon Mutallab babu jimawa kuma officer ya dawo ya ce" """Sir, Mutallab yana da taɓin hankali, domin har takardar zuwa Dawanau likita ya bashi, kuma dai ba'a shari'a da mahaukaci"" kafin Dig ya yi magana Mutallab ya ce ""Ƙarya ake yi, lafiyar tunanina lau, ba mahaukaci bane ni, na kuma kashe Diyna da Jaanah tabbas, na kashe su da hannuna ƙwarai basa raye tabbas haka ne"" Dig ya miƙe tsaye ganin jikin Mutallab na rawa ya kalli Officer ya ce ""Ga alama nan ma ai ya nuna, kaje waje ina zuwa"" Officer ya jinjina kai ya yi waje, Dig ya durƙusa gaban Mutallab ya yi ƙasa da" muryar ya fara masa magana. "Tana tsaye a reception idanunta ya kumbura saboda kuka ta ji an ce ""Yaya"" ta yi sauri ɗago kanta," "hannunsa ta riƙe ta ce ""Allahamdulilah na Ammo sun sake ka, ma sha Allah""" "Ya jinjina mata kai, sai kuma ya yi shiru yana kallon Sa'adah bai magana ba yana ji ta kama hannunta" "suka fice, a bakin gate na shiga state cid ɗin suka ƙara cin karo da Prof ya dinga kallon Mutallab, 2 times yana ganin yaron nan a wajan nan wanne irin babban mai laifi ne shi? Ya ji yaron bai masa a zuciyarsa baya jin tsanar mutane amma kana ganinsa ka san bashi da cikakkar tarbiyya. Ya yi saurin shigewa ciki, Mutallab kuma fuska kamar narkakken hadari haka ya haɗe fuska idanunsa na shigewa ciki sai ɗaɗɗaga kafaɗa yake yana jin Sa'adah na cewa ""In sha Allah ka yi zuwan ƙarshe wajan nan, babu ƙaddara da zata" "sake sawa kazo, babu bincike ba komai kawai a kama ka? Haka ake yi daman?"" Shi dai bai kulata ba, har" suka shiga napep ya kifa kansa a ƙarfen jikin napep ɗin yana fisgar numfashi can ya ɗago ya kalli Sa'adah da ƙyar ya iya juya bakinsa ya ce """Yaya"" ta kalle shi ta ce ""Autan Ammo ya aka yi? Sun dake ka ne? Mene ya faru?"" Ya jujjuya idanunsa ya" "ce ""Jaaanah "" Ya yi shiru sunan ma ya tsaya masa a ƙirji Sa'adah ta ce ""Sai dai addu'a kwanan Jaanah" "biyu a gidanta na gaskiya, ka yi mata addu'a tare neman gafara wajan Ubangiji""" """Hmmm"" ya ce daga nan bai sake furta ko a ba, duk da jan shi da surutu da Sa'adah ke yi har suka isa" "gida. Sa'adah ce ta fara yin sallama ta shiga, lokacin Malam yana yin alwala hannunsa riƙe da buta da wani zabgegen carbi a gefe, kafin ya amsa Mama Zaituna ta fito tana cewa ""Basu bari kin ganshi ba ko? Kema dai Sa'adah iska na wahalar da kayan kara, sun riƙe shi kenan fa idan ba sa'a akayi ba sai dai mu ɗauki gawa"" Sa'adah ta yi murmushi ta ce ""Mama kenan, Allah baya nuna mana wannan ranar ba, tare" "muke da shi ma"" da sauri malam ya miƙe tsaye yana faɗin ""Shi wa?"" Ta ce ""Mutallab, Malam""" """Su ƴan'sandan wiwi suke sha da suka sake shi?"" Sa'adah ta ce ""To dai sun sako shi, da kuma yana da laifi" "ai ba za su yi gaggawar hakan ba"" Malam zai yi magana ya fasa ganin wanda ke tsaye ya dinga kallonsa ya kasa cewa komai. Shi kuma ya fesar da iska daga cikin bakinsa ya ce ""Sannu Aby"" tsaki ya yi tare da yin waje bai amsa gaisuwar Mutallab ɗin ba, shi kuma ya yi tsaye ya kasa shiga ɗakin Ammo, ya jima a nan sai kawai ya ɗauki buta ya zuba ruwa ya yi waje jin ana cewa a daidaita sahu. Mama Zaituna ta shige" ɗaki "Sa'adah ta girgiza kai ta ce ""To shi malam tunaninsa yi wa Mutallab aure shi ne mafita? Don Allah Ammo" "shekarar Tayo nawa a duniya, anya baku shiga cikin lamarin Ubangiji ba? Me ya ɗauka a duniyar mema ya sani da ɗan ƙaramin yaron da ya kamata ace yana ƙarƙashin kulawarku wai shine kuke tunanin yi masa aure? A wannan zamanin masu hankali ma ya suka ƙare da lamarin aure balle Mutallab? Haba don" "Allah""" "Ammo ta ce ""Wa'azi kenan kike mini Sa'adah?""" """Nina isa Ammo?""" """To sai ki bari idan mahaifin naku ya shigo ki sanar da shi kin gane ko? Bana buƙatar jin wannan magana" "ki kiyaye"" a sanyaya Sa'adah ta ce ""In sha Allah, amma zan sanar da Anty Hameeda halin da ake ciki Ammo""" """Ki ce mata me? Ubanku na cin zalin ɗan'uwanku? Ko ubanku na shirin aurar da ɗansa? Ko ɗan'uwanku" "ya kashe mata har biyu? Me za ki faɗa mata daga ciki? Riƙe shin da hukuma ta sake yi, ko batun taɓin hankalin nasa?"" Ta jero mata tambayar a raunace, Sa'adah ta kalli Ammo jin yadda muryarta ke yin rawa kafin ta ce ""Duk abin da ya kamata na faɗa masa zan sanar da ita"" Ammo ta ce ""Ban amince ba ko a kan idanuna ko a bayan idanuna idan kin san ni ce uwarki, tabbas ban amince ba"" ta ce ""Yadda kika ce haka za a yi, amma Ammo har a zuciyarki kina jin kun bawa Mutallab tarbiyya da kulawar daya kamata a bawa kowanne yaro? Kin san yadda tarbiyyar namiji take da wahala kuwa? Gwara ɗiya mace a koyaushe tana tare da iyayenta, Ubangiji yana cewa ƴaƴa kiwo ne a gare ku, lallai akwai watarana da zata saka ku dawo gare ni na tambayi yadda kuka gabatar da kiwon nan, ba haka ya dace a tarbiyanta da Tayo ba Ammo. Nifa ina ganin duk wani abu da miji zai kafa miki idan har zai saka tarbiyyar yaranki ta lalace za ki iya haƙura da gidan mijin ji koma gidan mahaifa ki riƙe abin da ubangiji ya ba ki da addu'ar Allah Ya raya" "miki su Ammo"" Sa'adah ta yi maganar kamar za ta yi kuka." "Ammo ta dinga kallon Sa'adah sai kuma ta ce ""Kin san me Sa'adah yau ya zama rana ta farko da ƙarshe" "da idan kina magana za ki dinga sako batun ba koma gidanmu ko wani abu, wallahi duk sanda kika sake sai kin san wacce ni, daga ranar kuma zan zare ki a cikin yaran dana shayar da nonona"" a gigice Sa'adah ta ce ""A'a ki yi mini rai Ammo, Allah Ya baki haƙuri ba zan sake ba"" tana kaiwa ƙarshen maganar ta miƙe" "ta bar ɗakin, tsintsiya ta ɗauka ta fara share tsakar gidan sauran yaran duk suna waje." "**Baba Umaru ne ya fito waje jin cewa ana sallama da shi, yana fitowa ya yi sak ganin Mutallab domin" "ya ɗauka baban mutum ne ko an zo yi masa ta'aziyya. Baba yana huci ya ce ""Bayan ka kashe mini ƴar ɗan'uwa mene ya kawo ka? Fatalwarta ka biyo sahu ko ajjiya ka bata wacce bamu sani ba?"" Mutallab ya yi, Baba ya ce ""Bar ƙofar gidana yanzu yanzu""" """Ka bani photon Jaanah"" shine abin da Mutallab ya ce bayan ya gama tattaro kalaman a cikin bakinsa ya" "ɗora su a harshe, fuskarsa fayau alamar har lokacin akwai alwala a tattare da shi. Takaici ya kama Baba wato bai ma zo da nufin bashi haƙuri ko yi masa ta'aziyya ba. ""Wani mugun abin za ka yi da photon wanda zai hana ruhinta kwanciya lafiya a kabari? Tsakanina da kai da uban naka Allah Ya isa, ba zan taɓa yafe muku ran yarinyata ba wallahi""" """Na ji na kashe Jaanah, kai kuma daka kashe babanta ba? Ka riƙe dukiyarta?""" """Ita Jaanar ta faɗa maka haka?"" Baba Umaru ya faɗa jikinsa na rawa, ya jujjuya yaga su kaɗai ne a wajan." """Bata faɗa mini ba, kawai haka ɗinne ka sani ka bani photon tun muna mu biyu""" """Shikenan ina zuwa""" "Bayan shigar baba gida, Mutallab ya zubawa last inda suka tsaya da Jaanah idanu yana jin ƙofofin gashin" "jikinsa na bubbuɗewa wani abu mai sanyi yana ratsa zuciyarsa yana sakko a jikin nasa, ya daɗe zaune kafin baba ya fito hannunta riƙe da photon Jaanah ya miƙawa Mutallab amsa ya yi ko baba bai kalla ba ya bar wajan. Duk inda ya gilma a unguwarsu sai yaga ana shigewa tare da bashi hanya, wasu ma sai su sauya hanya ko a dinga nuna shi da hannu yana zuwa ƙofar gida ya samu Kimiyya a tsaye, jingine a jikin mota yana sanye da ƙananun kaya kamar na ball masu kyau kansa da hula p.cap ya yi murmushi yana" miƙawa Mutallab hannu ya ce """How are you? Kana lafiya?""" """Lou"" Mutallab ya ce yana lumshe idanunsa ya buɗe akan kimiyya da yake cewa ""An kawo kuɗin auren" "sister jiya"" da rashin fahimta Mutallab ya bubbuɗe idanunsa. ""Haysam, sai gashi a gigice ya turo iyayensa to cut you short an saka rana ma wai ake cewa ko?"" Ya ɗaɗɗage girarsa biyun ya cure su waje guda sai" bai magana ba. "Kimiyya yana danna wayar hannunsa ya ce ""Gobe Monday sai school ka shirya?""" """Shhhh, na manta""" """Dame? Ba dai makarantar ba kake nufi ko buddy?"" Abin da Kimiyya bai taɓa gani ba shi ya gani a tattare" "da Mutallab yau, autar ta motsa ya kwakkwaɓe fuska da langwaɓar da kai ya ce ""Na ji ban so, gwara mini shiga dawa"" Kimiyya ya ce ""To kuka za ka yi kenan akan zuwa makaranta? Innalillahi shagwaɓa ka yi" "yanzu fa daman haka kake?""" """What?"" Mutallab ya ce yana tsuke fuska, domin bai gane ma'anar shagwaɓa ɗin ba. ""Idan kana son" "shiga dawa ko farauta ai ba wani abu bane, domin ba'a taɓa raba mutum da abin da zuciyarsa take so, haka Jeddah take yawan faɗa mini; mu gino akan cimma burinmu da tsayawa akan ra'ayinmu. Buddy" "ilimi shine mutum, mutum ba zai taɓa cika mai nagarta da kamala ba sai yana tare da ilimi""" """Kuɗi dai"" Mutallab ya ce" """E, da hakan ma. Amma idan kana da ilimi zaka samu duk abin da kake fatan samu, da ilimi ake zama" "shugaban ƙasa ko Gwamna, sanata ko ɗan majalisa, chairman ko kansila, ba'a taɓa ɗakko jahili ya shugabanni al'umma, ba'a taɓa iya sarrafa dukiya ba ilimi zuwa gaba ko aikin learner ka nema sai kana" "da secondary certificate za'a baka, ka shirya zuwa makaranta zan biyo mu tafi tare""" "Mutallab ya shafa sumar kansa bayan ya cire hular saƙin ya ce ""Uhmm ni fa. ,"" Kimiyya ya tare shi da" "faɗin ""Kai me?""" """Wai ana duka fa"" da wani irin mamaki Kimiyya ya dinga kallon Mutallab kafin ya ce ""Don Allah idan" "baka da lafiya ya kake yi? Kana kuka ko? Allah Ya sa babu mace balle ta rainaka wai duka?"" Nan da nan Mutallab ya haɗe fuska jin Kimiyya ya yi mentioned sunan mace a maganar tasu, har kuma Kimiyya ya gama maganar bai ƙara tanka shi ba, daman tilasta kansa yake wajan yin maganar, ya ce zai bashi waya saboda karatu ya ce baya so sam. Ya amshi Uniform da books da komai sukai sallama ya shiga cikin gida, lokacin duk suna ɗaki Malam kuma ya zauna a makaranta sai ƙarfe tara zasu tashi. Ɗakin Ammo ya shiga" tare da yin sallama cikin kwantar da murya ya ƙarasa ya zauna. """Barka da dare Ammo""" "Ta yi kamar bata ji ba, ya sake maimaitawa ta ce ""Yawwa"" ya fito da kuɗi ya bata, ta kalli kuɗin ta kalle" "shi ta ce ""A'a, Allah Ya amfana"" zai mayar aljihu Sa'adah ta ce ""Ni bani ina so, sai na ƙara a jarin" "tsamiyage da albishir da fara da iloka, wainar fulawa ma zan fara alamjirai na siya""" """Duka mene waɗannan ɗin Yaya?"" Ya yi maganar ba tare daya kalleta ba, ya tanƙwashe ƙafafuwansa" "yana dudduba kayan da Kimiyya ya bashi ta ce ""Abubuwan daɗi bari ka gani"" ta janyo masa bokici guda na kayan, fara ya dinga kallo yana keɓe bakinsa tsigar jikinsa na tashi, ta ɗakko farar zata bashi ya yi saurin ture bokicin ya tashi yana girgiza mata kai ta ce ""Ci ake yi fa?"" Ya zazzaro ido sai bai ce komai ba ta ce ""Na Ammo kana yin sallah kuwa? Addini dai shine mutum, da kuma shi mutum zai kwanta a kabari" "wallahi, kafin a duba ayukan bawa sai an fara duba sallah, idan sallah ta gyaru dukkan ayyuka sun gyaru""" """Ka furtani za ki yi Yaya?""" """Tuna maka kawai na yi"" ya haɗe fuska tamau har zai mata shiru sai ya ce ""Shi addinin a goshi ake" rubutawa? Idan zan yi sallah a gabanki zan dinga yi Yaya? Ki daina ba kyau shiga hurimin bawa da "Mahaliccinsa"" za ta yi magana ya duka musu ƙofa a fuska, Ammo ta girgiza kai kawai Sa'adah ta ce ""Mai baƙar zuciyar jaraba kenan""" ***Misalin biyu da rabi na dare ya yinda kowa ke kwance yana runtsawa kamar yadda ake cewa dare "mahutar bawa a nasu ɓangaren shine safiyarsu da lokacin daya kamata a ce sun tattauna. Babban parlo ne wanda ya gaji da tsaruwa an narka uwar dukiya kamar ba za'a mutu ba, tsari irin na luxury life ɗin nan. Tsakiyar parlon shiryayyen dinner ce ta musamman ga kayan fruits nau'in kayan lambu kala daban- daban. Yana ki shingiɗe cikin shiga ta alfarma hannunsa riƙe da cocktail glass cup, an zuba lemon Chapman Drinka ciki. A hankali ya sha lemon kaɗan ya zame daga bakinsa idanunsa zube akan wanda" yake gabansa ya yi murmushi ya ce. """Laaa, we have to look back na abubuwa da muka tsara muna tafiya muna duba bayanmu, shekaru" "huɗun nan kamar yau ne tunda mun ƙara samu ka yi nasara a zaɓan nan ka sake hawaye kujerar ɗan majalisa ai Allahamdulilah sai mu sauya taku"" ya ce yana sake kurɓar lemon. Wanda ake yi maganar shima lemon yake sha can ya nisa yana kallon wanda yake gabansa ya ce ""Mun yi wahala sosai kafin mu ƙara samun damar hawa kujerar nan, so kuma dai menene wahala ta biya lokacin celebration ne"" suka yi" dariya lokaci guda. """Zan yi bacci yanzu har da minshari, talakawa sun wahalar dani sun saka na kashe kuɗi masu yawa amma" "duka zan fanshe yanzu a. ,"" ya yi shiru" "Alhaji Boɗejo ya ce ""A kuɗin kwangilar gyaran makarantu, titi, asibiti, tare da?""" """Hhhhhhh Boɗejo ikon Allah, na rabaka da sabgar nan ka yi shiru iya nan. Maganar da nake yi yanzu" "pretending zan yi cewa bani da lafiya, bayan maƙudan kuɗaɗen da za'a bani akan lafiyata ina son gefe da" "wasu manyan al'amuran shi ya saka zan yi tafiya zuwa ƙasar waje na samu cikakken hutu ni da iyalai na""" """Ka yi gaskiya Eng Ali wali, amma siyasa bata buƙatar a je a yi bacci dole ne idanunka ɗaya ya zama a" "buɗe ka fara tunanin shekaru huɗu masu zuwa wannan shine lissafin kowanne cikakken ɗan siyasa, kasan matakin da zaka ɗauka akan yaran nan""" "Eng Ali wali ya juya ya fuskanci Boɗejo ya ce ""Waɗannan yaran?""" """Ƴan daban nan, wanda suka yi maka bangar siyasa sune nake magana akai"" ya jinjina kai, mood ɗinsa ya" "sauya ya rage walwala ya ce ""Me kake nufi yanzu?"" Boɗejo ya ce ""Nothing but a true, sun satar maka akwatin zaɓe, sun tayar da tarzoma a wajan zaɓe, yan sassari mutane, sun sace ƙuri'un abokan hamayya, ƴan'sanda sun kama su kuma har aka kai kaya inec muka je tare da kai hukumar inec ɗin tsakiyar dare ba tare da an fargaba ba, an irga ƙuri'a waɗancan nada rinjaye mun saka shugaban mai faɗar sakamako zaɓe a gaba da bindiga wanda ya tilasta masa faɗar zaɓen cewa kai ne da nasara matsayin Ɗan Majalisar tarayya, kar kuma ka manta kafin hakan muna da cases na zaman kutu at the end ya zaman shari'ar ya" "ƙare can you remembering? You couldn't ko?""" """No, Boɗejo no please kar ka tuna mini da komai na wannan shari'ar mun yi nasara tabbas, mun yi" "galaba wannan ya shige, yaran da kake magana ba haka kurum aka kama su ba, nine na bada jerin list na kowanne ɗan daba da suke mini aiki saboda suna da kaifin baki za su iya tuna mini asiri ni kuma dai a gaskiya am not ready na jin matsalarsu, a taƙaice sun gama mini aiki sai wani yaƙin neman zaɓan kuma" "zan saka a fiddo da su na yi musu ƴan dabaru"" Boɗejo ya ce ""Hakan ma dabara ce Eng or Hon""" """Na the same, duk wanda ka ce zan yi accepting""" "Suka yi dariya suka haɗa baki wajan cewa ""cheers""" Har harabar gidan da suka tattauna Eng Ali wali ya rako Boɗejo ya shiga cikin jibgegigar motarsa mai "duhun glasses ko driver bai yadda ya ɗakko shi ba, yana shiga ya yi wa motar key ya bar gidan, Eng Ali wali kuma ya koma cikin gidan fuskarsa ɗauke da nishaɗi." "Misalin 7:15 Safiyyerh ta shiga sakkowa daga strains na bene, jikinta sanye da uniform hannunta riƙe da" "school bag sai marairace fuska take yi, kana ganin Safiyyerh kasan ba karaborin raino akai mata ba. Tana gama sakkowa ta zaune a kujera ta yi shiru, tunda take sakkowa kuma Ummeyh ta zuba mata idanu ganin yadda Safiyyerh ta yi wani irin fari jikinta ya goge ya buɗe tare da yin ƙiba, hatta buɗewar da hips" "ɗinta ya yi sai da abin ya bawa Ummeyh mamaki, ya dubi ƙirjinta at her young age bai ci ace girman ƙirjin" "Safiyyerh ya kai haka ba, tuna cewa likita ce ita kanta Ummeyh cima mai kyau yana saka yaro zama fiye da haka sai ta ɗaga shoulders alamun i don't care ya bayyana kafin ta yi murmushi ta ce." """Kin gama nuƙu-nuƙun kin sakko baby?"" Safiyyerh ta shagwaɓe fuska ta ce ""Ummeyh i don wanna go to" "school, a bar ni?""" """A bar ki da zuwa makarantar?"" Ta ɗagawa Ummeyh kai, idanunta na yin rau-rau da cika da hawaye," "Ummeyh ta ce ""A'a kul, kar ki yi mini kukan iska a nan wajan, wai Safiyyerh sai na yi miki ƙani za ki haƙura da kukan banza? Yaushe kika fara ƙin zuwa school for no reason? Eh Safiyyerh?""" "Ummeyh, kamar tunzura Safiyyerh ta yi nan take ta fara kuka wiwi tana zamewa ƙasa zata hau birgima" "ta cire hijab ɗin makarantar sumar kanta da Ummeyh bata tufke ba ta sakko a kafaɗa, Ummeyh ta riƙe haɓa ta ce ""Mun shiga uku, Ubangiji ka dawo mini da Haydar cikin aminci ya yi mini maganin yarinyar nan"" tsit Safiyyerh ta yi, jin sunan wanda Ummeyh ta ambata hawaye na cigaba da bin idanunta sai" "kuma ta sake narkar da fuska ta ce ""i don't want to hear his name, i don't want.... I don't like him """ """To kill him"" Ummeyh ta faɗa tana haɗe fuska. Daddy ya fito yana cewa ""Mene ya faru na ji ana a kashe" "shi?""" """Gata nan, akan Haydar """ Daddy ya kalli Safiyyerh da Ummeyh ke nuna masa yaga fuskarta ta yi jajur idanunta sun shige ciki "saboda kuka ya ce ""Yaushe Ƴan'matan Daddy ta fara kukan tafiya makaranta ne?"" Ummeyh ta ce ""Ohho" "mata""" """Haba daddy's angel, tashi muje we getting last"" ya ɗago ta cikin rarrashi ya amshi baby hijab ɗin da" "gabaɗaya bai fi a wuyanta ba ya saka mata ya ɗago fuskarta a hankali ya sumbaci goshinta, Safiyyerh ta yi saurin riƙe daddy tana lumshe idanunta tsigar jikinta na mimmiƙewa, a hankali ta ji yanayin data kwana da shi jiya na dawo mata ta ji inama daddy ya sake sumbatar ta? Idan ya tashi yi mata sumbatar kuma ya yi mata a saman laɓɓanta. ""Yawwa, ni yau ina sauri driver zai yi using another car ya kai ki" "makaranta ni ina da wajan zuwa kafin takwas ta cika, manage kin ji Safiyyerh?""" """To Daddy""" "Lunchbox ɗinta Ummeyh ta ɗakko, daddy ya amsa domin babba ne kuma an cika mata shi da kayan ciye-" "ciye, daddy ya kalli Ummeyh ta yi masa murmushi a hankali ta tako zuwa gare shi tare da shigewa jikinsa," "suka rungume juna idanun Safiyyerh zube a kasan su, har leƙawa take ta yi saurin saka ƙaramin hannunta ta rufe bakinta ganin yadda suke yin kissing juna, da sauri kuma ta juyar da kanta gefe kamar bata san me suke ba." "A hankali Ummeyh ta ce ""Bye sweetheart"" ya ce ""Bye Dr"" nan take Safiyyerh ta yi saving sunan" sweetheart a ƙwaƙwalwarta. "A entrance na sauka zuwa compound na gidan, daddy ya fara sunan Wizzy driver ba ya ce ""Za ka yi" "dropping Safiyyerh a makaranta, Please ka tabbatar ba ka yi gudu sosai ba kuma har ta makara ya ɗage glasses na motar naga yanayin kamar hadari damina ta kusa farawa so be careful"" Wizzy ya rusuna ya ce ""In sha Allah za a tafi da Zinariya a hankali, ai Alhaji azumin bana a ruwa za a yi shi"" daddy ya jinjina kai ya kama hannun Safiyyerh zai saka ta a back seat ta ce ""No daddy I'll manage here"" ta faɗa tana zama a empty seat dake gaban motar bayan an buɗe musu gate sun fice daddy ya shiga tasa motar shima driver" ya ja shi sukai waje zuwa inda za shi. FGC Federal Government College Zaria RD/ Kano Sanda suka yi parking motar ya rage sai few students a harabar da ake yin assembly every Monday and "Friday, ta bubbuɗe ido tana ƙiftawa tuna cewa class teacher na son ganinta, before she entering the class kafin frist subject ya shiga, ta buɗe ƙofa ta fito Wizzy ya yi saurin fitowa ya buɗe bayan mota ya ɗakko lunchbox ɗin ta amsa tana riƙewa a hannunta, ta juya ta kalle shi tana murmushi fararen haƙoranta a jere suna sheƙi ta ce ""Bye Uncle Wizzy"" ""Da dai kin bar ni a Wizzy na ƴar daddy shige kar ki" "makara""" "Ta jinjina masa kai ta shige, hall ɗin suke yin breakfast ta fara shiga ta ajjiye lunchbox ɗin kana ta nufi" "office ɗin, ƴar siririyar muryarta mai ɗauke da sallama ta ratsa office ɗin. Uncle Chidi ya ɗago kai ya" "kalleta, da ƙyar ta ce ""Good morning uncle""" """Morning Safiyyerh, have a seat please"" ya faɗa yana nuna mata kujera hankalinsa ya mayar kan" "waɗanda suke gabansa ya ce ""Ka yi ƙoƙari my friend, na kuma yi mamakin da na ji baka taɓa attending school ba, domin na ɗauka kai drop out ne, yanzu za a saka sunanka a list na ƴan jss 2, za a baka class" "pass za'a ke yi mata extra lessons na musamman""" """Thank you uncle Chidi""" """Let him talk. """ "Ya ɗago kan shi ya kalli Uncle Chidi ya kasa cewa komai, he feels uncomfortable a cikin school uniform" "ɗin, daya kasance farar riga ta ciki sai wanda dark green irin pine ɗin nan #234FIE, sai riga ƴar top da aka ɗora daga saman farar riga kasancewar shi baƙin mutum sai uniform ɗin ya yi wa fatarsa kyawu na musamman. Uncle Chidi ya yi murmushi yana duban Safiyyerh ita kuma hankalinta na ga wanda ake wa magana, jin cewa a class ɗin su zai zauna duk class ɗin kuma musamman a maza babu baƙi sai shi, ta dinga kallonsa ganin babba da shi wai bai taɓa attending school ba, ashe illiterate ne, ta dinga tunanin" searching ɗin da ta yi na most handsome guy taga baƙin namiji ne. "Uncle Chidi ya ce ""Za ku iya tafiya ai"" kamar jira yake cikin sauri ya miƙe yana kame fuska hannunsa zube" cikin aljihun wandon uniform ɗin har lokacin kuma Safiyyerh ba taga fuskarsa ba. Za su fita Kimiyya ya "ɗaga mata hannu ya ce ""Hy Safiyyerh. """ """Hy. "" Safiyyerh replied him." "Suna fita Uncle Chidi ya ce ""Safiyyerh Abdu mene matsalarki da karatu yanzu? Kina da issues da subjects" "ne? Ko class mates? Ko kuma teachers mene matsalar Safiyyerh daga cikin waɗannan abubuwan?"" Ta yi shiru kan ta a ƙasa tana wasa yatsun hannunta ya yi mata faɗa sosai kana ya ce ""Fita a officer nawa"" ta miƙe ta ɗauki school bag ɗinta ta nufi class jss 2 A, har lokacin teacher bai shiga, tana shiga Kimiyya ya" "miƙe daga mazauninsa ya zo wajanta yana leƙa fuskarta ya ce ""Makararriyya. """ "Ta juya masa idanu, sai kuma ta yi turus ganin wanda yake zaune a desk chair ɗin da take zama a aji" kasancewar kowanne mutane biyu ne. """New student""" """Kuma a inda nake?""" """Yes, da matsala ne?""" "Ta ɗage shoulders tana nufar wajan ganin Uncle John mai yi musu maths ya nufu class ɗin, kimiyya ya" "nufi wajan zaman shi. A hankali Safiyyerh ta raɓa ta zauna ganin ya babbake wajan, ta dinga kallon baƙar fatarsa inda take ta sheƙi ita kaɗai ta ɗan leƙa shi taga kansa a durƙushe yana kallon ƙasa, ta ɗan matsar da ƙafarta ta gyara zama a hankali ta sake durƙusar ta kanta can ƙasan desk ɗin tana ƙoƙarin leƙa fuskarsa ta ji ya saka ƙafarsa ya take yatsun ƙafarta ta yi saurin ɗaukewa tana zame kan ta cikin siriryar" "murya ta ce ""Auchhh My fingers"" tana yarfe hannunta." "Mutallab ko motsi bai yi ba, bata daddara ba ta sake tura kanta ƙasan desk ɗin again ta marairace fuska" "ta ce ""Who are you?....." "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 27: Safiyyerh Abdu" """Safiyyerh!"" Da sauri ta ɗago kanta daga leƙa fuskar Mutallab da take yi, sakamako kiran da Uncle John" "ya yi mata ta gyara zama da kyau tana kallon yadda Uncle John ɗin ya tsare ta da idanu, sai kuma ya girgiza kai, ya cigaba da bayanin da yake yi cikin harshen turanci. Safiyyerh ji ta yi bata gane me Uncle ke yi musu explanation ne akai, ta sake tattara hankalinta zuwa ga wanda yake kusa da ita, a wannan karan ta kan iya hango gefen zagayayyiyar fuskarsa, da yadda ya shigar da lips ɗinsa na ƙasa zuwa cikin bakinsa yana tsotsa a hankali kamar ya samu sweet, lips ɗinsa na sama kuma ya yi jajur da sauri ta lumshe idanunta tana girgiza kai saboda yadda jikinta ya sauya cikin ƴar ƙaramar muryarta ta furta a hankali" cewa """Strawberry kake sha?""" "Ya tsuke fuska ta mau, kamar kuma ya ce ya shiga uku haka yake ji a zuciyarsa game da yarinyar, sai ya" "daina tsotsar lips ɗin ya juyar da fuska, a hankali ta sake muskutawa a wannan karan a shagwaɓe ta ce ""Fenti ka shafa a fuska? E Blackman?"" Ya sake mata banza ta ce ""are you deep?"" Cak ya miƙe tsaye ta ɗaya side ɗin ya fara ƙoƙarin fita daga cikin class ɗin, Uncle John ya juyo hannunsa riƙe da maker ya kalli Mutallab ya ce ""Lafiya?"" Mutallab ya kasa cewa komai sai girarsa guda biyun daya cure su waje guda ya" "cak, sauran ɗaliban suka dinga kallon Mutallab har wanda basu san da zaman nasa ba." """Ina maka magana, go back to your seat""" """Akwai mara lafiya wajan, I'll manage, outside"" ya faɗa yana nuna waje wajan window. Da mamaki sosai" "Uncle John yake kallon Mutallab, Safiyyerh ma shi take kallo tana son jin waye bashi da lafiya kamar" "yadda ya ce. ""Waye mara lafiyar a nan wajan?"" Ya yi shiru, domin bai yadda cewa Safiyyerh lafiya lou" "take ba, ba kuma zai taɓa lamunta ba, ko ta tashi ko dai shi ne ya bar mata wajan ƙwaƙwalwarsa ya ji yana motsa masa har ciki yake jin ƴar mitsitsiyar muryar yarinyar." "Uncle John, ya ce ""Ɗaukan darasi a waje kuma wajan window? Yaushe ka fara attending class ɗin nan?""" "Uncle John ya yi maganar cikin faɗa yana nuna Mutallab, shi kuma ya yi shiru ya zubawa waje guda ido. ""Uncle new student ne""" """Idan new student ne, sai aka ce ya yi misbehaving haka? Abeg my friend go back to your seat"" bisa dole" "Mutallab ya juya tare da komawa wajan zaman, kamar jira take yi ya zauna ta sake yin ƙasa da murya ta ce ""Wani abu akai maka zaka fita? Ko baka da lafiya ne?"" Ta dinga masa surutu ko tari bai yi ba, har Uncle John ya fita, bayan nan Safiyyerh bata sake cewa komai ba lokaci zuwa lokaci sai ta durƙusar da kai ta leƙa fuskarsa, taga idanunsa a rufe." 10:35 Kimiyya na waje shi da abokansa su Nahyan ya yi murmushi yana duba agogon hannunsa ya ce """Bafa zai fito ba, ko ya fito zai kashe ku da miskilanci ne, ku bar shi cikin class har a koma ko?"" Captain ya taɓe bakinsa ya ce ""Shi ɗin waye shi? Da zai dinga ɗagawa mutane kafaɗa eh?"" Cikin sauri Nahyan ya ce ""Mutum, kamar dai kai haka yake"" Captain na mayar da wayarsa zuwa cikin aliju ya ce" """Daman aljani zai zo nan ne? Amma ni da shi akwai bambanci irin bambanci dake tsakanin sama da ƙasa," "irin bambancin dake tsakanin talaka da attariji, irin bambancin dake tsakanin fari da baƙi kamar dai" "haka....,"" ya faɗa yana haɗe farar wayarsa da baƙar ya ce ""Like this. Just like this. Irin haka, so ya" "daina ɗaga mana kafaɗa haka nan"" Kimiyya bai magana ba, sai Nahyan ne ya ce ""Brother, ko dai kana kishi ya samu waje kusa da mutuniyar ne?"" Duk suka yi dariya." """Kusa da wa?""" """Your Safiyyerh, kusa Safiyyerh ɗinka nake magana""" """Safiyyerh ta zo makaranta yau ne?"" Captain ya tambaya, ƙirjinsa na buɗewa idanunsa ya fito sai kuma" ya juya da sauri ya nufi jss 2 A domin duba Safiyyerh. """Shi Captain mene matsalarsa da new student ɗin nan? Ba class ɗin su ɗaya ba, amma ya addabawa kan" "shi haka kawai? Kar fa ya je ya daki ɗan mutane ko ya ja shi da rigima cikin aji, kasan matan ajinku kimiyya ƴan wahala ne, basu da kunya ga shegiyar ɗagawa da jin su wasu ne, shi ya sa ni bana ɗaukan raini, ko budurwa zan yi ba zan duba matan ajinku ba"" murmushi kawai Kimiyya ya ke yi, ya jinjina kai kafin ya ce ""Kana da ƴar gajiyarka Nahyan, amma kuma muna da kyakkyawa ma sha Allah, kuma bamu" "da daƙiƙai""" """E, na yarda kaf school ɗin nan babu ya ƴan'matan jss 2 A""" """Mufa a jininmu ne, kowa ka gani a class ɗin ba banza ba"" suka sake yin dariya gabaɗaya, Nahyan ya yi" "ƙasa da murya daidai kunnen Kimiyya ya ce ""Musamman su. ,""" """Kai, ba ruwana be careful""" """Ba wani be careful, ni fa crush ɗinta ne wallahi"" Kimiyya ya jinjina kai ya ce ""Bari na je can na yi gulma" "ina zuwa""" """Nima ba za a bar ni a baya ba, binka zan yi wallahi"" suka nufi class suna wata iriyar tafiya, kana ganinsu" "kasan iyayensu sun gaji da arziƙi komai expensive ne a tattare da su suna yin abu na matured people," duk da gabaɗaya ƙuruciya na tattare da su. "Safiyyerh tunda aka fita breakfast bata motsa ba, daman ba wani zirga-zirga take yi ba, cin abinci yake" "tasar da ita, da yawan lokaci kuma bata fiya cin abincin ba haka take komawa gida da shi. A hankali ta ja numfashi ta sauke, idan ta juya idanunta da suke farare tas zata sake kallonsa sai gabanta ya faɗi. Ta janyo lunchbox ɗin ta, side ɗin da aka zuba mata fruits ta buɗe ta zaro filas ɗin ciki ta ajjiye tare da spoon, one by one ta fito da komai ta jere saman table ɗin dat janyo. Indomie ta buɗe wacce aka yi mata" "fried Indomie ta ɗan yi ƙasa da murya ta ce ""In sammaka za ka ci? Baka zo da abinci ba?""" "Ya yi shiru, ta yi rau-rau da idanu ta ce ""To na bar maka duka cinye ma, ni zan sha fruits"" zata sake yin" "magana saboda shirun da ya yi mata taga Captain tsaye a kansu, ta haɗe fuska ba walwala ta cigaba da juya spoon ɗin hannunta, Captain ya kalli Mutallab ya juya ya kalli Safiyyerh sai ya yi murmushi ya duƙa daidai fuskarta ya ce ""Baby i missed you, I missed you yesterday, i miss you today,miss you every single day, missed you completely, ykk sweetheart?"" Ya ce yana lumshe idanunsa, ta ɗaga suka haɗa ido, ya juya masa idanunta sai ta yi shiru, ya yi saurin riƙe ƙirjinsa na yana jan numfashi a hankali ya ce ""Kina da kyau Safiyyerh, ki so ni kin ji tawan?"" Ta yi masa shiru, sai ya miƙe ya zauna saman desk ɗin ya ce ""Me" "kike a aji ke ɗaya?""" """Ni ɗaya kamarya?"" Safiyyerh ta tambaya, tana sake juya masa idanu, ya jinjina mata kai ya ce ""E, ke" "ɗaya. Kin so ki yi ta bani wahala na tsallake ƴan'mata da yawa da suke daidai ne na zo wajanki kike sha mini ƙamshi? Ya mike kyau, naga kina farinciki da hakan sosai""" """To ka nemi daidai kai mana, sai na nemi daidai ni nima""" """Ban gane ba?""" "Ta ce ""Ka gane mana, sai a yi soyayyar age mate, ko class mates tunda abin haka ne"" Captain ya dinga" "kallon ta da mamaki, yaushe bakinta ya buɗe har haka ne, sai a lokacin ya lura da wani irin kyau data ƙara, fuskarta sai glowing take, ta ƙara yin ƙiba sosai ya ja numfashi ta baki ya ce ""Har abada, ke ɗin dai ke ce, Safiyyerh bari na faɗa miki wani abu, ko yadda kike jin ban kai ɗin nan ba, kike sawa ranki ban isa ki so ni ba, wallahi zan iya zame miki matsala a cikin rayuwarki tabbas, idan kuma taƙamar mahaifinki mai arziƙi ne ki je ki bibiyi tarihin nawa uban ki ji waye shi, babu mamaki ya take naki uban a arziƙin da" "kike taƙama da shi, ban taɓa rasa abu ba, ba ki kai kuma na rasa kina cikin rayuwata ba, ki san da haka""" "Sosai abin ya bawa Safiyyerh mamaki, sai ta yi shiru idanunta na cika da hawaye jin yadda yake ci mata" "mutunci, ko yaushe ne ma take taƙama da arziƙin Daddy? Abin da kuma a wasa bai taɓa zuwa cikin kanta ba. Muryarta na rawa zata fashe da kuka ta ce ""Ni nake taƙama da arziƙin mahaifina? Ni me ya sa kake son takura mini ne? Kana neman ƙuntata rayuwata bana son haka ka daina, tun ban san mene soyayya ba har ka saka na haddace kalmar saboda yadda kake kwarzabata akai, a cikin kunnuwana na ji ana ce" "maka ni kwaila ce to ka rabu dani mana""" """E ɗin, ke kwaila ce rabuwa kuma ba ki isa ba, bana fara son abu don na daina Safiyyerh""" """To idan arziƙi na siyan soyayya bari muga"" ta faɗa tana murguɗa baki abin da bata saba ba. Captain ya" "yi murmushi ya ce ""Abubuwa nawa kuɗi ke siya a duniyar nan? Ko ba ki da labari, ai sai dai ubanka bame arziƙin bane, ki zuba idanu ki gani zan siyi soyayyarki da arziƙin da Allah Ya yi wa ubana, kuma za ki so ni, you most love me Safiyyerh... Ina ƙara jaddada miki ke ba tsarin talaka bace, ba kuma tsarin baƙin namiji bace ke, idan kikai dating da ɗan talakawa kin cuci iyayenka, kin cuci danginki, kin cuci yaran da zaki haifa mini kikai haramta mini zama ubansu za ki haifawa wani, ke hatta kan ki kin cucuta maimakon a ganki a gaban mota driver na jan ki, sai dai a ganki a bayan babur ko keke ko kuma kina takawa akan" "ƙafafuwanki"" ya ƙare maganar yana huci wani irin azababbiyar soyayyar Safiyyerh ke nuƙurƙusar" "zuciyarsa, ya juya ya kalli Mutallab yaga still idanunsa window suke kalla, kamar bai san da mutane ba a" wajan. "Kimiyya ya ƙarasu wajan daman tuni yake tsaye ya ce ""Wannan ba daidai bane ba, ka daina captain""" """Na daina me?"" Captain ya tambaya idanunsa a kan Safiyyerh ba tare daya kalli Safiyyerh ba. Kimiyya ya" "yi shiru ya kalli Mutallab ya ce ""Mutallab !"" Ya juyo a nutse ya kalli Kimiyya, idanunsa sun ƙara manyan" "ya lumshe su ya sake buɗewa bai ce komai ba. ""Mun kusa ƙarar da lokacin, baka fito ba an yi ko shira ba, ba ka yi breakfast ba?"" Bai san cewa ya ɗan kwakkwaɓe fuska ba sai da ya ji idanu da yawa a kan shi, ya shafa sumar kan shi ya yi shiru kawai, Kimiyya ya ce ""To ai shikenan"" Safiyyerh ta dinga kallon ikon Allah, har lokacin ba taga cikakkiyar fuskarsa ba, kuma yaƙi magana tun bayan fitar Uncle John. Captain ya yi" "waje rai ɓace, a nan kuma aka cigaba da ɗaukan darasi har lokacin tashi ya yi." "Suna harabar makarantar Kimiyya na jiran driver ya zo ɗaukan shi, haka ma Captain. Suna tsaye" "Safiyyerh ta ƙarasu wajan tana ƙifta idanu, nan da nan Mutallab ya kame fuska Kimiyya ya ce ""Kema ba'a zo ɗaukan ki ba kenan?"" Ta jinjina masa kai, ya ce ""Ok, kin san me?"" Ta girgiza masa kai, a hankali ya ce ""Wai meke haɗaki surutu da class captain ɗin jss 3 ne Safiyyerh?"" Ta narkar da fuska a hankali ta ce ""Ba" "komai""" """Bashi da kirki sam guy ɗin, ki daina biye masa kin ji?""" """Wannan abokinka ne?"" Safiyyerh asked him, tana kallon Mutallab daya juya fuska. Ya ce ""E, ɗan'uwana" "ne ke da yake seat mate ɗinki a aji, ba ku gaisa bane?"" Ta ce ""Ko baya magana?""" """A'a yana yi, ba kin ji ba?""" """Au, ya sunansa?""" """Mu ,"" da wani irin sauri Mutallab ya juyo ya kalli Kimiyya, yana zazzaro masa idanu, sai kuma ya juya" "ya kalli Safiyyerh a lokacin na farko, sukai shiru gabaɗaya na tsayin daƙiƙo, ya dinga kallon cikin idanunta, Safiyyerh kuma ƙafafuwanta ne suka fara rawa ta fara kokawa da nutsuwarta, wani abu ya fara yi mata yawo a jiki, kaf mazan a jin babu wanda ya kai Mutallab kwarjini da tsare gira, gashi dai baƙi ne amma" "yana da hanci mai tsayi, idanunsa manyan farare gashin idanunsa zara-zara girarsa a ɓaka wuluk kuma a" "cunkushe take sosai, duk bakinsa laɓɓansa jajur suke. Ta ji kanta na jujjuyawa a sama ta ji sautin" "muryarsa yana cewa ""Bana so"" daga nan bata sake fahimtar komai ba sai da ta ji kimiyya ya kira sunanta" "da ƙarfi ta ja ajjiyar zuciya ta ce ""na'am""" """Lafiya kike Safiyyerh?_" """E,. Yana ina?"" Kimiyya ya ce ""Wa kike magana?"" Ta ce ""Ɗan'uwanka mana"" sosai kimiyya ya yi dariya" "ya ce ""He lefted, ya tafi"" ta buɗe idanu sai bata ce komai ya ce ""Duk masifar da yake yi mini ba ki ji ba? Idan kina surutu ba za ku daidai da shi ba wallahi"" ta yi murmushi; lokaci guda kuma aka zo ɗaukan su, Wizzy ya amshi kayan hannunta ya saka a bayan mota tana kallon Kimiyya ta ce ""Ya sunansa?"" Yana shiga mota ya ce ""Ki tambaye shi"" yana faɗa driver ya ja shi suka fita, itama nata driver ya ja suka bar" makarantar tana lumshe idanunta. "Mutallab, tunda ya ga numfashin Safiyyerh ya ɗauke alamar ta ja numfashi da yawa ya zame idanunsa" "daga kan fuskarta ganin taƙi janye idanunta, cikin ɓacin rai ya juya ya kalli Kimiyya yana tattaro kalaman da zai yi amfani da su ya ce ""ka daina sako ni a sabgar raya, ina ruwanka ne, zan iya haƙura da karatun nan gabaɗaya ƙwaƙwalwata rawa take mini"" ya ƙare maganar ya furta ""Bana so"" da ƙarfi ya zazzaro ido, yana ganin Safiyyerh ta firgita kafin Kimiyya ya yi magana Mutallab ya juya da sauri ya bar wajan, duk irin kiran da Kimiyya ke yi masa na ya tsaya driver na hanya ya yi masa banza, har ya fice daga makarantar ransa a ɓace yake, gashi bai fito da ko sisi ba sai kawai ya fara tafiya a ƙasa, kan shi a ƙasa sai da ya ci rabin tafiya ya ji ana yin horn a bayansa, ya ƙi juyawa balle ya tsaya can ya ji motar ta tsaya a bayansa kamar za a taka shi, ya cigaba da tafiya da sauri muryarta ya ji ta ce ""Me ya sa kake tafiya a ƙasa? Tun daga school?"" Ikon Allah ya tsaya kallo, ya ɗaga kai ya kalleta ta yi masa murmushi ta ce ""Kamar" "hanyarmu ɗaya ma, mu tafi Wizzy yana jiranmu za ni Islamiyya kuma muje""" "Ya dinga kallonta, sai ya saka hannunsa ya matsar da ita gefe kamar zai cillar da ita ta yi saurin runtse" "idanunta tana yin ƙara, Wizzy ya riƙe ta ya ce ""Waye wannan ɗin yana da hankali kuwa? Ture ki ya yi fa?"" Maimakon ta yi kuka sai yaga ta yi murmushi ta ce ""Abokina ne ai, My Bestie"" Wizzy ya maimaita ""Bestie"" ta jinjina masa kai, sai ta koma motar suka cigaba da tafiya. Mutallab ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, wato dole sai an nuna shi talaka ne bashi da wani gata? Da wannan tunanin ya ƙarasa gida ya tarar" da Anty Hameeda ta ce """Na Ammo makaranta ka fara zuwa ne? Waye ya saka ka?""" "Bai amsa ba, yana shan kunu ya ce ""Yanzu kika zo?"" Ta ce ""Wallahi zuwan mu kenan bayan na huta na zo" "gaida su Ammo, naga duk ka sauya lafiya dai?"" Ya jinjina mata kai, ya dinga kallon kwanikan da suke ɗakin, ta lura abincin yake son ci ta janyo warmer ɗin data zo da ita, ta zuba masa tuwan samo da miyar ɗanyen kuɓewa ta sha kifi. Ya tanƙwashe ƙafafuwansa ya saka hannunsa ya fara ci yana lumshe idanunsa, kwasa uku ne sai da ya cinye tas ya sha ruwa ya yi gyatsa ""Allahamdulilah"" cewar Anty Hameeda ya buɗe ido ya ce ""Allah Ya saki a aljanna Yaya"" ta ce ""Amin tare da kai Auta"" ya gaida Ammo ta yi masa banza, Anty Hameeda ta ce ""Ammo wai laifi ya yi miki ne? Akwai abin da yake faruwa ne?"" Kafin Ammo ta yi magana ya miƙe ya fice daga cikin ɗakin. ""Ba komai"" Sa'adah za ta yi magana Ammo ta wurga mata wani irin kallo. ""To ma sha Allah, zuwa jibi zamu koma Legas ɗin ai, na ji daɗi da naga kin fara sana'a Ammo." "Mutallab ne naga duk ɗabi'unsa ya sauya"" daga Sa'adah har Ammo basu tanka ta ba." "Shi kuma yana fita ɗakin zaure ya shiga, idanunsa cike da bacci ya faɗa saman ƴar tabarmar dake gefe" "guda, ko kayan makarantar bai cire ba, ya lumshe idanunsa sai kuma ya ja tsiririn tsaki, ya gagara yin baccin sai juyi yake yi can ya miƙe ya cire uniform ɗin ta ɗauki wani gajeren wando ya saka, ya fito ya zuba ruwa a bokici ya shiga banɗaki, wanka ya yi ya ɗaura alwala ya sake shige ɗakin. Duk yadda ya yi yai bacci ya gagara sai ya miƙe ya fita, ya yi tafiya mai nisa sosai saboda ciyawa yake nema, a wannan lokaci ya shiga napep ya yi wajejen Kumbotso. Ya yi shiru a tsakiyar ciyayin yana kallon komai, iska na kaɗa shi ya ji kamar ya dauwama a wajan, bai san me ya sa ba komai na duniya ya tsaya masa baya jin daɗin komai, ya miƙe ya tsinke duk ciyayin da yake so har da ganyen tumfafiya, mamaki ya kama shi ganin Kimiyya a hanya cikin mota shi da Nahyan ya haɗe fuska kamar ya ce ya shiga uku, a ƙa'idar aikin da zai yi a hanyar ta dawowa ba'a buƙatar ya kula kowa balle yin magana, kuma a ƙafa zai je gida, saboda hakan duk maganar da Kimiyya ya yi masa yai mai banza bai taɓa jin an wulaƙanta shi irin na yau ba, ya ji" daman bai san Mutallab ba. """Kimiyya rabu da shi muje don Allah"" Ya girgiza kai ya ce ""A'a Nahyan dole na san me gayen nan yake" "taƙama da shi, na tsani wulaƙanci bayan ni ban wulaƙanta kuwa ba, driver stop the car"" driver ya tsaya, Kimiyya ya fito ya sha gaban Mutallab yana girgiza kai ya ce ""Dame kake taƙama da shi ne Mutallab?" "Daman haka talakawa suke an sha faɗa mini ban yarda ba"" Kamar idanun Mutallab zasu faɗo haka yake kallon Kimiyya da su, ya ce ""E, haka ne ma ka yi ma talaka rana ya yi maka dare, ka ja shi inuwa ya cilloka rana, talaka idan ya samu waje bai iya shanya ba ga alama nan kuma na gani, idan ka manta waye kai bari na tuna maka, Muhammad Mutallab Abdullahi, Ɗan'malam Abdullahi mai makarantar almajirai, Mutallab kai ba you're nothing but Ɗan'malam kai zero ne, no education, no power, no money, no freedom, babu ko ɗaya a tattare da kai, sai ɗagawa kana jin kai wani, hatta ga iyayensa fa sun tsane shi," "daƙiƙi jahilin banza wanda talauci ya zame masa abokin rayuwa""" "Wata zufa ce ta dinga tsattsafo wa Mutallab a tsakiyar ƙirjinsa, ya dinga kallon Kimiyya bai yi ko tari ba" "sai murmushi da ya yi asalin kyawunsa ya bayyana, idanunsa kamar garwashi haka sukai alamar" maganganun Kimiyya sun tsaki tsakiyar ƙirjinsa. """Boka, matsafi wanda ya kashe ƴan'mata biyu ya yi tsafi dasu""" "Kimiyya na cewa haka ya shiga mota, driver ya ja, ya durƙusar da kansa a jikin kujerar motar, idanunsa" "sukai ja, duk maganar da Nahyan ya yi masa bai kula shi ba a haka suka bar Mutallab tsaye a wajan. Bai san tsayin lokacin daya shafe ba sai ji ya yi ana masa dariya ya juya idanunsa ya sauka akan wata dattijuwar mata, tana dogara sanda. Tana ta yi masa dariya har ta shige cikin wata bukka ya bita da" manyan idanunsa. "***Safiyyerh na bedroom ɗinta a ƙwance lokacin ƙarfe tara ta shige ƙarar buɗe ƙofa ta ji, ta waiga da" "sauri kuma ta miƙe zaune ta ce ""Daddy"" ya yi mata wani irin kallo daya sanya ta sha jinin jikinta tai ƙasa da kanta ƙasa Daddy ya ce ""Safiyyerh Abdu """ """Na'am, Daddy"" ta faɗa muryarta na rawa ya ce ""Me kika yi a makaranta yau kuma?""" """Me aka ce na yi?""" """Ni kike amsawa tambaya da tambaya? Ƴar uwarki za ta yi miki ƙarya ne eh?"" Da mamaki Safiyyerh ta ce" """Wacce ƴar'uwar tawa Daddy?"" Daga bayan daddy ta ji an ce ""Ka gani ko Daddy? Ko a school sai ta nuna mini ni ba ƴar'uwarta bace ba"" Wahee ta fashe da kuma ta ce ""Daddy, Safiyyerh hates me, she hates me so much, daga na yi mata maganar ita macace bai kamata tana zuwa class namu tana kula class captain ba, shine ta dinga zagina ta uwa ta uba hadda cewa ba kai ne ka haife ni ba, daddy ina son Safiyyerh" "amma ta tsane ni""" "Tsoro da sharrin da Wahee da ta yi mata ya saka ta kasa magana, idanuna ta ta cika da hawaye ta fara" "girgiza kai ta ce ""Daddy wallahi ,"" a gigice cikin tsawa Daddy ya ce ""Shut up Safiyyerh, shiru shasha," Wahee ɗin kike faɗawa haka? Ashe yara kike kulawa a makaranta shine kika fara zama daƙiƙiyya? Haka "kike daman Safiyyerh?""" """Wallahi daddy bana. ,""" """I said shut up Safiyyerh, ki fito mini da books ɗinki wallahi kika bari naga ba daidai ba sai na zane miki" "jiki tas yau a gidan nan don kinga ina lalllaɓaki? Birthday ɗin da zan miki ma na fasa""" """A'a daddy kar ka dake ta don Allah, na yafe mata Safiyyerh jijina ce bana jin daɗin yadda take kula maza" "a makaranta ne"" Wahee ta ce tana fashewa da kuka itama sosai, fuuu daddy ya juya a ransa ya ji idan yaga ba daidai ba a books ɗin Safiyyerh sai jikinta ya faɗa mata tas wallahi. Yana fita Wahee ta share" "hawayen idanunta, ta fashe da dariya sosai tana tafa hannayenta ta ce" """Like this... Kamarya haka, idan har ba ki rabu da class captain ɗinmu, nawa ne ni ɗaya ne kin fahimta" "ko?""" "Safiyyerh za ta yi magana Wahee ta ɗora yatsa a bakinta ta ce ""No... No... No sister ki adana maganarki" "zuwa wani lokacin, ba yanzu ba akwai saura sai na tabbatar kin zama zere plus zero minus zero""" "Safiyyerh ta dinga kuka, tana jawa Wahee Allah Ya isa, yaushe ma take kula maza? Fuskarta ta yi jajur," "tana lumshe idanunta fuskarsa ta sauka cikin ganinta yadda yake tsotsar lips ɗinsa, da sauri ta buɗe idanunta saboda tsigar jikinta da suka mimmiƙe ta ji mararta ta ƙulle, har cikin dare tunaninsa take da muryarsa da yake cewa kimiyya “Bana so” kan ta kamar zai fashe ta ji wani irin zazzaɓi saboda kukan da ta yi. Ta miƙe ta fita zuwa bedroom ɗin Ummeyh taga bata ciki, duk inda zata duba magani babu, sai ta nufi part ɗin Daddy dake downstairs, abin da ta saba ji shi ne dai, yau na fi na kullum domin sosai take" "jiyo surutun Ummeyh sai muryar Daddy da yake yawan faɗin ""I am sorry. Sorry dr""" """Sorry for what?""" "Safiyyerh ta tambayi kan ta, ganin bata da amsa ta yi shiru ta ji inama ita take ihun da Ummeyh ke yi," "domin anata tunanin sai ta yi zaton wani special ihu ne, da gudu gudu ta sake komawa bedroom ɗin Ummeyh ta kwashi kayan S Bayero musamman na hips da breast, sai wata gumba ta musamman da bata san ta mece ce ba ta ɗauka ta cinye, bayan ta gama ta nufi bedroom nata. Ta dinga juyi a kan gado, can ta ɗakko wayarta sai taga notification an rubuta “ Happy birthday sweetheart” ta dinga mamakin waye? Bata da number ita mantawa take akwai sim a ciki, ta yi searching abin da ta saba gani a ƴan kwanikan nan tana jin daddy ta kasa jure kallon sauran bidiyon. Wata number ta lalubu ta kira a cikin daren, can aka ɗauka sai ta yi shiru ta kasa magana. A hankali muryarsa can ƙasa ya ce ""Safiyyerh. "" Ta yi shiru ya" "sake cewa ""Safiyyerh?"" Da sauri ta kashe kiran ganin yana kiranta after sai ta kashe wayar ta fashe da" kuka tana rungume filo. "Washegari Kimiyya ya yi mamakin ganin Mutallab cikin class, ya duba agogo yaga 7:30 da alama ya riga" "kuwa zuwa ajin, domin har lokacin Safiyyerh ma bata zo ba, shi kaɗai ne a desk ɗin. Kimiyya ya ɗauke kai ya ƙarasa wajan zamansa yana mata murmushi ya ce ""Hy"" bata yi mata magana ba, sai juya masa ido da ta yi, ya yi ƙasa da murya ya fara mata magana. A daidai nan Safiyyerh ta shigo, fuskarta ta yi jajur idanunta da ƙyar take buɗe su, ta zauna ta yi ƙasa da kai can ya ɗago ta kalle shi cikin sa'a suka haɗa" idanu ta yi murmushi ta ce """Ina kwana?""" "Ya zazzaro mata idanunsa ta shagwaɓe fuska tana matsawa more close to him ta ce ""Please"" bai amsa" "ba, sai idanunta ya cicciko da hawaye ta sunkuyar da kanta ƙasa yana ji tana shassheƙar kuka a haka Uncle John ya sake shigowa kusan shine first subject kullum. Bayan sun gaida shi cikin turanci ya ce ""Yau kowa zai gabatar da kansa, na lura da sabbin fuskoki a cikin ajin nan, zan fara da kaina, sai a fara ta right" "hand ɗina""" """Sunana Uncle John, kuma nine class teacher naku, next?""" "One by one kuwa ya dinga gabatar da kansa, Kimiyya ya miƙe ya gabatar da kansa, ya kalli ta kusa da shi" "da take duba littafi sai harhaɗe rai take yi a hankali ya ce ""Dear, ke ake jira"" ba tare data ɗago ba ta ce ""Jira, for?"" Ya ce ""Gabatar da kai"" ta ɓata fuska har sai da Uncle John ya sake magana ta miƙe ta ce" """Safiyyerh. Sunana""" """Safiyyerh. ?"" Mutallab ya nana a zuciyarsa, sai kuma ya kalli Parrot ɗin kusa da shi yaga ta miƙe tsaye" "tana goge idanunta. Uncle John ya ce ""Uhm sai ke""" "Muryarta a hankali ta ce ""My name is Safiyyerh Abdu."" Da mamaki Uncle John ya kalleta, sai kuma ya" sake kallon yarinyar dake bayanta ta kusa da Kimiyya """You Safiyyerh, itama Safiyyerh, ke Safiyyerh Abdu ko? Ke kuma?"" Ya faɗa yana nuna ta kusa da Kimiyya" "ya ce ""Safiyyerh waye?"" Kai tsaye ta ce ""Safiyyerh Abdu...." Not edited ฀ Mutallab Paid book Pay before you read 08164069385 "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 28: A phone call" "Kusan Mutallab ya riga ta zuwa da wuri, bayan ya shigo ya zauna ta shigo hannunta riƙe da bag, ta zauna" "a desk ɗin da yake bayansa, amma daga shi har ita babu wanda ya lura da wani. Da tsananin mamaki Uncle John ya ce ""So we have two different Safiyyerhs in this class, wanda suke amfani da suna ɗaya, kuma suna amsa sunan mahaifi ɗaya, wonderful; abin mamaki"" Uncle John ya furta yana jinjina kansa, duk da rashin kasancewarsa musulmi bai yi mamaki da hikimar Ubangiji ba. Ya dubi Safiyyerh ta kusa da Mutallab, ya sake duban Safiyyerh wacce take baya kusa da Kimiyya ya bubbuɗe idanunsa ya ce ""Idan an samu first name, da surname dole iri ɗaya a middle name dole a samu bambanci, mene sunan kakanki" "first Safiyyerh?""" "Ya nuna Safiyyerh da har yanzu take murza idanunta, ta ɗan ƙifta su sai kuma ta watsa hannayenta irin" bata sani ba can ta ce """Safiyyerh, just call me Safiyyerh Abdu """ """Abdu wa?"" Ta girgiza kai alamar bata sani ba, sai ya jinjina mata kai ya ce ""Second Safiyyerh fa? Mene" "sunan grandfather ɗinki?"" bayan ta ɗago kanta ta zubawa Uncle John idanu ta dinga kallonsa ta kasa magana, Kimiyya ya yi ƙasa da murya ya ce ""Me ya sa kike yin haka ne?"" Ta ware idanu bata kalli Kimiyya ba, tana dropping pen ɗin hannunta a desk chair ɗin ta ce ""To ya yake kallona haka? Ban gane ba, me kuma zan ce?"" Kimiyya ya ce ""Ke da Safiyyerh kuna amfani da suna ɗaya hadda na mahaifi, to yadda za'a" "gane ku yake nufi ki faɗi sunan kakanki"" ta sake juya masa idanu ta ce ""Wanda ya haifi babana?""" """Shi, haka nake nufi""" """Oh, Safiyyerh Abdu nake amfani da shi, a gida ma Safiyyerh ake ce mini, friends and family duka" "Safiyyerh Abdu ne. Amma zan ke amfani da wani sunan, Aafiyyah"" John ya ce ""Aafiyyah?"" Ta jinjina" "masa kai ya ce ""Ok, yanzu mun bambance akwai Safiyyerh Abdu akwai Aafiyyah Abdu, next person please?"" Ya faɗa yana nuna Mutallab da ya jingina baya ya harɗe hannayensa a ƙirji idanunsa buɗe ya zubawa yatsun Safiyyerh idanu a rashin abin da zai kalla, zuciyarsa sai ruɓanya aikinta take yi yana jin kansa daban a cikin sauran ɗaliban. Ta yi ƙasa da murya bayan ta leƙa fuskarsa ta ce ""Bestie Uncle John" "yana magana""" "Zame hannunta da ta yi, ya saka Mutallab lumshe idanunsa ya buɗe sai a lokacin ya yarda yatsun hannun" "nata yake kallo, bai kalleta ba kamar mai avoiding haɗa idanu da ita haka ya juya ya kalli Uncle John da yake cewa" """Mene sunanka""" """Mu ,"" Uncle John; ya dakatar da Mutallab wajan cewa ""Ka miƙe tsaye kamar kowanne ɗalibi ka ji?""" "Mutallab baya son hayaniya da son a dinga nanata masa magana, gently ya miƙe tsaye yana zuba hannunsa cikin aljihu fuskarsa ba yabo babu fallasa ba kuma a gane yanayin da yake ciki, domin babu wani mood akan fuskarsa da zai iya fasallata halin da zuciyarsa take ciki ya ce ""Muhammad Mutallab Abdullahi"" slowly slowly ta ɗago idanunta ta kalle shi, tun daga ƙafafuwansa da suke ƙasan desk, har zuwa yanayin yadda zuba hannunsa a cikin aljihu, ta kai dubanta ga faffaɗan ƙirjinsa daya ɗan ɓalle gaban rigar, ta juya idanunta lokacin da ganinta ya sauka akan fuskarsa da take baƙa, she can't describe abubuwan da idanunta suka gane mata, nan da nan gudun da zuciyarta ke yi mata ya ƙaro cikin sauri ta" ɗauke kanta tana taɓe fuskarta. "Kamar ya san cewa kallon shi ake yi ya cuccure girarsa waje guda, ya shigar da lips ɗinsa na ƙasa cikin" "baki wanda ya riga ya zame masa jiki a hankali ya koma ya zauna, sai kuma ya ɗago kansa jin ana cewa ""Muhammad ko Mutallab wanne zamu dinga cewa?"" Maganar ya fito daga cikin bakin wani ɗalibi, yaƙi magana sai Safiyyerh ce ta ce ""Ku kira shi da Mutallab haka sunan yake"" kasancewar subject ɗin maths ne ya saka aka fara yi musu rubutu, kuwa yana yi amma shi yana kallon rubutun Uncle John yana lissafa su a kan shi tas, ita kuma ta zubawa fuskarsa idanu musamman lips ɗinsa tana mamakin abin da yake jin" idan ya yi hakan. "Bayan kammala karatu Uncle John ya rubuta class work kuma nan da five minutes zai amsa, Safiyyerh" "tattaro dukkan abubuwan da suke cikin kanta idan ta yi calculating sai taga ba daidai ba, lokaci guda duk ƙoƙarin da take da shi a maths ɗin ya gudu, tare da yin hijira daga cikin ƙwaƙwalwarta, ta ji ta zama empty head bata fahimtar komai sai bugawar da zuciyarta take yi, tana doka mata da ƙarfi ta cikin ƙirjinta ta zama wata irin uncomfortable ta ji kamar bata taɓa sanin ma'anar 1 ba balle 2, littafin ma wani irin duhu yake yi mata a cikin idanunta, a hankali ta ajiye biron hannunta ta ɗora kanta a desk ɗin ta lumshe idanu, zafin da ta ji a saman fuskarta ta fahimci kuka take, irin kukan nan mara sauti kuma mai" cin zuciya. """2 minutes left""" "Uncle John ya faɗa, wanda ya sanya Safiyyerh ɗago kai, a hankali kuma ta fara rubuta abin da take" tunanin daidai ne daya zama amsar questions ɗin. "Da an gama class work ɗin sai fita breakfast, lokaci ɗaya suka fito a tare, bai ko kalli inda suke ba ya je ya" "yi dropping, Aafiyyah ta haɗe fuska sai kuma ta a ajjiye nata ta koma wajan zamanta, sai da kowa ya" "kammala kafin Safiyyerh ta miƙe ta isa wajansa ta bashi za ta juya ya ce ""Safiyyerh Abdu """ """Come back, zo nan Safiyyerh"" ya faɗa cikin ɗaga murya. Yana cilla mata ya ce ""Mene wannan ɗin?""" """Answers. Na yi answering duka tambayoyin Uncle""" """Ok na gani, shige ki zauna""" "Ta juya, haushi ne ya cika Uncle John ya kasa yi mata faɗa ma, sai kawai ya fice daga cikin class ɗin. A" "hankali kowa ya fara fita ya rage daga Safiyyerh sai Mutallab, sai kuma Aafiyyah data zaro wayarta hankali kwance tana dannawa. Kimiyya ya ce ""My crush lafiya bakya zuwa makaranta kwana biyu, sai na ji kamar duniyar ce zata rikito mini zuwa kai na. To Allahamdulilah yau dai kin zo zan samu sukuni" "acikin zuciyata amma da kamar mara lafiya haka nake jina"" Ta harare shi bayan ta miƙe tsaye ta ɗauki lunchbox ɗinta, Kimiyya ma ya miƙe tsaye bai ko kalli Mutallab ya yi waje abinsa, har Aafiyyah za ta fita" "ta ce ""Congratulations dear""" """For. ?"" Safiyyerh ta tambaya." """Happy birthday"" cewar Aafiyyah." """Oh ba ki manta ba, thank you ya hanya kuma? Kin dai yi niyyar zuwa makaranta yau ko namesake?""" "Aafiyyah ta ɗan shagwaɓe fuska a hankali ta ce ""Ya birthday partyn?""" """Daddy ya fasa, Wahee ta haɗa mini sharri"" Aafiyyah ta lailayo wata ashar ta yi ta ce ""Wannan na sha" "faɗa miki bata da hankali fa, kike zuba mata idanu watarana sai ta yi miki abin da ba ki taɓa tunani ba, kinga ni wallahi ko waye baka isa ka taka ni na rabu da kai ba, i skipped that level, idan kuma ba ka yi mini komai ba babu ruwan kallo da gajiya, ki rufe idanu ki ci ubanta sai ku zauna lafiya, ƴar abu ta kaza kaza, ƙazama irin ta ma"" Safiyyerh tana buɗe ido, haɗe da dafe ƙirji ta ce ""Daddy sai ya dake ni idan na yi haka"". Siririn tsaki Aafiyyah ta yi ta ce ""Sai ki ce aljanu ne suka buge ki, ba kisan kin yi ba ko?"" Murmushi kawai Safiyyerh ta yi ta ce ""Ke dai kawai masifa kike ji da ita yau, Aafiyyah meet my friend Mutallab," "bestie na ne"" ta faɗa tana nuna masa Aafiyyah dake tsaye a wajan." """Bestie ga Safiyyerh my namesake, domin ka fi ganewa ka ce mata Aafiyyah """ "Maimakon ya amsa, sai ya miƙe tare da zagayawa ya bar ajin daman basu yake kallo ba, takaici ya cika" "zuciyar Aafiyyah ta tsani jisgi ƙwarai, ta tsani wulaƙanci tabbas, ta tsani nuna mata bata isa ba zahiri, nan da nan ta ji idanunta ya cika da hawaye da sauri ta haɗiye su, ta kalli Safiyyerh dake cewa ""Ki yi haƙuri ko bai ji ba"" harara kawai Aafiyyah ta watsawa Safiyyerh sai ta koma wajan zamanta ta fasa fita gabaɗaya. Safiyyerh ta miƙe jikinta a sanyaye ta yi waje tana jujjuya da idanunta tana jin zuciyarta a dunƙule waje guda a ƙirjinta. A can ƙasan wata bishiya ta hango shi zaune saman kujera, ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora a saman kujerar ya miƙar, a hankali kuma ya buɗe gaban rigarsa domin duk a takure yake jin kansa, tun kafin ta ƙarasu ya san cewa ita ce ya kame fuska ta yi sallama a nutse ta zauna ta ce ""Abin da kake yi ba kyau fa, ka share Aafiyyah"" jin ya yi mata shiru ta rausayar da kanta zuwa gefe kafin ta ce ""Rayuwa ba zata taɓa tafiya daidai kana tare da mutane ka ce ba zaka kula su ba, wannan ba halin musulmin ƙwarai bane ba, Allah da kansa ya karrama Ɗan'adam domin mutum ne mai daraja da kima, babu riba a wulaƙanta jinsin mutum wala mace wala namiji, ka yi abota za ka yi farinciki zuciyarka za ta yi fari, ka yawaita magana da nishaɗi zaka rabauta da samun nutsuwar zuciya, mu fa duka ƴan'uwa juna ne"" ta" washe masa fararen haƙoranta da suke a jere. "He just staring at her, her face, listening to her voice kamar mai jin maganar na sauka a kansa, sai ya yi" "shiru. Har lokacin kallon ta yake yi. ""Thinking of me, me ya sa na fiye surutu ko?"" Safiyyerh ta tambaye shi tana dariya, ta sake cewa ""Zan iya cankar yaranka, muga, idanunka suna nuna wani abu, suna faɗar wani abu"" ta sake yin murmushi ta ce ""Got it, Yaruba boy bari na yi maka addition da Fulani, idanunka Yaruba and Fulani yake faɗa mini"" ta gyara zama ta shiga fito da chocolates ɗin jakarta, ta fito da" breakfast ɗinta ta ajjiye a gabansa. "Without looking at him ta ce ""Mayya kake ce mini ko bestie? I know, na ji zuciyata ta faɗa mini""" "E, da gaske mayya ya ce mata a daidai lokacin ya kuma ji mamakin yadda akai ta gane, ta ɗago kai ta ce" """Ina da wayo fa sosai, daddy yana yawan faɗa mini hakan...,"" a daidai wannan lokaci a tsakanin da suka gitta abin da Safiyyerh ta manta ne kawai fata faɗa masa ba, labarin gidansu da jama'ar gidan komai da komai sai data faɗa masa. Ta ce ""Ni dai ko za kana zazzaro mini sexcy eyes ɗinka na yarda, kai ne bestie na kuma kai ne"" shiru ta yi lokacin data ɗago kanta idanunta ya sauka a cikin ƙirjinsa dake buɗe, da chocolates ɗin bakinta da yawon da ya cika bakin gabaɗaya suka shige cikin maƙoshinta ta fara tari sosai" "har lokacin kuma ƙirjin nasa take kallo, shima ya cake a gabanta baya ko ƙifta ido." "Suna zaune Kimiyya ya ƙarasu, ya kalli Safiyyerh ya ce ""Budurwar Captain, ki je Uncle John na kira""" "gabanta ya faɗi ta sha jinin jikinta, sai kuma ta miƙe ba tare data ɗauki komai a wajan ba. Bayan ta bar wajan, Kimiyya ya nemi waje ya zauna ya ce ""Ashe ka zo makarantar kenan""" """Na koma ne?"" Mutallab ce a hankali yana zaro ɗan kuttun da yake kunna hayaƙin ƙarfe a ciki ""Na ji" "mamaki ne duk da abin da na faɗa maka ba ka yi zuciya ba"" yana busa hayaƙin kai tsaye idanunsa akan Kimiyya ya ce ""Wani abu?"". ""A'a mu bar maganar ya shige, ya kamata ka daina kula Safiyyerh saboda zama lafiya"" da mamaki Mutallab ya dinga juya sunan Safiyyerh kafin ya ce ""Safiyyerh? Waye haka mace ko namiji?"" Kimiyya ya ce ""Bana son wulaƙanci, Safiyyerh wacce ta tashi daga nan wajan yanzu ita nake" "nufi ka daina kulata saboda zama lafiya shawara ce buddy""" """Shi ne na ce a jinsin mace take ko namiji?"" Mutallab ya faɗa a kasashe. Ran kimiyya ya fara ɓaci don" "haka ya ce ""Mata maza ce, ji rainin wayo kai Mutallab komai sai ka jisgahi kake jin daɗi?""" "Ya girgiza kai ya ce ""Da gaske kallon namiji nake mata, ka sanni ai, na shafe minti talatin ina kallon ta,na" "tabbatar cewa wai ba ɗan'uwana namiji nake kallo ba, amma na kasa hango suffar mata a idanunta, na" "kasa gano irin abin da na gani a tattare da Jaanah, ka ɗauka kamar kai haka naga ita wacce kake magana" "akai""" "Kimiyya ya kalli Mutallab ya ce""Kasan wace Safiyyerh kuwa? Ita kakewa kallon namijin?"" Mutallab ya" "ɗaɗɗage girarsa, yana sake zuƙar hayaƙin da yake cikin ɗan kuttun idanunsa ya rikiɗe ya juye kamar gaushi a daƙile ya ce ""Nawa aka biya kuɗin makaranta ta? Uniform, books komai da komai"" Kimiyya ya faɗa masa ya ɗakko waya ya ce ""Wannan taka ce in ji Jeddah saboda karatu, system ta so siya maka ta ce" "ka fara da wannan, waya ce akwai sim a ciki da kuma numberta""" """Ita kuma nawa ce kuɗin ta?""" "Kimiyya ya faɗa masa, ya jinjina kai ya ce ""Zan biya, duka zan biya"". ""Ban gane zaka biya ba, me zaka" "biya?"" Cewar Kimiyya yana gyara zaman shi da kyau. Murmushi Mutallab ya yi yana lumshe idanunsa ya buɗe ya ce ""Ai ni ɗan Malam Abdullahi ne mai makarantar allo ta almajirai, ɗan talakawan nan, ni ne wanda bani da power, freedom, bani da ilimi, ni ne dai wanda ka kira da jahili, ni ne dai wanda ka cewa talauci ya zamewa abokin rayuwa, ni ne wanda ka aibata da ni da iyayena saboda talakawa ne, saboda naka iyayen jinin ƙaruna ke gudana a jikinsu"" Mutallab ya ciccije bakinsa yana sake tsuke girarsa har lokacin wani irin murmushin yake yi ya ce ""Ba ka yi ƙarya ba, Malam Abdullahi talaka ne bai ajjiye ba, bai kuma bawa Kowa ajjiya ba, sai dai Allah Ya bashi ɗa mai ƙaunarsa wanda zai iya sadaukar da komai domin shi, ka rubuta ka ajjiye ba zan taɓa wulaƙanta ba, kuma talauci ba zai taɓa zama abokin rayuwar Mutallab ba, zan biya ka In sha Allahu, ban yi lalacewar da za'a dinga mini gori ba, komai da ka yi mini da" "kai da Jeddah i appreciate it, na ɗauke shi matsayin bashi""" "Ya miƙe tsaye har zai juya sai kuma ya ce ""Shhh, ka ce mini boka, matsafi, zaka iya cewa na kashe Diyna" "da Jaanah idan ka so domin ina fargaba da cewa ba ni ɗin ne na kashe su ba, saboda taɓin hankali da nake da shi. Kayi ƙarya dai na faɗa tsafi nake ko bokanci, ko mene nake yi ka ganni da idanunka, ka huta lafiya abokina ɗan mai arziƙi, ka yi haƙuri ba'a bin Moh bashin magana"" ya tsallake ya bar Kimiyya a wajan, shima kimiyya ya bi Mutallab da idanu, bai taɓa jin takaici faɗawa wani ko gorantawa wani ba irin yau, maganganun Mutallab sun tsaye masa a zuciya, murmushin da yake fuskar Mutallab ƙirƙirar su ya yi, domin ya fi kowa sanin cewa Mutallab baya murmushi bare dariya jikinsa a sanyaye ya miƙe ya koma" cikin class. "Bayan komawa, Uncle John ya shigo class ɗin ya rabawa kowa class work ɗin, yana murmushi ya bawa" "Aafiyyah ya ce ""A karo na farko Aafiyyah score ɗin ki ya zo ɗaya dana wani, yama ɗara naki da kaɗan"" nan da nan ta haɗe fuska ta ce ""Uncle waye? Nawa score ɗin both"" ya miƙa mata nata ya ce ""8/10"" ya ce" """Mutallab ga naka, 9/10 keep it up my friend"" amsa ya yi ya juya, Aafiyyah ta amshi nata Uncle John na" "fita ya yayyaga kamar za ta yi kuka ta ce ""I hate him, na tsane shi""." ***Mutallab yana zaune a ɗakin Ammo dab da magariba bayan ya gaisheta taƙi amsawa zama ya yi tare "da cigaba da danna wayar hannunsa, juyawa kaɗan sai ya tuna maganganun da Kimiyya ya faɗa masa. ""Waye ya saka a makaranta?"" Ya ji saukar muryar Ammo a kunnuwansa ya ajjiye wayar a hankali kuma ya ce ""Wa..."" Ta katse shi da cewa ""Kodayake bana buƙata, Allah Ya taimaka""" """Amin"" ya ce" "Sa'adah ta shigo hannunta riƙe da bokicin farar data soya, yana ganinta ya tsuke fuska ya fara shirin" "miƙewa zai fice, ta ɗakko farar ta miƙa masa ta ce ""Auta ci ka ji"" idanunsa ya yi luu numfashinsa ya nemi tsayawa, da ƙarfi ya ce ""Yaya ban so kar ki sa mini, ban so"" bata yi aune ba taga ya yi ball da farar gabaɗaya ta tarwatse a tsakar ɗakin, jikinsa na tsuma idanunsa ya yi jajur masifa za ta yi masa taga ya kafeta da idanu da ƙyar ya ce ""Yaya..."" Ta yi masa shiru tana ja baya kamar zai mata kuka ya rausayar da kai ya ce ""Yaya na ce ban so"" ""Allah Ya baka haƙuri na ɗauka wasa kake yi mini"" yana ƙanƙance idanunsa ya nanata ""Wasa? Moh yana wasa ne yaro ne ni da zan yi wasa?"" Sai ya yi ƙwafa yana banko musu ƙofar" "ɗakin ya fice abin shi. Ammo ta yi murmushi ta ce ""Ikon Allah, Allah Ya rufa asiri""" "Sa'adah ta ce ""Ammo wai me ya ke yi haka ne? Naga har ƙadangare yana daƙƙowa idan fitinarsa ta tashi," "ranar nan fa da ƙatuwar mahauniya na gan shi ya shige cikin ɗakin zaure, akan farar zai fara abu kamar zai mutu"" tsoro duka ya kama Sa'adah, Ammo ita dai murmushi kawai take yi wanda bata saba yinsa ba ""Kinga wallahi zuwa gaba kika ƙara bashi farar nan haɗuwarku ba za ta yi da kyau ba, kin san halinsa ai da gaske baya wasa idan yace baya son abu da zuciya ɗaya yake faɗa, tun yana ƙarami baya son fara da" "ruwan sama wallahi""" "Sa'adah ta yi shiru, Ammo ta ce ""Na harhaɗa abin da zan iya haɗawa na kuɗi anjima ki kaiwa mai aikin" "kayan ɗakin naki Sa'adah """ """To Ammo, Allah Ya ƙara rufa mana asiri. Nima zai kai cikon kuɗin filas ɗin, shikenan Malam ba zai yi" "komai a bikin nawa ba? Haƙƙinsa ne fa?"". ""To jeki tambaye shi mu ji"" Sa'adah ta yi shiru a ranta tana jin" tausayin Ammo sosai. "Mutallab yana fita, ya nemi waje ya zauna har lokacin bai ci abinci ba ya kuma kasa faɗawa kowa yunwa" "yake ji. Haka kawai ya samu kansa da son duba karatun da aka yi, ya miƙe ya shige gida ya ɗakko jakar" "was the first abin da ya fara gani a cikin jakar shine farar takadda ƙarama, da short note a jiki ya nemi waje ya zauna ya warware takaddar a hankali ya fara duba abin data ƙunsa." "_Blackman with beautiful eyes, I love your angry face, I love your i don't care attitudes, I LOVE YOU_" "He reads, yes he reads it, he read the sentences more than ten times, ya sake yin shiru tare da addition" "na numbers ɗin adadin daya ɗauka yana karanta rubutun, babu abin da ya bashi mamaki sai angry face" "ɗin da aka rubuta, shi akwai wanda zai ce yana son shi ne after Jaanah? who wrote it. ? Who wrote this? Who says all this? Yake ta tambayar kansa ya kasa fahimta, bai san mene ya faru ba sai ya ji yana son adana wasiƙar, wanda ya bata title ɗin da _Forbidden message_ haramtaccen saƙo domin bai haɗa" "hanya da irin waɗannan abubuwan ba. Ya jingina da jikin bangon ɗakin nasa, ya rufe ido sai ya ji zuciyarsa na bubbuɗewa tare da tsuke masa a ƙirji, ya juya a hankali zuwa madubin da yake ɗakin ya zubawa kansa idanu, ai yama manta da wani abu da mutane suke halitta a duniya wanda zaka iya ganin biyuninka ta ciki wai shi madubi. Ya zubawa photocopyn nasa ido, yana son hasaso angry face ɗin, but he couldn't ta cikin ƙirjinsa zuwa maƙoshinsa ya ji maganar ta fito “liar” e, maƙaryaciya mana ya san ko waye macace ya sake lumshe idanunsa sai ya ji zuciyarsa na ƙara gutsistsirewa a ƙirjinsa into pieces, ba" akan komai sai akan wannan forbidden message ɗin. "***Fitowar ta kenan daga parlon ciki zuwa main parlor, jikinta sanye da dakakkiyar atamfa ta ji sarƙa a" "wuya, hannunta sanye da zobe. Tunda ta shigo take kallon shi, har ta ƙarasu ta zauna tana ɗaukan remote tana ƙaro gudun ac, ba tare data kalle shi ba ta ce ""ka bashi haƙurin?"" Kimiyya ya juya ya kalli Jeddah ya ce ""Eh"" ta jinjina kai ta ce ""Sai ya ce me?"" Ya yi shiru ya kasa cewa komai kansa kuma a ƙasa, ta ajjiye remote ɗin da take sauya channel dashi ta ce ""Bana maimaita magana ka sani kimiyya"" a hankali muryarsa na rawa ya ce ""Ya ce wai zai biya kuɗin daga baya"" ta yi shiru, irin shirun nan na fahimtar abu kana ta ce ""Kuɗin me zai biya?"" A hankali ya ce ""Wanda kika kashe na makaranta, da duka abubuwan da kikai masa har ma wayar da kika bayar ya ce zai biya"" ta girgiza kai sai kawai ta yi masa banza ta ɗauki wayarta tana dannawa bayan ta harɗe ƙafafuwanta ɗaya kan ɗaya, ya san ba za ta yi magana ba ya ce ""I am sorry Jeddah, ki yi haƙuri, i am so sorry don Allah"" ta ce ""haƙuri na mene kake bani shi har haka?"" Tuni idanunsa ya cika da ƙwalla ya zame daga kan kujerar zuwa ƙasan ƙafafuwanta ya ce ""Shine ya fara share ni, Jeddah kin sha faɗa mini babu kyau shariya ko wulaƙanta Ɗan'adam saboda kowa da kalar" "baiwa da ni'imar da Ubangiji ya yi masa. Wallahi Mutallab ne shine ya fara yi mini""" """Ya yi maka me?""" """Share ni, ya fara wulaƙanta ni""" "Jeddah ta jinjina kai ta ce ""You're not nice, you're not serious, you're not a good person, a good friend," "and you never be. Kai ba abokin ƙwarai bane, kai ba mai rufawa abokinsa asiri bane, ba irin abokin da" "ake fatan samu bane, ba kuma irin wanda ake cewa abokin a kashe a binne bane. Kana proud da kuɗin mahaifinka tunda shine ya bawa kansa ko? Ba Allan daya halicci Mutallab bane ya bawa babanka arziƙi, yana bacci ya farka yaga dukiya a kusa da shi ko? Ashe Islamiyyar asarar kuɗi muke yi, ka manta Ubangiji ke bawa wanda ya so, ya azurta wanda yaga dama, mutum baya taɓa zama hundred percent, shi uban naka ka tambaye shi hundred percent ne shi? Kuɗin shine komai nasa? Kowa daka gani a duniya Kimiyya Ubangiji tuni ya rubuta samu da rashinsa tun kafin zuwansa duniya, so ka yi farinciki ka yi wa abokinka gorin ilimi dana arziƙi, har Annabin Rahama ya bar duniya bai yi irin arziƙin da ake tunani ba, idan ya ci na yau yana fargabar na gobe ne, akwai sanda tsanani ya yi tsanani dutse ya ɗauka ya ɗora a saman cikinsa saboda ya yi masa nauyi ya daina jin yunwa. Batun ilimi, ka taɓa ganin wanda ana haihuwarsa a duniya ya ce A ko B? Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama matse shi akai a cikin kogon hira aka ce masa, iƙƙira ya ce naá ana bi ɗarik. Kimiyya ba wanda ake haifa da iyawa, ba wanda ake haifa da dukiya kowa yana zuwa duniya da al'ƙawarin Allah a tafin hannunsa, kowa yana rayuwa da ƙaddararsa" "ne wacce take bibiyarsa kamar inuwa ka gane""" "Kuka yake yi sosai, Allah ya ɗora masa ƙaunar Mutallab a zuciyarsa ya ce ""Ba zan sake ba, wallahi Jeddah" "sanda na faɗa ba har zuciya bane, i don't meant it, i regret it, Allah don ya ji haushi na faɗa ba zan kuma ba"" ta girgiza ƙafa ta ce ""Ƙarya kake, yadda ka daddage ka gasa masa wannan maganganu watarana ma zaka iya, ai wallahi gori sam bai yi ba, kuma za ka ci gidanku ne"" ya dinga kuka yana bata haƙuri hadda rirriƙe ƙafafuwanta ta ce ""Na ji, na haƙura je ka ɗauki abinci ka ci, Allah Ya tsare ya kiyaye gaba, ya kuma yi muku Albarka bakiɗaya"" Ajjiyar zuciya kimiyya ya sauke yana rungume Jeddah ya ce ""My favourite person as always. I love you"" ta shafa ƙasa sai kuma ta dungure shi ya hantsila ya tashi yana dariya." "Wanka ya yi, ya sanya jersey da wando trouser black ya ɗan kama shi ya taje kansa. Daman ya riga da ya" "yi sallar issha sai ya bararraje akan ƙaton gadonsa yana buga game, wayarsa ce ta fara ringing ya ɗaga ya kai kunne ya ji ta yi shiru sai ya yi dariya ya ce ""Safiyyerh """ """Yes, how are you?"" Ta faɗa a sanyaye cikin sanyin muryar nan nata ya ce ""Allahamdulilah, ke fa?"" Ta" "ɗan numfasa ta wayar can ƙasan maƙoshinta ta ce ""I want to invite you my birthday party"" Ya mirgina ya ce ""Haba dai, yaushe ne kuma? Time, venue? Dress code"" siririyar dariya ta yi mai sanyi ta ce ""Kai fa sai a hankali, wani abu ne dress code?"" Ya yi dariya shima ta ce ""Za mu yi magana gobe, daddy ne ya shirya mini ai amma a gida, ya ce na yi invating duka friends ɗina, both maza da mata"". Kimiyya ya ce ""Amma dai daddy ya duba mana, ki ce mutumin zai zo ya siyi cake abu nasu captain maganin a kwaɓe su"" ta ɓata fuska kamar yana ganinta ta ce ""You are not nice Kimiyya"" ya ce ""I know. "" Sukai shiru gabaɗaya can ya" ce """Yarinya ta girma kin fara amfani da waya iyeee, daman naga kwana biyu sai wani ma sha Allah kike abin" "ki, are you on WhatsApp?""" "Ta ce ""Naaa, ka faɗawa abokinka""" """Wanne abokin nawa?""" """Blackman""" Kimiyya ya tuntsire da dariya sosai shi dai muryarta na burge shi saboda sanyinta har ya yi yawa a "hankali ya ce ""Mutallab ko kike nufi? Ba zai zo ba"" a taƙaice ta ce ""Me ya sa?"" Ya ce ""Nasan halinsa"" nan" "ma ta ce ""Kamarya?"" Ya ce ""Kawai dai ba zai zo ba, kima sakawa ranki haka"" ta yi shiru ya ce ""hy dear"" ta ce ""send me his number, via dm ok""" """Safiyyerh jinin Prof ke yawo a jikinki ko? Magana kaɗan turanci, bashi da waya to ki siya masa""" """Bari mana, turan good night""" "Kashe kiran ta yi, kimiyya ya tura mata number. Sai kuma ya kunna data ya shiga WhatsApp, group zai" "shiga sai kuma yaga kamar Aafiyyah na online ya fara typing ya tura mata ""Hy Aafiyyah"" ta buɗe ta gani sai ta share shi." """Hy Aafiyyah""" """Hy Aafiyyah""" """Hy Aafiyyah "" Ya jera mata lokaci guda yana yin dariya don ya san halinta, emojin ta tura masa na" naushi tare da guntun saƙo kamar haka. “Headache” """Safiyyerh za ta yi birthday""" """Na sani""" """Za ki zo?""" "Sai ta zare masa idanu, ta fara typing ta daina. Ya ce ""Mene?""" """Mele""" """Za ki zo?""" """Maybe. I will think""" "**Safiyyerh ƙwance a ɗakinta saman gado, lokacin ta ci kuka ta ƙoshi tunda ta dawo daga makaranta" "Wahee ta sace score ɗin data samu a class work na math ta nunawa Ummeyh da daddy, ran daddy ya ɓaci sosai ya nemi bulala mai lafiya ya zane Safiyyerh cif numfashinta har ɗaukewa ya yi saboda azabar duka, data buɗe baki za ta faɗawa daddy cewa ita fa karatun ne kwana biyu bata ganewa sai ya daka mata tsawa. Ta dinga kuka kamar ranta zai fita, Ummeyh ma ta yi mata tas ba wanda ya bata listing ears, ta shige ɗaki taƙi fitowa cin abinci akai magariba akai issha shine abin ya damu daddy sosai yana son Safiyyerh kamar rai, ya shigo har ɗakin ya rarrahe ta ya mata alƙawarin birthday party a gobe da daddare" "ta yi invating duka friends ɗinta, hakan ya sauƙaƙawa Safiyyerh damuwar zuriyarta sosai." "Wahee ma ta yi farinciki, captain zai zo dake tafi Safiyyerh shekaru da kuma aji sai ta ji bari ta yi using" opportunity ɗin itama. "Was the first person da Safiyyerh ta fara invited shine Kimiyya, ta kira shi suka fara magana har zuwa" lokacin da yake ce mata; """Safiyyerh jinin Prof ke yawo a jikinki ko? Magana kaɗan turanci, bashi da waya to ki siya masa"" ta dinga" "jin abin da yake faɗa, wanda ita kuma bashi take son jin ba, da yawan lokaci kimiyya ya fiya wasa cikin lamuransa ta ɓata fuska kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce masa" """Bari mana, turan good night""" "Tana zaune a wajan hannunta riƙe da wayarta ta ji notification tana dubawa taga number ce, ya yi saved" "nata da buddy. Ta dinga kallon number sai ta shiga ta yi rename ɗinta da sunan “Bestie” ta samu kanta da fargabar kiransa, domin bata san a yadda zai ɗauki kiran ba ta ji kamar ta haƙura, amma daga dawowarta gida zuwa yanzu da take zaune a kan gado ta azabtu, ita kanta bata san ainahin abin da yake damunta ba. A hankali ta janyo filo ta rungume a ƙirjinta tare da yin dialing numbersa, tana ta ringing ba'a ɗauka ba har ta katse, ta sake kira nan ma shiru a kira na uku aka ɗauka, bayan ɗaukan kiran" "Safiyyerh ta samu kanta cikin tsoro da fargaba, ta sake ƙanƙame filon a ƙirjinta a hankali ta ce." """Hy""" "Bai yi magana ba, ta yi shiru tana jin saukar numfashinsu lokaci guda a hankali ta sake cewa" """Hy"" ""Hy"" ""Hy""" "Ta jera masa har uku, dib.. dib... dib... Kamar tafiyar agogo haka zuciyarta ke bugawa ta cikin ƙirjinta," "tana cure mata waje guda. Ta tattaro duka nutsuwarta ta ce ""Baka ji ba"" bisa mamaki ta ji saukar muryarsa a daƙile ya ce ""Na ji"" motsin da ƙirjinta yi ya saka ta fahimci cewa akwai wata halitta a jikinta bayan ita wato zuciya, wacce take bugawa domin shi, only him. ""Shi ne ka yi shiru?"" Daƙiƙo suka shuɗe" kafin ya ce """Mene hy? Arne ni? By the way, who am i speaking with?"" A hankali ta ce" """Oh! Assalamu Alaika""" "Ya yi shiru ta ce ""Safiyyerh ce""" """Shhh, Safiyyerh? A gender wacce, mace ko namiji?"" Tambayar ta yi mata girma a zuciya da zafi sai ta ce" """Bestienka ce fa, naga yau ka tafi gida da wuri daga makaranta"" ya yi shiru kawai tana ji yana jan" "numfashi ta cikin wayar ta ce ""Ina gayyatarka bikin ƙarin shekaruna, my birthday party""" """Birthday party?"" Ya nanata ba tare daya sani ba. Safiyyerh ta ce ""E bestie, a gidanmu za a yi""" "Kai tsaye ya ce mata ""Ni ba ɗan iska bane to, kar ki sake kirana"" zai kashe wayar ta ce ""Mene ya kawo" "maganar iskanci kuma? Ko zan maka iskanci kuma a gidanmu?..... No No please"" ta dinga masa" "magana ya yi shiru sai kawai ta fashe masa da kuka ta cikin wayar har da ɗan ihunta ta ce ""Wallahi wallahi idan baka yi mini magana ba sai na zo gidanku a daren nan ba tare dasu daddy sun sani ba, ai na san gidan naku ka ji na rantse maka da Allah kuma ka san na isa kaffara, Allah ko wani abu zai same ni a" "hanya sai na zo yanzu a daren""" """Ok, sai kin zo""." MUTALLAB 08164069385 A yi weekend lafiya "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 29: 2 fighters" "Safiyyerh sai ta ji tunaninta ya tsaya cak, wayar maƙale a kunnenta. ""Ok. Sai kin zo?"" Ta maimaita a" "zuciyarta, maimaicin da ta ji ya kusan tarwatsa jaririyar zuriyar dake son girmama shekarunta. Ta yi shiru, she just want to make a sense na abubuwan da suka tattauna tsakaninta da Mutallab, but ta kasa believing abin da zuciyarta take raya mata, idan zuciyarta za ta yi wa adalci dole ne ta yi following" "umarninta, wato bin abin da zuciya ke so, hakan kuma kai tsaye ne da cewa ta je gare shi. Ta duba" "screen ɗin wayar taga ya jima da katse kiran, daman muryarsa ta nuna kamar ya fara bacci, kiran da ta yi" "masa ne ya tashe shi, domin a daƙile yake maganar kamar an tilasta masa yinta bisa dole. A hankali ta" "ajjiye wayar a saman filon data ɗora a cinyarta, ta daddafe kuncinta duka biyun da tafin hannunta." """Na shiga uku ni Safiyyerh""" "Ta furta a fili, ta rasa yadda za ta yi da tunanin zuciyarta, ko rufe idanunta ta yi shi take gani, he saw him," "ganinsa take yi, he saw him with his face angry, and his sexcy eyes." "So take yi ta tabbatar da abin da take ji, duk da ta fahimta, sai sai abin da ta fahimta are different da" "yadda take ji a gangar jikinta. A hankali ta ɗauki wayar ta fara duba numbers ɗin da aka turo mata, ta ɗauki wata number ta kira har kiran ya katse ba'a ɗauka ba, ta sake kira cikin sa'a aka ɗauka a hankali ta ce ""Afuwa na tashe ki daga bacci dear"" ta ce a nutse, wacce ta kira ta ɗan yi shiru can ta cikin wayar ta ce ""Forget about me, ke me kike yi ba ki yi bacci ba?"" Safiyyerh ta ce ""Na saka baccin ne Aafiyyah, will you" "help me please?"" Aafiyyah dake jin Safiyyerh ta cikin wayar ta ce ""Ina ji, ki haɗe tambayoyin a cure""" """Aafiyyah idan mutum zai gane yana son wani ya ake ji don Allah? Amma don't take my question serious" "kin ji"". Ta ce tana marairacewa saboda fargaba. ""Tun da ba serious ba ce, carry your question and leave"" itama Aafiyyah ta bata amsa, da sauri Safiyyerh ta girgiza kai ta ce ""Kin ji matsalarki ai, ba'a magana ta fahimta dake, ina cikin wani hali""" """Kamarya?"" Aafiyyah said." """I think i am in love, na ji kamar na faɗa cikin soyayya Aafiyyah"" ya ɗauki Aafiyyah 30 seconds kafin ta ce" """Uhm, ina ji"". Safiyyerh ta ce ""Ai ban tabbatar bane, so nake ki faɗa mini yadda zan gane kuma na yarda da cewa e, i am in love ɗin, sai na san yadda zan tari aradu da ka, shine kawai"" Aafiyyah ta ce ""Ina aiki yanzu dai kam, amma kin bani mamaki Safiyyerh gabaɗaya guda nawa muke da za ki ce wai kina ji kin faɗa soyayya, ita soyayyar kogi ce da ake faɗawa cikinta? Ina jin yanzu ne za ki yi cikar shekaru goma sha biyar da haihuwa a duniya, ko dan kinga kina da girman da za a iya tunanin kin zarta shekarunki? Ko don kinga kina da kyau eh? Ko dan kin tashi gidan masu kuɗi eh? And don Allah tell me something where is your dreams? Ina mafarkanki suke? Ina long and short term goals ɗin ki da kika yi wa kan ki tsari, ki ka yi" "wa kan ki planing to achieve? Where are they? Ina kika yi keeping nasu?""" """Aafiyyah, i don't know what come over me, koma dai mene na fahimci a yanzu karatu ba shine tsarina" "ba, idan abin da zuciyata ke raya mini zan yi to babu karatu Aafiyyah, bani da wani plans da zan yi achieving nasu Da gaske"" sai kawai ta fashe da wani irin matsanancin kuka, Aafiyyah ta yi shiru tana" "sauraren kukan da Safiyyerh ke rera mata ta cikin wayar, tana shassheƙar kuka ta ce ""Kamar na samu matsala haka na ke ji, ko idanuna na rufe bana ganin komai sai idanunsa wanda suke faɗa mini abubuwa da dama, Aafiyyah i know nothing about the love, but a name, sunan kawai. Ba za ki gane ba, farkon sunansa idan na ji zuciyata bugawa take, ina son hira da shi, ina son ganinsa kusa dani Ban san me" "hakan yake nufi ba, i really really don't know, i don't understand!""" """This is what we call love and romantic. Ga amsar ki nan""" """Amma wa kike so haka?"" Aafiyyah ta ɗora da tambayar. Kamar Aafiyyah na gaban Safiyyerh ta girgiza" "mata kai ta ce ""Secret crush, zan faɗa miki not today not tomorrow ƙila watarana"" duka suka yi shiru, kowa kuma da tunanin da yake a cikin zuciyarsa, saboda hira suke a nutse they act as matured as other people, a maganganunsa ba zaka tsinci ƙuruciya ba. ""Uhm Safiyyerh kenan, shikenan?"" Safiyyerh ta yi murmushi ta ce ""wanne kalar cake kike ganin zai fi kyau?"". ""Za mu yi magana gobe idan muna raye a" "makaranta, and i will tell you something"" sai da safe suka yi wa juna kana suka kashe kiran gabaɗaya." "After a called, Safiyyerh ta yi shiru tana tunani ta rasa yadda za ta yi da zuciyarta. Ta miƙe a hankali tana" "ajjiye wayar daga ita sai kayan bacci ta buɗe ƙofa, ƙafarta sanye da bedroom slipper ta sauka zuwa" "downstairs, waje ta nema a parlon ƙasa ta zauna watching a movie, sai dai ta raba hankalinta gida uku, ɗaya a kallon, ɗaya a tunanin Mutallab, ɗaya a ɓangaren daddy." """Safiyyerh""" "Ta yi saurin juyawa taga Ummeyh ta caɓa uban ado, tana sanye da wasu kayan bacci masu masifar kyau" "sai ɗaukan ƙamshin kwalacca da humrar da ta yi order a wajan S Bayero take yi, hannunta riƙe da wata ƴar ƙaramar ruba ta zuma. Bayan Safiyyerh ta kalli Ummeyh sai ta ɗauke kai ta ji haka kawai ranta ya fara ɓaci, Ummeyh ta ce ""Me kike yi a cikin daren Safiyyerh?"" Da hannu Safiyyerh ta nunawa Ummeyh" "t.v lokacin an hasko wasu masoya rungume da juna, wanda a shekarun Safiyyerh bai ci ace tana kallon" "irin waɗannan movies ɗin ba. ""Idan kin gama ki kashe ki je ki kwanta, zan shiga wajan daddynki""" """Sai ki fito yaushe? Ko sai da safe?"" Safiyyerh ta tambayi Ummeyh har lokacin kuma bata kalli Ummeyh" "ba. ""Eh, sai da safe""" """Miji daɗi, Ummeyh kina son daddy da yawa, nima in sha Allah haka zan so nawa mijin fiye ma dake,ni" "idan na shiga ɗakinsa ma ba zanna fitowa ba""" """Sai ki haɗiye shi"" Ummeyh ta bawa Safiyyerh amsa, ta ɗora da faɗin ""Ƴar ƙaramar ki dake kin riƙe sunan" "miji ba tare da sanin ma'anar ta ba ko Safiyyerh?"" Safiyyerh ta juyo a lokacin ta kalli Ummeyh da idanunta da suke lumshewa ta yi murmushi ta ce ""Ummeyh kenan""." """Ban gane ba, kwalliyar tawa ce ba ta yi ba na sauya ko mene? Prof yana son jambaki da ƙamshi sosai," "duba mini kiga"" ta faɗa tana jujjuyawa a gaban ƴarta ta, Safiyyerh ta ce ""Shi jambakin zai kai Safiya ne a" "bakinki? Kin yi kyau sosai Ummeyh, Allah Ya nuna miki nawa auren"" Safiyyerh ta faɗa, tana jin wani abu na bin jikinta sosai. Ummeyh ta ce ""Amin ɗiyar arziƙi, goodnight""" """Goodnight""" "Safiyyerh na zaune tana kallon zuciyarta na sake jaddada mata cewa ""Follow your heart Safiyyerh"" ta" "ɗaga idanu ta kalli lokaci taga ai shabiyu na dare ya shige, ta fara tunanin idan ta nemi alfarma wajan Wizzy zai kai ai secretly ba tare da daddy ya sani ba, ta miƙe ta nufin hawa saman bene ta sako after dress sai taga Wahee ta sakko ƙas da alama ruwa ta sakko sha, cikin sauri ta fara murza idanu alamar bacci take yi, kallo ɗaya Wahee ta yi mata ta ɗauke kai ta nufi wakan deep freezer dake gefe guda." "Al'amarin daya tilasta wa Safiyyerh haƙura da zuwa ganin Mutallab, takaicin hakan ya saka ta ji hawaye" "masu zafi sun cika idanunta, gishirin da ta ji a bakinta ne ya saka ta fahimci hawayen ya samu damar" zuba da kansa ta miƙe ta nufi bedroom. "***Mutallab bayan ya gama duk abin da ya ke yi, ya je wajan Malam yi masa sai da safe ya yi masa" "banza, ya leƙa ɗakin Ammo ta tarar ta yi bacci suka haɗa idanu da Sa'adah ta yi saurin ɗauke nata idanunta, ya buɗe ido sai kuma ya ce ""Sai da safe Yaya"" ya juya ya nufi ɗakin zaure, ya barbaje tarkacan abubuwansa a gaba, hadda farin goro da wata wuƙa da ya yi rubutu a jikinta da tawada, wani kwalli yake son haɗawa daya binciko sirrinsa so yake ya tabbatar ko sirrin zai yi aiki. Bayan ya kammala haɗa kwallin ya zaro layoyin ya caccaka musu allurai a kai ya ajjiye gefe guda. Rigar jikinsa ya cire, har zai kwanta ya sake cire singlet ɗin ta ciki ya lumshe idanunsa jin iska ta ratsa shi wacce ta shigo ta tagar waje, ƙirjinsa a" "bubbuɗe ya sha ƙirjin ya buɗe ido, jin alamar kwantaccen gashi, ya tsuke fuska." "Ya dudduba littafansa na makaranta ya yi dukkan assignment, har zai kwanta sai ya tuna da wasiƙar nan," "ya ɗakko ya sake karantawa shi dai rubutun jiki ya na saka masa nutsuwa haka kawai, ya mayar ya ajjiye ya raɓa gefen tabarmar ya kwanta ya lumshe idanunsa, maganganun Kimiyya suka fara rige-rigen dawowa cikin ƙwaƙwalwarsa a hankali bacci ya ɗauke shi. Sama-sama ya fara jin vibration a ɗan nesa da kunnuwansa, bai buɗe idanunsa ba sai ɓata fuska da ya yi baya son fara bacci ya tashi gashi yana da nauyin bacci shi ya sa yana jimawa bai kwanta ba, vibration ɗinne ya cigaba da yi yaga dai za'a addaba masa, ko idanu bai buɗe ba ya miƙa hannu ya janyo wayar ya ɗaga ya yi shiru, wanted to hearing from the person, haka kawai jikinsa ya basa ita ce, no one but her. He got it right domin muryata ce ta sauka a" kunnensa inda ta ce. """Hy""" "Sarai ya jita sai ya yi shiru, ya kuma kasa kashe kiran, dalilin tashinsa ba gaira ba dalili yake son ji. Ta" "dinga magana har sanda ta ce yi maganar bikin ƙarin shekarunta, ya ji mamaki ƙwarai ƴar ita za a yi wa birthday? Iyayenta kuma su zuba idanu, kodayake ai ɗiyar Professor ce su masu kuɗi komai a wajansu lafiya lou ne. Amma mene haɗin namiji da sabgar mata? Iskanci ne kawai. Tsaki ya ja a ƙasan ransa jin yadda take kuka ba gaira babu dalili saboda sangarta da lalacewa irin ta yaran masu kuɗi. A hankali ya ce ""Ok. Sai kin zo"" yana faɗin hakan ya kashe kiran can ya kashe wayar bakiɗaya, tsaf zai mayar da wayar" "nan idan za'a addabi rayuwarsa don dai karatu kawai zai yi da ita, kuma ko ɗazo ta yi masa amfani." Ajjiye wayar ya yi ya juya tare da rungume hannunsa a ƙirji kamar yadda ya saba a haka bacci ya ɗauke shi mai nauyin gaske. "Bai sai ya aka yi ya makara bayan ya yi sallah ba, bai kuma san lokaci ya ja ba sai tsinkayo muryar Sa'adah" "da ya yi a cikin kansa, tana tashinsa a bacci, ta dinga kiransa yaƙi ko motsawa sosai yake jinta ko idanunsa ya kasa buɗewa, ta hau jijiiga shi tana faɗin ""Auta, Auta zaka makara a makarantar da kake zuwa fa, ka tashi takwas ta kusa"" bai san me ya ce mata ba sai ji ya yi ta ce ""Makarantar ce babu yau?"" Ya mata shiru. Miƙewa ta yi ta koma cikin gida ta samu Ammo ta haɗa kunu tana juyawa bayan ta ƙara gasara ta ce ""Ammo Muhammad fa yaƙi tashi, kuma zai makara a makarantar"" Ammo ta kalli Sa'adah" "kafin ta ce ""Ina ruwana kuma? Kika sani ko wani abu ya sha haka?""" """Wani kalar abu zai sha da zai dinga bacci ko motsi ba ya yi? Ammo mugun fata ne irin wannan wallahi" "irin wannan maganganun suna tasiri akan yaro ,""" """Bani waje Sa'adah"" Ammo ta ce tana yin cikin ɗakinta, domin zaman ci da kai suke yi a gidan." "Sa'adah ta koma cikin ɗakin ta same shi a ƙwace, ta daddage ta kira sunansa da ƙarfi, ya runtse idanunsa" "sai kuma ya mirgina tare da waigowa ya zubawa Sa'adah idanunsa, da suke lumshewa suna buɗewa, ita kuma Sa'adah mamaki ne ya cika mata zuciya ganin yadda Mutallab ya buɗe ƙirjinsa ya yi faɗi ga gargasa ƙwance a ƙirjin. Ta tsinkayi muryarsa a kanta ""Yaya idan na miki Allah Ya isa fa? Ki ce bani data ido haba Yaya"". ""To me na yi? Kai da ba a yi maka abin arziƙi"" ya ƙanƙance idanunsa ya ce ""Tsaraicina mana, yaya tsaraicina me ya sa za ki mini haka?"" Maganar ta girmame ta ya saka ta miƙe ta ce ""Masifaffe..."" Ta ce tana yin waje, ya haɗe fuska tamau can ya miƙe ya zira riga cikin ƙaramin lokaci ya yi wanka, ya shirya cikin uniform ɗin, yana mamakin yadda kullum Sa'adah bata gajiya da wanke masa su ta goge don ma kala biyu ne da shi. Cikin gidan ya nufa, ya durƙusa har ƙasa ya ce ""Ina kwana Ammo?"" Bata kalle shi ba" "ta ce ""Lafiya. "" Ya yi jim ya ce ""Ki ma yaya magana ta daina bana so"" ta ce ""Me ta yi maka?""" "Da sauri Sa'adah ta ce ""Ba abin da na yi masa daga tashinsa daga bacci fa shikenan""" "Ya wani kalleta sheƙeƙe, yana nutsar da idanunsa ciki ya ce ""Da daɗi na zo na buɗe miki riga kina bacci," "da daɗi na kalli ƙirjinki, me ya sa za ki kalli nawa"" ya faɗa da tsantsar gaskiyarsa jin maganar ta girmama ya saka Ammo cewa ""Tashi ka bani waje"" ya dinga kallon kunnun dake kofi, shi ba zai taɓa cewa a bashi ba ya miƙe ya fice a zaure ya ci karo da Aby ya ce ""Sannu Aby"" ""Yawwa ɗan'uwan turji saura zama yaronsa sai ka cigaba da kisan kai hankali ƙwance"" Mutallab ya yi ficewarsa domin ya saba da irin" wanɗannan maganganun. "Bayan fitarsa Ammo ta ce ""Sa'adah kina rayuwa da Mutallab ba ki san halinsa ba, kin san dai ba baki zan" "saka muku ba, bashi da wasu abokai a cikinku mata ya tashi, sai mu yi farinciki da bai zama ɗan daudu ba, ki cigaba da ya yi masa abin da baya so, ya miki da kirki ba da yake nanata miki baya so, ina mai tabbatar miki watarana zai ɗage rigar daga nan sai ki shirya bashi dukkan amsar tambayoyin da zai miki"" Sa'adah ta ce ""Yanzu shi sai ya ɗaga mini riga? Kamar mara hankali "". ""To hankalin ne da shi? Ki faɗa mini mata nawa ne a gidan nan kafin shi? A cikin mata nawa ya tashi, abubuwa nawa kuke yi a gabansa a kan idanunsa? Bai san wasu ɗabi'un masa yan'uwansa ba sai naku kawai dai Allah ne ya kissima masa wasu ɗabi'un, tun yana ƙarami yake sanya ku a gaba da tambayar abin da bai sani ba, kina nan aka faɗa mana cewa yana da taɓin hankali"" ta ƙare maganar a raunace, hawaye ya sakko idanun Sa'adah gabaɗaya ta manta cewa yana da taɓin hankali, ta dinga kuka Ammo ta yi mata shiru ""Yanzu ba za ki bari a faɗawa Anty Hameeda ba?"". ""A hir ɗinki, a kul na kuma ji, ko da wasa kika bari wannan ƴar ta ji maganar nan sai" "ranki ya ɓaci""" "He late, don haka kai tsaye ya nufi cikin ajin ya ci sa'a babu teacher fuskarsa kamar ya ce ya shiga uku, ya" "nemi waje ya zauna yana duba abubuwan da aka yi sai ya ga ba komai. Safiyyerh ta kalle shi a hankali ta ce ""How are you bestie? Ka makara ka jira bulala"" bai kulata ba, littafin daya gani a gabanta ya saka yatsu biyu ya janyo yana jingina da jikin desk ya fara duba note ɗin, duk inda bai gane ba sai ya rubuta a" "bayan littafinsa, ta matsar da fuskarsa tana yin ƙasa da kai ta ce ""Are you just coming...?""" """Hmmm""" """Laa, ka je ka saki baki da hanci kana ta bacci ai, na ji hakan ai a zuciya da jikina, Yaruba boy"" ya ajjiye" "littafin tare da sun kuyar da kansa, itama ta sun kuya tana leƙa shi ƙamshin turaren da take yi duk ya" "dame shi ""Bestie. "" Calmly ta kiranye shi, sai taga ya juyo ya kalle ta, suka haɗa idanu sosai Safiyyerh ta ji wani irin abu ya gilma a zuriyarta, zuriyarta ta dinga motsi a ƙirjinta da ƙyar ta sauke ajjiyar zuciya kuma har lokacin cikin idanunsa take kallo a hankali ta ce ""Ka zama abokina, kaga kowa yana da aboki ka" "ji don Allah"" ta marairace fuska sosai." "Ya zazzaro mata ido, itama ta zazzaro masa idanunta ya daƙile ya ce ""Dai na kallona""" """Daina kallona""" """Kee...""" """Kai...""" "Ya lumshe idanunsa, itama ta lumshe ""Hmmm"" itama ta ce ""Hmmm"" sai kuma ta yi murmushi ta ce ""As" "far as zaka ke hirar kurame dani, i will do the same nima. Na kira ka jiya fa"" shi dai kallon mara hankali yake mata don haka sai ya biye mata, tunda a ce zama lafiya da mara lafiya ka biye masa ya yi abin da yake so. Zata sake yin magana teacher ya shigo wanda yake ɗaukar su Agriculture. Bayan gama Agriculture duka students suka fita, Kimiyya ya ƙarasu yana cewa ""Birthday girl, yau kin buga sammako ykk ko?"" Bata kalle shi ba, attention ɗinta yana kan Mutallab ta ce ""Kimiyya kenan"" ya ce ""Ba wani kimiyya, ya shirye-shirye? Ƙarfe nawa ne sabgar kin san ina son abubuwan nishaɗi sosai, i like and i love entertainment"" ta zaro invitation a side ɗin jakarta ta kalli Mutallab ta ce ""First card, first invite, first" "person is you bestie, ina invating naka birthdayna""" "Ya amsa ya ajjiye kawai, not looking at her. Kimiyya ya ce ""Safiyyerh ya za'a yi ne?""" """Game da me?""" """Wallahi ina son Aafiyyah, sosai""" "A hankali Mutallab ya ɗago kai ya kalli Kimiyya, yana ƙara nanata abin da Kimiyya ya ce ""Wallahi ina son" "Aafiyyah, sosai "" ya yi shiru sai kuma ya miƙe gently hannunsa ɗaya a aljihu zai fita Kimiyya ya ce ""Ina zaka? Ana shirye-shiryen birthday party?"" Bai kula Kimiyya ba ya saka kai ya fice, siririn tsaki Aafiyyah ta saki tana ƙarasawa wajan su ya ce ""Aafiyyah ɗan bi bayan Mutallab ki kira mana shi"" ta yi masa banza ya dinga magana ta share shi. Yana fita Aafiyyah ta kalli Safiyyerh, Safiyyerh ta ce ""You came early today, akwai magana ne?"" Gira Aafiyyah ta ɗaga mata, sai kuma ta yi ƙasa da murya ta fara mata magana secretly a ɗan raunace, Safiyyerh ta dinga kallon Aafiyyah sai ta kasa ce mata komai ta yi shiru, a hankali ta ƙara kallon Aafiyyah sai ta sauke ajjiyar zuciya tana murmushi ta ce ""Ok, dear"" kafaɗa Aafiyyah ta ɗaga" tana barin wajan zuwa cafeteria bayan fitar ta Safiyyerh ma ta miƙe ta fita. Mutallab yana zaune ya lumshe idanunsa yana jin yadda cikinsa ke yi masa ƙugi alamar yunwa """Bestie. "" Ya buɗe ido Kimiyya ya ce ""Buddy ana neman shawararka fa akan batun birthday"" ya buɗe" "ido sosai ya dinga kallon su kana ya ce ""Me?""" """Zaka zo ai?""" """No"" ta ce ""Me ya sa"" kai tsaye ya ce ""Mene birthday? Na waye? Me ake? No please"" Kimiyya ya dinga" "murmushi kafin ma su ƙara magana ya tashi ya bar wajan. A hanya suka yi karo da Captain ya yi masa wani ban zan kallo yana mai jin takaicin yadda Safiyyerh ta ɗauki labarin ɗan talakawan nan very serious. Cafeteria shima ya shiga, yana shiga kuma suka yi ido huɗu da Aafiyyah dake zaune saman kujera, ta ɗan jingina bayanta da kujerar sai marairace fuska take yi, da alama Vcall take yi, ganinsa kuma ya saka ta haɗe girar sama data ƙasa, ita tunda score ɗinsu ya zo ɗaya ta ji bai yi mata ba, kamar zai ƙwace mata" "matsayinta a class ɗin, dama daga ita sai Safiyyerh." "Shi ɗin ma, kallon tsautsayin da ya yi mata bai sake yi ba, tana zaunen ta ganshi hannunsa riƙe da ruwa," "kamar mai takalarta haka ya ja kujerar dake fuskantar ta ya zauna, ya ɓalle ruwan yana kai wa bakinsa sai kame fuska take, bayan ya gama shan ruwan ya ajjiye ya dinga buga game a waya hankali kwance, yama manta da batun ta. Ta miƙe tsaye tana ƙara ja masa tsaki, ta zo gilmawa ta kusa da shi, ya saka ƙafarsa ɗaya ya taɗeta tare da murje yatsun ƙafarta guda biyar da suke cikin takalmi. Luu ta yi ta gaba zata kifa da fuskarta, ya ƙara saka mata ƙafa ta gaban sai ta yi baya daɓas ta koma ta zauna kan kujerar da take, cikin wani irin firgitaccen yanayi Aafiyyah ta ɗago idanunta da suka yi wani irin jaa, da sauri ta sunkuyar da kanta tana haɗiye wani irin abu, ta sake ɗago kai taga ya ajjiye wayar ya harɗe hannayensa" a ƙirji ya zuba mata idanu. """Are you mad? Wani irin banza ne kai shasha mara lissafi da tunani? Ni ka sakawa ƙafa na faɗi?"" Magana" "ake mata ta cikin wayar, sai kawai ta yi cilli da wayar tana nuna Mutallab daya kafeta da idanu ta ce ""Useless, kuma sai ka yi ladamar abubuwan da ka yi, har kana jin kai wani ne? Ɗan wahala kawai cima zaune"" masifa take yi ta ƙarfin tsiya har su Captain su Kimiyya suka shigo, Safiyyerh ta tsaya gefen Mutallab wondering me ya yi mata haka, Captain ransa fes, kimiyya kuma sam bai ji daɗi ba. Duk masifar da Aafiyyah ke yi idanunta yana ƙasa, shi kuma yana kallon fuskarta sai kaɗa ƙafa yake yi. Ta ja tsaki ta ce" """Stupid!""" "Duk kiran sunan da Safiyyerh ke masa bai kalleta ba, sai bayan fitar Aafiyyah ya juya suka haɗa idanu, ya" "sauke ƙafarsa ya duƙa daidai kanta ganin tana kuka a hankali ya fara mata magana ita kanta da ƙyar take jin me yake cewa can ta ce ""Zaka zo ɗin? Ƙarfe 8 ne, don Allah ka zo, zan yi kuka na kwana ina yi idan baka zo ba""" """Mene sunan ma?""" """Safiyyerh""" """No, rage masa tsayi FIYYA is ok for me, zan yi tunani, amma don Allah ki daina takura Mutallab, ki daina" "bibiyar Mutallab, tsakani da Allah nake faɗa miki yanzu bana son mutum mai naci, kai na juyewa yake, tunda na zo makarantar nan ba ki bar ni na yi numfashi mai kyau ba tare da addabawarki ba, a sanda na zo kuma na fara tattala maganganun da zan faɗa miki, sai yanzu suka kammala, i so much respect a woman, a girl, a mother, so i respect you Fiyya, wallahi bani da hankali da kike gani na, bana wasa ba wasa nake faɗa miki ba"" ya faɗa yana ɗaɗɗage girarsa tare da cure su. Safiyyerh ta dinga kallonsa, a" "kullum abin da take ji game da shi ƙaruwa yake yana habbaƙa a ƙirjinta tare da yin yaɗo. Sharrr, hawaye" "suka fara sauka daga cikin idanunta, sai kuma ta ji dama za ta iya duka hakan, dama zata iya, inama zata" "iya, how? Never. She failed as a girl. Ta fashe da kuka." Sai kuma ta miƙe tsaye ta saki murmushi mai tafe da dariya tana girgiza masa kai a hankali ta dinga ja da "baya, tana dariya tana hawaye yar ta kai ƙarshen cafeteria ɗin, ta ɗage masa gira itama ta ce ""What if i told you, I love you?"" Sai ta fashe da dariya, a lokacin ita tama manta a cikin makarantar suke, ta manta a gaban students suke, ta manta she is under age, ta manta cewa lokacinta bai kawo ba, ta manta karatu ta zo yi, ta manta ita ƴar gidan Professor Abdu ce, ta manta cewa Ita ƴar gidan Dr Ummeyh ce, ta manta ko zata mutu a yanzu ta farko babu wanda zai amince ya aurar da yarinyar mai shekarunta. Tana yin" "abin da take jin shine daidai, tana following zuciyarta ne wanda matakin Adolescencet stage ke" ɗawainiyya da ita. """What if I told you, i love you bestie? What if..... What if. Eh?"" Ta saka hannunta a fuska ta shafo" "ruwan da ta ji mai zafi a saman fuskar, ta ɗan waro idanunta tana dariya ta ce ""Ohh Allah! I am crying, Safiyyerh is crying "" Ta yi kamar zata fita daga cikin cafeteria ɗin, sai ta matsa kusa da Mutallab wanda" "kansa yake ƙasa yana game, ta saka hannunta ta dungure masa kai sai kuma ta ce ""Ina jiran zuwanka" "gidanmu, kai ne zaka yanka mini cake, ko dai ka zo ko kuma ni na zo har cikin gidanku, lastly i said what if you told you, I love you?""" "Ya ɗago ya kalleta, da a ce Safiyyerh ta san Mutallab nada taɓin hankali da ba zata tsaya yi masa ihu aka" "ba, ta harare shi ta ce ""Yaruba boy """ "Tana fita ta nufi class, Kimiyya ya sauke numfashi ya kalli Mutallab ya ce ""Ka ji daɗi abin da ka yi?""" """Hmm"" kawai Mutallab ya ce yana miƙewa, ƙofar cafeteria ɗin Kimiyya ya kalli Aafiyyah dake murza idanu ya ce ""Mene ya samu idanun naki ya yi ja?"" Ta ɗan tsuke fuska ta ce ""Ƙwaro ne ya faɗa mini ciki"" Ya jinjina kai, Mutallab ya yi shigewarsa. Bayan tashi, Safiyyerh kamar ba ita ta yi kuka ba, suka fito tare da Mutallab da Kimiyya zuwa harabar gidan, a daidai lokacin suka hango Aafiyyah a gaban wata mota Ash ta ƙanƙame wani, wanda ta ƙanƙame ɗin yana ta ɗan bubbuga bayanta can kuma ya buɗe mata ƙofa" ta shiga shima ya shiga driver ya ja su. "Tun daga nesa Daddy ya zubawa Mutallab idanu, ya ji zuciyarsa ta kumbura yanayinsa ya rikiɗe sosai ya" "yi sauri ya fito Safiyyerh ta ce ""Daddy kai ne?"" Bai mata magana ba sai Mutallab da yake kallo, kai gaisuwar kimiyya bai amsa ba ya ja hannun Safiyyerh zuwa cikin mota, Mutallab ko inuwar daddy bai kalla ba shima, ya matsa can. Daddy na kallon Safiyyerh bayan ya ta yar da mota ya ce ""Waye wancan dana ganku da shi?"" Ta ce ""Wa?"" Ya ce ""Baƙin"" kai tsaye ta ce ""Ok, ban san shi ba ai yau na fara ganinsa""" "ya jinjina mata kai daman ya san Safiyyerh ba zata taɓa kula maza ba, balle wannan kangararren yaron" "ya ce ""Good, koda wasa bana son naga kina magana da shi, abin da ya saka na miki magana naga a makarantar yake duk da na ji mamakin ganinsa a makarantar masu kuɗi haka, Safiyyerh kula wannan yaron shine abu na ƙarshe da za ki yi mini na ji zan iya sallama ki"" ta runtse idanunta tana ambaton sunan Allah. ""Kin ji?"" Ta jinjina kai domin bata jin tana da sukuni yin magana, data buɗe bakinta za ta iya cewa ""Daddy he is the one i love, daddy he is the one i pray for. Daddy he is the one da nake son" "rayuwa da shi, irin rayuwar da kuke yi a gida, a cikin ɗaki kai da Ummeyh"" a haka suka bar makarantar." "***Mutallab na gida a zaune aka ce ana kiransa a waje ya yi sak sai kuma ya miƙe tsaye ya fita, wata" "babbar mota ya gani sai ya cake yaƙi ƙarasawa a hankali mai motar ya fito cikin shiga ta alfarma yana murmushi ya kalli Mutallab ya ce ""Barka, kai ne Mutallab ɗin?"" Ya jinjina kai ya ce ""Ma sha Allahu, aiki muke buƙata muke so ka yi mana, na zo ne domin na shaida maka zuwa dare zan dawo aikin kuma na mai gidana ne"" Mutallab ya sake jinjina kai mutumin ya ce ""To da kyau, sai na zo"" ya shiga mota" Mutallab ya koma cikin gida. "Aby ya samu yana surfawa Ammo masifa har da kumfar baki yana faɗin ""Ni fa yaron nan ba zai ɗakko" "mini magana ba, na rantse da Allah ban haifi wanda zai saka mini hawan jini ba, balle ya saka zuciyata bugawa. Tsinannen yaro la'ananne wanda bashi da wani amfani, ƙiris nake jira ka tattara ka bar mini gidan nan"" ba ta yi magana ba, sai Sa'adah ce ta ce ""Yanzu me Mutallab ɗin ya yi maka Malam? Ɗanka ne fa zaka iya zama da shi ka ji damuwarsa ka ji mene ya saka yake yin abin da yake? Me ya sa ɗabi'unsa suka sauya ai da ba haka yake ba"" Malam ya ce ""Ubanwa zan ja a jiki? Ya cinna mini wuta nima? Ai yafi" "ƙarfina wannan da kike gani""" """Innalillahi, ya zaka haifi ɗa a cikinka ya fi ƙarfinka Malam""" """Ni dai ya fi ƙarfina shi ya sa na tattara shi na watsar, aure ma zan yi wallahi, wannan ɗakin na zaure fita" "za ka yi kamar shi, ga can wata bazawara na yawo sakin wawa a gari ita zan auro""" """Malam yaushe kake ciyar damu? Ba abinci, ba magani, ha suttura amma shine kake cewa za ka yi aure?" "Kana da kuɗin auren ka bar mu haka cikin ƙangin rayuwa da yunwa? Ka mance mutuwar Muneeberh? Haba Malam"" Sa'adah ta faɗa tana kuka, ya ɗauki bulala ya zarara mata a baya ya ce ""Muneeberh ga wanda ya kashe ta nan, kuma Allah Ya isa kashe mini yarinya daka yi"" yana cewa haka ya fice. Mutallab ko motsi bai yi ba, sai danna waya yake yi, Ammo ta kalli wayar tana mamakin inda ya samu sai ta kasa" tuhumarsa yana ta zaune har akai kiran magariba ya miƙe tsaye tare da yin waje abinsa. "***Safiyyerh tuni ta mance ta batun daddy da gargaɗinsa, ta shige ɗaki tana ta shirye-shirye, Wahee ma" "haka. Sai da aka yi kiran sallar magariba ta fito tare da sakkowa ƙasa. Ummeyh ta ce ""Da dai kin ci-gaba da zama a ɗaki sai a zo a tarar dake haka, tuni an gama yin decorations. Murmushi ta yi wa Ummeyh sai" "kuma ta leƙa wajan decorations ɗin ya yi masifar kyau, Black and white." """Ga rigar ki can""" """Ummeyh ina tawa?"" Safiyyerh ta kalli Wahee, Wahee ta harareta. ""Ba Black ce taki ba?"" Ummeyh ta" "tambaya ta ce ""To tana cikin bedroom nawa, ku je ku shirya sai na yi muku rolling ko? Safiyyerh ko kina son makeup?"" Ta girgiza kai ta ce ""No Ummeyh""" "Farar duguwar riga gown Safiyyerh ta saka mai buɗewa wacce ta zauna cif fa ita a jikinta, hatta ƙirjin ya" "zauna a gidansa Ummeyh ta yi mata rolling kamar Balarabiya, Safiyyerh na son Abaya sosai, bata da wasu kaya sai so. Ummeyh ta kalleta ta ce ""Ma sha Allahu dear, kin ga yadda kikai kyau? Sai dai girma ya zo ba hankali kalli jikinki fa?"" Safiyyerh kallon Ummeyh kawai take yi wai bata da hankali. ""Ai Friends ɗin" "sun fara zuwa, naga ƙawarki mai fara'ar nan?"" A hankali ta ce ""Kinal"" Ummeyh ta ce ""Sure, ita""" "Hannunta riƙe da waya ta fita kowanne tables an shirya abubuwa, hatta wajan zamanta har cake ya" "zama ready ta yi murmushi ta ce ""Kinal, your welcome"" ""Thank you"" Nahyan ya ƙarasu da wasu class mates ɗin nasu ganin Captain is here too, ya saka ran Safiyyerh ɓaci, ita ai bata ce ya zo ba. Ta kalli Kinal ta ce ""Ina zuwa"" Kinal na danna waya ta ce ""Take your time dear"" wajan duk ya fara cika da mutane yaran masu hannu da shuni kowa ka gani a wajan ɗan gata ne, daga mazan har matan shigar baƙaƙen kaya sukai, cold music na tashi a hankali. Cikin sauri ta kira Kimiyya yana ɗagawa ta ce ""Baka zo ba?"" Ta cikin wayar ya bata tabbacin yana hanya, sai ta samu relief da tunanin suna tare da Mutallab. Tana tsaye a wajan wata baƙar mota ta yi parking, Aafiyyah ce tunda taga an daɗe ba'a fito ba, Safiyyerh ta ƙarasa wajan ta leƙa ta ce ""Yaya"" ya ce ""Birthday girl, mu ba'a gayyatar mu a wajan?"" Ta ce ""Ku ai ƙatin ƙatinne"" ta faɗa tana kallon Aafiyyah da ta yi luff a cinyarsa ya ce ""Lallai, to Allah ya raya ki ƴar nan. Ina Aliyu?"" Ta ɗan yi shiru sai kuma ta ce ""Baya nan"" ya ce ""As always. Ke ɗaga ni"" ya faɗa yana ɗago Aafiyyah, ta" "tashi tare da zaro shade glasses ɗinta ta saka a idanunta ya yi mata kyau sosai, ta buɗe mota ta fito, Black ɗin abaya ce a jikinta expensive one, hannunta riƙe da L&G handbag, sallama ya yi musu ya juya" "Safiyyerh ta ce ""Sai yanzu?""" """Na koma kenan?""" """A'a ban ce ba"" suka tsaya a jikin wata bishiya dake harabar wajan, daidai nan drivern Kimiyya ya shigo" "wajan, a daidai nan shima ya buɗe ƙaramar ƙofar gidan ya shigo, yana cika da batsewa, at the same time kuma wasu manyan lafiyayyun ƙadangaru suka rikito kan su Safiyyerh ɗaya ya shige cikin rigar Aafiyyah, ɗaya ya sauka a saman fuskar Safiyyerh. Safiyyerh ta saki wani gigitaccen ihu tana kiran sunan daddy, ƙadangaren ya sake mannewa a fuskarta, Aafiyyah kuma ajjiyar zuciya ta sauke jin kai tsaye cikin rigarta ya shige, ta cake waje guda ta kasa motsi. Yadda take tsuma ita kaɗai ya ja hankalinsa, ya kuma dubi yadda Safiyyerh ke ihu tana neman shiɗewa ya yi kamar ya share sai kuma ya ƙarasa wajan, yana zuwa Safiyyerh numfashinta na ɗaukewa a hankali ya ce ""DEER. "" sai kuma ƙadangaren ya samu ya sauka ya" "yi baya da gudu, ya ɗaga kai ya kalli Aafiyyah suka haɗa ido, ya kalli ƙirjinta dake ta motsi alamar ƙadangaren na ciki kuma kamar bashi kaɗai bane a hankali ya sake cewa ""TIGER. "" Sai ya nufeta yana" "zuwa ta cafke hannunsa, ta riƙe ƙam zufa na yanko mata, cikin sauri kuma Safiyyerh ta miƙe bata ma kula da shi ba, a gigice ta nufi ƙofar fita, tunda taga kimiyya shi ɗaya to ba zai zo ba kuma ta yi alƙawarin zuwa har gidansu. A hankali Mutallab ya kalli Aafiyyah dake kallonsa, ya sake duban ƙirjinta sai kawai ya saka ɗaya hannunsa ya cafko ƙirjin gabaɗaya, hakan ya yi daidai da shigowar motar daddy kuma kai tsaye ganinsa ya sauka akan fuskar Mutallab da hannunsa dake riƙe da ƙirjin Aafiyyah ita kuma ta riƙe" hannunsa. Mutallab Pay before you read ₦500. 0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S. Shaidar biya ta nan 08164069385 Follow me on Arewabooks ❤🔥 "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 30: Safiyyerh & Aafiyyah" "Kimiyya ne ya bi bayan Safiyyerh da sauri yana kiran sunanta, da ɗan gudu take tafiya bata ganin ko" "gabanta saboda hawayen daya cika cikin idanunta, ganin tana ƙoƙarin kai wa ƙarshen street ɗin yasa" "Kimiyya ƙara gudu har ya cimmata, ya tsaya a gabanta tare da yi mata duba na tsanaki ""Safiyyerh. "" Ta ɗaga masa hannu idanunta jiƙe da hawaye ta ce ""Safiyyerh me?.""" """Mu koma gida don Allah""" """Sai a yi me a gidan? Me ya sa yake haka? Me ya sa baya cika kalamansa me ya sa yake yi kamar babu" "zuciya a ƙirjinsa, bai yi kama da mara imani da tausayi ba, me ya sa ni yake son gina tunanina da hakan? Me ya sa yake sawa da abin da nake ji a zuciyata? Is he even okay?"" Kimiyya ya ji tausayin Safiyyerh, domin shima yana cikin yanayi irin nata, koma fiye da nata, sai dai suna da tarin bambanci kasancewar shi namiji mai haɗiye abubuwa da yawa a ransa, bai kuma juriya saɓanin ita data kasance ƙashin haƙarƙari mai fidda rauninta a fili, wacce bata iya controling kanta ta kuma ɗaukaki soyayyar Mutallab a" cikin zuciyarta fiye da zaton duk wani mai tunani. Ya sauke numfashi kafin ya dube ta ya ce """Da kika fito yanzu a haka sai ina? A cikin wannan duhun?""" """Zani wajan shi ne, na ji abin da ya hana shi zuwa"" Ya dinga kallon ta sai ya yi murmushi ya ce ""Oh, to ai" "kin baro shi a cikin gidan naku tuni"" Ta buɗe ido ta ce ""Da gaske ko wasa, ka mini wasa da komai banda" "lamarin bestie"" ya ce ""Me ya sa na makara? Saboda shi ne ai kin san da yadda ya zo? Sai dana haɗa shi da Jeddah, so you have to appreciate me""" """Aikin da ka yi, Allah ne zai biya ka domin zuciyar Safiyyerh ka ce to thank you dear"" ya ɗage mata kafaɗa" "ya ce ""A'a ba wani thank you, rabin cake za'a bani shine tukuci na, shawo kan mutum kamar buddy abu ne mai ɗan banza wahala. Mutum ne kamar me ba'a taɓa gane masa ba'a saka shi sam yin abin da bai yi niyya ba, da kuma ya yi miki alƙawari zai zo, so he told you already ai ha zai zo ba, yanzu kar ki tilast" "masa yin abin da zai zo yana abin da ba shi kenan ba a cikin mutane""" """I won't. "" Safiyyerh said, da murmushi a fuskarta har ta mance da batun ƙadangaren da ɗaurewar da" numfashinta ya yi. Tun kafin su ƙarasa shiga harabar gidan ƙirjinta ya yi wani irin tsalle tare da doka mata a tsakiyar "zuciyarta, ganin daddy tsaye ga Mutallab sai Aafiyyah, wacce take zaune saman kujera ta sunkuyar da kanta ƙasa, har lokacin fuskarta sanye take da shade glasses ɗin. Idan ta tuna yadda ya cire ƙadangarun guda biyu da suke faɗa da juna a cikin rigarta sai ta ƙara jin ta yi addition akan tarin tsanar da ta yi masa," "madadin minus a'a, Aafiyyah kullum addition take. Daddy ya juya ya kalli Safiyyerh da idanunsa da suka" "sauya launi, ya yi mata wani irin kallo wanda yake alamta mata cewa tuhumarta yake ta yi ƙasa da kanta." Daddy na kallon ƴar tasa ya yi poiting Mutallab da hannunsa ya ce. """Safiyyerh, who is he? Waye shi, what he bring him to my house? What exactly abin da yake yi a cikin" "nan?"" Safiyyerh couldn't speak; ta dinga girgiza masa kai ta kasa furta komai sai ƙanƙame jikinta da ta yi da ƙarfi cikin tsawa ya ce ""Ya zama tambaya ta ƙarshe da zan miki, da zan nanata miki ina fata ki ƙaryata tunanina da zatona akan ba gayyatar shi kikai ba, he isn't... Baya daga cikin baƙin ki Safiyyerh""" """Waye wannan Safiyyerh?""" """Abokin Kimiyya ne tare suka zo daddy"" ta faɗa hawaye masu zafi na sakko mata, ta ji ta tsani kanta a" "dalilin ƙaryar da ta yi wa daddy, da kuma ƙasƙantar da kimar Mutallab da ta yi a gaban jama'a da kuma ƴan ajinsu, ta yi hakanne don kuɓutar tare da kautar da zargi daga zuriyar daddy. Aafiyyah dai na zaune tana danna waya, tana kuma jin komai ba zaka taɓa cewa ta san me ake yi ba. Mutallab kuma yana tsaye ya zubawa Safiyyerh idanu, kamar mai yin studying halin da take ciki, ya cije lips kawai. ""Bake kika gayyace shi ba?"" Ta girgiza masa kai ya juya ya kalli Mutallab, sai kuma ya kalli Kimiyya da sauran wanda" suke wajan ya ce. """Kimiyya ka bani mamaki, gaka yaro mai hankali da nutsuwa mahafinka ɗan mutunci mai ƙashin arziƙi" "wanda ya baka tarbiyya, ya ɗora ka a tubalin daya dace, ya ci da kai, ya shayar da kai da tufatar da kai daga taskar arziƙinsa. Amma ka ƙare da zama tare da tantirin yaro iron wannan?"" Ya nuna Mutallab ya ɗora da faɗin ""Mai ubansa yake da shi a unguwarsu, balle garin balle ƙasar? Wanne mataki ubansa ya taka ko wani ɗan'uwansa? Prof ne ubansa? Engineer, Dr, Alhaji, Senator, Rep, custom, Governor or President? Soldier or police? Waye ubansa daga cikin waɗannan abubuwan dana faɗa?. Yaron da bashi da cin yau balle na gobe da shi kake mu'amala har ka jawo mini shi cikin gidana? Kasan waye shi bari ka ji to, sau biyu ina zuwa state cid ina ganinsa an ɗaure shi, ko dana bibiya cewa aka yi ya gagari iyayensa shine aka bawa iyayen shawarar a yi masa aure ko zai nutsu, dake iyayen wawtattu ne kamar shi suke tunanin yi masa aure shine zai kawo ƙarshen matsala ko a ina aka taɓa aurar da yaro kamar shi?. Sau biyu suna nema masa matar da zai aura sai an kusa biki sai a samu ya cinnawa yarinyar wuta ta mutu, yanzu haka cases ɗin dake kansa wanda kuma akai recorded nasa akan batun kisan mata biyun ne, ubansa malamin allo ne na ji labarin har mari ya taɓa ɗaura masa"" Daddy ya yi maganar cikin zafi da" "ƙonar rai, sai turanci yake yana jefa Hausa kamar zai taune harshensa ya ce." """So all this... Kuka jawo mini dauɗa cikin gidana?""" """Ƴarka ta yi maka ƙarya, idan ni ne ita ba zan ƙarya ba saboda ina tsoron Allah ya kama ni a kan hakan," "ko ana zaka gane bambancin tarbiyyar talaka dana mai kuɗi"". Daddy ya juyo ya kalli Mutallab, Kimiyya zai wa Mutallab magana ya hankaɗe shi. Daman wani blue black ɗin yadi ne mai kyau a jikinsa daya sha goga kasancewar yana da ɗan kauri kayan ya kama shi ya yi masa kyau duk da duhun fatarsa. Mutallab ya nuna Safiyyerh data daskare ta ƙura masa kallo irin why are you doing this to bestie? Ya yi murmushin" gefen baki. """Za ka ji kamar bani da ɗa'a ko? Da iya kai na ne zan maka shiru amma ka taɓa martaba ta da abin da" "nafi ƙauna a duniyata; mahaifina. Ni dai ban taɓa ganinka ba, balle na nemi alfarmar wani abu a gare ka har ka goranta mini, domin iyayene kawai a duniyar nan suke wa yaransu abu ba don son kan su ba, su dai buƙatarsu yaransu su yi nasara, na ji nawa iyayen basu da wannan halin, ba'a taɓa kama mahaifina da laifin sata ba. Muna rayuwa a yadda muka tsinci kan mu, babana malam ne bai sam komai ba sai almajiransa da allo da tawada, ni ma kuma ina rayuwa ne a yadda ta zo mini bana ɗorawa kai na abin da bani da shi, kuma ina tsagewa iyayena gaskiyar dake ƙirjina koda za su hukunta ni. Yarinyarka ta maka ƙarya, ita ke bibiyata, ita ce ta addabi rayuwata, ita kuma ta gayyato ni nan da sharaɗin idan ban zo ba zata je har can gidan Malam Abdullah mai allo da almajirai ta dawo da ɗansa, arziƙi ba shi ne rayuwa ba, ka zauna cikin farin ciki hakan ma ya wadatar"". Da ƙyar ya ƙare maganar saboda muryarsa data shaƙe a" "maƙoshinsa ya kafe Daddy da kallo ya ce ""Da na so zan yi arziƙi fiye da kai, ka ji daɗi ka huta masu arzƙi""" Ya taka a hankali ya juya sai kuma ya juyo jin Kimiyya ya riƙe shi kafin ya yi magana daddy ya ce. """Ɗaya daga cikin halayyar talaka da yaran talakawa, su ji cewa mai arziƙi ne ya tare musu hanyoyin ƙofar" "samu, banda rashin tarbiyya har ni kake kallon idanuna kake faɗawa haka? Idan duka ubanka baya abin da ka lissafa amma halinsa ne auri saki, ya tara yara kamar kaji ya sallama su, na san komai a kanka tun ranar dana kanka na ji ba ka yi mini ba"" sheƙeƙe yake kallon daddy sai bai ce komai ba, da sauri kuma Aafiyyah ta tashi tare da barin wajan daman tuni ta sakawa kunnenta earpiece bata jure hayaniya. ""Fita" "ka bar mini gida """ """Bestie. """ "Safiyyerh ta kira shi a gigice tana sakin kuka zata bi bayansa daddy ya ce ""Idan kin amince ni mahaifinki" "ne, idan kin gamsu cewa nina kawo ki duniya, idan kin ji a ranki dole ki mini biyayya ya zama dole ki kiyaye kula shi." "Wallahi by mistake kika ƙara taku guda za ki sha mamaki Safiyyerh. "" ""Daddy please!"" Ya yi shigewarsa" "cikin gida rai ɓace. Ta sulale a saman ƙafafuwanta ta saki wani irin raunataccen kuka, zuciyarta na bugawa tana jin numfashinta na tafiya daidai ta takun sawayensa, fitarsa daga cikin gidan sai ta ji kamar ƙarewar rayuwarta duhu ya mamaye cikin idanunta, tamkar wata ya nutsa cikin kwanaki ashirin da bakwai don duhu, zafin da ƙirjinta ke sai take ji kamar dalma ake ɗiga mata ta dinga kallon ƙofar, jikinta" "na rawa zuciyarta ta dinga cewa ""Follow him, bishi, follow him Safiyyerh, your love is runaway bestienki""" """I am sorry daddy "" Safiyyerh said loudly. Tana miƙewa." "Da gudu ta kwasa tare da bin bayansa, ganin ta yi waje ya saka Wahee juyawa da gudu zuwa cikin gidan" "to tell daddy cewa Safiyyerh ta bi bayan Mutallab. A tsaye ta ganshi yana danna waya fuskarsa wasai kamar bashi aka wulaƙanta ba, ta dinga kallonsa shi kuma ya mayar da wayar aljihun gaban rigarsa Safiyyerh ta fashe masa da kuka tana ƙoƙarin shigewa jikinsa ya yi saurin yin baya ta girgiza kai ta ce." """I am sorry for what I did, i am sorry for what my father did, I am sorry for what we did to you. Ba wata" "kalma da zata iya tausasa zuciyarka a yanzu, babu tabbas"" ta share hawayenta tana kallonsa kamar yadda yake kallonta ta ce ""Ka tuna? Ba na ce zan faɗa maka wani abu ba? Ba na ce zan baka gift ba?....." "Bestie I LOVE YOU""" “I LOVE YOU” "Ya ji kalmar har tsakiyar kansa haka ya ji ta dirar masa, ya dinga kallon Safiyyerh domin har lokacin" "tunaninsa bata da lafiyar ƙwaƙwalwa kamar dai shi. ""Can you love me? Za ka iya so na?"" Yaƙi magana, ya kuma ƙi tafiya ya kuma ƙi daina kallonta, a daidai nan Aafiyyah ta fito sai a lokacin Safiyyerh ta lura da driven Aafiyyah ta ce ""Wai tafiya za ki yi?"" Ta cire shade glasses ɗin idanunta, ta kalli Aafiyyah da idanunta da suke tarr, wani irin kallo ne mai nufin You disappointed in me, you disappointed me Safiyyerh!. Sai kuma ta ɗaga mata gira ta ce ""Me za a yi after wanda kikai yanzu Safiyyerh? Kin kawo" "mana shasha ya rusa komai ya lalata komai, ba wani abu wanda ya fi haka, sai ki basa cake ɗin damar kamar shi ya biyo Ai wallahi Safiyyerh kin faɗo wanwar, akan wannan abin? saboda shi za ki saka ƙafa" "ki rushe sharaɗin mahaifinki, yanzu na sake yarda ƙuruciya na damunki""" """Aafiyyah Please, kar mu fara haka dake ko dan alaƙar dake tsakaninmu. Batun ƙuruciya ni za ki kalla ki" "cewa ina ƙuruciya, ki sani na riga jin iskar duniya ko tazarar daƙiƙa ɗaya dole ni na fara zuwa duniya" "kafin ke, balle ya shige haka. Idan har ba za ki iya taya ni fighting akan soyayyarsa ba, bai kamata ki" "ƙuntata mini ba, ko za ki ƙuntata mini kina yi i will take it, but i won't take it idan za ki wa""" """Shi wa?"" Aafiyyah, asked Safiyyerh; tana rungume ƙirjinta da hannu bibbiyu ta tambayi Safiyyerh Abdu" "Marafa, tana sake juya idanunta ga wayarta dake ta ringing silently. ""Wannan?"" Ta nuna Mutallab" "dake tsaye ko inda take baya kalla ta ce ""Lallai kin yi asarar bakinki idan akan shine, kuma har yanzu ba ki san waye Aafiyyah Abdu ba, bana ɓata lokacina akan abin da ba zai amfane ni ba, balle akan shi, balle na taya ki ɓatawa mahaifinki rai"" Aafiyyah ta yi maganar tana murmushi ganin yadda ta kunna Safiyyerh gashi bata iya faɗa ba ko kaɗan idanunta ya cicciko da hawaye muryarta na rawa da ƙyar ta iya kallon" Aafiyyah ta ce. """Now, now Aafiyyah. Mind your manners"" yanzu, yanzu Aafiyyah ki iya kalamanki." "Aafiyyah ta ɗaga kafaɗa ta juya zuwa inda motarsu take, kafin ta ƙarasu ma an buɗe mata ƙofar bayan" "motar, wanda ke ciki ya rufo dirver ya ja a hankali tare da yin reverse ya juya kan motar. Aafiyyah na shiga cikin motar, ta cire rolling ɗin kanta, ta ajjiye ta sunkuyar da kanta ƙasa tana sauke numfashi. ""Yaya aka yi? Faɗa kukai ne?"" Ta kasa magana sai kawai ta sakar masa kuka tana faɗawa jikinsa ta ƙanƙamesa, he hold her back, very tight, ta dinga kuka da ihu a motar tana birgima a jikinsa ""Na shiga uku Yaya, na shiga uku yaya, wayyo yaya"" sune kawai abin da take iya faɗa, wani irin karkkar jikinta ya ke yi, lokaci guda kuma jikin ya ɗauki zafi sosai, ya kasa mata magana sai kanta daya ɗora a saman ƙirjinsa, he could feel yadda hawayenta ya jiƙa masa gaban riga, duk yadda yake ƙokarin rarrashinta amma ta ƙi fahimta sai buga ƙafa take ƙaramar mitsitsiyar yarinya, bayan rungumeta da ya yi bai sake magana ba, sai ya ji tana sauke ajjiyar zuciya ta yi lamo Jikinsa ya ce ""Mene ya haɗa ku?"" Ta ɗago kai ta kalle shi da jiƙaƙƙun" "idanunta, ya kama fuskarta ya fara share mata hawayen ta ce ""Dawa?"" Kai tsaye ya ce ""Safiyyerh. """ """Oh, ba komai ni fa kaina ke mini ciwon sosai ba ka ji ba""" "Ta ce tana langwaɓar da kanta gefe, zai magana sai kuma ya sake ganin ta saki wani raunataccen kukan" "tana rirriƙe kanta ya buɗe ido ya ce ""Subuhanallahi, Safiyyerh. Safiyyerh!"" Ya faɗa a ruɗe ganin ganin" "tana sanƙamewa ta kasa jan numfashi ""Driver, asibiti please wanda ke kusa damu"" ya ce yana cigaba da" kiran sunanta da jijjigata. "After Aafiyyah lefted, sai ta ji wani nutsuwa sai dai kuma bata ji daɗin yadda suka rabu ba, basu taɓa yin" "faɗa ba ta ji ta damu akan maganganun data faɗawa Aafiyyah, amma ai ita ta fara faɗa mata komai, ita mema ta ce what exactly her fault?. Ta juyo ta kalli Mutallab da ta ji ya ce" """Zan tafi"" ta marairace fuska tana ɗan buga ƙafa ta ce ""To mu koma ciki, a yanka cake ɗin""" """Shekararki nawa ne?""" """Age mates muke da kai""" """Ƙarya kike... Ki koma gida""" "Mutallab ya ce, domin shi yanzu uzuri yake mata, ba kuma lallai ta gane nufinsa yana son kyautata mata" "da gaske su zauna lafiya, domin duka yan'uwansa wanda Allah Ya basa mata ne irinta, mata ne kamar Safiyyerh masu rauni, but no love just friendship, shima" ya ɗauki hakan kamar childhood friends da zarar ya san me yake ba zai iya cigaba da ƙawance da wata "mace ba. Ta kalle shi ta ce ""Zaka zo makaranta gobe ai?"" Ya ɗage mata gira, itama ta ɗage girarta tana masu wani irin kallo fuskarta ɗauke da kyakkyawan murmushi ta ce ""Wai ya aka yi ka cirewa Aafiyyah" "lizards ɗin nan?""" """One day, i will tell you, u most laught"" ta yi murmushi." "Ya juya ya fara tafiya a hankali, he looks so classy a nutse yake sosai. Har ya ɓacewa ganinta ta ja ajjiyar" "zuciya da sauri kuma ta juya zuwa cikin gidan, sai a lokacin ta lura ai duka babu kowa sai Captain dake zaune tare da Wahee sai kuma Kimiyya da ya yi shiru tun bayan tafiyar Mutallab. Bata kalli kowa ba ta" shige cikin gidan nasu kai tsaye. "Daddy dake tsaye ta can saman bene ya saki labulen windown ɗakin Safiyyerh a hankali, tun bayan fitar" "ta yake tsaye a saman benen yana kallon komai, har tafiyar Aafiyyah har lokacin tafiyar Mutallab da sanda ta juyo ta dawo cikin gidan. Ya daɗe tsaye a wajan kafin ya nemi waje ya zauna a saman gadon Safiyyerh kamar mai jiran shigowarta. A hankali ta buɗe ƙofar ta shigo, ta yi turus ganin daddy zaune ya" "harɗe ƙafafuwansa waje guda ya zabuwa ƙofar idanu, da wani irin sauri ta juya zata koma waje ta daki" "jikin Ummeyh dake shigowa itama fuska a haɗe, ta saka hannu ta tura Safiyyerh cikin bedroom ɗin ta" janyo hannunta ta dunƙufar da ita gaban Prof. Gabaɗaya takaici ne ya hana shi magana wai yau shi aka bijirewa magana? Ya dinga kallon Safiyyerh wacce ke durƙushe ƙasan ƙafafuwansa. "Ummeyh ta ce ""Aliyu yana kan hanya, yanzu yake sanar mini sun samu hutu Allah Ya sa kar ya ce ya fasa" "dawowa nasan hali""" """Zan zo ya zo ɗin, zan so kuma a ce kar ya zo ɗin "" Ya furzar da iska daga cikin bakinsa ya juyar da kansa" "ya zubawa photon Safiyyerh idanu dake gefen gadonta idanunsa na juyewa ya ce ""Me ya sa Safiyyerh?" Ya kike abu kamar ba professor Abdu ya haife ki ba? Ya kike abu kamar ba jinin ilimi da arziƙi ba? Me ya "sa, why Safiyyerh?""" """I'm sorry daddy """ """Sorry for yourself, sorry for yourself Safiyyerh!""" "Ta yi ƙasa da kanta, ya gyara zama sosai ya ce ""Ya sunansa?"" A hankali ta ce ""Mutallab"" daddy ya ce" """Nice name, mene sana'arsa data mahaifinsa, mene alƙarki da shi kuma? Da har kika manta cewa ni mahafinki ne?"" Ta yi shiru, Ummeyh ta buga mata tsawa sai ta fashe da kuka ta ce ""Ummeyh daddy don Allah ku yi haƙuri ba zan sake ba"" daddy ya kalli Ummeyh ya ce ""Dr dai na yi mata tsawa kar ki firgitar mini da yarinya for no reason"" Ummeyh ta ce ""Ba wani dalili? Wanne dalili bayan abin da muka gani da wanda ta aikata Prof?"" Idanunsa still akan Safiyyerh ya ce ""Still dai, mu ji daga bakinta. Safiyyerh"" ta kalli" daddy cikin shassheƙar kuka ta ce masa. """Mutallab sunansa""" """Na haddace sunan ai, ba kya buƙatar maimaita mini""" """A makarantarmu ta FGC yake, class ɗinmu ɗaya ajinmu ɗaya, kujerarmu ɗaya, abokina ne kawai na" "karatu. Ai baya sana'a nima ai kaga bana yi karatu muke, wallahi daddy he is the nice person yana da kirki ,""" """Waya tambayi kirkin nasa?"" Daddy ya ce yana gyara zamansa a hankali kuma ya janyo wayar Wahee" "dake kusa da shi ya fara dannawa. ""Kalli Wannan Safiyyerh"" ya juya mata screen ɗin wayar, muryarta ya sauka raɗau inda take kuka cikin cafeteria tana cewa ""What if I tell you, I love you"" ta runtse idanunta zuciyarta na rarraɓewa into pieces ""Wahee munafuka"" ta faɗa a ƙasan ranta kanta a ƙasa. Idanun daddy ya yi jajur sosai ya ce ""Abin da kike a makarantar kenan shi ya sa kika zama daƙiƙiyya? Shine abin da na" "tura ki yi a FGC ɗin kenan ko?""" """I'm sorry. "" She gasped out, double over in pain and trying to catch her breath. ""Wanne sorry? Sorry" "to tell me that you love him? Ɗan mai makarantar allo da almajirai? Soyayya at your young age? Yanzu me kike buƙata?"" Kai tsaye ta ce ""A aura mini shi"" wani irin juyawa Ummeyh ta yi ƙirjinta na bugawa da ƙarfin gaske zata daki Safiyyerh, daddy ya girgiza mata kai ya ce ""Shi Ɗan'malam ɗin? Karatun kuma fa?"" Ta ce ""Bana son karatun Daddy, bana gane masa auren nake buƙata"" Ummeyh ta zauna daɓas tana zabga salati, ba tare da daddy ya tambayi dalilin rashin gane karatun nata ba ya ce ""Ƙila ke da Fgc har abada, ƙila mu bar ƙasar gabaɗaya, batun aure ke da wancan ɗan me makarantar allon babu. Safiyyerh shekara 15 kike a duniya kin san wai a yi miki aure, me kika sani a rayuwa?"" Ba ki ta buɗe da nufin cewa ""Na sani mana daddy, I can tell you abubuwa da yawa akan aure daga cikin har irin abubuwan da kuke yi kai da Ummeyh cikin dare a kuma kullum, wanda surutunku da ihunku ya saka mini son abun, ka fuskanci kuma ba haka kawai ake samun abun ba sai dai idan anyi aure, daga lokacin kuma bana gane komai na karatu sai wannan mikin da kwaɗaitar son abun a zuciyata"" haka ta yi nufin faɗa, sai ya katse ta da cewa ""Bana son jin komai, bana son jin dalilinki na banza da iska, Wahee ta yi gaskiya. Za kuma ta cigaba da saka miki ido da ita da sauran ƴan'uwanki daga nan har na yanke hukunci. Kuma a gobe ban amince ki je makaranta ba, ki ƙaddara kin isa aure Safiyyerh babu Mutallab a jerin samarin daya kamata ya zama surukina, we may leave this country as soon as possible, as far as kin cigaba da yi mini taurin kai" "Safiyyerh""" "Miƙewa ya yi ya fita, Ummeyh ta kasa cewa komai ita buɗaɗɗiyar zuciyar Safiyyerh ke bata mamaki, duk" "haƙurin Safiyyerh amma yau ta buɗe baki ta ce wai aure take so? Ga wata uwar ƙiba da take yi ƙirji ya haɓaka ga buɗaɗɗan hips skin ɗinta sai wani ƙyalli take yi. Miƙewa ta yi ta fice domin ta cigaba da zama zata iya zane Safiyyerh cif wallahi. A downstairs ta samu daddy na waya da Dr bayan ya kammala ya kira Uncle Musbah suka fara magana a hankali bayan ya kammala ya ɗago ya kalli Ummeyh sai ya yi murmushi ya ce ""Ni Safiyyerh ke faɗawa aure take so? Ɗan zamani ka haifa baka haifi halinsa ba, zan" nuna mata ni nake da iko da ita zan nuna mata ni na haife ta. "***Washegari Mutallab shi kaɗai ne a desk ɗin, babu Safiyyerh domin bata zo ba, haka Kimiyya shi kaɗai" "ne babu Aafiyyah koda ya kira wayarta tun jiya bai sameta ba. Gashi bata zo makaranta ba, har aka tashi daga school ɗin Mutallab bai kula kowa ba karatu kawai yake yi yana kuma fahimta. Bayan tashi ya bi" "bayan Kimiyya har zuwa ɗakin computer suka dinga danne-danne a hankali ya ce ""Ina recorded ɗin" "nan?"" Kimiyya ya ce ""Yana nan"" Ya jinjina masa kai, wani location ya nutsu yana dubawa ya yi hakan ta bin diddigin wata number, kai tsaye ya yi sharing location zuwa ga Computer Kimiyya da mamaki ya ce" """Asibiti? Waye a can?"" Mutallab ya ɗaga kafaɗa ya fice." """Ya karatu Muhammad? Kimiyya ya faɗa maka sauyin ra'ayin da akai masa? Zai bar maka sabgar" "na'urorin nan, zai juya shi kuma zuwa ga zama barrister in sha Allah"" Mutallab ya jinjina kai ta ce ""Allah Ya yi muku Albarka""" """Amin"" ya ce." """Muhammad baka da wasu kaya ne sai waɗannan?""" """Ina jin daɗin su ne""" "Ta dinga jan shi da hira jinjina kai kawai yake yi ko ya lumshe idanunsa, Kimiyya kuma daɗi yake ji a" kullum idan ya ga Mutallab by his side sai ya samu kansa da jin zafin mahaifin Safiyyerh ƙwarai. Sun jima har Jeddah ta kwaso shadda su yadika ta bawa Kimiyya ta ce ya kaiwa tela ya ɗinkawa Muhammad ɗin. Bayan sun fito harabar gidan idanun Mutallab ya sauka akan wasu kyawawan karnuka ƙanana da su an yi "musu irin kiwon turawa, ɗaya baƙi da ɗaya ruwan ƙasa ɗaya mai ratsin baƙi da fari ""Ma sha Allah"" Ya furta yana durƙosawa akan ɗaya da ya fi jan hankalinsa. ""My dogs karnunaka nane, ko kana so?"" Mutallab ya jinjina kai, bai taɓa nunawa Kimiyya yana son wani abu ba sai yau ya ce ""Take them, na bar maka"" ya riƙe ɗaya da yafi faɗa da safi ya ce ""Tiger"" ya shafa ɗayan ya ce ""Rainbow"" ya kuma taɓa ɗayan ya ce ""Spider"" Kimiyya ya dinga jin daɗi, ya ɗauki ɗaya shi kuma ya kwashi guda biyu sukai waje. Sun isa gidansu Mutallab dake da ɗan tazara da gidansu Kimiyya, Mutallab ya lura kimiyya baya cikin nutsuwa can ya yi gyaran murya ""Uhm emm, ya dai?"" Ya ce ""Aafiyyah bata ɗaukan kirana duk na damu"" sai Mutallab ya yi shiru kawai cikin sa'a kuma aka ɗaga wayar Aafiyyah aka shaida masa ai tana kwance a asibiti tun ranar birthday ɗin Safiyyerh. ""Asibiti?"" Sai ya tuna location ɗin da Mutallab ya tura masa ya" juyo zai yi magana tuni Mutallab ya tashi ya bar wajan. """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, karnunka a cikin gidana masifa ta ƙaro na banu ni Malam Abdullahi""" "Mutallab ya yi shiru. ""Tattara tsinannun kayanka ka fice daga ɗakin zaure juma'a ta sama amaryata zata" "tare, kar na dawo naga komai ka je can cikin almajirai ka dinga kwana ban amince ka shiga ɗakin uwarka ba kana baligin yaro, domin wannan ɗan tsurut ɗin gemun a tsakiyar haɓa kamar na iska daka gani na girma ne ba zai haifar da ɗa mai ido ba"" Mutallab ya sake yin shiru. Malam ya ce ""Tijararre, ina magana""" "ya ɗago kai. ""Aby na ji, zan fita In sha Allah """ """Malam aure za ka yi?"" Cewar Sa'adah. Ya ce ""E, kina da matsala da aurena ne Sa'adah?""" """Baka ciyar damu hakƙin ciyar da yaranka a wuyanka yake Malam""" """Ki je ki yi ta kan ki Sa'adah ki nemi kuɗi kici abinci, idan kin yi saura ki bani, bani da ƙarfi bani da halin" "ciyar da tarin yara kamar na maguna kin ji"" yana cewa haka ya fice. Ammo dai murjin taliya take yi" domin tun safe ake zuwa nema ta yi har ta ƙare. "Sati guda cif, ba Safiyyerh ba Aafiyyah a makaranta har an kammala c.a ana shirye-shirye fara exam ta" "3rd term. Shi ko a jikinsa domin har yanzu maganganun Kimiyya na zane raɗau a zuciyarsa na cewa talauci zai zama abokin rayuwarsa, sai maganganu mahaifin Safiyyerh, wanda suka ƙarasa confidence wajan ganin zama mai arziƙi ko wani mai faɗa aji. Ya samu sassauci daga wajan Ammo ta sakko tana kula shi wanda bai san dalili ba sai ya samu relief a zuciyarsa nutsuwa ta saukar masa sosai ya ƙara jin ƙaunar" iyayen nasa har da Aby. Yana zaune a gida a lokacin yana jin yadda karatun Almajirai ya cika masa kunne ya yi kicin-kicin da fuska. "Ammo ta kalle shi ta ce ""Yau kuma waya taɓa jarumin Ammo?"" Ya yi mata shiru don bai fiya cewa komai ba idan ran shi ya ɓaci kafin ta sake magana wani yaro ya yi sallama ya ce ""Wai bestie ya zo in ji bestie""" """Waye bestie? Injiwa jeka tambayo""" "Mutallab a lokacin bai motsa ba ya hakimce kamar sarki kansa a ƙasa yaron ya dawo ya ce ""Wai in ji" "Safiyyerh matar Mutallab bestie""" "Baki buɗe Ammo ke kallon Mutallab ta ce ""Na Ammo yaushe ka yi aure bani da labari yau naga abin da" "ya fi ƙarfina, yara ƙananu daku wacece Safiyyerh?"" ya miƙe tsaye daga shi sai gajeren wando ta wata riga ƙarama ""ban san ta ba""" """Ikon Allah""" Fita ya yi yana shan kunu ganinta tsaye suna haɗa idanu ta yi ƙasa da kan ta. Ya dinga kallon ta yana jiran "ya ji mene ""meye ne?"" Ya tambaya. Hawaye ya gani a idanunta fal ""Ni a gidanku zan kwana"" tar ya gama buɗe shanyayyun idanunsa a kanta ""wanne gidan?"" Ta nuna masa gidan ""sai ki ce ke wa?"" Tana masa shagwaɓa wacce daman ya san hali tace ""Matar Mutallab, baka zo makaranta ba yau ba kyau fashi"" ji wacce ta shafi sati bata je ba ita ke faɗa masa yau bai je ba, kuma haka kawai ya ji baya ra'ayin zuwa makarantar. Ya cigaba da danna wayarsa ya barta tsaye, ita kuma sai kallon jikinsa take ya yi mata kyau sosai cikin ƙananun kayan daya saka sumarsa duk a birkice sai taga ya ƙara girma a idanunta da kwarjini ga wani tsayi da ya yi damtsen hannunsa wani abu kamar laya a duka hannu biyun. Ya ɗago kai ya kalleta suka haɗa idanu a hankali ta ce ""I love you bibi"" ya watsa mata harara kamar kuma an ce ya juya idanunsa ya sauka akan daddyn Safiyyerh daya fito daga cikin mota hannunsa riƙe da zabgegiyar bulala." "Da wani irin ƙarfi Mutallab ya ce ""Safiyyerh!"" Ganin kai tsaye daddy ya yi kanta." MUTALLAB. PAID BOOK NE PAY BEFORE YOU READ DEAR. 08164069385 "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 31: Yaa Muhammad" Not edited "Kallon Safiyyerh kawai daddy yake yi, irin kallon da yake nuna na haifi yarinya a cikina tana neman fin" "ƙarfina, idanunsa jajur saboda ɓacin rai ya ce ""Ba shakka Safiyyerh, ashe kin yi girman da za ki saci hanya tun daga gidan ubanki zuwa wajan saurayi? Saurayin ma ki biyo shi har gidan nasa iyayen Safiyyerh?" "Anya. "" Ta yi ƙasa da kanta a hankali kuma take jan jikinta zuwa bayan Mutallab saboda bulalar dake" "hannun daddy. Ɓacin ran daddy ya kuma bayyana a fili wai yau shi Professor Abdu, ƴar cikinsa guda ta nemi fin ƙarfinsa? Duk yadda ya kai da yi mata bazarana akan yaron nan amma kamar ƙara tunzurata" yake yi. """Safiyyerh nuna duniya kike ban isa dake ba? Ki rasa wa za ki so a duniya sai mai kashe ƴan'mata? Mai" "lalata su, ki rasa wa za ki ji kina ƙauna sai ɗan talaka futuk, ki rasa wa za ki ji kina ƙaunar rayuwa da shi sai wanda ubansa bai bar masa gadon komai ba sai na allo da tadawa? Ɗan'malam mai almajirai Safiyyerh? Shi Safiyyerh? Har ki iya fakar idanuna ki biyo shi?...."" Jikinta ya dinga rawa, ta sake maƙalewa a bayan Mutallab idanunta na cika da hawaye, Mutallab shi ko a jikinsa kallon daddy kawai ya" ke yi. Takaicin daddy ya sake ruɓanya a cikin ƙirjinsa da zuciya. """Kai ne ɗan iskan da yake hure mata kunne ko? Kai ne kasa ta fara bijirewa umarnina?""" """Ask her. "" Mutallab ya faɗa a daƙile, idanunsa a ciki yana murza goron da yake damtsen hannunsa na" "dama. Daddy ya ce ""Ka fita sabgar ƴata, ka fita daga cikin idanuna babu kai babu jinjina, kuma wallahi ƙararka zan yi wajan hukuma su raba mu"" a gigice Safiyyerh ta fito daga bayan Mutallab, tana girgizawa daddy kai muryarta na rawa ta ce ""Daddy ni na zo wajansa, daddy ni na ce ina son shi don Allah kar ka yi" "masa komai, kar ka ce zaka haɗa shi da hukuma Please""" """Akan wannan ɗan iskan kike magana? Wannan wanda da bashi da wani future mai kyau a rayuwa?""" "Mutallab ya ce ""Ka ɗauki ƴarka kuje ina da abin yi, don Allah ka ce ta rabu dani kar ta lalatawa iyayena ni," "Ɗan'malam ɗin da kake magana ai bai taka zuwa ƙofar gidanka ba ya ce ana sallama da Safiyyerh ɗiyar Professor. Ita ƴar taka ƴar masu kuɗi ita ke bibiyar rayuwata, ita kuma ta addaba mini, bani da wani sukuni ita ce mara tarbiyyar, ita ce mara ajin, ita ce mai neman ribatar zuciyata, ita ke son lalata mini ƙuruciyata, ita ta aiko har cikin gidanmu wajan mahaifiyata ta ce tana sallama dani, so Please carry your daughter and leave, idan kuma za ka kyauta ka saka ta daina bin Ɗan'malam kuma ɗan talaka"" ya ƙara maganar yana huci idanunsa akan cikin na surukin nasa. Safiyyerh ta dinga girgizawa Mutallab kai, tana fashewa da wani irin gigitaccen kuka mai taɓa zuciya kamar ta haɗiye zuriyarta ta mace haka take ji don" damuwa. """Idan ma asiri ka yi wa Safiyyerh sai dai ya koma maka ka, domin ko aure Safiyyerh ta isa sai da a yi" "ƙwarya ta bi ƙwarya domin kowacce ƙwarya akwai burminta"" daddy ya yi furucin yana nuna Mutallab da" "yatsa shi kam ko a jikinsa, almajirai suka fara taruwa a wajan suna kallon yadda daddy ya damƙi hannun" "Safiyyerh, bayan ya falla mata lafiyayyun maruka a fuska, tsananin gigitar da ta yi da yadda marin ya shige ta ya saka ta ƙanƙame mahaifin nata, tana fusgar numfashi ta kasa kuka yatsun hannun daddy ya fito jere a fuskarta ya damƙi hannunta ya buɗe mota ya cilla ta a ciki, kamar zai tashi sama haka ya ja" motar ya bar unguwar yana baɗesu da ƙasa. "Mutallab ya bi motar da kallo, ya ji wani iri a ƙirjinsa sai dai ba zai kwatanta abin da ya ji ba, domin bai" "san ma'anar hakan ba. Ya jima tsaye yana tunanin to dame Ubangiji ya tauye shi da shi? Saboda kawai su talakawa ne? Kenan talaka ba zai iya aurar yarinyar masu kuɗi ba? Ita soyayya ta gaskiya kuma ta domin Allah ai bata duba kuɗi, nasaba ko cancanta, mutumin da kake so shine kawai a allon ƙirjinka da idanun zuciyarka... The person you loved, you still love him/her for no reason, you love him/her for the sake of Allah, for the sake of love da baya shawara da zuciya. Kuɗi na siyan soyayya, na siyan komai na rayuwa banda kwanciyar hankali da lafiya, duk auren da aka yi shi domin kuɗi baya nisa zai lalace. Ya lumshe idanunsa da ƙyar ya buɗe su, ya sake bin hanyar da motar daddyn ta bi sai ya ja ƙafafuwansa ya koma cikin gidan har lokacin Ammo na zaune tana aiki, ya yi tsaye yana jan numfashi tare da furzar da iska" daga cikin hancinsa. Ta ɗaga kai ta duba shi kamar za ta yi shiru sai kuma ta ce. """Hayaniyar me nake jiyowa daga waje har nan cikin gida? Muryar waye kuma a wannan lokacin?""" """Mahaifinta. ,""" """Mahaifin wa kuma?""" """Safiyyerh. !""" "Ya ce a hankali yana danna wayarsa ba tare daya kalli Ammo ba. Ta dinga kallonsa, sai ta tuna muryar" "yaron ɗazo da yake cewa “Wai in ji Safiyyerh matar Mutallab bestie ” tuna hakan ya saka Ammo cewa ""Wace ita Safiyyerh ɗin?"" Ammo ta buƙata da mamaki fal fuskarta cikin yanayin na shakku da kokwanton abin da zata ji ɗin daga bakinsa, ta san baya ƙarya, kuma ba zai taɓa faɗa mata abin da ba ita ta tambaya ba komai nasa yana da tsari, ta dinga kallonsa don ta ɗauka ba zai yi magana ba kamar yadda ta" tsammata haka ɗinne ba tare daya kalleta ba idanunsa ƙasa ya fara bata raddi da faɗin. """Wai so na take yi, shine kawai"" ya ce yana lumshe idanunsa tare da saka hannu ya shafa sumar kansa da" "take baƙa ƙirin. ""So kuma?"" Ta yi furucin da madaukakin mamaki sai kuma ta ce ""So na mene kenan?"" Ya ɗaga kafaɗa yana miƙewa tsaye ta ce ""Dawo ka zauna Muhammad"" ya yi jim sai ya koma ya zauna domin allurar shiga daji ce ta tsikare shi ainun..ta duba shi ta ce ""Bani labari"" Ya ja numfashi ya sauke a hankali kuma ya kwashe labarin komai ya faɗa mata, banda yadda akai ya shiga makarantar iya abin da ya faruwa between him and her. Ammo ta ce ""Ikon Allah, to ka daina kula musu yarinya kaga dai abubuwan da suka faffaru ina goje mata zama gawa ta uku, kuma babu mamaki shima yana da nasa dalilin, kuma kowacce ɗiya mace ai da kamon kai aka santa, nutsuwa, da kamala bai ci ta biyoka har gidan iyayenka ba, su mata ai da alkunya aka san su, ita ma zan mata uzurin wawta da ruɗin ƙuruciya da na zuciya, yarinyata ce ba wani abu ba"" jin Ammo yake bai tanka ba, ta nisa ta ce ""Oh wannan zamani" "ina zaka damu? Shine har da cewa wai matarka ce? Allah Alhakkamu""" "Da zai iya murmushi ko yaya ne shi zai yi, amma ba kasafai ya fiya ba, musamman Ammo wacce a" "kwanakin baya da suka shuɗe ta gama gasa shi da fushinta mai albarka. Sai ya ɗan cuccure girarsa waje guda ya tsuke su yana miƙewa tsaye, kamar zai fita sai kuma ya dawo ya shiga ɗakinsa wanda kullum malam yake cewa ya fita. Kamar yadda baya gajiya da karanta saƙwannin a kullum da yake musu karatun zuban hadda, haka yanzu ma ya kwaso su kashi na uku kenan, hadda ranar birthday ɗin Safiyyerh. Ya tanƙwashe ƙafafuwansa yana kumbura zuciyarsa dake rayuwa a ƙirjinsa take motsa masa a kullum idan" yana karatun saƙon. A hankali ya sake ware sabuwar mai ɗan jan hankali da sanya zuciya nutsuwa. "“Can you feel it? The way i feel it in my heart? In every moment we share, my love for you grows" "deeper. I love you.” Ya buɗe idanunsa da ƙyar da suke lumshe masa, wani irin abu yake ji na musamman game da takardar, ya ji ina ma zai ga mai wannan rubutun a gabansa, dole taci gidansu ta faɗa masa dalili daya saka a dole take son ya fara ƙaunarta, domin da gaske he love kowacce kalma dake zane a jikin takarda, ya dinga kallon handwritten ɗin, tare da fatan ko zai gane hannun mai rubutawa. But he" can't! Ya kasa. Ya ajjiye ya sake ɗakko wata second paper ɗin yana buɗewa ya ci karo da. “Allah na son ka da Rahama "YAA MUHAMMAD, shi ya sa zai jarabce ka da abubuwa masu yawa, kar ka ji babu daɗi ka ɗauka rabauta ce daga Ubangiji ka samu, ka yarda da Allah shi kaɗai ya isar maka, ka yarda babu mai yi kuma sai shi." "When you feel bad, don Allah ka ɗauki rubutuna ka karanta, akwai watarana da zan tsaya a gabanka na faɗa maka yadda nake ji a ƙirjina” ya ɗan marairace fuska ya ja numfashi a hankali kuma ya ce ""Why not now?"" Kamar ya shiga cikin zuciyarta sai ya ga amsar tambayar a ƙasan takardar an rubuta ""Ba yanzu ba, kana da abubuwa da yawa da kake buƙatar cimma, mu jira lokaci shine bamu damar kasancewa da juna, bana buƙatar komai sai alƙawari. Ka yi mini wannan alfarmar don Allah Yaa Muhammad"" ya dinga kallon rubutun yana jin zufa na tsattsafo masa ta cikin ƙofofin gashin jikinsa, a hankali ya ajjiye paper ɗin ya" "rufe ido, sai kuma ya sake ɗakko wata paper yaga ɗan short note ne. In a love way." “I love you more than pizza (and that's saying a lot)!” aka rubuta playful. Haɗe da zanen emoji na zuciya dana kuka. "Tsaki Mutallab ya ja, yana jin duk sanda ya kama mai yi masa irin wannan abubuwan sai sun samu" "mummunan saɓani. Ya yi shiru, yana ta zaune kamar an cillo Malam haka ya shigo ɗakin Mutallab ya ɗago kansa ya kalli Malam bai ce komai ba. Malam ya dinga kallon ɗakin, ya hangame baki ya ce ""Iyee, likafa ta cigaba duka wannan na uban mene ka mayar mini da ɗaki kamar na aljanu? Ubanka ne ya gina" "mini ɗakin don ubanka?""" """Ubana Malam Abdullahi shi ya gina mana, kuma ko mutuwa ya yi ina da hakƙi akai"". Baki buɗe Malam" "Abdullahi ya ce ""Daman mutuwata kake jira kenan?"" Mutallab ya girgiza kansa a ƙasa kamar zai yi shiru sai kuma ya ce ""Bana fatan ganin mutuwarka Aby, sai kaga na zama abin kwatance in sha Allah. Za ka ɗauki zuri'ar Mutallab"" ""Kai nan tunaninka zaka zama abin kwatance ne kamar kowanne yara? Ai bana hango maka wata kyakkyawar gobe mai kyau a nan gaba, tantiri yaro mai idanu a tsakiyar ka wulaƙantacce"" Mutallab ya miƙe tsaye, sai ya ji dama zai samu damar rungume Aby ya faɗa masa abin da yake damunsa, ya samu dama ko yaya yane ya zubar da hawaye, ya faɗa masa bai san yadda aka yi Diyna ta rasa ranta ba, ya faɗa masa bashi da hannu wajan mutuwar Jaanah, bai san kuma ya aka yi hakan ya faru ba, ya faɗa masa sabon abubuwan da ƙaddara ta saka ya kutso rayuwarsa. Sai dai bashi da wani damar hakan, bashi da ikon yin hakan, bashi da wata jituwa da mahaifinsa balle ya tsaya ya ji mene" yake faruwa da rayuwarsa. Da ƙyar ya ce. """Idan bakinka ya kama ni Aby shikenan, idan abin da kake fata ya faru shikenan. Duk inda zan je kai zan" "nuna matsayin wanda ya haife ni, in sha Allah kuma ba zan zama silar mutuwarka ba, sai na sanyaka cikin farinciki, ko lalacewa na yi ina nan tare da kai""" "Malam ya ce ""Ban haifi wanda zai kashe yaran jama'a ba, ban kuma mai haura katanga ya yi sata ba"" kai" "tsaye Mutallab ya ce ""Aby, daka ciyar damu a matsayinka na uba a gare mu da hakƙin hakan yake a kan ka, ta ina zan haura katanga? Daka cinyar damu, da yanzu muna tare da Muneeberh muna rayuwa, daka ciyar damu da yanzu ƙaddara bata cilla ni halin da nake ciki ba, ka taɓa zama ka tambayi dalilin daya saka na haura katangaa? Ka zaunar dani ka ce Mutallab ya aka yi Diyna ta mutu ya aka yi Jaanah bata duniyar a yanzu. Sai dai ka aibata ni, kullum; a koyaushe duk wani responsibilities naka a matsayin uba babu wanda ka ɗauke mini, ai shikenan Aby ya yi kyau hakan ya yi kyau"" ya juya zai fice daga cikin ɗakin Malam ya ce""Dawo ka kwashe komai naka, fenti za a yi ciki matar da zan aura ce zata tare a cikin ɗakin""" Mutallab ya kalli Aby kallo na anya kai mahaifina ne? Wanne laifi na yi dana cancanci hakan? Ya cije "bakinsa a hankali muryar a rauna ce ya ce ""Sai na koma ina da kwana kuma?"" Kai tsaye Malam ya ce ""Sai" "ka dinga shimfiɗa a saman kai na kana kwana, ko a ruwan cikina""" """Zan kwashe"" ya ce kawai yana fita daga cikin gidan bakiɗaya zuciyarsa na rarrabewa da tunanin" "makomar yau ɗinsa, da abin da gobensa zata haifa zuwa ga jibin da bashi da tabbacin ganinta. What should i do?...." "Safiyyerh ji ta yi kamar zuciyarta za ta yi bindiga ta tarwatse a ƙirjinta haka take ji, ba kukan marin take" "ba, kukan yadda ya hanata magana da Mutallab take yi. Ta durƙusar da kanta tsakanin cinyoyinta ta fara rera wani irin kuka mai sauti tana jin yadda yake sharara gudu a mota amma bata ɗago ba, to ta ɗago ta yi me? Ta kalli yadda yake mayar da ita gida zuciyarta na ƙara raɗaɗi a zuciyarta ta tsinewa Wahee ya yi cikin carbi domin ta san ita ta faɗawa daddy cewa ta fita, sai dai ta yi mamakin yadda daddy ya gano gidansu Mutallab ɗin kai tsaye har yazo. Mai gadi ne ya buɗe ƙofa da sauri daddy ya shigar da motar tare da yin parking ya fito, daidai nan Uncle Musbah ya fito daga cikin gidan hannunsa riƙe da key ɗin mota yana kallon yadda daddy ya fincikota Safiyyerh yana shirin ɗaga bulala ya zane ta. A hankali ya ce ""A'a, kar ka yi haka kar ka fara"" ya ce yana zuwa wajan, da gudu Safiyyerh ta yi bayan Uncle Musbah tana" shassheƙar kuka. "Rai ɓace kuma daddy ya ce ""Wai ashe gidansu yaron ta bishi? Yanzu har Safiyyerh ta gane bin saurayi" "gidan iyayensa? You disappointed me Safiyyerh""" """I am sorry... I'm sorry daddy""" """Zan lallasaki ke da sorryn"" Ya faɗa yana girgiza kai, yana matuƙar so da ƙaunar yarinyarsa amma tana" "neman bashi ciwon zuciya akan wani dalili mara tushe. Uncle Musbah ya ce ""Yi shiru haka nan daughter mu je ciki ko?"" Ya juya cikin gidan daddy ya bi bayansa har zuwa main parlor suka tarar da Ummeyh ita Wahee a zaune. Ummeyh ta ce ""Ina ka same ta?"" Daddy ya kasa magana can ya nemi waje ya zauna, Uncle Musbah ya ce ""Safiyyerh, Wahee go inside kun ji ko? Allah Ya yi muku Albarka"" kamar jira Safiyyerh take yi haka ta yi sauri ta hau upstairs ta shige bedroom ɗinta ta rufe tana sake wani sabon kukan domin ita kaɗai ta san mene take ji a zuciyarta. Wahee ma ta shige ciki hannunta riƙe da waya har zata zauna sai ta dawo ɗakin kamar ta manta abu, ta saka wayarta a recoding ta ajjiye ta ɗauki ruwa a" deep freezer ta koma saman benen. "Uncle Musbah ya ce ""Me yake faruwa ne har haka?""" """Musbah ai ka gani, daga wajan saurayi na ɗakko ta""" """Saurayi? Shi Ɗan'malam ɗin?"" Ummeyh ta faɗa tana riƙe haɓa tare da yin salati da sallallami." """Bafa wani abin mamaki bane kuke ta jimami, ku bar sharrin Adolescencet stage ɗin nan ya fi komai" "hatsari a rayuwar yara daga mata har maza... Yanzu ba wannan ba meke faruwa briefly?""" "Daddy ya gyara zama ya ce ""Wani yaro ne nina manta sunansa ba, ɗan iska ne bashi da kunya data ido," "babbar damuwa criminal ne ƴan'mata biyu ya kashe sau biyu yana kashe mata biyu"" da wani irin shock daya kama Uncle Musbah ya kalli daddy sosai ya ce ""Kisa kuma Prof? Ba ka ce age mate bane? A age ɗin nasa zai yi kisan kai har mata anya?"" Daddy ya yi murmushi ya ce ""Ina da hujja ai, i have a reason...." "Many reasons daya saka na ce haka. Frist of all, I don't like him, na ji bana son shi. Ka san halina da bibiyar abu ranar dana fara ganinsa a cikin state cid ne, a rana ta biyu kuma na sake ganinsa, sai na sawa kai ne duk inda yake wannan bashi da wata cikakke tarbiyya, ba shiga na samu wani Dig Johar domin bincike ya shaida mini cewa kawo yaron na farko akan cases ɗin sata ne, kuma an kama shi da wata bindiga wanda jami'an SSS state security service suke nema domin akwai laifin zargi akanta na jami'insu da ya munafurce su bayan ya san sirrin su. Abu na biyu kuma saboda da rashin ji da ɗaukar magana da yake wa iyayensa na sace sacen kayan al'umma da lalata yara, ya saka aka bawa iyayen nasa shawarar su yi masa aure, domin wata fitinar ta raya idan suna yi aka yi musu aure sai kaga an samu albarkar dake cikin auren ta daidaita komai, akai yunƙurin aura masa wata yarinya a ranar da ya je gidansu a ranar ne yarinyar ta mutu, aka sake yunƙurin aura masa wata yarinyar abu kamar gaske a ranar da ubansa ya kai sadakin auren yaron gidansu yarinyar, da daddare yarinyar ta mutu mutane sun tabbatar shine ya babbake ta. Ban san mene ya kawo shi Fgc ba, ashe ɗan ajinsu safiyyerh ne kimiyya ya saka iyayensa suka sa shi, kenan yana da planing na kashe mini yarinya ko? Yana so ya ce Safiyyerh ce gawa ta uku?...." "No please impossible""" """. Mene impossible ɗin? Hana shi auren, ko hana Safiyyerh bibiyar yaron, ko hana Safiyyerh son" "yaron? Wanne daga ciki Prof?"" Cewar Uncle Musbah yana murmushi domin daddy baya fahimtar abi kao tsaye. ""Komai ma impossible ne, idan akan maganar Ɗan'malam ɗin can ne, kama ture komai a gefe just keep a joke aside Safiyyerh ba zata taɓa auren ɗan talaka ba, ina da kyakkyawan tanadi a kanta in sha" "Allah""" """Ok, amma ba zaka hanata haihuwar ɗan talaka ba? Ina nufin baza ka ji komai ba when you saw her with" "pregnant"". Daddy ya ce ""Ban gane ba Engineer, wanne irin ciki ana zaune lafiya?"" Uncle Musbah ya yi murmushi yana gyara zama ya ce ""Da farko a cikinku wane ya nutsu Da sauyin dake tattare Safiyyerh?"" Daga daddy har Ummeyh suka yi shiru alamar tunani ya ce ""Daga shekaru 15-17 zuwa sama mataki ne da yake da matuƙar hatsarin gaske kafin yaro ya tsallake shi, according to psychologist suka ce a wannan matakin mu lura da yaranmu, kalamansu, furucinsu, ɗabi'arsu, abokansu... Abin da yaro ya fi yi maka magana akai shine abin da yake zuciyarsa, kuma shine abin da yake so. Ko a karatun yaro mu kaga sauyi yana da kyau mu bibiya a tsanake lamarin yaro baya ɓaci muddin akwai kulawa da saka hannun iyaye a ciki"" Ya yi jim sai kuma ya ce ""Kune iyayen Safiyyerh, kuma kuke tare da ita, musamman cikin dare za kufi" "gane komai""" """Ni bana kwana tare da ita, bedroom ɗinta daban ai""" """Da gaske? Really Ita ɗaya ke kwana kenan ashe?""" "Ta jinjina masa kai alamar eh. Ya ce ""Ikon Rabbi, ga wani salo duk wayewa ce haka ta gidan Professor" "Abdu kenan? Ai duk me za ki yi Dr ko ƙarfe 3 na dare ne yana da kyau ki dawo kusa da yarinyarki ki kwana da ita, wata matsalar ai cikin dare take faruwa tunani kuma ya fi zuwa kan yara a lokacin kwanciya bacci, kin yi kuskure wannan kuma ba wayewa bace ba matar Prof, lack of parent audience" "kenan""" """Wallahi iskanci ne lamarin Safiyyerh, gudanawa take?""" """A faɗar gudanawa kuke ƙara ɓatar da zuciyoyinku, karka manta makaranta take zuwa, ƙawaye ne da ita," "duk ƙanƙantar shekaru karka raina su wajan yaro, wayen su ya fi ƙarfin tunaninsu wallahi. Age is nothing but a number, wayo da ƙawa zuci abine da Ubangiji ke ƙissima bayinsa. A yanzu ba zaku iya tanƙwarata zuciyarta ba, domin ta bushe yau da ace bata kalli cikin idanunka ta faɗa maka cewa aure take so ba, to me sauƙi ne. Amma duk yarinyar data ce aure take so mafi sauƙi ayi mata shi kafin rawar ta sauya salo, shi ita ce tun yana ɗanye ake tanƙwara shi, kuma wallahi yadda yara suke saka lamarin soyayya a zuciya yanzu Uhm"" Ya miƙe tsaye yana ɗaukan wayarsa ya ce ""I will talk to her, kuma Prof ka sauya salo duka" "ba zai maka ba, domin ita yanzu wannan ba shine gabanta ba, the more kana dukanta the more tana" "ƙara yin abin da take yi, da zan bada shawara ka yi mata auren, idan kana tsoron talauci ko gudun" "wahala sai ka bawa yaron jari, gida, da duk abubuwan da suka kamata ai ƴarka zai aura"" ya ce hakan" yana nufar upstarts zuwa ɗakin Safiyyerh. """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"" Ummeyh said loudly." """Ina tunani za mu bar ƙasar nan, ba zan jira dawowar yaran nan ba"" Ummeyh ta yi shiru, ya juya ya" "kalleta cikin ɗacin rai da ƙonar zuciya ya ce ""Ina ce shikenan idan muka bar ƙasar ko? Mene zai faru idan ta dawo new Safiyyerh, muka bar old a Nigeria? We have to leave da zarar na kammala haɗa komai ko zuwa next week ne"" tashin hankalin Ummeyh ya ninka na daddy kashi sittin ta ci kuka ta ƙoshi idanunta" "ya yi jajur tama kasa cewa komai a hankali ta ce ""Aliyu ya dawo""" """Yana ina?"" Daddy asked." "Ta ce ""He lefted already, wai da ƙyar ya samu ya dawo, shima duk ya yi wani iri da shi, na ce ya jira ka da" "ƙyar yana ficewa daga cikin ya dube ni ya ce... He can't wait any longer, shi wai lokacinsa baya shuɗewa haka kawai""" "Daddy ya ce ""Ba zai sauya ba, ba ya saka abu a ransa ba na yi na yi ya haƙura yaƙi ai shikenan""." "Ummeyh ta miƙe ta ce ""Amma zai biya ta wajanta dole na sani, ba zai iya zuwa bai je wajanta ba""" """Dole kam""" "Ummeyh ta shige bedroom ɗinta, ta ɗauki waya suka fara chatting da S Bayero akan wasu haɗin kaya da" "za ta yi mata. Tabbas kayan S Bayero ba kowane zai dace da samun nagartattun irinsu ba, musamman masu fama da matsalar shigar sanyi da yake saka gurajen gaba, har miji ya daina zuwa turaka, masu matsalar bushewae fata musamman a lokacin sanyi, wanda basu da wadataccen mama a ƙirji ki wanda suka kwanta,domin a zamanin nan na yanzu mace ma gyara ya aka cika balle babu, ƙarara za su nuna miki rashin ɗa'a. Masu buƙatar hips ko wanda duk abin da za suci basa ƙiba masu ƙashin wuya, ko gogewar fata tana gyalli da haske sa uwar gida tsaki, duk wani abu na mata ba'a bar S Bayero ba." "Product guda take haɗawa na kamfaninta kuma testing and trust ne, da zarar ka siya you most come for" more. Wata gumba ta saka order nata da wata Haɗaɗɗun kayan ƙamshi wanda kai tsaye daddy ya nuna "yabawa akan su. Bayan ta gama ta ajjiye wayar ta fara tunanin ina zata saka matsalar Safiyyerh? Ta ina zata fara? Duk inda ta juya ta yi nazari ta kasa hango sauyin da Uncle Musbah yake magana, bata kuma" kawo ƙibar da safiyyerh ke yi da kuma matasan ƙirjinta da sukai girma na ban mamaki ta buɗe sosai ba. Ta yi ƙwafa tana jiran Uncle Musbah ya fito ta shiga ta ci ubanta... Daddy ya tashi ya shige part ɗinsa ya fara tattara muhimman abubuwan domin barin ƙasar gabaɗaya hakan shine mafita. Ganin ba kowa a parlo ya saka Wahee sakkowa ta ɗauki wayarta tare da yin saving recording ɗin. "Safiyyerh, tana shiga ɗakinta ta kulle da key saboda tsoro, a hankali ta sulale ƙasa a jikin ƙofar ta durƙusa" "wani irin zafi take ji a zuriyarta, ta yi kuka har dana Allah wadai ta fara sauke ajjiyar zuciya, ta lumshe idanunta tana hango fararen idanunsa ta ciki, da yadda kayan jikin nasa sukai masa kyau she love everything about him, she like everything when it comes to him. Ta jima a wajan kafin ta miƙe ta ɗauki wayarta, sai tunanin kiran Aafiyyah ya zo ranta, ƙila ta ji sanyi idan sukai magana da ita sai ma ta bata" "haƙuri. Number ta kira kamar ba za a ɗauka ba sai kuma aka ɗauka, ta ji mamaki jin ba Aafiyyah ba ce ba." """Ina yini?""" """Lafiya Safiyyerh, ƙawar taki bata jin daɗi ai muna asibiti""" """Aafiyyah ba lafiya Yaya? Mene ya sameta to?"" A hankali ya ce ""Lalura ai jikin nata da sauƙi ma""" "Ta yi jima sai ta ce ""Can i speak to her?"" Ta can ɓangaren ya ce" """Anya? Tana bacci ne""" """Ok ka bani address ɗin asibitin, zan faɗawa Ummeyh sai driver ya kawo ni ko? Allah Ya sauwaƙe""" "Bayan ta kammala wayar, sai ta fara kiran number Mutallab tama ta ringing bai ɗauka ba ta haƙura sai" "kawai ta yi masa dm da “I love you bby"" ta ajjiye wayar da sauri jin ana knocking. Ta miƙe ta buɗe ganin Uncle Musbah ya saka ta yi ƙasa da kanta, ta gaishe shi ya zauna. A nutse ya ce ""Daughter dawo nan kusa dani mana"" ta ƙarasa ya sauke numfashi ya ce ""Meke faruwa dake?"" Ta yi shiru sai da ya zama very" friendly to her ta kalle shi ta ce. """Uncle aure nake so""" """Wa zaki aura?""" """Bestie. "" Ta faɗa hawaye na cikowa ta cikin idanunta." """Waye Bestie kuma?""" """Mutallab Shi zan aura""" Uncle Musbah ya dinga kallon Safiyyerh da mamaki ganin how serious she is akan maganar kuma yana "hango gagarumar matsala nan kusa. A hankali ya ce ""Kina son shi?"" Ta yi saurin jinjina kai ya ce ""Shi kuma fa?""" """He love me too""" "Mutallab na zaune a ƙofar gida har wajan ƙarfe 2 na dare Malam har ya rufe ƙofa, shi ba zai iya shiga" "cikin almajirai ba ƙila ma akwai masu fitsarin ƙwance. ""Mai dawa"" aka kira sunansa domin inkiyar da aka" fara yi masa kenan. Ya juya a hankali ya kalli TARIQ. """Mai dawa""" """Tariq"" Mutallab ya ce." """A'a ka ce mini Goje kawai, me kake yi zaune a nan kai ɗaya?"" Ya buɗe idanunsa sosai ya kasa magana, ai" "da kunya ya ce Aby ne ya kore shi daga cikin gidan, ba zai iya tozarta Aby ba balle wasu suga baƙin shi. Da ƙyar kamar mai lissafa kalmomin da zai faɗa ya ce ""Shagonka, kai ɗaya ne?"" Goje ya ce ""Ni ɗaya nake kasa a ciki ya aka yi?"" Mutallab ya yi shiru Goje ya fidda ran zai yi magana sai ya ji ya ce ""Zanna kwana duk wata na baka kuɗi, haya kenan"" Sai Goje ya dinga dariya ya ce ""Allah Ya sauwaƙe saboda zaka kwana na karɓi kuɗinka, mu je kawai"" ya miƙe a ran muhallin yana mamakin yadda dariya bata bawa wasu" wahala. Bacci ya gagare shi duk juyi ɗaya biyu sai Goje ya banka masa tusa ya kasa sukuni. "Washegari a makaranta daga Safiyyerh har Aafiyyah babu wanda ya zo, ga exam na ƙara zuwa domin" "Monday za'a fara. Bayan an tashe school Kimiyya ya ɗauki Mutallab zuwa wani waje, ya yi ta mamakin" ganinsu cikin asibiti bai ce komai ba har suka isa ɗakin da Aafiyyah ke ciki. Kimiyya ne farko Mutallab "kuma ya ja ya cake a waje yaƙi shiga ciki. Ya shiga da sallama ya buɗe ido ganin Aafiyyah zaune ta kishingiɗa da jikin gado, ga Safiyyerh zaune a gefen gadon sanye da wata lafiyayar Abaya a jikinta ya ce." """Wonder shall never ends, Safiyyerh you are here""" """Kimiyya"" Safiyyerh ta ce." "Shi kuma ya juya ya kalli Aafiyyah da duk ta rame lokaci guda, ta sake haske kyanta ya bayyana a fili" "kanta ba ɗan kwali sumar ta har baya ya ce ""Crush za ki shige lahira babu announcement? At least ki sanar mini yadda zan fara tunanin rayuwa babu ke"" da mamaki ta juya ta kalle shi ya kashe mata idanu ya ce ""Yes, i am nothing without you, rayuwa zata mini wahala"" Ta yi masa shiru, ya ce ""Ya jikin crush?"" Muryarta can ƙasa ta ce ""Jinya nake yi?"" Ya ce ""A'a, saboda bake ce a gadon asibitin ba, ke da mutuminki muke yana waje yaƙi shigowa ki je ki lallaɓa shi"" ya faɗa yana kallon Safiyyerh a hankali ta ce ""Waye a" "wajan?"" Domin tunaninta Captain yake nufi ya ce." """Bestie""" "Kamar an tsikare ta haka ta miƙe tsaye, Aafiyyah ta bita da kallo secretly tana lumshe idanunta tare da" "ɗan ya motsa fuska. Jingine ta ganshi a jikin bango, ya haɗe ƙafa yana kallon wani waje daban idanunta ya sauka a ƙirjinsa, bata ya aka yi ba sai jin saukar hannunta ta yi a tsakiyar sumar ƙirjinsa da babu riga, da sauri Mutallab ya juyo saboda wani irin da ya ji da kuma tsigar jikinsa daya tashi idanunsa ya sauka cikin nata kafin ya yi magana ta marairace fuska cike da shagwaɓa tana ɗan turo bakinta gaba da babbuga ƙafa ta ce ""Bestie. My love"" ta ce tana murza hannunta dake tsakiyar ƙirjinsa zuciyar Mutallab" "ta girgiza, a tsora ce a zuciyarsa ya ce ""Shaiɗaniyya....." A cancana Allah Ya kaimu Monday kuma. Mutallab paid book ne. Pay before you read ₦500 08164069385 Na'ima Sulaiman Sarauta (Nimcyluv) "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 32: Nothing will happen." "Ƙanƙance idanunsa ya yi, kallon da ya yi mata kuma bai saka Safiyyerh dai na abin da take yi ba. Ta" "rausayar da kanta gefe cike da shagwaɓa ta ce ""Ka yi kyau, kuma sai ka tsaya a nan?"" Ta zubawa ƙirjin nasa ido, taƙaici ya kama Mutallab ya saka hannunsa yana make nata ciki ciki ya ce ""Ashe ƴar iska ce ke?"" Safiyyerh ta ce ""Ƴar iska kuma? Iskanci me na yi?"" Kamar zai kuka muryarsa na rawa ya ce ""Ƙirjina fa, ƙirjina kika taɓa ba ki da kunya? What nonsense"" Ta tuntsire da dariya tana juya masa idanunta ta ce" """Kai kuma ɗan ruwa ne ba ɗan iska ba? Ka yi mini kyau ne"" ta faɗa romantically." """Mu je ciki, Aafiyyah na ciki"" ya yi mata shiru, ya juyar da kansa gefe ta sake matsawa ɗaya gefen suka" "haɗa ido ta ce ""To haka ake zuwa dubiya?"" Ya juya ido." """Dubiyar wa?""" """Aafiyyah"" Safiyyerh ta nanata masa, duk da ta san ya sani amma ba zata biye masa ba. Ya nutsar da" "idanunsa ciki ya kame fuska ya fi ƙarfin 30 seconds da ƙyar ya ce ""Waye haka kuma?"" Ta harare shi ta ce ""Aafiyyah ɗin? Ba kyau ka daina irin wannan class mate ɗinka ce, da ana rabawa ƴan makaranta gadon mutum tsaf zata ci, Aafiyyah zata ci gadon mijina na gobe"" Ya ɗaga mata kafaɗa yana tsotse lips ɗinsa na ƙasa ya bubbuɗe idanu ya ce ""Sunan bai yi kama dana mutane ba, irin na wani teddy"" ya faɗa yana" mayar da wayar cikin aljihu. """Teddy kuma?"" Ya jinjina kai, yana sake suɗe lips ɗinsa wanda ya zame masa ɗabi'a. Ta yi jim ta ce ""Ka" "shiga ka yi mata sannu, ta rame sosai"" ya sake mata banza, kuma ya kafe ta da idanu, ita ma shi take kallo domin bata yi wa idanunta shamaki da cikin fararen idanunsa. A hankali ta zame nata idanun tana kallon gefe ta yi shiru can kuma ta yi murmushi ta ce ""Ni dai kawai na san ni ce ƙaddararka, soyayyarka" "kuma a zuciyata ita ce tawa ƙaddarar, Ubangiji shi kaɗai ya san ma'anar haɗuwarmu a Fgc, in ma ka so ni" "ko ka ƙi ni, ni dai na ji zan rayuwa da kai bestie. Safiyyerh zata rayuwa da kai, kuma na ji a jikina soona or" "later zan amsa sunan matar Mutallab"" ta yi shiru, sai kuma hawaye ya cika idanunta sosai a hankali ta ce ""My parents doesn't understand me, Aafiyyah doesn't understand, and you ,"" ta yi shiru." """You never understand ma"" ta sake yin dariya tana rufe idanunta, ya bi fafaren haƙoranta da kallo tana" "da dariya yanayinta ya nuna farinciki sosai ta kuma kasa magana ya ga ji da dariyar domin gundirarsa take yi, ya ɗan kame fuska daman kamar ya ce ya shiga uku a daƙile ya ce." """Kee""" """Kai...""" "Ta ce tana yi masa fari da jiƙaƙƙun idanunta, ta sake murmushi ta ce ""Wallahi ina jin farincikin sosai mara" "iyaka when i am with you, bestie ba zaka gane ba, amma watarana za ka ce na faɗa maka, akwai wata manufa da Ubangiji ya ɓoye na dalilin haɗuwarmu, da kuma dalilin da yasa na ji ina son ka. Dole zama ka tuna one day, ko Safiyyerh bata raye"" Ta matsa kusa da shi ta ce ""Za ka dafe zuciyarka ka ce why Safiyyerh? You never tell me. ,"" sai kuma ta yi shiru ganin yana ƙoƙarin barin wajan ta yi saurin riƙo" hannunsa tana buga ƙafa ta ce. """I am sorry, ban san ina da yawan magana ba sai ina tare da kai""" "Ya kalle ta, ya kalli hannun ya ce ""Kina son taɓa jikina Fiyya""" """Fiyya!"" Safiyyerh ta maimaita sunan ta ce ""Fiyya, i like it """ """What?""" """The name you gave me now, Fiyya"" ya girgiza kai kawai a hankali ya ce ""You are impossible Safiyyerh" "Abdu Professor""" """I love you!"" Ta faɗa soundly." "Ya dube ta sai ya kame fuska, domin shi tausayi al'amarinta suke bashi, da yana da iko daya bada" "shawarar ubanta Professor Abdu ya ɗauki ɗiyarsa zuwa asibiti a duba lafiyarta. Ta jinjina kai while smiling ta ce ""I got you dear, ka ce i love you too"". Taɓara ta dinga masa shi dai bai tanka ba, ya dinga kallon ta yana jan halaula a zuciyarsa, da ƙyar ta sakko da shi ƙasa akan ya shiga ya duba Aafiyyah da jiki, yaƙi ce mata komai sai ƙanƙantar da idanunsa daya ke yi a kanta. Ita ta fara yin gaba ya bita a baya yana" tafiya majestically hannunsa a aljihu. "Kimiyya ne ya dinga bin Aafiyyah da kallo musamman sumar kanta, tun bayan fitar Safiyyerh ko ɗaga kai" "bata sake yi ba, balle ta tanka Kimiyya yana ta bata tabbacin nothing will happen to her, kuma ta dage da addu'a ga kuma exam. Da sauri yaga ta ɗauki mayafin dake kusa da ita ta yafa saman kanta ta kuma tattare sumar data sauka a bayanta ta tura cikin mayafin ta ja duvet ta rufe jikinta har ƙirji. Safiyyerh ce ta fara shigowa har lokacin tana dariya da faɗin ""Ai bai wani dake ni ba, faɗa ya dinga yi wai ka yi mini asiri, na san kuma ba wani asiri idan ma akwai i appreciate it, domin ka taimaka mini sosai"" ta faɗa tana" "shigowa ciki, kimiyya ya ce ""Safiyyerh kamar an aiki bawa garinsu? Daga ki shigo da shi""" """Uhm, shi ai sarki ne sai da biyayya da lallashi baya tanƙwaruwa ta sauƙi"" ta faɗa tana kallon Aafiyyah ta" ce. """Bacci ta yi ne?""" """Maybe, baccin ne ma"" Kimiyya ya bata amsa. Ta ɗan matsa gefe ta ce ""Bestie ka yi mata sannu"" shiru ta" "ji ta juya taga waya yake dannawa ta marairace fuska ta ce ""Ina magana fa"" gently ya ɗago kansa suka haɗa ido, hankalin kimiyya yana ga Aafiyyah da take danna tata wayar a nutse alamar kamar game take yi. ""Tunda ya zo har asibiti ai ya wadatar kika sani ko azumin magana ya fara yi?"" Ya girgiza kai ta ce" """Naaaa, Aafiyyah is my best friend, childhood friend"" ta ce tana zama." """Waye ba lafiya?""" "Daga Safiyyerh har kimiyya suka kalli Mutallab jin wata tambayar rainin wayo da ya yi. ""Aafiyyah Abdu," "ƙawar Safiyyerh Abdu ita ce babu lafiya tun ranar birthday party ɗin Safiyyerh, aka kwantar da ita a gadon asibiti ta yi kwanaki, shi ne daga makaranta na ɗakko muka taho dubata ba tare daka sani ba, mistakenly kuma ashe budurwarka ƴar anacenka ta zo itama, na shigo kai kuma kaƙi shigowa, shine na ce ta fita ta kira ka, gashi kuma ka zo ɗin, shine yanzu take faɗa maka ka cewa Aafiyyah sannu da jiki"" Kimiyya ya faɗa yana sake cewa ""Na sake maimaitawa ko hakan ya wadatar da kai?"" Mutallab ya yi shiru, hakan ya saka sukai masa banza suka cigaba da magana da Safiyyerh. Aafiyyah na jin komai ko motsin" kirki ba ta yi ta haɗe fuska tamau. """Zan tafi"" cewar Mutallab, ya furta a hankali can ƙasan zuciyarsa" """Wani ya riƙe maka ƙafafuwa? Ba komai rayuwa ce, crush ɗina ka ƙiwa sannu jeka to ba yanzu zan tafi ba," "sai na ƙara ganin jikin nata"" Kamar jira yake yi ya ɗaga kafaɗa tare da ficewa daga cikin ɗakin, da sauri Safiyyerh ta biyo bayansa tana kiransa. ""Middle class"" Aafiyyah ta ce a hankali, kimiyya ya kalleta ganin ta kwanta a hankali ta juya baya. Ya miƙe ya ce ""My crush, Ubangiji ya ƙara sauƙi da afuwa zan tafi babu wanda ya zo daga can gidan naku, fatan ba za ki kaɗaita da shirun ba?"" Ta janye mayafin kanta kaɗan ya" "ce ""Ba dai ciwon kan bane na ga idanunki ya yi jajur?""" """See you, i am fine""" """Glad to hear this, Rabbi ya ƙara sauƙi my crush""" """Amin dear. Ka turan timetable na exam ok?"" Ya ce ""Za ki iya karatun jarrabawar ne ko na yo mana?""" """Kamarya?"" Ta tambaya tana tsattsare shi da shanyayyun idanunta, very sexy eyes. Ya yi mata" "murmushi ya ce ""Shikenan Allah Ya kaimu Monday, wish you a very quick recovery, don ina jin sai na je" "na yi Jeddah shagwaɓa"" ita dai bata kula shi ba har ya gaji ya fita, ya tarar Wizzy driver tuni ya ɗauki Safiyyerh sun tafi, sai ya ɗauka tare suka tafi da Mutallab." "***Eng Ali wali zaune akan kujera ta alfarma jikinsa sanye da wata jallabiya mai taushi da tsadar gaske," "ya ɗan kishingiɗa yana sauraran abin da matarsa take cewa, ya dube ta kaɗan ya ce ""Madam kenan, siyasar don suwa nake yinta? Saboda kune, domin ke matata da ƴaƴana, sai kuma yan'uwana"" Ta haɗe fuska ta ce ""Wanne yan'uwa kuma? Ni kake kalla kake cewa domin ƴan'uwaka? Duk faɗi tashin da na yi" "wacce gwagwarmaya ce ban yi ba akan harkar kamfel?"" Eng Ali wali ya ɗan shafa kan shi ya ce ""You are" "right, kawai dai suma yana da kyau na taimaka musu"" ta saks haɗe fuska sosai ta ce ""Sai ka yi na gani, ina faɗa kana faɗa"" ya sake yin murmushi ya ce ""Yadda kika ce haka za a yi Madam"" Ta taɓa fuska ta ce ""Ko wani abu za ka yi wa yan'uwan naka, ka tabbata ka fara sanar mini"" ya buɗe ido yana faɗin""Kin tuna mini, akwai wani Uncle nawa da ya nemi alfarmar kuɗi za a yi wa ƴarsa aikin ƙoda, shaf na manta bari na saka" "p.a ya tura masa""" """Har nawa ya nema?""" "Eng Ali wali ya ce ""500k ne babu yawa ai, sai na shi 1m""" """Ya yi yawa, tura masa dubu ashirin kace harkar kamfel ta cinye maka kuɗaɗe kuma yanzu daka samu" "kujerar kana biyan mutane bashin daka ranta musamman banki. Amma miliyan ɗaya ta yi yawa Hon, zuwa gobe wani ma zuwa zai yi da tasa buƙatar kaga ka bashi 20k"" ya yi ɗan jim ya ce ""Kina ganin dubu ashirin ya isa?"" Ta ce ""Ko bai isa ba sai su nema wani wajan, ciwo ai ba kai ka ɗora mata ba"" Sai ya yi" "murmushi ya ce ""Yadda kika ce haka za a yi Madam""" """Hon"" ta kira sunansa." """Ya aka yi kuma? Babu dai wata matsala na sani "" ta jinjina masa kai ta ce ""Batun ƙanina, brother na" "yana son tafiya karatu ƙasar waje, ni kuma bana son sabgar scholarship ɗin nan, naga kuma Allah ya" "hure maka shine nake so ka ɗauki nauyinsa zuwa ƙasar da yake buƙatar yin karatun a can"" yana kallon ta ya ce ""Ba case, ku yi magana da shi za'a nema masa ko wacce ƙasar yake son zuwa""" """Na gode, idan ka tashi raba kujerar umara ina buƙatar guda biyar zan bawa sauran familyna da basu je" "ba"" Nan ma ya ce an gama ya nisa ya ce ""Ina Noor ne? Yana da kyau itama a fara shirin tafiyarta karatun nan, ni makarantu ƙasar nan namu sam ba su yi mini ba Wallahi, kira mini ita mu ji nata ra'ayin"" ta ce ""bacci take yi yanzu sai ta tashi, zata same ka yaushe zamu tafi Abuja ɗin?"" Yana danna kiran P.a ɗinsa ya ce ""Satin gaba, yanzu akwai wani kuɗin kasafi da ake bawa kowanne ɗan majalisa, ya siyi kayan sawa sabbi, da mota da sauran su kimanin wajan miliyan 40. Suna nan an bani, muna jiran a fara kasafin" "wannan shekarar naga ta wanne sashe ya kamata na sha kwana, amma dole kwangilar gyaran titi, da" "asibitoci zuwa makarantu ta zo wajena, ina fanshe duka wahalar da na yi. Kafin nan a ƴan'uwana su" "waye masu ilimi haka da wayo""" """Tajuddeen ne""" """Good, zan tura wasu miliyoyin kuɗi zuwa account ɗinki da kika buɗe da wannan Bnv ɗin, idan na tura" "miki kuɗin sai ki fara transfer ɗin su zuwa account ɗin driven gidan nan, shi kuma ki bashi account number Tajuddeen ya tura masa, kinga kuɗi ne gama shawagi babu wanda zai yi tunanin daga wajena ya fito, akwai kamfanin da nake so a buɗe, sai a buɗe da sunan Tajuddeen ɗin"". Hakan ya yi wa matar Eng Ali wali daɗi. Kana ta fara nuna masa wasu experience kaya ta ce ""Ina buƙatar wannan atamfofin da laces ɗin Distinguish"" ya dinga kallon kayan kafin ya nisa ya ce ""Wannan kayan Arɗo groups ne,sune na biyu a duniya fa, mai kamfanin ya ji arziƙi sosai, kuma sunan kawai aka sani har yanzu ba'a taɓa ganin Arɗon ba, tun daga kan Manager, accounter, sectary da komai ma'aikatan a cikin Arɗo's family suke, major holders sune the Arɗo's family hatta founder"" ta jinjina kai ta ce ""Ikon Allah, lallai ahhalin kuɗi ne"" yana Miƙewa tsaye ya ce ""Ardo groups ai yana daga cikin manyan Companies a ƙasar nan, domin gab" "yake da shige Fs world investment company""." "Eng Ali wali ya dinga duban P.a kafin ya ce ""Sau nawa zan ce maka karka sake kirana akan batun wasu" "ƴan daba? Aikin su ya ƙare ai sai zuwa nan gaba, ma'ana nan da shekara huɗu ko"". P.a ya ce ""Amma saboda nasarar zaɓenka suka je filin zaɓe suka ta yar da hatsaniya, sun sace ƙuri'un abokan hamayya, sun fasa akwati al'amarin da ya nemi sawa a yi inconclusive kenan, saboda har an ɗauki niyyar sauya zaɓen wasi local government guda biyu. Yaran sun shiga tsari wasu na hannun hukuma wasu sun ji rauni" "kasan mun raba musu kayan da aka kawo na caji a lokacin""" """P.a""" """Ranka ya daɗe Distinguish""" """Leave, ka fita kafin ka ɓata mini rai, daman can ƴan iskan gari ne kuma ƴan daba basu da wani amfani a" "cikin al'umma. Wanda hukuma ta kama baza su taɓa taɗin sunana ba, ka bar su a hannunsu akwai sanda zan saka a fito da su. Na asibiti kuma zan ɗan iya yin wani abu, amma kar ka kuskura su san asalin sunana ka ji ko? Ai iyaye su ne suka bar su shigowar bangar siyasar bani ba"" P.a ya ce ""Na gama hon, ka yi ka kuma idan ka gaji ka karya kujerar dambu mai hawa uku"" Eng Ali wali ya geɓare baki yana" murmushi. Bayan fitar P.a Eng Ali wali ya juya ya fuskanci Boɗejo suka fara magana hankali kwance. "Gabaɗaya ya manta da batun wata amaryar Aby, ya shiga gidan kai tsaye kuma ya nufi cikin ɗakin domin" "ya yi mantuwar abu mai muhimmanci, saka ƙafar da zai yi a ɗakin ya ji an fasa ihu ana faɗin ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, jama'a ya leƙo ni kwarto ne"" cak ya tsaya yana mai da ƙafarsa waje, bata fasa ihun da take ba Malam ya shigo daga waje da sauri yana faɗin ""Yaa ya na ce ya ya? Mene Binta?"" Ta nuna masa Mutallab ta ce ""Ina shirin saka riga a jikina sai kawai ya bankaɗo labule babu ko sallama, da na yi masa magana ya ce ya shigo ɗin ai jikina ya shigo gani, da ƙyar na ƙwaci kai na"" ta faɗa tana kuka sosai, Malam ya juya ya kalli Mutallab ya ce ""Bayan kashe yara leƙe ka fara da neman mata? Anya ba ka yi asara a rayuwarka ba kowa Muɗallabi? Matata ta sunna kake leƙawa?"" Ammo ta ƙarasu wajan ita da Sa'adah, Mama Zaituna na tsaye a hankali ta ce ""Muhammad ka leƙa ta da gaske?"" Tambayar ta basa mamaki ya kalli Ammo ya juya ya kalli Inna Binta yana ƙanƙance idanunsa da ƙyar ya ce ""E, na leƙa"" ya ce" kai tsaye. """. Ka leƙa fa ka ce? Ka kalli tsaraicin matar ubanka Mutallab?"" Ya sake jinjina kai ya ce ""E, amma banga" "tsaraicin da kyau ba maybe ko ta sake buɗewa na gani na haddace"" Ammo ta ɗauke fuskar Mutallab da mari ta kasa cewa komai, Malam ya ce ""To Allah Ya isa ka kalla, tsinannen yaro na kusa haramta maka" "shigowa gidan nan gabaɗaya""" """Amma ina da gadonka """ """Kashe ni ka ɗakka, anya ba gidan kangararru zan kai ba?""" """Kai ni mana, duk inda na je zan amsa sunan Muhammad Mutallab Abdullahi Ɗan'malam, ɗan ka""" """Ammo kin cuce ni, ba zan yafe miki ba kin cutar da zuciyata"" cewar Aby, Mutallab ya ɗaga shoulders ya" "yi waje ransa a cunkushe saboda ɓacin rai. Yana fita kuma ya shige shagon Tariq, ya yi shiru yana tunani can kuma ya miƙe zaune ya ɗauki ƙwayar daya fara yin rubutu a cikinta da wadata, ya ƙarasa rubuta ayar da yake so, ya ajjiye ƙwayar ya kunna kyandir ya tsaka a tsakiya a hankali kyandir ɗin ya dinga ci yana cilla wasu layoyi a ciki har ya kammala, ya ɗauraye rubutun cikin ƙwayar ya ɗaure a leda. Wayarsa ta fara ringing ya juya yaga Safiyyerh ce, bai yi saving number ba amma ya haddace yaƙi dauƙan kiran daga" ƙarshe ya kashe wayar gabaɗaya. "Washegari Monday suka fara exam, safiyyerh ta zo haka Aafiyyah kuma aka rarraba wajan zama cikin" "sa'a number exam ɗin Aafiyyah data Mutallab ya yi ɗaya. Ba wanda ya kula kowa a cikinsu har suka kammala paper ɗin, a ɓangaren Safiyyerh ta amsa ne kawai amma even questions ɗin bata fama" "fahimtarsu ba, balle kuma amsar da zata bayar. Aafiyyah na zaune tana danna waya idanunta sanye cikin" "shade glasses fuskarta ba yabo ba fallasa. Mutallab na zaune shima yana danna waya zumbur kuma ya juya saboda wani abu ɗaya faɗo masa, daman ya zo da shirin duba handwriting ɗin matan ajin yaga wacce ke yi masa haka. Da sauri ya ja littafin gaban Aafiyyah, gently ta ɗago kai ta kalle shi ganin yadda yake ta duba ruhutunta, a hankali ya ja numfashi ya sauke ganin kwata-kwata rubutun wasiƙar bai yi iri ɗaya dana Aafiyyah ba. Ya miƙe ya fara dubawa matan ajin suna ta kallonsa. Kinal ta ce ""Yau kuma mai muka yi wa Moh, ake bincikar mana littatafai"" ya gama duba nata bai kulata ba. Har ya zo kan Safiyyerh" tana tsaye ita da Captain daya tsare ta da surutu ya ƙarasa ya ce. """Ina littafinki""" "Safiyyerh ta ce ""Me za ka yi da littafi kuma? Ba dai karatu ba?"" Ya tsare ta da idanu ta ɗakko ta basa, da" "wani irin sauri ya ɗago kansa yana jan numfashi a wahale ganin exactly handwriting ɗin Safiyyerh iri guda ne da wanda ake tura masa, kenan ita ke yi masa wasa da zuciya? Idan yana son ruhutunta to tabbas yana son Safiyyerh. Ta yi masa murmushi ta ce ""Waya taɓa mini Mai dawa?"" Yaƙi magana ya dinga kallonta sai ya ji a karo na farko ya nutsu da ita ya lura da ramewar da ta yi sosai ta sauya kamar ba" "ita ba. Captain ya ce ""Kai wai yane ka zo ka tsayawa mutane a gaba? Kana sa wani business damu ne?""" """Bestie. "" Mutallab ya ce a hankali yana cure girarsa waje guda tare da nuna Safiyyerh da tsaya." """Wannan ai ba kayan talaka bace, ko a duniya Ubangiji ya ware matayen talakawa ka ji ko? Wannan" "tawa ce ni ɗaya""" """Ni kuma kaga bana son ka captain, Bestie nake so""." """Safiyyerh ni kike faɗawa haka?""" "Ta share shi ta yi waje abin ta. Suna zaune a harabar makarantar ranar da suka kammala exam ta ƙarshe," "kimiyya ya ƙarasu wajan Aafiyyah shi da Mutallab ya ce ""My crush, ya exam?"" Ta jinjina masa kai ya ce ""Wai daman kin sauya club ne? Ba'a English club kike ba? Naga sunanki ya fito a Hausa drama kuma za ki yi playing role na budurwa"" ta ɗaga idanunta ta kalli Kimiyya sai ta ce ""Maybe na sauya, akwai matsala ne?"" Ya girgiza kai ya ce ""Kawai na ji inama nine saurayin da za a haɗaki da shi"" ta juya idanunta ta ce" """Ko?"" Ya ce ""Serious, ai ke ba zaki gane ba shi yasa""" """. kamarya?""" """Kamarya yadda kika ji Aafiyyah""." "Idanunta ya kalla muryarsa a hankali ya ce ""There's something about you that make me feel like you" "actually use magic about me, many things I do because you, many things I don't even know or remembered when I started doing them. The love I have for you is so real baby. Yet, ban san me ya sa" "zuciyata take yawan bijiromin da kokwanton yiwuwar samunki a rayuwata ba. I love you Safiyyerh""" "“I love you Safiyyerh, or Aafiyyah"" Kimiyya ya ce muryarsa na rawa saboda kwarjinin da idanunta suka yi" "masa, ta ɗago kai sosai suka haɗa idanu da Mutallab ta haɗe fuska shi kuma ko a jikinsa, shi tunanin yake ko tana da matsalar ido ne? Da sun haɗa ido take yin ƙasa da kai ko duk tsanar ce? Aafiyyah ta ce ""Kimiyya kenan, a yanzu ai kaga makaranta nake yi, idan ka so ni babu laifi amma ka yi mini uzurin karatu ka ji ko?"" Ya jinjina mata kai ya kasa magana kuma. Ta miƙe ta bar wajan domin gobe ne Friday za" a yi ball kamar yadda aka sawa da clun competition. "***Safiyyerh na zaune a parlo ta kalli Ummeyh dake cewa ""Kaya suna da kyau sosai, na ji daɗin su Allah" "dai ya biya ki S Bayero tamu ta mutunci"" magana sukai sosai duk Safiyyerh na ji amma ta yi shiru ta rungume filo a ƙirjinta sosai tana jin wani iri a cikin zuciyarta a hankali kuma take tuna tambayar da Uncle Musbah ya yi mata cewa ""Daughter kin fara al'ada ne?"" Ta kalle shi ta ce ""Uncle mene al'ada?"" Sai ya yi mata shiru ya ce ""Shikenan Daughter idan na dawo zan yi miki bayani kin ji ko?"" Ta jinjina masa kai," ya miƙe ya nufi ƙofa har zai fita Safiyyerh ta ce. """Uncle za a yi mini auren?""" "Uncle Musbah ya dube ta, tsoro labarin yarinyar ke bashi shekarunta 15 a duniya ko al'ada bata fara ba" "ita ke maganar aure? Ya nisa ya ce ""Safiyyerh karatun fa?"" Ta girgiza kai ta ce ""Uncle bana son makarantar bana gane karatun zuwa kawai nake yi, idan na rufe idanuna Mutallab nake gani a cikinsu Uncle, idan na rungume filo sai na ji kamar Mutallab na rungume, bana iya bacci Uncle ina son Mutallab sosai ka tausaya mini, daddy da Ummeyh sun kasa fahimtar aure nake so zuciyata kamar za ta yi bindiga" "haka nake ji""" """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, wanne irin matakin balaga ne ya zowa Safiyyerh a haka? Ya aka yi ta" "fahimci feelings na ɗa namiji?"" Da ƙyar ya shanye mamakinsa ya ce ""Safiyyerh kina da sauran lokaci fa," "ke yarinya ce har yanzu""" """A'a Uncle, yaro ai shine wanda bashi da nono a ƙirji, ka dubi Ummeyh ka gani ai ta girma nima ina da" "irin abin ta""" """Safiyyerh!!!!"" Ummeyh ta kira ta s lokacin cikin tsawa, da sauri kuma Uncle Musbah ya fice daga cikin" "bedroom ɗin zuwa downstairs. Yana fita Ummeyh ta zari wayar caza ta dinga tsulawa Safiyyerh, tana ihu da komai ta yi mata lalas kana ta fice daga cikin ɗakin. Jan numfashi Safiyyerh ta fara a hankali, duk wani numfashi da yake fita daga ƙirjinta da soyayyar Mutallab yake fita, ta dinga kuka tana jin duniyar ta yi mata zafi, ta rasa yadda za ta yi gashi an hanata fita ko'ina tana jin idan ba haɗa idanu da Mutallab ba zuriyarta za ta iya yin bindiga, ta manta cewa soyayya ta ɓangarori biyu ce. A wannan ranar ta saci jiki zuwa wajan Mutallab ta bisa har gidansu inda ta tura yaro ta ce wai bestie ya zo, aka sake dawo da yaron" ta sake mayar da shi ta ce wai in ji Safiyyerh matar Mutallab bestie. "Ajjiyar zuciya ta sauke, domin principal ne ya kira daddy, principal na makarantarsu Fgc tsoro ya cika" "mata zuciya, sai kuma ta dinga addu'ar Allah ya kawo sanadin da za a cire ta daga makarantar gabaɗaya." "Ta miƙe ta nufi bedroom wayarta ɗauka ta kira Aafiyyah ta ce ""Dear kina lafiya? Ya gajiyar exam kuma?""" """. Good, Safiyyerh, how can i help you?"" Safiyyerh ta ce ""Aafiyyah mene al'ada? Na taɓa jin sunan a" "Islamiyya amma malamin ya ce karatunmu bai kawo nan ba tukunna"" Aafiyyah ta yi shiru, Safiyyerh ta ce ""Kin yi shiru?""" """I don't know ne, Safiyyerh""" """Kai Aafiyyah ke ana raba ki da sanin abubuwa ne? Kawai ba za ki faɗa bane shine"". Aafiyyah ta ce ""Bar" "shi a haka ba zan faɗa ba"" tana cewa haka ta kashe kiran." Safiyyerh ta kasa jurewa sai ta kunna data cikin sa'a aka nuna mata Mutallab a online. Bata taɓa sanin "cewa yana yin WhatsApp ba, ba lallai ta sani ba domin yau kimiyya ya buɗe masa, aka tura saka shi a" "group na Hausa drama, aka tura musu script ɗin da su hau a goben. Shi dai kawai bin komai da idanu ya ke yi." """Hy chocolaty""" "Ta tura masa, taga alamar ya buɗe ya gani amma bai kulata ba. Ta sake tura masa ""Hy love. Hy my" "man Hy sweetheart"" sunayen da Ummeyh ke kiran Daddy dasu." Typing ta ga ya fara sai kuma ya daina sai ta tura masa emojin sai taga ya cigaba da typing. """Kee"" ya tura mata" "Ita ma ta ce ""Kai """ """Zo nan""" """Zo nan"" ta ce itama." """Kamo ta nan""" """Kamo shi nan""" """Uhm'uhm"" ta ce ganin ya yi mata shiru ya ƙi kulata ta sake tura masa ""Uhm'uhm""" """Uhm'uhm, nima"" ya ce." "Safiyyerh ta dinga dariya, ta lura gabaɗaya bai iya hirar bane sai ta kira shi vedio call ya katse." """Bestie can i ask you?"" Ya buɗe ya duba ya share ta ce ""Mene al'ada""" """Wacce daga ciki, ta Hausawa ko ta mata?"" Ya tura mata. Sai ta ce ""Mata, Uncle ya tambayan wai ko na" "fara al'ada ne?""" """To kin fara?""" """Ai ban san mene ba""" "Ya tura mata emojin na dariya ya ce ""So fiyya still yarinya ce""" """Yarinya ita ce wacce bata da nono ai, kuma ni ina da shi""" "Ya tura mata ""Uhmmm""" """Zaka gani?""" """What?""" "Kafin ta faɗa masa koma mene ya yi saurin cewa ""Al'ada jini ne da mata suke yi duk wata, idan mace ta" "fara hakan yana nuna ta isa ɗaukan ciki, go and read ƙawa'idi ko fighu. Bye""" """To yaushe zan fara? Za ka iya mini ciki kenan?""" Mutallab Paid book #500 0116886423 Na'ima Sulaiman S. Shaidar biya 08164069385 "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 33: Love is flying" """To yaushe zan fara? Za ka iya mini ciki kenan?"" Mutallab ya zubawa saƙon na Safiyyerh idanu, a hankali" "ya ji zuciyarsa ta buɗe, wani abu ya bi fatar jikinsa yarr, abubuwan da yake ji kuma is very different da abin da yake, Ji idan yana karanta wasiƙun nan, idan yana karantawa ya kan ji he can give his whole life, just to be with person me tura masa wasiƙun nan, ko waye, ko waye, he feels better da nutsuwa idan yana karantawa. Saɓanin wannan maganganu na Safiyyerh da suka saka masa wani tunani na daban, wanda yake shirin neman sashe na musamman cikin ƙwaƙwalwarsa ya zauna, sai ya ji sanyi na neman kama shi haka kasai ba don yana jin zazzaɓi, ya fara tunanin sanda ya ji Ammo na cewa ""Hameeda wani cikin kika samu?"" Ya buɗe ido, ba dai irin wannan cikin Safiyyerh ke nufi ba. A hankali ya ce ""You are impossible Safiyyerh"" bai sake buɗe saƙonta ba, ya lura da emojin da take tura masa na kuɗi, da kuma" na zuciya a rabe. "Hankalinsa ya mayar zuwa ga cikin group wanda suke tattauna yadda Hausa drama ɗin sai kasance, ya" "kura malamin ne yake bayani da kansa, shi dai bai ce komai ba, lura da wani username da ake typing da shi na S.Abdu. a hankali ta fice daga group ɗin, sai a lokacin ya lura da maganar Kimiyya data Nahyan, sai kuma main group na makarantar Fgc da aka yi adding nasa, immediately ya yi exit daga cikin main group ɗin sai kuma ya kashe datar ya fara duba karatunsa don shi ne a gabansa, kiran Safiyyerh bai ƙaƙƙauta a" "wayarsa ba, har sai da ya kashe wayar bakiɗaya." "Mutallab ya yi tsaye a tsakar gidansu jin yadda Inna Binta ke cewa ""Ke har kin isa ki hanani yin abin da na" "ga dama? Ina cewa kwana ne kuma girki nane ko? To wallahi dole ki jira na ba ki iya tuwon da na yi niyyar bayarwa"" caraf Mama Zaituna ta ce ""Saboda kin samu yau an yi cefane har kike da bakin magana ko? To a yi dai mu gani idan tusa zata hura wuta, idan yau kin samu na dare bari muga wayewar garin gobe juma'a ko?"" Inna Binta ta yi shewa da ta fi tana buga cinya ta ce ""ahhhayee cas, ai daman albarkacin kaza ƙadangaren ke shan ruwa, kinga ko babu komai kin ci albarkacin Binta, kuma ba zan taɓa zaman yunwa a gidan nan ba"" Mama Zaituna ma ta yi nata shewar tana buɗe hannu ta ce ""Ai bari kiji na faɗa miki, ko yanzu Giwa ta faɗi, tafi ƙarfin Allah wadai, kuma ban miki kama da bora ba, ba boranci nake a gidan nan baƙi wannan uwar matan ba"" ta yi maganar tana nuna Ammo da hankalinta ke kan" "manjan da take aunawa, duk abin da suke tana jinsu bata kula su ba." "Inna Binta ta ce ""Ke da kika sani, tuwo ne dai kwasa uku zai kai ɗakina saboda tsaro""" """Ai kowa ba ki isa ba, sai dai a yi a sarar tuwon duk mu rasa""" "Inna Binta ta juya mazaunai ta ce ""Allah ko? Shege ka fasa"" ta ce tana kwasa tuwon a ƙatuwar ruba ta" "ƙiba ta saka murfi ta rufe. Mama Zaituna ta ce ""Ki daina wani juyi kina taƙamar jina da ƙiba, muma duk da ita muka zo wannan gidan, wannan tuwon ɗuwawun da kike taƙama da su in dai a cikin gidan nan ne sai sun dawo silifas, zaman ci da kai da wahala kike taƙamar kin aure mana miji"". ""To ko duka na za ki yi" "ne ban sani ba? Na ce ko za ki dake ni na matso?""" """Allah Ya rufa mini asiri haɗa ƙirji da kishiya, bai san da uwar da kike taƙama ba ki ci kan ki""." "Janye idanunsa Mutallab ya yi daga kallon su, ya nufi ɗakin Ammo yana ɗaga labule, Sa'adah ya gani" "zaune tana yanka alawar madara gwanin sha'awa, ya ƙarasa shiga ciki ya yi tsaye akan Sa'adah can ya nemi waje ya zauna kusa da ita, ya dinga kallon alawar madarar a hankali kuma ya saka yatsu biyu ya ɗauki guda ɗaya ya cilla a baki, ya yi saurin runtse idanunsa saboda wani zaƙi daya ratsa kunnensa can ya buɗe ido jin Sa'adah ta ce. ""Ta hamsin ka shafa Tayo, hamsin zaka bani"" bai kulata ba ya ƙara ɗaukan guda biyu ya tura a bakinsa, ta ɗago kai ta ce ""Tayo, kasan neman kuɗi da wahala kuwa? Kasan nawa ne" "gwangwanin madara yanzu?""" """Tsaya wai jarin zaka rusa mini ne?"" Ta faɗa ganin ya sake biyu ya tura a bakinsa hankali kwance. Baya ya" yi a hankali yana jingina ya harɗe ƙafafuwansa ya zubawa waje guda idanu. A hankali kuma bayan shafe "mintina ya ce ""Yaya"" ta kalle shi ta ce ""Autan Ammo ya aka yi ne?"" Ya ja numfashi ya ce ""Yaya me ya sa ni kaɗai ne namiji ne? Ina yan'uwan Ammo?""" """Suna gidan ubanka, na ce suna gidan ubanka"" ta faɗa tana ƙarasa shigowa cikin ɗakin, idanun Ammo ya" "yi jajur ta ce ""Mutallab, duk sanda na kuma jin ka yi tambaya makamancin haka wallahi idan ranka ya yi duhu sai ya ɓaci. Da kake tambayar me ya sa kai kaɗai ne namiji daman Ubangiji idan ya tashi yin halitta a ciki yana yin shawara da mai ɗauke da cikin? Ko butukcewa Ubangiji za ka yi da ka zo a namijin?" "Muhammad na daɗe ina taraka, yanzu kamar kai ka yi wayon da zaka riƙe waya? Kasan yadda ake bada labarin waya na lalata mutane? Ka ɗauki wasu halayya ka azawa kan ka babu gaira babu dalili? Idan ka sake na kuma ganin waya a hannunka sai ranka ya yi mummunan ɓaci, sakarai kawai"" kan shi a ƙasa, jiyiyon kansa na sarawa har tsakiyar kan shi yake jin faɗan Ammo, he miss it, tabbas wannan abun ya yi missing tare da kewa a rayuwa, faɗan uwa mahaifiya, sai dai ta yi masa faɗan a lokacin da bashi da iko da kansa a can baya kafin yau ya kamata a yi masa faɗan. Ya na ji ta gama ta sake fita, ko motsi bai yi ba. Sa'adah za ta yi magana sai ta fasa wayarta ce ta fara ringing ta yi saurin ɗauka ta ce ""Assalamu Alaika" "Habibi"" shiru ta yi sai kuma ta kashe wayar, a hankali ta fara hawaye tana kuka sosai, ta dinga kuka idan" "ta ji alamun Ammo zata shigo sai ta yi saurin goge hawayenta. Siririn tsaki ya ja, yana miƙewa tsaye" "kamar zai fita sai kuma ya saka ƙafa ya yi ball da wani kwano ya ƙara saka ƙafa ya daki ƙofar ɗakin idanunsa na fitowa waje ya ce ""Wai mene Yaya""" Ya ce a firgice. """Wai ya ce ya fasa auren nan nawa"" ta faɗa tana sake wani kukan, sai ya zama kamar shi ne babba ya" "dinga kallon ta. A daƙile ya ce ""Shi wa?""" """Saurayina, wanda zan aura""" "Mutallab ya ce ""Namiji kikewa kuka, namiji kikewa kuka yaya? Raina ki kike so ya yi ko mene?"" Ya ce" "yana ɗaɗɗaga mata gira, ta shiru ya sake matsawa wajanta muryarsa a saman kanta ya ce ""Kuka kikewa namiji?""" """Na Ammo baka san soyayya ba ko? Saboda kai yaro ne?"" Ya dinga kallon ta, yana nanata yaro a kansa ta" "ce ""Wallahi ina son shi sosai, burina bai shige na yi aure na bar zaman gidan nan ba, na je gidan ƴanci ko zan samu halin taimakawa Ammo, shine yanzu sai ya fasa auren, ya gaji da ɗagawa da ake yi, ga matsalar Malam na aure aure yana sakin yara kara zube ya je kunnen iyayensa, ina jin tsoron gorin dangin miji, kuma ina son shi"" A hankali ya ja numfashi ya durƙusa daidai kanta fuska a kame yana yi yana riƙe gefen kansa, ya dinga kallon ta ya nisa ya ce ""Sau biyu kenan, sau biyu yaya, kin kalle mini ƙirji, kin ce mini" "yaro"" idanunsa har wani ruwa ne yake kwanciya a cikinsu, jikinsa na ɗan rawa. Sa'adah ta ce ""Tayo""" Ya zuba mata ido. """Daman ba rarrashi na za ka yi ba? Yayarka ce ni fa?""" """Na sani ai yaya, bana son ana ƙasƙantar da kimata, da gaske ban so"" a sanyaya Sa'adah ta ce. ""Allah Ya" "baka haƙuri"" ya ƙanƙantar da idanunsa ciki, ƙirjinsa na buɗewa ya daɗe a haka sai kuma ya ja numfashi ta ƙirjin ya haɗiye ya ce ""Ki ce ya zo gobe ya amshi komai nasa"" ta yi saurin kallon shi ta ce ""Bama a sasanta ba? Na gaji da zama a gidan nan shine zaka ce ya zo ya amshi kayan, wallahi ina son shi ,""" """Quiet yaya, silent""" "Ya ce yana miƙewa sai ya girgiza kai ya ce ""Abin da zan yi dole sai ya zo ok,ai bani da burin lalata miki" "farinciki ok? Zan kawo miki ganyen LIMƘABIN KALGO ki haɗa da jar kanwa ki jajjaga shi, bayan kin jajjaga ki saka a rana ya bushe, bayan ya bushe sai ki daka ya zama gari. Sai ki samu madubi irin naku ki wanke ki shafe garin da kika haɗa da jar kanwar ki shafa a saman madubin, idan ya ɗan jima kaɗan sai ki kwashe na saman madubin ki shafa a fuska, ba shima ko Gwamna sai buzunsa ok, aure dole ne"" ya ce kai tsaye yana taune lips, Sa'adah ta dinga kallon shi tana tsoron ta yi magana ta tunzuro shi. Ta kasa yin shiru ta" "ce ""Ina kasan wannan sirrin Tayo?""" """Ki bar shi idan bakya so, sirri ne mai zaman kansa na ba ki saboda Allah da Manzonsa, wallahi ko faɗa" kukai da mijinki kafin ya dawo kikai wannan sirrin uhm... Yaya kenan kina bina sau da ƙafa ina miki "abubuwa, amma yaya ni kike cewa yaro ni, a nan ɗina na ji zafin maganar nan yaya""" "Ya nuna mata tsakiyar ƙirjinsa, yana shigar da idanunsa ciki, Sa'adah ta miƙe tana murmushi ta ƙarasu" "zata taɓa shi sai data miƙo hannunta ya zame, ta tuntsira ta kifa ƙasa ta ce ""Wayyo hannuna,zaka karya ni fa"" ya kalleta sai kuma ya dunƙule hannunsa ya dinga haɗa zufa, ta miƙe tsaye ta ce ""Saboda ka taimaka mini shine kuma zaka kassarawa mijina ni? Ture ni fa ka yi Mutallab?"" Bai tanka ta ba, sai kallon gefe da ya dinga yi, hannu ta miƙa zata riƙe shi babu zato kamar kuma daga sama ta ji saukar kunama a cikin rigarta, wani ihu Sa'adah ta kurma a gigice ta hau zazzage rigarta tana cewa ""Wayyo Allah, Ammo, Malam Anyy Hameeda, Bafullatana wayyo na shiga uku wani abu a rigata wayyo Allah, Mutallab ka taimaka mini"" ya saka hannu ɗaya ya ɗan tushe kunnensa guda, bai kuma motsa ba. A haka Ammo ta shigo da gudu zuwa cikin ɗakin ta ce ""Sa'adah lafiya ne wani abun ne?"" Sa'adah ta kasa magana sai haki take tana ƙanƙame hannun Ammo. Rigar suka fara zazzagewa sai ga ƙatuwar kunama ta faɗo daga cikin rigar Sa'adah ta mace, Ammo ta ce ""Subuhanallahi kunama ce ai garin yaya haka?"" Ta girgiza kai tana kuka har lokacin, ta juya ta kalli Mutallab ta ce ""Auta kai kuma kana jinta ko ka taimaka mata eh?"" Ya juyo ya kalli Ammo sai bai ce komai ba sai zufa dake tsattsafo masa a tsakiyar goshinsa ta ce ""A rayuwa idan baka taimaki yan'uwanka ba Muhammad suwa zaka taimaka? Baka da kamar su a duniya wallahi, ina sake maka tuni da ƙarfin zumunci idan mutum bai yi a duniya ba dole zai yi a lahira. Ka fita can ana kiran sallah ka bani waje"" ta yi ta gama bai motsa ba a hankali ya saka babban yatsarsa ya shiga murza tsakiyar goshin nasa. Har zai fita ya juyo ya ɗauke bokitin alawar madarar ita dai Sa'adah bata kula shi ba" ta a hankali take jan numfashi saboda zafin ya fara raguwa ba karamar ɗazo ba. "***Tana zaune a ɗakin tsakiyar gado ta tanƙwashe ƙafafuwanta waje guda, ta ɗora filo a cinyarta" hannunta ɗaya riƙe da waya ɗayan kuma wani ƙaramin littafi ne a hannunta. A hankali take danna wayar "tana yi tana sauke numfashi a hankali take duba bayanin da ake yi akan drama ɗin, ita ba san ya aka yi aka cire sunanta a English club, aka mayar da ita Hausa drama shi ya sa ya rasa amsar bawa Kimiyya," "gashi kuma dole idan aka zaɓi mutum sai ya yi abin da ake buƙata, but ita a takure take wannan bayanin" is too much ita duk ta ina zata iya haddace waɗannan? Babu space ɗin haka a ƙwaƙwalwarta. """Safiyyerh...!"" Aka kira sunanta a ana buɗe ƙofar tare da shigowa cikin ɗakin nata." """Ummi"" ta ce a hankali." "Ummi ta ƙarasa shigowa cikin ɗakin hankalinta duka a kan Aafiyyah. Ta ce ""Me kike yi ba ki fito dinner ba?" "Kin sha maganinki"" Aafiyyah ta buɗe ido sai ta ce ""Laa, bana jin yunwa ne Ummi"" Ummi ta nemi waje ta zauna gefen gadon, ta miƙa hannunta, Aafiyyah ta miƙa mata wayar hannunta, Ummi ta amsa ta shiga WhatsApp ɗin Aafiyyah ya gama dube dubenta, ta shiga wajan bidiyos da photos ta gama dubawa, ta dawo wajan call logs ta duba ta shiga wajan messages nan ma empty sai alert na banki da aka tura mata" "kuɗi. A hankali ta ce ""Safiyyerh...!""" """Na'am Ummi"" Aafiyyah said." """Ki yi haƙuri kin jini daughter, kina kan daidai muma haka, haka kuma daddy don't feels bad""" "Jinjina kai kawai Aafiyyah ta yi tana lumshe idanunta bata ce komai ba. ""Safiyyerh""" """Uhm'uhm Ummi, kar sunana ya ƙare haba Ummi"" ta ce tana yarfe hannunta idanunta ya cika da ƙwalla" "kamar mai jira dama. Ummi ta ce ""Wai yaushe za ki daina shagwaɓa da kukan banza ne? Ni duk na rasa meke damunki sai wani zuƙewa kike kina ramewa? Ko wani abu kika saka a ranki?"" Sai Aafiyyah ta fashe da kuka, ta faɗa jikin Ummi tana birgima da ihu tana cewa ""Ummi kai na, kai na ne?"" Ta dinga kuka tana" "birgima, Ummi ta saki baki tana kallon ikon Allah, can kuma ta buɗe ido a tsorace tace." """Safiyyerh mene a jikinki nake gani kamar jini? You are bleeding""" """Bleeding?"" Aafiyyah said, loudly with shocked a fuskarta. Sai ta tsayar da kukan nata tana zazzare ido. A" "hankali Ummi ta yi murmushi ta ce ""Ashe da akwai abin da zai ba ki tsoro? Yaushe kika fara ganin haka?""" "Aafiyyah ta gigice ta sake sakin wani kukan cikin shagwaɓaɓɓiyar muryarta ta ce ""Innalillahi, Ummi I'm" "scared jinina zai ƙare wayyo daddy my blood jinina"" Ummi ta riƙe ta, ganin how scared of na abin da ta gani, gabaɗaya bata son ganin jini hankalinta tashi yake yi. Ummi ta jata har zuwa bathroom ta ce ""Yi wanka ki wanke jikinki sosai ina zuwa"" har Ummi ta fita sai ta dawo ta ce ""Ki saka warm water"" fita ta yi. Kafin ta dawo Aafiyyah ta gama yin wankan, ta buɗe banɗakin kai tsaye ta shiga, tana sanye da towel a jikinta Ummi ta dinga kallon ta sai ta miƙa mata pant da audigar data haɗa mata ta ce ""Saka"" bata musa ba ta amsa ta saka, bayan ta kammala ta bata wani ƙaramin turare ta ce saka a ƙasan wuyanta a" hammata. "Aafiyyah na zaune tana jinta duk wani iri a jikinta, ƙaramin short jeans ne a jikinta sai wata rigar pallazo" "mai faɗin hannu. Ummi ta kira sunanta ta ce ""Safiyyerh wannan jinin da kika gani a jikinki shi ake kira da jinin al'ada, wanda Ubangiji ya ɗorawa kowacce ɗiya mace hakkin yinsa face wacce take da ciki ko shayarwa, ana cewa wacce bata al'ada to bata haihuwa ne. Ina faɗa miki wannan ne saboda hakkina ne nauyi nane, it's my responsibilities ba sai na jira malami ba, ni ce nan malamarki Safiyyerh. Wannan jinin da kika gani duk wata ake yinsa, wasu farkon wata wasu ƙarshe, wasu tsakiya idan ana yi ba'a sallah kuma ba'a yin azumi, kinga kenan bake ba yin azumin ranar litinin da kike na Alhamis da juma'a, ba'a" "rama sallah amma ana rama Azumin da mutum ya sha kin gane?"" Aafiyyah ta jinjina kai." """Abu mai mahimmanci""" """Ummi"" Aafiyyah kira sunan a raunace ta ce ""Tsoro kike bani da waɗannan bayanin""" """Babu tsoro Safiyyerh, matakin girma ne duk da na yi mamaki da ganin hakan sai dai ko wacce ɗiya mace" "da yanayin yadda take farawa, sai yanzu na san dalilin rashin lafiyarki farawar da za ki yi ne, sai dai Dr bai yi mana mentioning hakan ba. Safiyyerh daka ranar da mace ta fara jinin al'ada tana bari namiji ya taɓa hannunta zai mata ciki, kuma kin san yin ciki haramun ne Ubangiji ya yi hani ga hakan idan ba aure aka yi ba, shi kuma aure ana yi ne sanda yarinya ta cika shekara 25 a duniya ba a irin wannan shekarun ba, kinga You have to be very careful, cikin shege ai ba kyau ɗiya mace da nutsuwa aka sonta da kamewa ki" "riƙe mutuncinki sai kowa ya girmama ki, mu mata ƙashin haƙarƙari ne""" "Ta sauke numfashi ta ce ""Ki taya mu tattala tarbiyyarki har zuwa sanda ya dace kin ji?""" "Aafiyyah da idanunta ya cika da ƙwalla ta ce ""I will, i will Ummi as so much as I can, zan kula""" "Sai kuma ta yi shiru, can ta ɗago kai ta kalli Ummi ta ce. ""You promised me, daddy promised too," "everyone promised me Ummi, don Allah keep your words and promised don Allah Ummi, zan yi abin da kuke so nima ku yi mini""" "Ummi ta dinga kallon Aafiyyah kallo na tsanake da haƙiƙa, ta san halin yarinyar da mugun saka abu a rai," "amma tana kiyaye duk wani abu da za ta yi ransu ya ɓaci tana tsananin ƙaunar mahaifinta. Ummi ta sauke numfashi slowly ta ce ""keep praying Safiyyerh"" ta miƙe ta fice. Aafiyyah ta bita da kallo a hankali ta cije lips ɗinta, tana kiran sunan Allah a zuciyarta. Daman 10:00 ake sawa ta kashe ta ajjiye idan karatu ne ta buɗe system, ta kwanta ta shige cikin duvet ba bacci take ba tana ji Ummi ya shigo ɗakin ta kwanta kusa da ita, har wajan 2 da rabe na dare da Ummi ta miƙe a hankali ta fita without making any sounds da zai sakawa Aafiyyah ya farka ba tare data san idanunta biyu ba, har dab da asuba da Ummi ta sake dawowa ta kwanta kusa da Aafiyyah idanunta biyu still. Har aka fara kiran sallah ta farko ta miƙe, ta yi wanka ya sake gyara jikinta sanin ba sallah za ta yi ba sai ta zauna ta fara azkar thinking ko daddy na gari" yau?. "7:15 ta fito entrance na gidan a hankali take tafiya, kasancewar kuma Friday ne sai ta yi using sportswear" "na makarantar wanda yake kasance brown colour ya yi mata kyau sosai, ta saka baby hijab ko breakfast bata tsaya ba. Murmushinta ya faɗaɗa tana lumshe idanu ta buɗewa a hankali ta ce ""So you are here" "Baba, daka yi zamanka sai na yi driving""" """Rufa mini asiri ƙaramar Hajiya, ai tuni na gyara mota muje kawai""" """Baba. ,"" Aafiyyah said with smile on her face, tana zura hannunta ɗaya wando ya ce ""Hajiya ƙarama" "barka da wayewar garin juma'a muje na kai ki makaranta na dawo na yi shirin masallaci"" Aafiyyah ta dinga murmushi ta ɗan rusuna kaɗan ta ce ""Ina kwana Baba?"" Ya amsa cike da farinciki, ya buɗe mata bayan mota sai ta ingiza kai ta ce ""Ko gaba zaifi?"" Ya buɗe mata ta shiga, a hanya ya dinga mata hira ta yi shiru wani lokacin kuma sai ta yi murmushi ta juyo ta kalle shi ta ce ""Baba ka yi mini addu'a"". ""Addu'a kullum ana yi Hajiya ƙarama, rayuwa za ta yi albarka in sha Allah"" ta ɗakko kuɗi ta ce ""To ga sadaƙa"" ya" amsa ya dinga sanya mata albarka cike da fara'a. A kusan tare motoci wajan ukun sukai parking a harabar makarantar Fgc. Kimiyya ya buɗe ya fito yana mamakin ganin Aafiyyah yau a gaban mota kuma ita da driver ya yi murmushi ya ƙarasa yana buɗe mata "ya ce ""Barka da zuwa crush"" Ta yi masa murmushi ta ce ""Morning Kimiyya"" Safiyyerh ta ƙarasu ta ce ""Hi""" "Kimiyya ya ce ""Ta bestie ikon Allah irin wannan sammako haka, ko kema kina da drama a club naku?"" Ta" yi murmushi kawai. """Safiyyerh how are you?""" """Allahamdulilah, as you can see Aafiyyah ya jikin nakin?"" Shoulders Aafiyyah ta ɗaga, bayan ta fito da" "shade glasses ɗinta ta saka hannunta duka biyun cikin aljihun, ta ɗan matsar da ƙafarta ɗaya baya, ɗayar kuma a gaba, yanayin tsaiwarta zai saka ka fahimci ta saba buga ball. Gabaɗaya sportswears ne a jikinsu, na Safiyyerh black colour Kimiyya ma nasa black ne sai Aafiyyah mai brown. Tafiya suka yi a tare har zuwa cikin makarantar tun daga nesa ta hango shi ya harɗe ƙafarsa ɗaya a saman ɗaya, shi kaɗai sai hannunsa dake riƙe da wani abu da yake busa yaƙi a hankali yana yin sama. Murmushi ta yi tana jin wani irin farinciki a zuciyarta ganin Aafiyyah kuma ya saka ta kasa ƙarasawa gare shi ɗin, duk da yadda zuciya" "ke janta zuwa gare shi, daman da damuwa ta kwana kuma." "Aafiyyah ta zaro wayarta a aljihu, still hannunta ɗaya a cikin aljihun, ta ɗan matsa kusa da Safiyyerh a" hankali ta ce. """Ba'a sanyin jiki, da sanyin safiya ake kama fara safiyyerh. Ga bestienki can ki je""" """Aafiyyah!""" """Yes, go mana""" "Safiyyerh ta kalli Aafiyyah da mamaki ta ce ""Wonderful, Aafiyyah kuma lafiya kike yau ɗin nan? Naga" "bakwa shiri da Mutallab what exactly wrong with you har kike cewa na je wajansa, shi ya ce yana buƙatar ganina?"" Aafiyyah ta girgiza kai, tana ɗan cilla ƙafarta gaba ta cake ta akan ball ɗin da Kimiyya ya cillo mata ta ce ""Oh, ai bani da wani business da shi, me ya sa zan faɗa da shi? Why should i Safiyyerh? Bani da matsala da shi and he never be my headache. Tunda daga nesa kike ƙoƙarin sauya hanya zuwa gare shi, Safiyyerh ki yi soyayya mana ai ba wani matsala idan hakan zai sama miki farinciki, kina yi kina" "tuna muhimman abubuwa, soyayya akwai daɗi sai dai love is flying """ """... love is flying?""" "Safiyyerh ta maimaita tana kallon Aafiyyah. ""Yes, mana""" """Bangane ba, me hakan yake nufi?"" Safiyyerh repeated again. Aafiyyah ta ɗaga kafaɗa ta ce ""Love is" "flying, ki yarda mana""" """Aafiyyah kenan, kina raina tunanina sometimes, ko babu komai i older than you""" """And? Shi wai shekarun nan da kike proud da su kina ɗaɗɗaga shoulders a kan su, a tsakiyar goshi ake" "rubutawa ne?""" """Namesake kenan, na san ki fa""" """Kamarya?"" Aafiyyah ta tambaya tana murza ball ɗin ƙafarta Kimiyya na jin su. Safiyyerh ta yi shiru kawai," "Aafiyyah za ta yi magana Kimiyya ya ce ""No, please. A bar maganar my crush"" banza ta yi masa, ya miƙa hannunsa zai riƙe nata ta yi saurin kallon shi tana buɗe masa manyan idanunta ta ce ""Kar ka fara Kimiyya"" ta juya kan Safiyyerh ta ce ""Ke sometimes kan ki baya kawo nepa Saff, ki yi amfani da lokacinki wajan janyo hankalin wanda kike so a kan ki, love him, care about him, ki sauya shi zuwa yadda kike so, ina ba ki tabbacin zai ba ki duk me kike buƙata trust me"" tana cewa haka ta sunkuya ta ɗauki ball ta ce" """Ki je mana, bari na ɗan buga ball""" "Aafiyyah ta juya ita da Kimiyya. Safiyyerh kuma ta nufi inda yake zaune ya hakimce tare da kame fuska," "shima sportswear ne a jikinsa brown colour, sun haska baƙar fatarsa ya saka p.cap ta rufe masa ido. Ta ƙarasa tana cewa ""Assalamu Alaika bestie me"" bai kalle ta ba, sai naɗe ƙafarsa da ya yi kawai ta nemi waje ta zauna a hankali ta leƙa fuskarsa suka haɗa ido, ya buɗe mata manyan idanunsa. Ta yi murmushi" ta ce """Good morning Mai dawa""" "Ta miƙa hannunta ta amshe abin hayaƙin da yake busawa, ta miƙa hannunta a hankali zuwa bakinsa ta" "buɗe, a hankali ta kai nata bakin ta shanshana ta lumshe idanunta jin ƙamshin minti. ""Na ɗauka zan ji" "warin hayaƙi, so amazing bakinka ƙamshi sosai"" ta buɗe abin hannunta, breakfast ɗinta ta buɗe ta gyara" "zamanta, soyayyan dankali ne da ƙwai sai Indomie wacce aka yi fried Indomie with egg da sauran potatoes soup. Ta saka masa spoon a gabansa ta ce ""Ina gaishe ka kaƙi amsawa babu kyau fa, kuma" amsa sallama wajibi ne in ji faɗar Annabin tsira. """Kina zuwa islamiyya ashe""" "Ta ji maganarsa a nutse ta sauka a kanta har zuwa ƙirjinta ta ce ""Me ka ɗauka to? Ina zuwa makarantar" "islamiyya a bayan layinmu, weekend ma ai tahfix nake yi don ka ji, ina da ƙoƙari sosai sai dai"" ta yi shiru yanayin fuskarta duk ya sauya idanunta ya cika da hawaye ta ce ""Bestie, ban san meke damuna ba, an kasa fahimta ta, ba wanda yake son jin damuwata, hatta kai ma da abin da nake yi, na yi dominka ka kasa fahimtar zuciyata ka kuma kasa yi mini uzurin cewa ba yin kai na bane, hatta a Islamiyya bana gane karatu wallahi, a baya na fi kowa bada hadda amma yanzu ko aya biyu bana iya riƙewa, na kasa yanzu bana fahimtar karatu"" ta sunkuyar da kanta ƙasa tana goge hawayen idanunta ta ɗago ta ce ""Ni sai nake" "ji kamar na mutu"" ta sake yin shiru ta kalle shi tana murmushi ta ce." """Kuma ba lallai na mutun ba ko?"" Hawaye ya zararo mata ta kifa kanta a kan ƙafarsa ta shiga rera masa" "kuka, irin kukan data ke fata ta samu damar yi ta kasa, sosai take kukan wanda hakan ya saka take jin sauƙi a zuciyarta. Mutallab dai kallon ta yake, deep down na zuciyarsa yana jin tausayinta, idan ya tuna Jaanah baya jin daɗi, ba zai so Safiyyerh ta rasa ranta sabo da shi ba, baya kuma buƙatar zutar da" zuciyarta. """Maybe ban da rabo ne, wannan Safiyyerhn ba rabon Mutallab ba ce. Soyayya rayuwa ce bestie, abu" "biyu ke cutar da kowanne mai rai SO da ƘI, ka yi mini uziri maybe ina over acting, wallahi ban san ina yi ba, da so kawai idan Ubangiji yaga dama sai ya azabtar da bawansa, ƙilan akwai abin da na yi wanda bai kamata ba"" Ta yi dariya tana goge hawayen idanunta, ta ɗaga masa gira da kashe ido, a hankali kuma ta" "ɗaga kafaɗa ta ce ""So i realise cewa na yi failing, na faɗi a soyayya kuma i accepted it.""" """Are you going to give up?"" Ya ce yana tsattsare ta da idanunsa." "Safiyyerh ta ce ""Over my died body Ina nan ina son ka, kuma i will wait for the day da zaka amince zan" "ihu da murna sosai""" """Hmmm""" """Mu ci abinci""" "Ya kalli spoon ɗin, ya kalli hannunta ya girgiza kai ya ce ""Da hannu nake ci ai"" ta ce ""Tab, ban yarda da" "tsaftar hannunka babu mamaki ka shiga jeji jiyan nan, muga hannun"" ta saka hannu ta janyo hannunsa ta dubi yatsun hannun taga farce ya taro sosai ta ce ""Ƴan ƴan ƴan mai dawa ƙazami, bari na yi aikin lada na fara aikin lada, kuma aikina tun yanzu, as your wife"" ya dube ta, ta ɗakko abin yankan farce mai kyau ta fara yanke masa a hankali. Bayan ta kammala tas ta saka ruwa ta wanke masa daidai nan su Aafiyyah" suka ƙarasu wajan Safiyyerh bata lura da su ba don haka ta ce. """Bestie...""" """Hmmm"" ya ce yana duba yatsun hannunsa yadda ta yanke masa farcen ya yi kyau sosai." """Sweetheart" """Hmmm""" """Ka san me? Dole sai fa ka aure ni wallahi, ko kana so ko baka so i don't care, Allah sai na zama matarka" "da gaske kuma zan zame maka mace ta gari da na ji ana faɗa i promise you, zan amsa sunan matar Mutallab""" """Matar Moh, za ta zama mai irin halin Moh ne kawai Safiyyerh """ "Safiyyerh ta gyalgyale da dariya sosai, har tana ƙwarewa ta girgiza kai ta ce ""Mene a halin naka banda" "son kai? E, kana da halin son kan ka as always, baka damu da damuwar wani ba, you don't care about my feelings, all the time kana wasa sa emotions and feelings nawa saboda wani ra'ayinka mara tushe." "Shariya, rashin fara'a kamar ka ce ka shiga uku, rashin sukuni da zuciya ƙifaɗi ɗagawa taƙama, duk halin" "mijina Mohammed Mutallab Abdullahi, kuma bai daman ba i am still loving you dear, the way you are" "zaka sauya ne""" """You are not serious Safiyyerh""" """I love you """ "Aafiyyah na zaune ta ce ""Iyee ga wasu sabbin ƙinƙisa, lemme snap them na nunawa jikoki da ƴa ƴa""" "pictures ta yi musu. Mutallab ko inuwarta bai kalla ba, ya tattara hankalinsa waje guda yana cin abincin yana sauraren hirar Safiyyerh jinjina mata kai kawai ya yi. Ji ya yi ta yi shiru ya ɗago kai ya kalleta, ya ga shi take kallo idanunta cike da hawaye ya ɗauki dankalin ya miƙa ta maƙale masa kafaɗa a kumbure ya ce ""Ko dai ki amsa, ko na danne ki na ɗora miki da sai ki tsaya kina kallo na"" ɗan ƙaramin bakin nata ta buɗe masa ya zubawa fararen haƙoranta ido ya zura mata dankalin ta amsa ta fara ci. Safiyyerh ji ta yi" "nauyin ƙirjinta ya ragu, suna zaune aka ce lokacin drama ya kusa a shiga drama hall." Hall ɗin ya cika sosai Safiyyerh ta dinga dubawa babu Mutallab. Hausa drama aka shirya wani ɗan "ƙaramin script da yake nuna rashin jituwar aure da ake samu akan ƙabilu biyu Yaruba da Hausa Fulani, yadda Yaruba basa son bawa Hausawa auren yaransu daga ƙarshe yaran su bijire musu illar hakan har a rasa ɗaya daga cikin yaran, inda macen ke mutuwa shi kuma namiji ya samua depression. Title kuma na Hausa drama ɗin shine DANGANA. A hankali aka dinga gabatar da gida-gida na shirin har aka zo inda za a" nuna saurayin ya zo wajan budurwar har ƙofar gidansu ita kuma ya fito a gigice. “Yaruba boy” "Safiyyerh ta ce a hankali, ganin ya shigo hall ɗin a hankali jikinsa sanye da kayan yarabawa, har da gashin" "hannun ya yi wani irin kyau, ba zaka taɓa cewa shi ɗin ba jinin Yarabawa bane yana wata tafiya" "majestically sai cije laɓɓansa yake da sukai jajur. A hankali ya duba agogon hannunsa sai wani yaro ya zo shigewa a hankali Mutallab ya ce ""Hey you""" "Yaron ya tsaya ya ce ""Bawo ni MO ṣe le ṣe iranlọwọ? Ta ya zan iya taimaka maka?""" "Mutallab ya yi jim, zuciyarsa cike da tsoro da fargabar ko za ta fito? Ko iyayenta a wannan karon za su" bar ta? Ko za su yi masa alfarmar auren Aafiyyah? He can't do without his Iyafin. """Call.....,"" ya ja numfashi a ƙirjinsa ya ce ""Kira Aafii....." """Aafiyyah dai?"" Cewar yaron. Mutallab ya jinjina kai, yaron ya juya zuwa cikin gidan. Mutallab ya tsare" "ƙofar gidan da idanu, babu jimawa sai gata ta fito kyakkyawan shigar Hausawa ce a jikinta shigar Hausa Fulani, atamfa riga da zani ɗaurin ya ɗan zame ganinta ya fito. Kallon cikin idanu suke wa juna, Aafiyyah na yi wa Mutallab kallon ""You are here?"" Shi kuma yana mata kallon ""Are you ready to runaway" "Aafiyyah?""" "Aafiyyah ta zame idanunta ta ƙarasa muryarta na rawa ta ce ""Suna nan a kan bakan su, ba za su bari mu" "yi aure ba, za su raba mu"" hawaye ya fara zuba daga cikin idanunta ya matso dab da ita, numfashinsa na sauka a fuskarta har tana jin ƙamshin bakinsa calmly ya ce ""I know, na sani"" Aafiyyah ta yi shiru. Ya saka hannunsa ɗaya ya tallafo haɓarta ya ce ""We have to runaway Aafi..""" """Kana nufin mu gudu daga wajan iyayenmu? Kana nufin na bar iyayena na bika?"" Ya ɗage mata girarsa" "duka biyun yana sake ƙarewa fuskarta ta asalin fulani kyau, ya saka yatsa ya dinga share hawayen fuskarta da tsayarsa ɗaya a hankali ta matso kusa da shi, ta saka hannunta ta kamo nasa ta riƙe sosai ta ce." """Iyayenmu masa son soyayyarmu Tayo, Kabi umarnin naka iyayenka nima zan bi nawa, ka auri" "ƴar'uwarka Yaruba, nima na auri Hausa Fulani. Something is over doesn't mean your life is over, love is flying, shi kuma zan iya ajalina"" Aafiyyah ta ɗago ta kalli cikin idanun Mutallab ta ce ""Wannan shine damar da nake shi na faɗa maka how much i love you. Idan har zuciya zata dinga bugawa da amfanin iska tana zagayawa da jini a dukkan lungu da sako na jiki tsawon shekaru ba tare da gajiyawa ba, bana tunanin zan taɓa gajiya da son ka Tayo. Da ace ana ganin shauƙi da tunanin zuci a zahirance, da na nuna maka yadda son ka ya mamaye zuciyata. Tun dana sanka zuciyata ta kasa tsayawa da tunaninka, akwai wani abu na musamman game da kai da bazai taɓa barina na manta da kai ba. I love you endlessly! I love" "secretly! I love you like a crazy! I love you today tomorrow and always""" "Aafiyyah ta fara ja baya yana binta, ya rufe bakinta saboda kuka sosai ta ce ""You still remain in my heart," "amma mu haƙura da juna mu bi umarnin iyayenmu""" """I can't Aafiyyah!""" """Why?"" Ta ce masa, tana sake yin baya yana matsowa wajanta ya saka hannu ya damƙo hannunta a" "daidai kunnenta ya ce ""Because you are a tiger, ke ya dace da zama matar Moh fil'duniya kuma til-janna i adore you Aafi"" juya ta yi saboda kukan da ya ƙwace mata yaƙi sakinta ""Ka cika ni, ka sake ni Please mu haƙura da juna haka Tayo"" Ya girgiza mata kai sai kawai ta faɗa jikinsa tana sakin wani irin raunataccen" "kuka zuciyarta na bugawa da ƙarfi, Mutallab ya yi shiru sai ya fara tuna last abin da zai yi a cikin script ɗin, he hold her back a jikinsa ya rungumeta, Aafiyyah ta dinga kuka zuciyarta na buɗewa, a hankali ta fara tari jini na fita ta cikin bakinta idanunta na rufewa jikinta ya saki ta zame daga jikin Mutallab ta faɗi a" wajan babu numfashi. "“Cut. !"" Mai kula da drama ɗin ya ce, aka buƙaci Aafiyyah ta miƙe. Abu kamar wasa Aafiyyah bata" "motsi. Class teacher ɗin ya ƙarasu ya fara kiranta ""Aafiyyah, Aafiyyah"" amma shiru ya ce ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Aafiyyah died bata numfashi"" da sauri Muhalli ya ture class teacher ya durƙusa akan ƙafafuwansa ya fara jijiiga Aafiyyah amma ina bata numfashi bata motsi. Safiyyerh da tun ɗazo ta daskare tun farkon fara drama ɗin tanja wani irin numfashi ta miƙe da gudu ta ƙarasa wajan itama, a daidai nan daddyn Safiyyerh ya shigo hall ɗin hannunsa ɗauke da tafkekiyar bulala, daman daga office ɗin principal yake kai tsaye, idanunsa ya sauka akan Mutallab, sai yake ganin Aafiyyah dake kwance" tamkar Safiyyerh bai tsaya jiran komai ba ya rufe Aafiyyah take sume a ƙasa da duka idanunsa rufe. "Gana yau da Laraba, mu haɗu Alhamis ." Mutallab paid book ne #500. Pay before you read 08164069385 "[1/7, 9:35 PM] Sis Fauzy: Chapter 34: Frist visit" "Safiyyerh ta ƙarasa wajan da sauri tana fasa ihu ta ce ""Daddy Aafiyyah kake duka, Aafiyyah ce"" amma ina" "sam idanun daddy ya rufe, tsoro kuma da mamaki ya saka mutanen wajan suka kasa yin wani motsin" "kirki. Da dukkan ƙarfinsa ya saka hannunsa a ƙirjin Prof ya hankaɗe shi zuwa baya, jikin Mutallab sai kyarma yake yi sai kuma girgiza kansa yake yi." "Da mamaki Prof ya kalli Mutallab da kyau yana gyara tsaiwa ya ce ""Wato ba za ka rabu da ƴa ta ba? Ka" "zame mini masifa da anno ba?"" Ya yi ƙwafa." """Point of correction, ƴarka ta zame maka masifa dai ba ɗan Malam Abdullahi ba"" Mutallab ya ce yana" "huci kamar ya ci babu, yana sake kallon bulalar dake hannun daddy. Shima daddyn ya ce ""Ka bani waje, laifina ne dana saka Safiyyerh a makarantar da zata iya haɗuwa da ƴaƴan talakawa irinka. Kuma zan yi wa malaman magana na ji yadda aka yi suke barin lalataccen yaro irinka a wannan makarantar mai mugun nufin lalata mini yarinya""" """Ko? Wannan da kake duka ba ƴar taka bace, ka je ka yi iko da wacce ka haifa ba wannan ba. Kuma ba'a" "nunawa Mutallab ba'a son abu ka gane ko?"" Ya ce yana cije lips. Har zai juya sai kuma ya ce ""One more thing, zan yi farinciki idan ka hana gudaliyar ƴarka bibikona"" kafin Prof ya yi magana principal ɗin makarantar ya shigo hall ɗin, tare da wani, sai bawa wanda suka shigo da shi haƙuri yake ko kallonsa bai yi ba, da wani irin mamaki yake duban Aafiyyah dake ƙwance kamar bata numfashi, ya yi saurin durƙusawa ya ɗago ta zuwa jikinsa yana jijjigata idanunsa yayi jajur ya ɗaga kai ya dubi malamin nasu" "Aafiyyah ya ce ""Waye ya yi mata dukan nan? Wane ya dake ta?""" "Teacher ɗin ta ce ""Don Allah ka fahimta, kuskure aka samu""" """Problem? Kuma akan ta za'a samu matsalar? Kalli jikinta? Ya haifeta ne da zai mata wannan jahilin" "dukan? Mari wannan rabon da ta yi abin da za'a mare ta na manta ba wai don ta shige duka ba, shine zai yi mata wannan mummunan dukan? For what reason eh?"". Cike da banbaki Principal ɗin ya ce ""Ka yi haƙuri, kowa ya san yarinyar nan bata da wata matsala a makarantar nan, kuskure aka samu, ya ɗauka" "yarinyarsa ce shine ya rufe ta da duka da nufin hukunci"" teacher ɗin ya ce" """We are very sorry please""" """Sorry for yourself. Idan ƴarsa ce haka ake tarbiyyar yarinya, wane ya ce duka yana gyara yaro? To" "hukuma zata raba ni da shi"" teacher zai sake magana ya ɗaga masa hannu ya ce ""Ka yi addu'ar wani abu bai same ta, sai mu ɗora bayan jan kunnen da na yi akan kada a saka ta a drama ɗin, ai tun kafin yau na san za su yi kuma ban amince ba, har makarantar na shigo na nemi alfarmar hakan"" ya ja siririn tsaki tare da ɗaukan Aafiyyah ya fice daga cikin hall ɗin. Tun kafin ya ƙarasa wajan motarsa dake waje guda sai sheƙi take yi, kafin ya ƙarasa driver ya buɗe masa ƙofar, ya shiga cikin motar hannunsa ɗauke da Aafiyyah, a tsorace yake jijjigata da kiran sunanta tare da fargabar abin da zai faɗa a gidan, they won't take it, ciwon Aafiyyah barazana ce a gare su, musamman mahaifinsu ba zai ɗauka ba,sau huɗu yana kiransa a hanya akan is she ok? Wani abu ya samu Safiyyerh ne? Jikinsa ya yi babu daɗi, go and check her, ka tabbatar lafiya take kuma ka kira ni vedio call na ganta i want to see my daughter. Shine abin da Paah ya dinga faɗa masa a waya, bai san zai zo ya same ta haka ba yana shigowa yake ganin ƙaton banza" na dukanta? Yana da hankali? Ko ƴar cikinsa zai wa haka ne?. Ya sake jan tsaki ya ce """Mu je asibiti Baba, ba zan iya zuwa gida da ita haka ba, ina mai jin tsoro a zuciyata sosai"" Baba ya ce ""Ka" "yi addu'a babu abin da zai samu Hajiya ƙarama""" """I hope so "" Ya ce yana rungume Aafiyyah a jikinsa cike da ƙauna." * "Safiyyerh ta durƙushe a wajan, dukkan jikinta rawa yake da ɓari hatta zuciyarta rawa take yi" "kwatankwacin yadda jikinta ke rawa, ta cure waje guda, ko kukan ta kasa yi wani abu ya tsaya mata a ƙirji ta fara kokawa da abin da kuma numfashin daya tokare mata ƙirji zuwa maƙoshi, a yanzu ba damuwarta faɗan daddy ba, ba damuwarta dukan da zai yi mata ba, ba damuwarta hantarar da Mutallab zai yi mata ba, ba damuwarta ƙazafin Wahee ba. Wani abu take ji yana rayuwa a ƙirjinta da ginowa a cikin ƙwaƙwalwarta mai kama da kishi, baƙin ciki, takaici ta kasa goge bidiyon Aafiyyah da Mutallab a idanunta, ganinsa take kamar zahiri ba shirin kwaikwayo ba, ganin abun take kamar labaran nan na littafan Hausa na soyayya da ta ji ana faɗa, shakku da tsoro sukai mata hawan ƙawanya a zuciya ta kasa sukuni ta ji ta tsani kanta komai ya dai na yi mata daɗi, bata so koda wasa zuciyarta ta kamu da tsanar wani rai a duniya ballantana Aafiyyah, her childhood friend, forever and ever wani irin deep" "friendship mai wahalar bada wani labari ne, a tsakaninta da Aafiyyah." "A razane ta ɗago saboda fisgota da ta ji an a yi, tana ɗago kai ya sauke mata lafiyayyun maruka a fuska," without letting her to recovering daga marin ya sake sauke mata wasu a gigice ta yi baya ta cakume Mutallab tana haɗiyar zuciya. """I am sorry daddy, don Allah ka yi mini komai a rayuwa ban da raba ni da bestie, zuciyata zafi take mini," "daddy don Allah ,""" """Ko mutuwa za ki yi ki farfaɗo wallahi Safiyyerh kin yi kaɗan na yi miki yadda kike so, ki je ki yi duk abin" "da zuciyarki ta raya miki"" ya yi ƙwafa ya juya tare da ficewa daga hall ɗin, ya ji tsoron dukan Aafiyyah ƙwarai, tsoron daya sanya jikinsa yin sanyi wanda daya tabbatar cewa ba Safiyyerh bace ba zai taɓa saka hannunsa akan ƴar mutumin nan ba, still tsoron ya saka ya kasa huɓɓasa hukuncin da ya yi niyya akan Safiyyerh, again tsoron ya saka ya ƙara yin addition na irin matakin da zai ɗauka akan yaron da ita kanta Safiyyerh, again and again wannan tsoron ne ya saka ya kasa tafiya da gudaliyar tasa ya nufi waje kai" "tsaye idanunsa kuma a rufe, komai zai zo ƙarshe, but when? Dole sai ya bar ƙasar." """Safiyyerh!""" "Captain ya ce yana tsayawa dab dasu, ta kasa ɗagowa domin ganinta har yanzu daddy na tsaye ta" "ƙanƙame Mutallab ƙirjinta na ɗagawa da ƙarfin gaske. Shi ma Mutallab bai motsa ba, gabaɗaya jinsa yake wani iri abin da bai taɓa ji ba a duniya, jin Safiyyerh a jikinsa, kukan nata, marukan da aka yi mata ya ƙara tunzura hauhawar zafin da zuciyarsa take masa, da wani irin jin zafin Aafiyyah da yake ji haka" "kawai, daga yin abu ta faɗi kamar ba jaruma ba abin wasa shine zata faɗi haka? Shine za ta yi haka?." """Leave, bar nan"" Mutallab ya cewa Captain yana fiddo idanunsa waje." """Idan naƙi fa?""" """Tambaya ta kake? I said leave""" """Ba inda zani sai da Safiyyerh na mayar da ita gida ka gane, tunda naga Safiyyerh taƙi so na, na san cewa" "ba haka kawai bane, domin ruwa baya taɓa yin tsami banza. Ina son ka buɗe kunne da kyau ka ji, Safiyyerh ba ajinka ba ce, she never be your mate, gwara kasan na yi tuntuni domin matar talaka daban Ubangiji yake yin su, tare da halittar su a duniya, ka fara gina kanka domin a yanzu baka da abin kula da Safiyyerh ko abincin da take ci a gidan ubanta baka da kwatankwacin shi, ita ɗin tawa ce kuma zan" "tabbatar maka da haka very soon""" """Ok..."" Mutallab ya ce a kumbure, har yanzu Safiyyerh na riƙe da shi bai kuma hanata raɓarsa ba domin a" "tsorace take. Hannu Captain ya kai zai riƙo Safiyyerh, bai san ya aka yi ba, shi dai ya samu kan shi da yin wani irin azababben ihu yana kiran hannunsa kafin ya ji sautin ƙarar ƙashin hannun nasa dake alamta masa Mutallab ya karya masa hannu, ya ji wani irin fitsarin wahala na bin cinyoyinsa. Cikin sauri Kimiyya" ya matso ya ce """Buddy sake shi, ka karya masa hannu fa? Ka cika shi""" "Yaƙi sakin hannun yana ƙara murɗewa, Captain sai ihu yake. ""Mutallab me ya sa kake yin haka ne? Ka" "karya shi bayan haka me kake buƙata kuma?""" """Stay away from her""" """Ita wa?""" """Kimiyya ka daina saka mini baki cikin lamurana, bana son illataka"" ya ce yana sakin hannun Captain tare" "da saka ƙafa ya hankaɗa shi baya sai kuma ya damƙi hannun Safiyyerh ya jata zuwa waje, kimiyya ya bisa da idanu domin yanayin idanun Mutallab da sautin muryarsa ya firgita shi ainun tare da bashi maɗaukakin mamaki, sai ya nufi wajan Captain shi da Nahyan, Wahee ma ta ƙarasa wajensa tana cewa ""Kai ma ka daina kula shi, idan Safiyyerh ce ka rabu da ita don Allah, let her be, kai ba ajinta bane"" wani lafiyayen mari ya saukewa Wahee a fuska zuciyarsa na yi masa ɗaci, kafin ya miƙe da ƙyar yana riƙe" karyayyen hannunsa ya yi waje. "Sai da suka yi nisa sosai a dai cikin makarantar ya sake ta yana cilla ta baya, idanunsa ciki-ciki, yanayin" kallon da yake mata ya saka ta marairace masa fuska hawaye na bin kuncinta. """Ka yi haƙuri""" """Da haƙurin ya mutu sadaƙar nawa kika bayar?"" Ya ce yana tsuke fuska, babu walwala sam a tattare da" shi. Ganin yadda ya fusata sai ta fara dariya tana girgiza kai tare da ja da baya ta ce """You are impossible, you are impossible Fiyya""." """Kee"" ya kira ta a tsawace, kiran da ta ji ya saka zuciyarta girgiza fitsari na shirin ƙwace mata wando" "saboda firgice. Maimakon ta bar shi, kamar yadda yake fata sai ta matsa kusa da shi tana maƙale masa kafaɗa ta ce. ""Bafa rainaka na yi ba, ni ban ce haka ba, yaushe ma na ce haka? Sai ka yi ta tsangwama ta wai? Nima fa mutum ce kamar ka wallahi, at least ka girmama ni saboda kasancewata ƴar'uwarka musulma"" ta saka kafaɗa ta ture shi, ko gezau, kamar ta ture gini. Tana sake yin murmushi ta ce ""Dalilin Annabi Adamu, Alaihissalam muka zama ƴan'uwa don ka ji, kuma na zama matarka very soon na haifi" "Yaruba child""" "A hankali ƙanƙancewar idanunsa ke rikiɗewa zuwa wani yanayi nada ban, ya lashe laɓɓansa, sai kuma" naman ƙirjinsa ya fara rawa yana jinsa kamar a tsakiyar daji ana kaɗa masa ƙahon busa yayin farautar naman jejin. "A ƙirjinsa ya ji maganar ""Me kika ce za ki nuna mini? Nunan"" ya ce yana narkar da idanunsa." "Girgiza kai ta fara tana buɗe ido ta ce ""Laaa la la ni kuma? Yaushe? A ina? Ba dai Safiyyerh ba""" """Kin ce, kin fara irgan dangi""" """Wanne dangin zan irgo?""" """Na girma"" ya ce a daƙile." """A'a, ba ruwana, ba wani irgan dangi""" """You are not serious, sai kin nuna mini, ko ki nuna ko na buɗe na gani na tabbatar"" ya faɗa very serious," "yana kuma haɗe fuska da kyau kamar ya ce ya shiga uku. Ta dinga masa dariya ta san wasa kawai yake mata, sai dai babu alamar wasa a tattare da shi, ya yi taku ɗaya, ganin kamar kamata zai yi ta juya da sauri tana masa gwalo, duguwar ƙafarsa ya saka mata ya taɗo ta, ta fasa ihu zata faɗi ya riƙo hijabinta," "tare da ɗago ta tsaye kamar abin arziƙi sai ta ji ya damƙi kunnenta ya murɗe sosai, idanunta ya cika da" "hawayen azaba amma murmushi take masa, domin bata bashi damar da zai gane fushinta." """Kakewa matarka mugunta ko? Kake mini mugunta ana mana aure zan ,"" bata ƙarasa ba, ta ji ya kama" "lips ɗinta na ƙasa ya murje, ta kasa kuka ko ihu, sai zufa take yi na azaba, tana jin kamar leɓen bakinta zai cire gashi sai sake murɗe mata lips ɗin yake. A hankali wasu hawaye suka fara sintiri a idanunta, bata san cewa yana da taɓin hankali ba, da ta yi yunƙurin ƙwatar kanta for sure." "Ya zame hannunsa, sai kuma ya shaƙe wuyanta kamar zata rasa mutu haka tane ji, ta fara shura ƙafa," "tare da kakarin ceton rai a firgice shima jikinsa na rawa ya ce ""Me ya sa kika zame mini ƙarfen ƙafa? Me ya sa kika zame mini kaska ne? Me ya sa kike so mahafinki ya yi ta cin mutuncina? Saboda kina son haka?"" Ya sake shaƙe wuyanta idanunta na fitowa alamar numfashi na yi mata wahalar shaƙa, domin maƙoshinta take jinsa, baya sauka ƙirjinta yadda zata shaƙa da kyau ɗin." "Ya sake lashe laɓɓansa ya ce ""Ni mahaukaci ne, mahaukacin gaske. No ina da hankalina me ya sa zan" "zama mahaukacin? No... No...""" "Ya ce, jikinsa ya dinga kyarma da wani irin ɓari da kakkarwa wata asaba yake ji a tsakiyar kansa tana" "sauka cikin kwakwalwar sarrafa tunaninsa, ya birkice haukan ya motsa masa da gaske." "Da sauri wasu securities suka ƙarasu wajan, su wajan huɗu suka fara ƙoƙarin ƙwace Safiyyerh daga" "hannun Mutallab, amma suka kasa, ya saki dukkan ƙarfinsa, yadda yake misbehaving, zai nuna da gaske bashi da hankali, aka fara kokawa da shi da ƙyar aka ƙwace Safiyyerh ta faɗi a wajan tana dafe ƙirji da shaƙar wata wahaltacciyar iska, ganin suna kokawa da shi da alama za su iya yi masa duka tunda sun fi" "ƙarfinsa, kuma su biyar ne ta miƙe da ƙyar ta shiga tsakiya tana girgiza kai." """Kar ku yi masa komai, ina ruwan ku da shi? Me ya yi muku?""" """Saboda kin yi free, kike tambayar me ya yi mana, da mum bari ya kashe ki fa?""" """Ko kashe ni ya yi mene ruwanku ne? Ina saboda Allah kuka taimaka mini ko?"" Safiyyerh ta ce idanunta" "cike da hawaye. Mutanen suka kalli juna kana suka ce ""Mahaukaci ne fa?"" Rai ɓace ta ce ""Ko a turo yake mene naku? Mijina ne shi ɗin""" """Mijinki? You are too young for marriage yarinya""" """Ko yanzu aka haifan dai, mijina ne, shi ɗin mijina ne"" ta juya ta ce ""Ko Bestie. "" Kifa mata mari ya yi," tare ƙoƙarin shaƙe mata wuya. """Kin gani ko? A haka kike cewa mijinki ne?"" Safiyyerh da ƙyar take buɗe idanu, saboda tsananin azaba ta" "yi murmushi hawaye na bin fuskarta ta ce ""E, mijina ne"" ta ce tana nufar Mutallab, ya yi saurin kawar da kansa wani irin ciwo kansa yake masa, kamar ya rabe biyu, ƙirjinsa sai rawa yake masa, fuskarta ɗauke da murmushi ta ce ""Manta da su ƴan saka eyes ne"" bai kalle ta ba, bai kulata ba, tana tafe yana binta a baya, yana ƙarewa dukkan wani takunta kallo har suka fita titi, ta tsayar da napep ta ce ""Birget zaka kai mu, nawa ne kuɗin?"" Ya faɗa mata, ta juya ta kalli Mutallab, taga ita kawai yake kallo ta kashe masa ido" "ɗaya ta ce ""Kuɗin napep?"" Ya ɗaga mata shoulders." "Hannu ta saka cikin aljihunsa ta dudduba babu ko sisi ta ce ""Laa dattin aljihu bashi da ko sisi"" shiga" "napep ya yi itama ta shiga, mai napep ya ja su, yana tafe yana kallon su ta madubi, shi kansa ya ji shakkar ganin idanun Mutallab ɗin balle ita ɗiya mace. Har ƙofar gida suka tsaya, ta fito shima haka ta ɗakko kuɗi ta bashi kana ta kalli Mutallab sai zare ido yake yi kuma yana ta binta da kallo a ransa yana jin anya tana da hankali kuwa? What wrong with Fiyya? Is she even okay?. Yaga ta shiga gidansu, ya bi bayanta da sauri ta shiga da sallama. Sa'adah dake zaune da Ammo a tsakar gidan suka amsa, Ammo ta dinga kallon" "Safiyyerh kana ta kalli Mutallab, bata je komai ba." """Ina yi Ammo?""" """Safiyyerh ko?"" Ammo ta ce, tana bin Safiyyerh data tsuguna kanta a ƙasa ta ce ""E, sunana Safiyyerh""" """Allah sarki, ta shi mana"" Safiyyerh ta miƙe tsaye Ammo ta shanye mamakin daya gama cika ta, ta ce ""In" "ce dai lafiya?""" """Rako bestie na yi, baya jin daɗi ne"" ta ce a hankali, fuskarta faɗaɗe da murmushi tana jin kamar a gida" "take. ""Sannun ki da ƙoƙari Safiyyatul-khairi, sannu da ɗawainiyya kin ji, kema ki tafi gida ki daina biyo namiji kin ji ɗiyar arziƙi"". Sa'adah ta dinga kallon Safiyyerh, ganin yarinya kyakkyawa fara tas, idanunta manyan farare ga gashin gira a cunkushe baƙi suɗik so ma sha Allah, ganin jikinta kasan tana hutawa sai dai babu nutsuwa a tattare da ita sam. ""Safiyyerh"" Ammo ta kira sunanta ta ce ""Jeki gida yamma na yi" "kar aga kin jima"" ta girgiza kai ta ce ""I will stay with you, zan zauna a nan ni""" """Ikon Allah, dole ai ki tafi""" "Safiyyerh ta fashe da kuka sosai, Sa'adah ta dinga kallon ikon Allah. Inna Binta ta fito tana masifar abinci" "hakan ya baƙanta ran Sa'adah bata ganin idon baƙuwa. ""Idan na je gida daddy duka zai yi, zai buge ni zai" "mini faɗa, zai hanani fitowa, zai bar ƙasar dani ,"" ta kasa maganar ta fashe da kuka tana haɗe kanta da" "cinyoyinta ta dinga rera kuka ta ce ""Ammo don Allah ki faɗawa Ummeyhna ta aura mini Mutallab please, don Allah ni bana son zaman gidanmu Please Please""" """Turƙashi!""" """Safiyyerh, wakike so ɗin?""" """Mutallab""" """Yana son ki?""" """E, yana so na""" """. Liar, ƙarya ne"" ya ce a hankali, ta kalle shi ta ce ""Wallahi kana so na, Ammo ko baya so na ba dai ni" "ina son shi ba?"". ""Haka ne, to babu damuwa zan zo da kai na gidan naku sai mu yi magana ta fahimta da" "mahaifiyar taki ko? Amma ki je gida yanzu"" a hankali ta ce ""Daddy shirin barin ƙasar yake dani"" sosai ammo ta yi mamaki, kuma ta ji tausayin Safiyyerh yarinya ƙarama amma zuciyarsa ta buɗe ta samu" "balagar zuci ta lallashi Safiyyerh ta kalli Mutallab ta ce ""Auta raka ta ko?"" Ya yi kicin-kicin da fuska, domin" "kawo lokacin daidai yake jin kansa zai ciwon kai. ""Muhammad""" "Gaba ya yi, Safiyyerh ta yi wa Ammo sallama ta bi bayansa da sauri ta ruske shi a waje. Ya dube ta sosai" "cikin ɓacin rai ya ce ""Ya zama First and the last time da za ki yi yunƙurin biyo ni gida ok? Kar ma ki cigiyata ko result aka fitar ba zan zo ba, sai an dawo hutu kin gane ai?"" Ya yi maganar yana ɗaɗɗage mata girarsa biyun. ""But i am going to miss you"" ya mata banza idanunta ya cika da hawaye da sunkuyar da kanta ƙasa, tana shassheƙar kuka ya matso dai-dai da ita ya ce ""Only friends. Only friends, friends" "kawai"" ta yi murmushi ta ce." """I appreciate hakan ma""" """Fece to""" """Uhm'uhm"" ta ce. Ya juya." """I love you Mai dawa, ka kawo mini naman jeji ka ji? Kuma ka zo zance if not i will come, idan ka ji ka" "neme ni ka ji masoyi? I love you"" ta sake yin murmushi ta ce ""I heard you, ka ce i love you too """ """Allah Ya baki lafiya Fiyya""" "A hankali wani mutum dake cikin baƙar mota da ya zo wajan Mutallab ya dinga bin Safiyyerh da kallo," "musamman fuskarta ya ɗauki wayarsa ya ɗauki photon fuskarta, cikin sauri kuma ya tayar da motar ya bar wajan, domin wannan abin ya fi batun wajan Mutallab amfani. A good and bad news in the same" time. * "Yana cikin jeji wajejen Kumbotso yana neman kayan LIMƘABIN KALGO, da zai wa Sa'adah magani jikinsa" "sanye da bunjuma sai hular saƙi, da sauran kayan mafarauta daga bayansa ya ji an ce ""Ga ganyen nan a" "gabanka"" ya ɗago kai, tabbas ya gano dattijuwar nan, karan farko da ya zo har suka samu saɓani da Kimiyya, me take yi to? Me ya sa take son shiga rayuwarsa saboda shisshgi? Ya ɗauke kai ta ce ""Me ya sa" "baka son yi wa kan ka aiki domin zama mai kuɗi duk da zaka iya? Baka yadda da aikin naka bane?"" Ya yi" "mata banza ya ɗauki ganyen, da sauran abubuwan da suka kamata zai bar wajan ta ce ""Gaba kaɗan bukkata take, ina cike da farincikin sanar da kai cewa a shirye nake da taimaka maka, a duk sanda ka yi" "niyyar zuwa wajena, ina baraba lale"" ya juya yana tafiya cike da buɗawa ya bar wajan. Ta bishi da idanu." "Tiger da yafi ƙauna fiye da sauran ya dinga tajewa gashi sosai, yana jin yadda saurayin Sa'adah ke ta" "magiya da ban haƙuri cewa da wasa yake ba har zuci ba. Ya miƙe tsaye ya shige shagon Tariq, tiger kuma" "ya dinga zagaye Sa'adah yana shanshanata. Wandon kayan daya cire ɗazo ya ɗakko yana duba abu, takadda ya ji, da sauri ya ɗakko ya buɗe idanunsa ya sauka akan rubutun dake ciki." "“Ban taɓa tsintar kai na a mai raunin zuciya irin wannan lokacin ba, do you know why? Masoyi may find" "himself screaming Saboda raɗaɗin dake addabar zuciyarsa akan soyayyar abin son zuciyarsa, ina son ka, abin ƙauna na nesa da idaniya, abin ƙauna kusa without feeling. Ya ilahil alamin,so ne lakin ɓuɗini shu'urin. Duk tarin dangin da mutum, duk yadda ake son shi duk abin da ya mallaka,so na sawa ya ji ya kaɗaita, ana kaɗaici a ƙauna komai tarin dangi,when your love cast aspersions on you violently Tash'uru bi'annaka wahidan a duniya kuma ba ruhi ,” da sauri ya ja numfashi, yana sake zubewa rubutun idanun" "wani abu na fusgarsa, abin da baya taɓa rabe ɗaya biyu a ciki,ko shauƙin kalaman, ko shauƙin furucin mai kalaman data zuba su bisa tsari masu taushi da ratsa zuciya, idan baya son ƙaryata kansa lallai yana jin wani abu, yana son rubutun, yana son mai rubutun, he just falls in love with the secret love message. A hankali ya sake buɗe idanunsa domin bawai ya kammala karantawa bane, a'a; ya tsahirta daga ainahin bugun luguden da zuciyarsa ke masa tana masa tsalle a ƙirji, ya ji ya fara rayuwa as a man, as a good" "man, who is ready to find himself in love." "“Ba za ka gane ba! Domin masoyi bai cika sai ya zam majnuni If you have any sensibility, sonka fih" "nuƙsani Overemotional connection ba zunubi ba saɓo kawai biyayya na kewa son, yana ta rayuwa a zuciya, ina jin motsin numfashinsa a ƙirjina. Ina rayuwa ne kawai amma ba tare da ruhi ba, Yaa Muhammad, kalmar so ya yi kaɗan ƙwarai wajan faɗa maka kawai tuni ne, lallai watarana ka tuna I LOVE" "YOU, INA SON KA, ANA UHIBBUKKKKAAA”" “Smile... Smile” "Mutallab, he really out of words ya dinga jin kamar yana faɗaɗa fuskarsa, sai ya tsuke tas ya tuna kalar" punishment ɗin da zai yi mata Fiyya ta raina shi. "Wayarsa ya ɗakko, kamar zai kira ta sai kuma ya rasa to me zai ce mata? Ya ce ya karanta saƙon ko ya?" "Ya girgiza kai kawai, ya damƙe takardar zuciyarsa na tsuke masa a ƙirjinsa tana tatarewa tare da fara sabon gini, ginin daya tabbatar na so ne, motsin da ya tabbatar na ƙauna ne, sabuwar halittar data fara rayuwa a ƙirjinsa matsayin abar so, son bana kowa ba, son ɗiyar Professor Abdu, son Fiyya, shauƙin" Safiyyerh Abdu. """But, Jaaanah is no longer alive, Diyna is no more, after them, who is the next person?""" “Safiyyerh” "Shauƙin fuskarsa ya fara rikiɗewa sannu a hankali zuwa yanayin na damuwa, damuwar Safiyyerh, tsoron" "rasa Safiyyerh, tunani yadda zai ruski gawar Safiyyerh. A hankali ya yi shiru yana jin sanyi na ratsa ruɓin" fatar jikinsa har bakwai yana ratsa ƙashin jikinsa. * Da sauri ya fito daga cikin ɗakin emergency dake ɓangaren ICU ɗin yana yarfe zufa daga tsakiyar goshinsa a gigice kuma ya nufi Ummi zuciyarsa na rarrabewa da wani irin rauni ya ja ya tsaya a gabanta yana fusgar numfashi. """Ya aka yi? Ta dawo hayyacinta?""" """Ummi ,""" """Kar ka wani damu, ko mutuwa ce ai haka zamu haƙura ko? Mu ɗin musulmai ne, zan ɗauka ba zan ji" "tsoro ba, faɗa mini mene?""" """She is not responding The the treatment bata amsa Ummi"" Ummi ta zubawa fuskarsa idanu, kamar" "mai yin studying yanayinsa sai kuma ta ce ""Ikon Allah""" "Kafin ya yi magana sun ji kyakkyawan takun Paaah wanda ke alamtar dasu gare su yake, hakan yana" "nuna daga saukarsa airport asibiti ya yo kai tsaye, ya juya a hankali zuwa bayansa suka haɗa idanu da Paaah ɗin kamar ya tsammata haka ne, idanun Paaah ya rikiɗe sosai tare da yin launi na ban tsoro, kyakkyawar shigar dake jikinsa kaɗai zata nuna maka arziƙin da yake da shi, da kuma tarin kadarorin daya mallaka. Simple jallabiya ce a jikinsa da alama kuma da ita ya shiga jirgin sai takalmi mai kyau sauciki hannunsa goye a bayansa sai farin Bluetooth ɗin dake kunnensa da alama magana ake masa ta" ciki amma ya raba hankalinsa gida biyu. "Paaah ya yi wa Ummi kallo ɗaya ita da wanda suke tare, a hankali ya shige su kai tsaye daƙin ya nufa duk" "da tarin doctors ɗin wajan da yadda ake ƙoƙarin nuna masa komai zai daidaita ba wanda ya kula ya sanya ƙafarsa cikin room ɗin hakan ya yi daidai da buɗewar zuciyarsa, wani jiri ya neme zubar da shi a wajan, hannunsa ya hau rawa kamar jira ake ya shiga kafin komai ya faru ya wakana ya runtse idanunsa" "a rarrabe da ƙyar ya iya cewa ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Allahu Akbar...." Na'ima Sulaiman sarauta Nimcyluv 08164069685 "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 35: Husband and wife" "Kacokan ta baru zuciyarta a wajansa, duk da cewa she feels better and comfortable a zuciyarta, sai dai ta" "wanzu da tunanin shirin da daddy ya yi mata daga shi har Ummeyh, ta dai ji koma mene she is ready to farc it. A hankali ta lumshe idanunta tare da mirginawa a tsakiyar gadon da take ta yi lamo, tana hasaso kanta ta cikin idaniyar zuciyarta a matsayin matarsa, matar Mutallab, halaliyyarsa, sai ta ji gudun zuriyarta na ninka aikinsa a kaso tamanin bisa ɗari. Murmushi ta yi kamar a lokacin take hango masifar" dake cikin idanunsa da ƙifaɗi yana nanata. """Only friends. Only friends, friends kawai""" """Daga aboki zaka koma saurayi, daga saurayi zaka koma mijin Safiyyerh Abdu""." "Ta mirgina kaɗan sai ta ƙanƙame filo tana murmushi ta ce ""Allah ka bani Mutallab, Allah ka duba ni""" "Sai ta ji zuciyarta na tuna mata da cewa Safiyyerh ki yi addu'a, ki faɗawa Ubangiji. Siririn tsaki taja sanda" "ta tuna abinda ya faru, ya shige, ya zama tarihi ga duka su biyun,amma banda ita, maimakon ta ji sassauci a zuciyarta sai ta ji ta sake ruɓanya abin da take ji dongane da Aafiyyah, ta ji kawai ta yi ladama, da nasani mai girma, fiye da girman yadda take fargabar amsar hukuncin daddy, ta yi regret, regretting na sani Aafiyyah, she regretted knowing anything, she regretted knowing Aafiyyah as her childhood friend, to wanne abota? Duk wani abu da zai mata togashiya ga sadata da Mutallab bata so, she hates it don haka ba wata abota, the friendship is gone ya mutu, mutuwa a zuciyarsa Safiyyerh, ko motsin sa" bata ji balle ta sakawa ranta tashin nasa. Wayarta ta ɗakko tare da shiga message ta nemo number Aafiyyah kai tsaye ta fara typing tare da tura "mata saƙon karta kwana, ta riga ta mance yadda aka ɗauki Aafiyyah tsakanin rayuwa da mutuwa. Idan ta tuna abin daya faru ranta ɓaci, it hurts her, a lot hurts. Ta miƙe tsaye tana jin zuciyarta ta rage mata nauyi, wanka ta yi kana ta ɗaura alwala tare da yin sallah ta jima saman ladduma kafin ta miƙe ta nufi gaban dressing mirror ta ɗauki, set ɗin mayukan da aka haɗa mata wanda sai yanzu ta lura order ne, kuma products ɗin Aysha S Bayero ne, ta ɗauko Oil mai sanya fata sheƙi da glowing ta ɗakko ta shafa, tana jin jikinta daɗi, kana ya ɗakko corrector mai fidda tabo ko wani ɓoyayyen abu da baka san da shi ba. Bayan ta gama shiryawa ta ɗauki turare ta fesa, ta ji ƙamshin har tsakiyar kanta, wani sabon shauƙi ya" "kama ta, murmushi ta yi kawai a haka ta nufi ƙofa tare da sauka downstairs." """Safiyyerh!""" """Na'am, Ummeyh""" "Safiyyerh ta ce jiki a sanyaye ta nufi wajan Ummeyh dake zaune saman kujera, ta nemi waje ta zauna" "kanta a ƙasa. Ummeyh ta dinga kallon ɗiyarta ta kafin ta ce ""Kin ji daɗi ko Safiyyerh? Kin yi farinciki ko?"" Ta ce cike da ɗacin rai da ƙonar zuciya." """Me na yi Ummeyh?""" """Kike tambayata? Da gaske tambayata kike yi? Kuma amsa kike buƙata ko? Kina son ji?""" """Ki yi haƙuri don Allah Ummeyh, ku yafe mini please """ "Ummeyh ta juyo, da ƙyar ta ce ""Sorry for what? There is nothing to forgive, kin nuna dai kin isa ne, kin" "kuma yi farinciki kin saka jinin mahafinki hawa, Safiyyerh wannan shine tarbiyyar? Wannan shine sakayyar da za ki yi mana a matsayinmu na iyayenki? Tun kina zanin goyo muke ɗawainiyya, har girma har kika isa zuwa makarantar, makarantar da yanzu muke dana sanin saka ki gwara ki zo a jahila kuma ki koma wajan Ubangiji haka, kin mini kuka, kin mini fitsari, kin mini abubuwa da yawa, ba ki taɓa cewa wayyo Allah bamu yunƙura mun ji matsalarki ba. Shi ne yanzu za ki yi ƙoƙarin kwasar ƙasa ki baɗa mana a idanu? Za ki wofitar da tarbiyar da muka yi miki? Ki ka rusa kuma Safiyyerh? Why Safiyyerh why me ya" "sa? Shin bamu cancanci ki yi mana wannan alfarmar ma, bamu dace da alfarmarki da biyayyarki ba?""" "Kuka Safiyyerh ta fara ta ce ""Ummeyh ku yi mini afuwa, don ku yi mini afuwa ku yafe mini"" Ummeyh ta" "ce ""Ki manta da batun shi, batun auren, ki yi karatu we can leave the country idan kina so ma, kin ji ko?""" """Ummeyh, Mamansa ta ce mini za ta zo ku yi magana "" ta ce cike da ƙoƙarin tsage gaskiyar dake ƙirjinta." "Ummeyh ta ce ""Maman wa? Maganar me?""" """Mutallab, na je gidansu. ,""" "Saukar duka ta ji a jikinta, ta ko'ina ta fara ihu da ƙoƙarin neman ɗaukin Ummeyh, amma Ummeyh bata" "motsa ba, duk da kukan na Safiyyerh na taɓa ta. ""Daddy ka yi mini komai amma don Allah ka aura mini bestie, ka yi mini aure da Mutallab, na rayuwa da shi kamar yadda kuke rayuwa da Ummeyh..."" Ta saka ƙafa ya yi ball da ita, cikin sauri Uncle Musbah ya zo ya fisge bulalar hannun daddy, yana janye Safiyyerh" "da jikinta ya yi jina-jina. Uncle Musbah ya ce ""Mene ya yi zafi haka? Kashe ta za ka yi ne?""" """Musbah, ka rabu sani ka bari na kashe Safiyyerh na huta, Safiyyerh ta ɗora mini hawan jini, ina saurayi" "ban yi hawan jini ba sai yanzu? Ka duba a makarantarsu aka kira ne gabaɗaya exam ɗinta zero, f f kawai nake gani, still dai Ya sayyadi ya kira ni Safiyyerh bata gane yanzu ko karatun Alkur'ani me take nema me" "take so? Mene kuma ban yi mata ba""" """Aure nake so daddy, aure ne ba ka yi mini ba wallahi bana gane karatun ma sam, uncle ka taimaka" "mini"" Safiyyerh ta ce tana daga bayan uncle Musbah." """Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un""" """Uhm, professor kenan, auren nan fa shi za a yi mata in sha, da Mutallab ɗin""" """Wallahi wallahi dana aurar da Safiyyerh at her young age kuma aurar ma ga Ɗan'malam gwara naga" "gawarta a gabana na san cewa mutuwa ta yi kawai""" Juyawa ya yi zuwa part ɗinsa yana neman layin Aliyu. Uncle Musbah ya ja hannun Safiyyerh zuwa "upstarts, Ummeyh kuma kamar statue haka ta zama saboda shocked." * "Paaahh ya sandare ganin yadda Aafiyyah bata ko motsi, ba zai ce ta mutu ba, tunda bai ji tasa zuciyar ta" "tsaya ba, yana mai jin tsoron abin da kan iya zuwa ya dawo don gane da abin da yake damun Aafiyyahr kai tsaye." "Bai kai ga shiga cikin ɗakin ba, wani likita ya dakatar da Paaah ta hanyar cewa ""Ranka ya daɗe ka yi" "haƙuri ka jinkirta mu ƙarasa aikin da muke yi Please"" Paaah ya dinga kallon likitan kana zame idanunsa ya kalli Aafiyyah dake kwance a saman gadon asibitin ta yi flat lokaci ɗaya ta yi wata muguwar rama kamar ana zuƙe ruwan jikinta, ta zama kamar wata kuɗin guzuri. Ya ja numfashi ya sauke yana sake kallon Aafiyyah da ƙyar ya iya cewa ""Ya jikin nata? Is she response?"" . Dr ya ce ""Za ta yi in sha Allah, mu yi addu'a"" yana faɗin hakan ya shige ciki, Paaah ya yi sak, yana jin nutsuwarsa na yin hijira daga zuciya da gangar jikinsa, a shirye yake da rasa ko mene muddin Aafiyyah zata samu lafiya. Juyawa ya yi yana gyara" Bluetooth ɗin kunnen nasa ya ce """Ko anjima? Maybe zuwa gobe, yanzu na sauka ƙasar nima, mu yi addu'a shine don Allah"" shine abin da" "ya ce kana ya nufi inda su Ummi suke, ya duba agogo Ummi ta ce ""Ka samu ganin nata? Ya take? Tana" "magana? Ƙirjinta na ɗagawa zan dai ta samu lafiya?""" "Paaahh ya ce ""In sha Allah""" "Shiru duka sukai kafin Paaah ya ce ""Ina son ganin mahaifin ita ƙawar daughter, dalilinsa na dukan gudan" "jinina zai bani""" """Sun ce kuskure ne, ƴar shi ya je duka ya ɗauka Aafiyyah ita ce""" """Ko?"" Paaahh ya ce, yana duban mai maganar, MJ ya yi saurin sauke kansa ƙasa sai kuma ya duba wayar" "Aafiyyah dake hannunsa, bai san mene ya ƙunshi saƙon ba amma saƙon karta kwana ne kai tsaye ya sauka a cikin DM ɗinta ɗauke da number mai rubuce da sunan Safiyyerh. MJ ya juya cikin sasarafa ya bar wajan bayan ya yi nisa ya buɗe saƙon tare da karantawa." "“Ko a wasa ban ɗauka za ki aikata abin da kika aikata ba, haka kuma ban ji wani mamaki ba, na san cewa" "kin faɗi da gangan ne bisa son zuciya da kifar da tunanina da kike raina nawa Aafiyyah. Ina tuna miki wanda ya rigaka kwana ya rigaka tashi. Na ji bana buƙatar sake ganin fuskarki a cikin idanuna, Aafiyyah kar ki yi kuskuren nuna mini fuskarki saboda i don't know what i am going to do, kin san wace ni, duk haƙurin da nake da shi idan na yi niyyar abu bana fasawa, ki manta kin taɓa sanin wata Safiyyerh a cikin rayuwarki, bana buƙatar ko a zuwa gaba ki yi mentioning sunana a matsayin wacce kika sani, ina miki" "fatan alheri, stay away from me”." "MJ ya ji mamakin saƙon na Safiyyerh, sarai ya santa ai, abotar da suke da Aafiyyah tun ta primary school" "ce, duk da cewa Aafiyyah ta samu ƙalubale amma bata da magana sai ta Safiyyerh, dalilin ƙaunar da Aafiyyah ta kewa Safiyyerh ya saka Paaah zama a Nigeria, ya tattara nutsuwarsa a naija. Ya ja numfashi ya dinga kallon saƙon baya son Aafiyyah ta gani, amma ya zama dole ta sani ya dinga mamaki sai dai ya jingina hakan da ƙuruciya kuma daman zaman duniya a saɓa ne yau a kuma shirya gobe wannan" tabbataccen abu ne dake zuƙatan duk wanda suke abokantaka. "Dr ne ya fito, har lokacin Paaah na tsaye hannunsa goye a bayansa yana yi yana sauke ɓoyayyiyar ajiyar" "zuciya, Ummi ma tunani ne fal ranta da tsoron abin da kan iya biyo bayan ciwon na Aafiyyah." """Dr ya ake ciki""" "Ya yi murmushin yana zare glasses ɗin idanunsa ya ce ""Allahamdulilah, numfashinta ya dawo mun cire" "suka oxgeyn ɗin zuwa anjima zamu mayar da ita ɗakin hutawa daman matsalar ɗaukewar numfashi ne""" """Bayan shi fa?"" Paaah ya buƙata a ƙagauce, domin jikinsa da zuciyarsa basu gama amsar batun Dr ɗin ba." "A hankali dr ya ce ""Ranka ya daɗe mu yi magana office please"" ya yi jim sai kuma ya miƙa hannunsa ya ce ""After you"" Dr ya yi gaba Paaah ya bi bayansa zuwa cikin office ɗin, Mj ya yi shiru yana ta tunanin masifar ƙaddarar dake shirin kunno kai babu gaira ba dalili." """Alhaji wannan shine gwaje-gwajen da muka yi wa yarinyarka. Maganar gaskiya bai dace ace kamar" "Aafiyyah a ƙarancin shekarunta ba ta kamo da hawan jini ba, yana da kyau a tsaya a duba idan wani matsalar ne a fara jin damuwarta sai a magance mata, na san duk abin da yake damunka ba zai fi ƙarfinka ba, so ka fini sanin abin da take buƙata meet your daughter"". Paaah ya yi shiru, shirun zullumi da tunanin abin da ya saka Aafiyyah ta samu hawan jini. A hankali ya ce ""So ba Limoniyyar ce ta tasar mata ba?"" Dr ɗin ya girgiza kai ya ce ""Ai kuna kula da ɓangaren limoniyyar, Aafiyyah bata bacci, Aafiyyah ba nutsuwar zuciya a tattare da ita, Aafiyyah bata cin cikakken abinci, ba komai a tare da ita sai damuwa, here is the results"" Paaah ya amsa da ƙyar, Dr ya dinga bawa Paaah tabbacin zata warke idan an shawo" kan matsalar. "A hankali ya tura ƙofar room ɗin da aka sauya mata, hannunsa ɗaya ya saka ya cire Bluetooth ɗin" "kunnensa sai ya jinkirta ya ce ""Tunda dai haka ne ka yi zamanka kawai, nima zan yi tafiya idan ta samu sauƙi ina tunanin tunda hutun makaranta sukai, zan tafi da ita, i will go with her sai ta sami peace of mind"" ya ce yana cire Bluetooth ɗin. Kujera ya ja ya zauna ya ce ""Sweetie"" Aafiyyah ta juyo tana buɗe idanunta a hankali ta kalli Paaah ta yi murmushi da ƙyar tana miƙa masa hannunta, riƙo hannun ya yi" "cikin nasa gam, ta lumshe idanunta tana jin yadda Paaah ya riƙe ta da kyau irin he is already missing her." """Dad ,"" Aafiyyah said, a hankali har yanzu fuskarta ɗauke da murmushi, shi dai kallonta yake yi yana" "sake damƙe hannunta da ya ji zafi sosai, amma ita sai murmushin nan nata take irin you will never" "understand my situation daddy. ""I miss you so much Dad, yaushe ka dawo?""" """You will never change Safiyyerh, you are smart, smarter as always""" """Daddy """ """Zan tafi dake, kafin ku yi resuming school ok"" ta yi shiru ya ce ""Ya jikin naki?""" """Alhamd, dad ko ɗan rungume ni ba ka yi ba, na yi kewarka ba"" ya ɗan harareta sai kuma ya miƙe ya" "ƙarasa wajan gadon, yunƙurin miƙawa ta yi sai kuma ta runtse idanunta saboda ƙirjinta da yake doka mata, kanta ya sara da wani irin ƙarfin, yanayin daba kowa zai jure ba amma fuskarta ɗauke da murmushin tana lumshe idanunta ta buɗewa, ganin ta kasa tashi sai ƙifta idanu take ya saka ya janyo ƙafafuwanta zuwa dab dashi, da sauri Aafiyyah ta shige jikin Paaah tana sauke ajjiyar zuciya, a hankali" kuma hawaye ya dinga taruwa a cikin idanunta. "Kwananta biyu aka sallame ta zuwa gida, Paaah ya fara shirye-shiryen nemawa Aafiyyah visa, ita dai bata" "cewa komai saboda bata fiye magana ba, ta dinga avoiding kanta ga mutane." """Assalamu Alaiki""" "Mj ya ce yana shigowa ɗakin, tana daga kwancan ta buɗe idanunta hannunsa ta gani ɗauke da wayarta" "har ya ƙarasu ya zauna ya ce ""Favourite ya ba ki fito wajan ba"" ta yatsuna fuska tare da ɗauke kanta zuwa gefe ya yi murmushi ya ce ""I'm sorry I was so overjoyed to ask, ya jikin naki?"". A hankali ta ce" "“Absolutely fine physically, but not mentally and emotionally”" "Ya zuba mata idanu sai kuma ya ce ""Ki yi haƙuri don Allah Safiyyerh, kar ki ɗauke ni matsayin mai laifi, ni" "bani da iko ban san kuma yadda zan yi ba"" ta ɗan ɗaga masa kafaɗa tana share hawayen idanunta. ""Mene ya haɗa ku da Safiyyerh ƙawarki?""" "Aafiyyah ta ce ""Kamarya?""" """Kamar yadda kika ji""" "Ya zaro wayar ya shiga message ɗin ya nuna mata, ta yi mitsi-mitsi da idon murmushi kawai take yi bata" "ce komai ba, sai ta juya bayanta tana sake share hawayen idanunta." "Paaahh ya ɗauke Aafiyyah ya bar ƙasar, gabaɗaya. Safiyyerh ƙuncinta ya ƙaru, an ƙwace wayar hannunta" "an hanata fita ko'ina bata da wani sukuni sai kuka, ta rasa meke mata daɗi ta ji duniyar ta mata girma sosai, ta ji kamar ita kaɗai ce a cikinta wani tashin hankali ne ya rikitowa rayuwarta. Sauƙinta ɗaya an ƙi bawa Prof damar barin ƙasar har yanzu. Kullum cikin lissafa komawa makaranta take yi, ba don karatu ba, ba kuma don Aafiyyah ba, saboda shi, shi kawai just for him. Only for MUTALLAB. Sai ta ji kuma ta" "damu, da ace Aafiyyah na nan tabbas zata nema mata mafita, ta ji dama bata turawa Aafiyyah saƙon ba." "A hakan lokaci ya dinga mirginawa, rana na juyewa zuwa kwanaki, kwanaki na juyewa zuwa satuttuka" "har suka cinye adadin kwanakin da aka basu, za su koma makaranta, komawar kuma da kusan shine ya zama silar faruwar ƙaddarar, komawar da ya yi kama da ƙaddara ce ke kiran su tare da jirayar zuwan nasu, komawar data baƙanta zuƙanta kowa, komawar data raya zuƙata biyun, komawar data zama silar farinciki da baƙin ciki ga zuƙata da yawa, komawar data saka suka fahimci wata duniya bayan wacce suke ciki, komawar data tunasar da Prof abubuwa da yawa, wacce ta raba abu mai muhimmanci ga Ɓangaren" da idan babu ginin nasa ɓangaren kan iya rushewa. When a destiny call. "Da sauri take sakkowa daga steps ɗin benen, hannunta riƙe da school bag, sai wayar data samu aka bata" "da ƙyar, cikin sabbin uniform kana ganinta kasan she is ready for Jss3. Prof baya nan, Dr kuma dutyn" kwana ta yi daga ita sai Wahee hakan ya sake tabbatar mata Allah ne ya ɗora ta a sa'a Wahee bata isa ta hanata fita ba. "Tana ƙoƙarin fita Wahee ta ce ""kurkuku ta sake ki kenan, ai na so an saka ki a mari kuma kika fita sai na" "faɗawa Daddy""" """Wahee, kin jima ba ki faɗa ba""" "Miƙewa Wahee ta yi daga kan dining ta ce ""Oh, haka ma kike cewa ko? Haka za ki ce ya miki kyau, sai ki" "fita mu gani, kuma in sha Allah sai kin fara bin maza tunda hakan kike so ƴar wahala kawai banza mai ƙaunar Almajiri""" "Murmushi Safiyyerh ta yi, maganar ta yi mata zafi sosai sai ta shanye ta ce ""Idan har ba zina aka yi aka" "haifi Safiyyerh ba, to ƙaddarar Safiyyerh bata iskanci bace, wannan dalilin ya saka nake so a yi mini aure." "Ke kuma da kike zaune Form dubai to America daga gidan ubanki zuwa nan ai kin fini wahala, Wahee ki" "fita a lalurata ki fita ba ruwanki"" Wahee ta ce ""Kan uba kike zagin ubana? Ni kikewa gorin gidan uba?"" Ta" "yi kan Safiyyerh ta ce ""A'a kar ki fara, ba wani hankali garan ba a yanzu, ba Safiyyerh baya bace wannan Safiyyerh a shirye take, kafin na yi miki rauni leave""" "Ta matsa, ya shige kitchen ta ɗauki lunchbox nata ta nufi waje ta bar Wahee a wajan. Wizzy na ganinta" "ya miƙe tsaye ya ce ""Barka da fitowa""" """Good morning Wizzy""" """Morning how are you?""" """Allahamdulilah""" "Motar ta shiga, suka fita Safiyyerh ta ji kamar ta fita daga cikin kurkuku ta dinga jin farinciki a zuriyarta a" "hanya ta dinga kiran number Mutallab tunda ta haddace sosai, tana ta ringing mai ɗauka ba. Motar Safiyyerh ta riga tasu Aafiyyah tsayawa, Wizzy ya buɗewa Safiyyerh mota ta sakko ya miƙa mata jaka da lunchbox ɗin, kai tsaye motarsu Aafiyyah da taga an buɗe murfin ƙofar ta ƙarasa da mamaki ta kalli Aafiyyah dake ƙwance a cinyar Mj shi kuma yana riƙe da gorar ruwa da magani data lura sai taga kamar" ma kanuna ce a hannunta. """Yaya""" "Mj ya ɗago ya ce ""Safiyyerh ya kike?"" Ta yi murmushi ta ce" """Alhamd Yaya, ya ayyuka?""" """Good, Aliyu bai dawo ba?""" "Ta ɗan ɓata rai sai bata ce komai ba. Mj ya ɗago Aafiyyah, ƙirjin Safiyyerh ya buga ganin wani irin" "ramewa da Aafiyyah ta yi, idanunta sun sake girma ƙwarai sai cute lips ɗinta da sukai jajur sai kuma ɗan haki take. ""Favourite mu koma gida ko? Paaah shi ya biye miki wallahi""" """Safiyyerh help her kin ji, bata jin daɗi jiyan nan suka shigo Nigeria ita da Paaah so Please take care of" "her zan dawo na ɗauke ta""" """In sha Allah Yaya, kenan ba'a nan ta yi holiday ɗin ba?""" """E, ku je ga can za'a fara assembly"" ya gyarawa Aafiyyah baby hijab ɗin jikinta kana ta sauka suna haɗa" "ido da Mj ta ce ""Kuma sai ka yi ta tallata dani Yaya? Kowa sai ya san bana ƙasar kuma bani da lafiya, haba" "Yaya""" """Ohhho miki dai"" ya faɗa yana ɗaga mata shoulders." """Aafiyyah ya kike?""" "Aafiyyah ta juya ta kalli Safiyyerh, sai ta ji tsoron kallon kamar kallo ne na zargi ta ce ""Good""" """Ya jikin""" """He just kidding you, lafiya lou nake fa"" ta ce seriously. Daidai nan suka ƙarasa wajan assembly ɗin," Kimiyya ya dinga murmushi ganin Aafiyyah suna haɗa ido ta ɗaga masa gira alamar ya?. "A hankali ta shigo cikin class ɗin hannunta riƙe da lunchbox da textbook sai school bag data goya, hijab" ɗinta daidai da ƙirjinta ita ce ta fara shigowa da mamaki take kallonsa zuciyarta na bugawa ta je ga zauna "inda yake ta zuba masa idanu sai kuma ta ce ""Ka yi holiday assignment?""" "Ya buɗe manyan idanunsa bai ce komai ba ta sake yin ƙasa da murya ta ce ""Na san bama ka yi ba ka" "daina haɗe mini fuska, ka naso a yi ta faɗa da kai da teachers"" nan ma bai kula ta ba a hankali ta ji sautin da cikinsa yake yi sai ta jawo lunchbox ɗinta ta buɗe tare da tura masa gabansa ta ce ""Your breakfast, ka ci kafin a shigo na san baka karya ba"" sai a lokacin ya buɗe idanu ya juya gabaɗaya yana kallonta sosai ya" yi ƙasa da murya kamar zai yi faɗa sai kuma a hankali ya ce """Kuma ga mayunwaci ko?"" Ta yi murmushi ta ce ""Da ƙyar na jure ban biyoka gida ba, na yi kewar ka" "sosai bestie"" ya yi mata shiru sai kuma ya haɗe fuska da kyau yana janyo abincin yaga dankali ne aka" soya da ƙwai ya yi ɗan tsaki ya ajjiye spoon ɗin ya damƙa ya kai bakinsa ta yi saurin kama hannunsa ta ce """Kai baka iya komai bane? Sai a yi maka dariya cin abinci da hannu"" ya ware idanu sai kuma ya murtuke" "fuska ya ture hannunta a hankali duk da muryarsa a kumbure take ya ce ""Ki daina kusanta kan ki dani, ni fa ba ɗan iska bane""" """Laaa Allah Ya baka haƙuri kai duk abin soyayya baka iya ba"" a taƙaice ya ce ""Ke kika santa"" ta ja baya" "tana ɗaga hannu ta ce ""Lalala to shikenan ni dai ƙaddararka ce, na faɗa a gida a yi mini aure, ka san me na ce?"" Ya girgiza mata kai kawai yana sake damƙo dankalin yana dannawa cikin bakinsa saboda yunwa ko gani baya yi sosai ta buɗe gorar ruwa ta miƙa masa a hankali ta ce" """Na ce su yi mini aure wallahi bana son karatun nan, na ji aure nake so kuma na faɗa musu kai nake so," "amma wai ban isa ba karatu ya zama dole kuma shekaruna sun yi kaɗan amma ai na girma shekararmu 15 years fa, ko kai baka isa aure bane?"" Ya yi mata shiru sai ta fashe da kuka sosai ta ce ""I love you so much Bestie, don Allah ka aure ni zan zauna dakai a duk yadda kake ka taimakawa rayuwata"" ya zame hannunsa tas ta miƙa masa tissue ya goge ya ja baya yana lumshe idanunsa har yanzu students basu fara" "shigowa ba, ta ɗan yi gaba kamar za ta shige masa cikin tsawa ya ce" """Zan kwaɗe ki kuwa""" """But what if i told you i love bestie? You mean the world to me, wallahi aure nake so ba karatu ba"" ta" faɗa tana shassheƙar kuka sai a lokacin ya kalleta fuska babu walwala ya dubi yadda take kukan sosai ya ce """Ke, babanki ne ya mutu? Ko uwarki ce?"" Ta girgiza masa kai ya sake haɗe fuska yana rarraba idanu a" "cikin ajin kamar mai neman wani abu can ya ce ""To kece za ki mutu kenan?"" Ta girgiza kai sai kuma ta ce ""A'a""" """Kukan fa?""" """Na soyayyarka ne bestie taɓa ƙirjina ka ji wallahi ni ce ƙaddararka ba zaka gane hakan a yanzu ba, da ina" da ikon cire abin da nake ji a ƙirjina da na yi hakan ina jin dama na mutu na huta kuma idan ban aure ka "ba zuciyata zata iya bugawa""" """To gwara ta buga na huta da na ci, shekaruna 15 za ki lalata ni da batun aure, ke tashi ki ware daga nan" "ɗauki kwanukanki kar ki ƙara kawo mini abinci"" ta miƙe jiki a sanyaye zata bar wajan ya nuna mata" lunchbox ɗin daya cinye komai """Ko daɗi bai yi ba abincin""" "Sai a lokacin ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ta yi kukan ba, dimples ɗinta na lomawa ta ajjiye masa" "500 ta yi waje tana cewa ""You're my darling jarumina, i love you Mai dawa da jeji"" ta faɗa tana sake yin dariya tare da yin waje......." "Ya bi bayanta da kallo cike da tausayawa, idan ya tuna Jaanah ji yake ba zai yafewa kansa ba, idan ya" "tuna Jaanah ji yake yi ya tsani kansa, haka idan ya tuna Diyna sai ya ji duniya ta masa faɗi, ba zai ƙara sakacin barin wani rai ya salwata ba a dalilinsa, kula mace ba dole bane, aure ba wajibi bane, soyayya ba tilashin ɗan gidan Malam Abdullahi ba. But..." """But what?"" Zuciyarsa ta tambaye shi kai tsaye, ya cije lips ɗinsa ""But what about the secret love" "message? Idan zuciyarsa zai wa adalci ya san yana son mai message ɗin nan, hakan ya tabbatar da yana son Safiyyerh." "Bayan fitowa break, Aafiyyah na zaune ita da Kimiyya a cafeteria meat pie ne a hannunta da Kimiyya ya" "kawo mata da ƙyar ta ɗauka amma ta kasa ci sai ta ajjiye ""crush wai meke damunki""" """Like?""" """Duk kin rame, kin zame wata kala kin zama so silence haka""" """Shine na ce Kamarya?""" """To Allah Ya baki haƙuri""" """Dame?"" Ta ce tana taɓa wayarta. Safiyyerh ta shigo ta nemi waje ta zauna a hankali ta ce ""Aafiyyah i" "need a favour kin ji"" Aafiyyah ta dinga danna waya, Safiyyerh ta ce ""Ki yi haƙuri da message ɗin dana tura miki, a lokacin ban san meke damuna ba, i don't know what comes over me, ki yi haƙuri don Allah Ki taimaka mini kamar koyaushe ki yi Mutallab magana, ki fahimtar da shi halin da zuciyata take ciki"" da" "sauri Kimiyya ya kalli Safiyyerh, saboda ya san komai shi kallon mamaki yake mata data iya rufe idanunta." """Soyayya ƙaddara ce Aafiyyah, rayuwa wa'adi ce, mutuwa wajibi ce, hisabi gaskiya ne, soyayya halitta ce" "a ƙirji a zuciyar kowanne mai raye, don Allah don ko tausaya mini wallahi na kai stage ɗin da zan iya rasa" "raina"" ta yi shiru tana fashewa da wani irin raunataccen kuka ƙirjinta na buɗewa. ""Ba lallai ki gane ba, saboda ba ki taɓa faɗawa cikin jarrabawar so ba""" """Ai kam"" Aafiyyah said." """Ya kike so ta yi miki"" cewar Kimiyya." """Ta yi magana da Mutallab""" """Amma Safiyyerh. ,""" """Uhmm ehem, shikenan zan masa magana Safiyyerh, kin dai san ba wani magana muke ba amma zan yi" "saboda ke. Maganar wasiƙa ƙila kin yi missing number ɗaya daga cikin number Aafiyyah saƙon bai zo ba""" ta saka shade glasses ɗin ta miƙe tare da ficewa daga cikin cafeteria ɗin. "Yana zaune a cikin aji har lokacin yana buga game a wayarsa, ta ƙarasa cikin ajin tare da jan kujera ta" "zauna a gabansa. Ƙamshin turaren da bai taɓa ji ba ya ji, yana ratsa hancinsa da saukar masa a ƙirji, ya" "cigaba da game bai ɗago ba, amma sai ya zubawa yatsun ƙafarta idanu saboda flat takalmi ta saka." "Aafiyyah ta kasa magana sai a hankali ta ɗora kanta a saman table ɗin da yake zaune, sun jima a haka," "zaman ya gundire shi ya miƙe zai fita ya ji siriryar muryata, sautin daya fito a raunace ta ce ""Love" "Safiyyerh""" """Ka so safiyyerh""" "A hankali ya dawo ya zauna. Ya fara kallonta ganin ta gyara zama, ya dubi kanunar hannunta sai ya ja" "tsaki ya saka hannu ya zare glasses ɗin idanunta, sai ya ga ashe shi take kallo ta yi saurin haɗe fuska tamau." """Munafuka ce ke? Za ki magana kamar bani kike kallo ba""" """Hmmm""" """Hmmm ɗin""" """Ka auri Safiyyerh""" "Ya dinga kallonta ganin yadda take jan numfashi ""Don Allah""" "Miƙewa ta yi zata fita ya ce ""Jiiiii"" sai ta tsaya ya ƙarasu inda take ""Are u sick?"" Tsaki ta ja masa kawai ta" fice da sauri. Baya ta koma can ta goge hawayen idanunta da yaƙi tsaya mata. * Duka suna a cikin ajin a washegarin ranar da aka koma makaranta. Mutallab da suka bashi nickname na "MOH, sai Kimiyya da Nahyan, sai Kinal da sauran students. Kamar an cillo captain haka ya shigo class ɗin ya ce ""Safiyyerh ji mana""" """Ya aka yi Captain?""" """Magana za mu yi""" "Ciki ciki Moh ya ce ""Yi a nan""" "A ƙufule shima ya ce ""Baka isa ba, kuma ka yi kaɗan wallahi, baka da uban komai ka zauna har kake bata" "umarni kamar wani mijinta""" "Moh ya ɗan shagiɗar da bakinta yana murza goron hannunsa ya ce ""Zan aure ta ne"" cike da baƙin ciki" "Captain ya ce ""Idan zaka iya aure ta yanzu mana"" ya faɗa yana huci kamar kumurucin maciji." """Kaga ni sai na zama waliyin ango, Nahyan ya zama waliyin amarya Safiyyerh, Kinal da kai Captain da" "sauran students su zama shaidu"" Nahyan ya dinga dariya ya ce ""Bari na fita na siyo chocolates matsayin goran ɗaurin aure"" ya miƙe ya fice. Kimiyya ya ce ""A'a abu ya yi kyau, kamar na san da wannan sabga na watsu kuɗi cikin aljihuna ashe rabon na biyawa yarona kuɗin sadaki ne"" Kinal ma dariya ta yi ta ce ""Kaga ni kuma sai na zama photographer, na ajjiye shaidar ɗaurin aure mai albarka"" suka dinga shaƙiyanci." "Safiyyerh tana ta murmushi abin a haka Nahyan ya dawo, Kimiyya ya ce ""To bisimillah, ni Kimiyya ina nemawa ɗana Muhammad Mutallab Abdullahi neman ƴar wajanka Safiyyerh Abdu"" Nahyan ya ce ""To na gode, nima Nahyan Nasim Wasim, ina mai farin cikin faɗa maka na bawa ɗanka Muhammad Mutallab" "Abdullahi auren Safiyyerh Abdu""" "Kimiyya ya ce ""Thank you, ga sadaki har naira dubu goma, sai mu yi salati"" kamar wasa suka fara salati" """Allahamdulilah aure ya ɗauro"" Ya fara raba chocolates Nahyan, Kinal ta dinga yin recoding tana dariya" "ya ce ""Safiyyerh ga sadakinki"" ya miƙa mata kuɗin ta amsa." A hankali ya juyo ya kalli Safiyyerh ganin ta amshi kuɗin sai taga ya kashe mata idanu ɗaya ta masa "gwalo ta ce ""Mijina""" """Anyi abu kamar wasa, haka watarana zai muje ɗaurin auren MUTALLAB da SAFIYYERH bestien beastie """ "Daga bakin ƙofar shigowa class ɗin aka ce ""And who told you ana wasa da aure? Yanzu ma ai kun yi" "musu aure, kuma auren gaskiya they're now husband and wife." Sai kuma Saturday. MUTALLAB Paid book ne 500 Yi magana via WhatsApp only 08164069385 to subscribe urs Na'ima Sulaiman Sarauta NIMCYLUV "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 36: The first kiss" "Ɗaya daga cikin ɗaliban ya yi furucin yana shigowa cikin ajin, Nahyan ya ce ""Wanne irin aure ya ɗauro?" "Kamar a garin gaɓa-gaɓa?""" """Yes, auren safiyyerh da Mutallab ya zama halittacen aure, on my understanding"". Ya ce yana zama tare" "da juyawa ya kalli Safiyyerh ya ce ""Kuka ya ƙare ko? Lallai Safiyyerh soyayya ta miki mugun kamu, to, mu dai mu ne masu shirya events idan al'amarin ya kankama"". Duk suka yi, banda Kimiyya da ya yi shiru yana tunani can kuma ya ce ""How comes auren zai zama halittace?""" """Kai bafa wani abu ka basar kawai, is just a suggestion""" """To haka ake suggestion ɗin?""" "Nahyan ya ce ""Amma ku tsaya, na yi missing wani abu bayan fitata siyan chocolates. What did i missed?""." "Kimiyya ya ce ""zazzafan kisses ka yi missing don ka ji"" jikin Nahyan na rawa ya ce ""Haba? Don girman kar ka yi haka, da gaske ango da amarya sumbata sukai wa juna?""" "Kimiyya ya jinjina kai ya ce ""E, halal sumbata mai zafi""" "Mutallab dai bai ce komai ba, jinsu duka yake yi, ya san dai ba wani aure domin ba haka ya yi lissafin" "yadda ya kamata aure ya kasance, kuma ya kasance ba. Ya yi shiru, yana ƙanƙance idanunsa akan safiyyerh da take kashe masa ido tare da masa murmushi, murmushin dake nuna masa cewa “Ka gani ba? Ba na ce sai na zama matarka ba? Gashi na zama, Safiyyerh ta zama matar Mai dawa"". Shi kuma kallon tsaf yake mata, yana son ya ji zuciyarsa ta gamsu da Safiyyerh kamar yadda ta gamsu da wasiƙun" da take tura masa kodayaushe. "Nahyan ya yi gyaran murya da gyara zama ya ce ""Ehmn, amma kun yi hauka fa, ta ya kuka bari suka" "sumbaci juna auren wasa ne fa? Haramun sukai""" """Ba wani auren wasa, me ake buƙata da aure? Shaidu, waliyai, sadaki, amincewar ma'auratan ko na ce" "masoyan shikenan fa"" Kinal ta ce, tana watsa hannayenta. Ta ƙara da cewa ""Kuma ai kai Nahyan uncle" "din Fiyya ne, kana da ikon zama waliyin Safiyyerh ko a ina ne, domin mahafinka ai ƙanin mahaifinta ne" "ko?"" Nahyan ya ce ""E, haka ne kuma, amma ai sai da amincewarta idan ta amince na zama waliyinta""" """Ta amince ai"" cewar Kimiyya." """I said, what did I missed?""" * “What did I missed?” Nahyan na murmushi ya fita siyan chocolates ɗin matsayin goran ɗaurin auren Safiyyerh da Mutallab "kamar yadda suke planing ɗin yi, auren wasa ne, amma basu ɗauka zai zama silar shigar zuƙatan wani" "irin aure ba, ba tare da duk sun san sharuɗan auren ba, ba tare da sun san cewa ba'a yin auren wasan ba. Nahyan ya ji zai yi komai ko dan ya baƙanta ran Captain, da kuma wannan tunanin ya fice daga ajin nasu na Jss 3 cikin sa'a kuma duk suka zauna a A ɗin gabaɗayan su." "Bayan fitar Nahyan, Kimiyya ya kalli Safiyyerh ya ce ""Bestien beastie kar mu shiga haƙƙin ki, kin amince" "Nahyan ya zama waliyin aurenki? Ya karɓi aurenki, kuma kin amince da dubu goma matsayin sadakin aurenki da Mutallab"" ya yi tambayar in a serious way, cike da zaƙwaɗin jin amsar da zata mayar masa, deep down na zuciyarsa yana addu'ar Allah ya sa watarana su halicci auren nasu a zahirance domin cikar burin Safiyyerh. Safiyyerh ta kalli Mutallab da yake kallon ta, har mamakin kallon da yake mata take yi" "kamar mai zarginta ko tuhumarta, idanunta ya yi rau-rau hawaye suka ciki idanunta ta ce" """Ni a raina nake jin auren gaske za ku yi mana, a raina nake jin yau zan amsa sunan da nake mafarki, a" "raina nake jin nima zan zama wata wacce zata iya cimma muradinta kafin wa'adin da Ubangiji ya ƙare mini a duniya. Wallahi Kimiyya duk yadda zan kwatatan maka halin da zuciyata ke ciki ba lallai ka fahimta ba, ba kuma lallai ka gane ba, auren Mutallab da rayuwa dashi matsayin miji shine fatana. Me ya sa kake tunani a wannan halin da nake ciki zanƙi amincewa bayan na san daddy ba zai taɓa cika mini muradina" "ba? Ko da kuwa zan mutu ne na bar duniyar""" "Ta sunkuyar da kai, tare da kallon Mutallab sai ta juya ta kalli Kimiyya ta ce ""Duk na amince, ni kam na" "amince da gaske ta amince Nahyan ya zama waliyinta"" ta ce in her lower voice." """Allahamdulilah, daman amincewar muke buƙata ai Nahyan ya cika ta amshi walicci domin a girme ma" "ya girme mana, bana ya dawo daga kawo goran auren kai har musulmar walima zamu haɗa ko dan su" "ƴan hana ruwa gudu. Kuma auren nan til-janna in sha Allah""" """Allahumma amin, Ubangiji ya amince Kimiyya, shi ya sa nake yin ka kana da fahimta""" """Uhmm, anything for you Safiyyerh ai kin cancanta kina bani tausayi""" """Thank you, again and again"" ta ce cikin karewar muryar mai matuƙar sanyi irin ta yi giving up tuni sai" "kuma abin da take fata ya kasance. Suna cikin maganar Nahyan ya dawo ɗauke da chocolates da yawa masu kyau kuma, ya zauna aka fara gabatar da aure har aka kammala shine shine yake tambayar ne aka yi bayan ya fita me ya rasa a hirar he, yake faɗin what did i missed?" * Present continues.... Suka sauke ajjiyar zuciya a tare fuskarsu ɗauke da farinciki musamman da suke tunanin a yanzu su bawai "auren wasa sukai ba, maybe wata hanya ce da Ubangiji ya nuna musu wajan kuɓutar da daughters daga kamuwa da ciwon zuciya. Nahyan ya ce ""Kenan dai yau da gaske na amsa matsayin babban yaya kuma ni uncle ne ko cousin, I don't know actually, wish you all the happiness in your marriage dear""" "Safiyyerh ta yi murmushi ta ce ""Thank you"" tana jin wani irin farinciki na ratsa mata zuciya tamkar bata" "da wata sauran damuwa a duniya haka ta ruski kanta ta samu wani sashe mai girma a cikin gurbin zuciyarta ta sanya Mutallab ciki matsayin abokin rayuwa, kuma Matsayin mijinta, Safiyyerh's husband." """Ango naga akwai free time bari na leƙa waje ko?"" Kimiyya ya ce. Cikin sauri Nahyan ya miƙe ya ce ""Bari" "na biyoka a bar su, su ɗan sarara su huta kuma su sha iska""" """Gaskiya dai"" cewar Kinal." "Bayan fitar su, Safiyyerh ta kalli Mutallab da yake danna waya a hankali ta matsa kusa da shi, sai kuma ta" "saka hannunta ta ƙwace wayar hannunsa, a wani irin firgice ya ɗago rikitattun idanuwansa da suka ƙanƙance, ya kasa magana saboda murmushin da ta yi masa, ya yi yunƙurin miƙewa ta yi saurin saka hannunta ta riƙo hannunsa, ya haɗiye maganar maƙoshinsa da ƙyar, jin ta manna tafin hannunsa a ƙirjinta, bugun zuciyarta ya dinga ɗagawa da tafin hannun Mutallab, ta riƙe hannun da kyau a ƙirjinta ta ce. ""Ban taɓa jin kalar wannan bugun zuciyar ba sai yau, sai na ji kamar tana bugawa ba bisa ƙa'ida ba," "sai na ji kamar ta fara bugu a ƙirjina irin bugun nan na wa'adin ƙarshe a rayuwa""" """Ko dai yanzu na mutu, ai na san zan mutu ne a tafin hannunka, a jikinka, kuma a ƙirjinka"" a hankali ta" "share hawayenta tana murmushi ta ce ""Soyayyata a gare ka tsarin Ubangiji ne, don Allah ka kyautata mini Ka ji?""" """Fiyyya..."" Shi kan shi a saman kan shi ya ji kiran sunan nata, ya ji kalamanta da hawayenta na narkar" "masa da zuciya, ya ji saukar abu mai kama da tuni, da tunasar da shi Jaanah da Diyna sai firgici ya gitta masa a zuciya. Ta yi murmushi ta ce ""Kai nawa ne, ni taka ce in sha Allah, koda daddy bai amince ba ai yanzu mun yi aure ko? You are my husband ni kuma matarka ce, ka je ka faɗawa Ammo matarka na" "gaishe ta""" """Fiyyya, zare hannuna a ƙirjinki""" """Ina so ka ji yadda zuciyata ke bugawa"" ta faɗa truly, with smile on her face tana sake riƙe hannun." """Wani abu nake ji, zunubi Fiyya, ɗan iska za ki mayar dani, na ce iskancin kike ji da shi"" ya ce yana mata" "ihu a saman kanta tare da ƙanƙantar da idanunsa ciki-ciki. Safiyyerh ta buɗe ido cike da tsoro ta ce ""Wani abu? Wanne abu kenan?"" Ta ce a ruɗe." "A ruɗan shima ya ce ""Tomatir""" """Tomatir? A ƙirjin nawa?""" "Harara ya watsa mata ta kyakkyawa ta yi da dariya ta ce ""Yanzu fa kai babban mutum ne, ka fahimta ni" "matarka ce""" """Safiyyerh!"" Ya kirata." Ta ɗago ta kalle shi a hankali tana tsayar da dariyarta while she is keeping eye on him. Tare da jinkirin jin "abin da zai fito daga cikin bakin nasa, she wish ya ce Fiyya i na son ki, na amince dake." "Ya durƙusa dab da fuskarta, suna shaƙar numfashin juna ya ce ""Ke barewa ce, ke deer ce, deer ce" "Safiyyerh, matar moh daban, mai halin Moh daban, matar moh, zata kasance mai hali irin na Moh ne kaɗai, ki gane ki fahimta kin ji?""" """Me zan fahimta?"" Ta ce a rarrabe, kamar kuma yadda ta yi furucin a rabe haka ta ji zuciyarta na" "rarrabewa a cikin ƙirjinta. Ya ɗage mata gira biyun tare da tsuke bakina ya yi mata feɗuwa mai sauti ya ce ""Just friendship, abota kawai Fiyya ya wadatar"" ta ce ""Aure na da yake kan ka fa to?""" "Ya ɗage kafaɗa ya ce ""Sake ni""" "Fita ya yi daga cikin ajin ya yi waje, idanunsa ya fara sauka akan Aafiyyah ita kaɗai zaune ta yi shiru" "hannunta riƙe da counter, kamar koyaushe ta saka baƙin gilashi a saman fuskanta ya yi mata kyau, ramarta ta sake fitowa fili kallo ɗaya za ka yi mata kasan cewa bata da lafiya, baki yaga ta murguɗa masa ta kawar da kai gefe da sauri kuma ta miƙe ta bar wajan tana ɗan danna wayarta ta yi hanyar lap ya" tsuke fuska shima. * "Paaahh na zaune a cikin ƙaramin parlonsa nasa yana sanye da men's slim fit 3pcs suit dark blue, ya" "jingina bayansa da jikin wata Morden chenille flocking floor yana juyawa a hankali idanuna zube a kan wanda yake gabansa, Yana sauraron abin da yake cewa. Mutumin ya gyara zama ya ce ""Kamar yadda tawa Safiyyerh take ƴa ta, haka na ɗauki ƴar wajanka Aafiyyah matsayin ƴa ta, wallahi dukkan da na yi mata akasi aka samu kuskure ne na san kuma sam ban kyauta ba, shi ya sa na nemi ganawa da kai domin" "na sake baka haƙuri don Allah""" "Paaahh ya ce ""Professor""" """Na'am, Prof """ "Daddy ya amsa, kamar yadda shima mutane da yawa suke kiransa Matsayin Prof ya ce ""I am very sorry" "professor""" """Idan dukan ƴa ta kuskure ne, dukan taka yarinyar fa?""" """Dukan tawa yarinyar gyara ne, saboda ta ɓata mini"" daddy ya ce cike da damuwa ya ɗora da faɗin" """Kamar Safiyyerh shekarunta 15 a duniya ita ce zata zo ta kalli cikin idanuna ta ce mini wai wani take so? Wanin ma ɗan iska can wani waje? Wai Ɗan'malam wanda bashi da cin yau balle na gobe. Gudanawa Safiyyerh take banda cewa ka haifi yaro baka haifi halinsa bane, wai ita aure take so ba karatu ba kuma bata gane karatun, ka duba fa?""" "Paaahh ya ce ""Ka fara fuskantar ta, amma duka baya kawo mafita a rayuwar raya, Aafiyyah da kake" "ganinta nan uhmmm"" ya cije lips sai ya ce ""Ina tsananin so da ƙaunar ƴata Aafiyyah bana iya kwatanta son da nake mata dana wani abu a duniya. Ba zan cika ka da magana ba, kawai don batu kake akan abin da ya shafi tsagina ne Allah ya raya mana su""" "Daddy ya miƙe yana miƙawa Paaah hannunsa ya ce ""Thank you professor"" ya ce na jijjiga hannun." """Ba damuwa, Prof""" "Miƙewa ya yi a hankali hannunta riƙe da ƙaramin bottle of water, ya nufi hanyar shiga main parlo yana" "shiga ya samu MJ, da sauri ya ce ""Sannu da zuwa dad""" """Safiyyerh fa"" Paaahh ya tambaya kai tsaye ba tare daya kalli MJ ba, Ummi ce ta fito daga kitchen ta ce" """Tunda ta dawo daga makaranta take ɗaki fa, sau biyu ina shiga ina tararwa tana bacci sai ban tashe ba domin kwana biyu bata baccin""" """Kuma kin yarda baccin take?""" """Na yarda mana Paaah""" """Uhmm"" ya ce yana nufar ɗakin Aafiyyah, a hankali ya yi knocking can ƙasa ya ji muryarta ta ce ""Daddy" "come in"" buɗewa yi ya shiga, tana ganinsa ta miƙe tsaye tana murza idanunta ta ce ""dad ƙwaro a ido, idona dad"" ya dinga kallon ta, ya san cewa she is crying sai ya juya ya kalli frame ɗin photonta a hankali ya yi murmushin ya ce ""As always, she is clever girl, smartness"" ƙafarta ta ɗan buga a ƙasa ta fara yarfe hannunta tare da kiran sunan dad. Paaah ya juyo ya kalleta sai ya kama hannunta tare da janta zuwa bakin gadon ɗakin nata a hankali ya duba ta da kyau sai kuma ya ce ""Gaya mini inda na taɓa tauyar rayuwarki?"" Ta girgiza kai, ya tsare ta da idanu ya nisa ya ce ""buɗe baki ki mini magana Safiyyerh"" ta ce ""Dad, komai ka yi da rayuwata daidai ne kuma ka cancanta ka yi komai ɗin, kai ne ka haife ni ka kula dani tun ina zanin goyo, ka ciyar dani daga halak, ka shayar dani daga halak, ka tofatar dani daga halak, ka bani kyakkyawar tarbiyyar da nake farinciki da ita. Babu wani hukunci a rayuwa da zaka zartar a rayuwata ban amsa ba Paaahh, zan maka biyayya ko da zai cutar dani ne "" da sauri ta buɗe idanunta tana masa dariya ta rufe bakinta ta ce ""Oh no my mouth, my mouth dad, na ce Professor Abdu the" "whole prof""" "Idanun Paaah ya jirkice ya san wace Aafiyyah farin sani ya girgiza kai ya ce ""Safiyyerh""" """My handsome dad""" """Yi kuka Safiyyerh don Allah""" Ta yi saurin ɗago kanta ta kalli Paaah da tunani daban-daban a ranta sai ta yi ƙasa da kanta ta shiga wasa "da yatsun hannunta, ya kamo hannunta cikin nutsuwa ya ce ""Komo zai daidaita kin ji, kar ki ji kamar ke kaɗai ce a duniya, You are not alone Safiyyerh, Paaah is here, Ummi, Mj da sauransu kin ji? Ki yi ta addu'a zan ƙaro miki wasu azkar ɗin. Ki yi ibada, ki karatu zan ma kawo miki wasu teddy amma ki rage abubuwa kina bacci, ina buƙatar rayuwarki, ki taimaka mini wajan ganin mun inganta lafiyarki kin ji?"" Ta jinjina kai ya ce ""Ki kuma taya ni kula da tarbiyyarki kin ji?"" A hankali ta ce ""In sha Allah, dad amma ban son teddy na ji bana son komai kuma a dai kawo mini teddy ɗin kuma na bana son wayata dad ka amsa""" ta ɗauki wayar ta miƙa masa. """Zo nan Safiyyerh""" "Aafiyyah ta ƙarasa wajan Paaah, ya sanyata a jikinsa ya rungume ta sosai ya ce ""Yanzu ko a kilo na saka ki" "ba lallai ki yi jaka guda ba"" murmushi ta yi tana jin daɗi ta rungume Paaah, addu'a ya dinga mata yana shafa sumar kan nata. A hankali ya ji hawayenta na sauka a jikinsa ya ce ""Ai na ce ki yi kuka, cry Safiyyerh" "ki yi kuka""" Shassheƙar kuka ta fara ta riƙe shi gama ta saki wani irin raunataccen kuka Paaah ya rungume ta yana jin "kamar ya tsaga ƙirjinsa ya mayar da ita ciki. A hankali ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, fuskarsa nan kamar ya ce ya shiga uku, Paaah ya ɗaga kai ya kalle shi ba sai kuma ya juya ya ce ""Mj ka same ni a part ɗina""" """Ok Paaahh """ "Ya fita, yana ta tsaye a hankali kuma shima ya juya ya fice daga ɗakin. Paaahh ya ji saukar numfashinta a" hankali ya ɗago ta daga jikinsa ya kwantar da ita ya rufe ta da duvet sai sauke ajjiyar zuciya take yi ganin kanta a buɗe ya ɗauki abu ya rufe mata ya rage mata gudun a.cn sosai ya kunna mata karatu ya kashe hasken ɗakin a hankali ya fita yana rufe ɗakin. Bacci ta fara yi peacefully. * Malam ne ya fito ƙofar gidansa da sauri saboda busar da ya ji da kuma ƙara kamar ana gangi tare da "haushin karnuka, sak ya yi ganinta Mutallab wanda ake wa kirarin tare da laƙaba masa sunan Mai dawa. Shi kuma ya cake a tsakiyar tarin mutanen wanda suke sanye da kayan farauta, bunjimar riga da hular saƙi ga gorori a hannunsa yawanci hannunsa duk sun maƙala goro sai tarin karnuka da suke a wajan." Ƙaho suke busawa sun zagaye Mutallab da yaƙi motsi ya cake waje ɗaya yana jin naman jikinsa na "motsawa da yin wani irin karkarwa musamman ƙirjinsa bai taɓa yin kirari ba, baya so kuma a tunzura shi" amma gani yake da ƙyar ya iya shallakewa. """Kai ne uban masu dawa, shiga jeji idan babu kai ƙarya ne, sai kai mai gidan tururuwai. A gaida ɗan gidan" "Malam Abdullahi shalelen Ammo, ba dai gaba da gaba ko ta baya sai an shirya don abin takazan nan. Mai dawa katarin masu dawa mai Sa'adah da Hamida, ina gwanin wani gana Bafullatana mai tiger kaga gwanin masu shiga farauta, farauta idan babu Muɗallabi yawan ta zubar ne, a lafiya Muhammad Mutallab Abdullahi Ɗan'malam""" "Jikin Mutallab ya hau rawa, gabaɗaya gaɓɓan jikinsa mazari suka ɗauka kansa a durƙushe wani irin" "kururuwa Goje ya yi yana cigaba da yi masa dariya. A kiɗima ya ɗago kansa kamar an ce ya juya ya hango ta tsaye tana ta yi masa dariya, a mamakin ta sai taga ya kashe mata ido tare da yi mata alama ta zo." "A hankali ta taka tana shige mazan wajan ta ƙarasu tsakiyar filin ta tsaya a gabansa, uniform ɗin" "makaranta ne a jikinta. Ya tsora mata ido sai kawai taga ya rabe ƙafarsa biyu, ya ɗaga hannayensa sama ya buɗa su cikin wata murya mai sauti a kuma kumbure ta ji ya fasa wani ihu da kururuwa ya ce." """Sai ni Muɗallabi na Bestien beastie, mai ƙaunar Allah da Manzonsa, ɗan Abdullahi da ammo ƙanin" "Hamida da Sa'adah, Allah ya ji ƙan Jaaanah Allah ya gafarta ran Diyna, dawa tamu jeji namu, naman jeji namu masoyin tiger da teddy wo!wo!wo!!! Sai ni Ɗan'malam jikam yarabawa"" gabaɗaya ya firgice ya fita hayyacinsa yana jin busar ƙahon na tsuma naman ƙirjinsa zuciyarsa na motsa masa. Safiyyerh ta yi baya zata gudu ganin idanunsa kamar hayaƙi yake, tako ɗaya ta yi ya damƙo hannunta ya dawo da ita gabansa, ya saka hannunsa ya murza gashin kansa da gumin kansa ya saka hannunsa ya farke gaban rigarsa ya shafo gumin jiki, Safiyyerh ta daskare a wajan ganin ya shafa mata gumin a fuska, tare da zaro harshe" "kamar zai suɗe fuskarta sai taga allurai suna fita, askira ya ɗakko a jikinsa bata taɓa sanin yana da ita ba." "Ji ta yi fitsari na neman ƙwace mata, numfashinta ya fara ɗaukewa ta gama sandarewa tare da tunanin" "wa'adin rayuwarta ya zo ƙarshe a lokacin daya fara dirza mata askirar a fuska kamar zai mata bille. Luuu ta yi zata faɗi saboda sumewar da ta yi, ya saka hannu ya taro ta, ta faɗa jikinsa ya riƙe ta gam kuma ya kasa cigaba sai jikinsa daya ɗauki rawa, dakatawa sukai da kirarin da kuma busar, Goje ya ƙarasu wajan" "ya taɓa Mutallab ya ce ""Mai dawa""" Cak ya miƙe tare da saɓa Safiyyerh a wuya ya shige da ita cikin shagon Goje dake ƙofar gidan Malam Abdullahi. Malam ya yi saurin juyawa ya faɗa cikin gida yana tattare babbar riga ganin Mutallab kamar gidan zai "shigo. Mama Zaituna ta ce ""Malam ko lafiya?""" """Wanne lafiya? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, matar nan ta gama cutata Allah ya yi wadaran halin" "Muɗallabi ya yi gutsi -gutsi da halinsa, na shiga uku wannan yaron shi ne zai yi ajalina""" """Hakan ba zai taɓa faruwa ba In sha"" cewar Ammo. Cikin faɗa ya ce ""Zaki rufa mini baki ko sai na yi ƙasa-" "ƙasa dake a wajan nan? Kina ganin masifar da kika ja mana, kina kallon yadda zunubin da kika aikata" "yake yawo ko? Kina gallo yadda shuƙar da kika yi take yaɗo ko? To gashi can kuma ya kashe wata baturiyar yarinya ba ruwana wallahi tallahi """ """Safiyyerh?"" Cewar Ammo a kiɗime kuma ta yi waje cikin sauri malam ya ce ""Kina fita ina miki Allah Ya" "isa, kuma a bakin auren naki "" cak ta tsaya ta zubawa idanunta da sukai jajur a hankali ta juya kuma ta shige cikin ɗaki zuciyarta na yi mata wani irin zafi da raɗaɗi a hankali ta fara kiran sunan Allah" maɗaukakin sarki. "Mutallab ya zubawa Safiyyerh idanu da har yanzu taƙi motsawa, sai ya lumshe idanunsa a hankali ya ce" """Deer""" """Matar Moh, zata zama irin moh""" "Wani abu ya shaƙa fata ta tashi a firgice tana kiran sunansa dana daddy da Ummeyh, hannu ta saka ta" "fara kai masa duka a ƙirji ya tsaya yana kallonta can ya fisgo hannunta ta dawo dab da shi cikin faɗa na ce ""Bana ce miki abokai kawai ba? Ban ce haka ba?"" Girgiza kai ta fara ta ce ""Wallahi ni matarka ce ba abokiya ba"" kuka take masa sosai jikinta na rawa bai kulata ba, bai kuma ce ta yi shiru ba a hankali ta zame jikinta ta kwanta a cinyarsa ta sauke ajjiyar zuciya, kansa a ɗora a fuskarta ya leƙa suka haɗa idanu" "ta yi masa murmushi ta ce ""Kana da kyau sosai, ina son ka sosai, ina son yadda kake tsoro na ji ne""" """Hmmm""" """Nima hmmm"" ta ce tana kallon lips ɗinsa da suke da damshi, hannu ta miƙa zata taɓa ya make" "hannunta ya ce ""Tashi ki fece""" "Miƙewa ta yi, ta ɗauki jakarta ta yi waje ta ce ""Ba zaka raka ni ba? Na san ma sai an dake ni kamar" "koyaushe, to ai gwara su kashe ko?"" Ta faɗa a raunace tana langwaɓar da kanta gefe ya zazzaro mata idanunsa. Ta ce ""Bye bestie. I love you""" "A wannan karon ma akan idanunsa ta fito yana daga cikin motar ya zuba mata idanu, cikin sauri ya sake" "ɗaukan photonta wannan lokacin har bidiyo ya yi mata, bayan ta tafi shi kuma ya sakko daga motar ya shiga wajan Mutallab domin aikin daya kawo shi sai juya masa tunani yake." * “Banbancin kowacce shigewar rana tana tare da yadda take sake kusanta zuciyata da kai Yaa Muhammad. WAIT FOR ME” "Ya dinga karantawa da wani irin sabon feelings a zuciyarsa, feelings ɗin rubutun, feelings ɗin mai" "rubutun, feelings Safiyyerh." * Har ta shiga gidan ta yi wanka tai sallah ba wanda ya nemeta sai ta naɗe ƙafa kawai domin hakan ya yi "mata daɗi sosai a cikin ranta ta kuma ji daɗi da babu wanda ya tanka mata ɗin. A hankali Wahee ta buɗe ƙofa ta ce ""Ki zo in ji daddy"" Safiyyerh ta juya ta ce ""Daddyana kike nufi?"" Wani irin kallo Wahee ta yi mata sai ta ce ""Allah ya sa ba daga sama na faɗo ba Safiyyerh balle ki mini gorin gidan uba, ke da Captain" "kuma sai dai gani daga nesa wallahi""" """Matsalata dake kan ki baya kawo wuta Wahee, ke Captain ya dama""" "Fitowa ta yi, ta samu daddy shida Yaa sayyadi ta zauna bayan ta gaida Yaa sayyadin daddy ya ce ""Bayan" "tashi daga makarantar ina kika je Safiyyerh?""" """Gidansu Mutallab""" """Uhmm ka ji ko malam? Ta shi ki tafi ina zuwa"" ta miƙe ta koma sama, uncle Musbah ya bita da idanu" "kawai tausayin yarinyar ya ke ji ta samu balagar zuciya har haka wanann zamani ina za shi dasu ƙananun yara su ɗora kansu masifa har haka? Yaa sayyadi ya ce ""A shawarce ka aurar da Safiyyerh, ita ɗiya mace idan ta nuna aure take so mafi samun kwanciyar hankali kawai a yi mata shi, saboda gudun samuwar wata fitar tada ban, ka daina ganin Safiyyerh tsaf za ta yi zaman aure ka tuna zamanin baya har a" "shekaru 9 an aurar da yarinya duk da cewa su ba fita suke janyowa ba, tunda Safiyyerh ta san ta fara bin" saurayi har gidansu to abin ya lalacewa. Ita ɗiya mace fitina ce musamman idan suka samu balagar "zuciya, Safiyyerh ƴarka ce ka aura mata yaron, ka bashi sana'a, gida yadda zai kula da ita, idan ka yi" "hakan ai ba faɗuwa ka yi ba ko? Yi wa kai ne da kuma kare tarbiyarta""" """Ai har yanzu ba wanda ya san dalilin daya saka take son auren"" cewar uncle Musbah." """Masifa mana irin ta yaran yanzu"" Ummyh ta bada amsa kai tsaye." """Ƙaddara Safiyyerh ta isa aure ba zan taɓa aura mata Ɗan'malam ba, domin za'a kawo mini ita gawa ne" "kamar sauran ƴan'matan, ƙaddara ba hakan bama, wallahi ba zan bawa Safiyyerh auran talaka futuk kamar Ɗan'malam ba, jira nake komai ya yi daidai zata gane bata da wayo kam"" ya girgiza kai ya ce ""Kai bama shirya ganin auranta yanzu ba, bu bar maganar nan"" Yaa sayyadi ya dinga janyowa Prof aya da" hadisai amma ua rufe kunne tas. * "Kimiyya ya dinga murmushi ganinta yau akan wani ɗan ƙaramin lifan ya ce ""Yau an tuna babur ɗin nan" "kenan"" ta yi masa murmushi kawai Safiyyerh ta ƙarasu ta ce ""Yau kam dole a ɗana ni"" Aafiyyah dai" "murmushi kawai take yi can ta ce ""Ki je wajan bestie ya ɗana ki"" Safiyyerh ta ce ""Mijina za ki ce ai, au bakya nan aka ɗaura ko kimiyya baka bata labari ba kenan?""" """I almost forgot """ """Shi ya sa bata mini murna ba""" "Aafiyyah dai murmushi kawai take tana kallon wani waje daban Safiyyerh ta ce ""Kuma bai iya babur ba ai," "even keke ma""" """Anya?"" Aafiyyah said without looking at her tana ta gyara glasses ɗin idanunta." """Bai iya bafa""" """Gwada shi kiga"" cewar Aafff." """My crush yau ba gaisuwa, to good morning baby"" ya ce yana murmushi. Safiyyerh ta ce ""kaga Aafiyyah" "na gaida mutane daman?"" Daidai nan Mutallab ya ƙarasu, kamar Aafiyyah shima yau ba uniform suka" "saka ba, sportswears ne a jikinsu kuma duka farare gabaɗaya, abayan rigarsa an rubuta masa MOH ita kuma an saka mata S. ABDU." "Aafiyyah na kallon Safiyyerh ta ce ""Hmm, mene a gaisuwa ne namesake? Kawai bana yin abin da ban" "niyya bane, amma wanda na girma ma ai zan iya gaishe ki""" """Then. Greet us""" """Kimiyya good morning""" """Lafiya lou za ki yi albarka Aafiyyah in sha Allah""" """See, Safiyyerh ina kwana?""" "Safiyyerh na dariya ta ce ""Alhamd"" Aafiyyah ta ɗan gyara zama glasses ɗin, ta ɗan yi baya kaɗan a" hankali ta sake ja-da-baya direction ɗin idanunta kamar akan Safiyyerh a hankali ta ce """Good morning Tayo""" "Da sauri ya ɗago jin an ce Tayo, tuni Aafiyyah ta juya ta shige class, bai taɓa jin maganarta mai ɗan tsayi" "ba sai yau akwai sanyi da kuma tsiwa a sautin muryarta, akwai haƙuri da juriya da ƙulufuci duk a cikin" "muryarta, sai ya basar kawai ya yi gaba shima bayan ya dungurewa Safiyyerh kai da take masa dariya, ta" bi bayansa da sauri tana riƙe hannunsa ya mintsini tafin hannun nata. "A hankali Kimiyya ya ce ""take heart please Aafiyyah""" "Suna tsaye za su shiga practical a lokacin, ya jingina da jikin bango ƙafarsa ɗaya a jikin bangon ɗaya a" "ƙasa ya harɗe hannayensa duka biyun a ƙirji students ɗin yake kallo yana mamakin abin da ya saka ƴan mata ke burge wasu mazan, as a man kuma good man kawai ka nemi kuɗi ka yi arziƙi ka shahara a duniya shi ya fi, ka zama mai iƙo da faɗa a ji, ka zama wanda zai iya samun abincin da zai ci da safe kuma ya ci da rana ya ci kuma da dare ya bawa ƴan'uwasa da duk mai jin yunwa ya zamana kuma ka kasance mutumin da ake shakka duniya ta san da zamansa bawai kana namiji ka ƙare a wajan wata yarinya ba." Yana cikin wannan tunanin ya ji an ja mugun tsaki ya buɗe idanu ya ganta sosai ya buɗe idanunsa da suke a rufe kodayaushe cike da gashin idanu masu tsayi. Aafiyyah ce tsaye take kallonsa can har zata shige sai ta ce """Kai ai babu macen da zata so ka a school ɗin nan, sai dai kaga ana soyayya"" bai taɓa tsayawa ya tanka ta" "ba sai lokacin har zai mata shiru sai ya ce ""Ok"" ta haɗe fuska ""Saboda macen abinci ce ko iskar shaƙa daya zama dole Mutallab ya amfana dasu?"" Ta yi masa sheƙeƙe tana nuna masa ɗaliban makarantar da kana ganinsu zaka san iyayensu nada arziƙi sosai kowanne a cikin students ƙuruciya da tashen balaga na ɗawainiyya da su. Ta ce ""Mata ai sune jin daɗin maza, kai fa mace ko kiss bata taɓa yi maka ba a school ɗin nan"" Mutallab ya yi ta kallon ta daga sama har ƙasa ""Matar Moh zata zama mai irin halin MOH"" har ya juya sai yaga bata ci bulus ba ya tako har inda take ya zuba idanunsa cikin nata kamar yadda take kallon tsakiyar nasa idanun a karon farko yana sake matso da fuskarsa ""About the kiss, ƙilan Moh ya ji" "ƙan ki ya yi miki don naga shi kike buƙata""" Tsoro ya kamata amma ta dake ta fara ja baya ya yi saurin saka ƙata ya falleta kamar zata kifa ya saka hannu ya cafko gaban wandon uniform ɗinta ya dawo da ita dab dashi yana sauke mata numfashi a hankali kuma ya ɗora fuskarsa a saman tata yana zare glasses ɗin idanunsa sai ya ga ƙwalla ta cika "idanunta fal ta dinga kallon tsakiyar idanunsa, suk dinga kallon kallo ta kuma jan tsaki." """Aafi yyahhhh""" """Yaaa..."" Sai ta yi shiru baki ta buɗe da niyyar cewa ya sake ta sai ta ji saukar bakinsa cikin nata, ya haɗe" bakinsu waje guda. Sai kuma ranar talata. Za'a samu page 37-41 a ArewaBooks yanzu haka. MUTALLAB "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 37: Heartbreak" "He just give her a small kisses, gani ya yi numfashinta ya tafi zai ɗauke, sai ya fasa abin da ya yi niyya ya" "tura ta baya ba can ba, da ƙyar ya ce ""hmm bakin ma wari"". Aafiyyah ta miƙe da sauri jikinta na ɗan rawa, ta yi kuma ƙasa da kanta taƙi yarda ta kalle shi, shi kuma ya cake a gabanta ganin yadda take ta murguɗa masa mitsitsin bakinta ya saka kawai ya girgiza kansa tare da ɗage mata kafaɗa ya yi gaba yana abinsa" yana faɗin. """Na sha banza""" "Ta yi shiru kawai, kanta har lokacin a ƙasa, sai ya tsaya ya juyo da baya da baya yana ɗan tsalle ya dawo" "gabanta, ya jima sama da minti biyar sai ya sake juyawa ya tafi yana sake nanata mata. ""E ɗin, na sha banza"" a hankali Aafiyyah ta ja jikinta tare da jingina da jikin bango ta yi shiru, maganganun Ummi take tunawa ""Ko hannu namiji ya riƙe miki, to ya miki ciki"" hawaye masu zafi suka cika idanunta ta lumshe idanun, zafi kuma da damshin da ta ji a saman fuskarta da kuma ɗanɗano mai kama da gishiri ya gamsar" "da ita cewa kuka take yi, zafin hawayen ya sake ƙara tabbatar mata hawayen baƙin ciki ne." """Allah na tuba, wallahi shine""" "Sai kuma ta sulale a wajan tare da cusa fuskarta a tsakanin cinyoyinta tana fusgar wani irin numfashi," "bata son tunawa, bata son tuna yadda abin ya ruskeka wani sanyi-sanyi ya ji yana ratsa fatarar jikinta yana kaiwa ƙashinta hari karkarwa bakinta da haƙoranta ya alamta mata zazzaɓi ne ke shirin rufe ta. A hankali ta duba lokaci, taga an kusa tashi ma daman tuni ta daina zaman extra lessona ɗin nan gwara ta zauna a gida kawai ta yi bitar karatun yafi mata, ta miƙe tsaye bayan ta saka glasses ɗin ta nufi hanyar class ɗin ta fasa zuwa lap ɗin daman wannan shine lokacin na farko dalilin wani abu da za'a nuna musu," tunda sai sun je Ss1 kowa zai bi layin da yake buƙata domin cimma muradinsa. """Moh"" Kimiyya ya kira shi, sai ya basar da kiran duk da ya ji." """Da gaske fa an aura maka Safiyyerh wallahi ita matarka ce""" "Mutallab, ya sake yin shiru tas kuma yake jin maganganun Kimiyyar a kunnuwansa kawai he is not" "interesting anymore. ""Amma a ganina kar ku bari a gida a sani, more especially ita Safiyyerh saboda" "daddy ɗinta kaga ba zai amince ba zai iya rabaka da matarka ni kuma bana fatan abin da zai iya rabaku"" sai a lokacin Mutallab ya ce ""Hmm""" """Ba hmm, gaskiya ce ni a matsayin ɗan'uwana na ɗauke Mutallab, wallahi ban taɓa yi maka kallon aboki" "ba, ko a baya misunderstanded ɗin da muka samu laifinka ne, ka wulaƙanta ban maka komai ba, ni kuma bana ƙaunar wulaƙanci na ji zafi da gaske, na ji babu daɗi a cikin zuciyata. Jeddah ta ce mutum tara yake baya cika goma, to as a brother nake cewa don Allah ka daina wulaƙanta Safiyyerh tana tsananin son ka sosai wallahi tana maka son da ba zata iya yi maka bayani ba, da gaske nake trust me"" ya yi shiru ""don Allah Mutallab, ka gwada bata lokacinka ku tattauna wasa da zuciya babu daɗi raunin mata daban yake, koda muke yara ai wani abun mun san gaske and we are no longer a kids, beside yaran ne ma shi yaro ai" "yana son mai kyautata masa da gaske wallahi""" """Safiyyerh zata mutu ne, idan na ce zan yi soyayya da ita, ka sani""" """Ba lallai Safiyyerh ta mutu ba, idan ma ta mutu wa'adin ta ne ya cika da Ubangiji ya ɗiba mata, kuma" "kowanne bawa mai rai akwai silar mutuwarsa, ko ka ƙi ko ka so Safiyyerh cikon lissafin rayuwarka ce ka" "yi accepted nata ka amshe ta don Allah""" """I can't, Kimiyya """ """Za ka iya mana""" """Ka tsahirta mini, ka fini sanin daidai ne? Ko ka fini sanin rayuwata da kai na ne? Na san komai ina" "fahimtar komai, sai dai bada idanun da kake fahimta ni nake fahimta ba, ƙaddarar Moh bata zama da mace bace za'a dinga bi ana kashe duk wanda na nuna interest na aurenta ko wacce nake developing feelings a kanta. Rayuwata ba irin taka bace, ina da ƙalubale ina da muradan da nake son cimma, ni" "talaka ne futuk, ka sani""" """Mena na sani?""" """Ubanka ka sani, banza mayan magana kawai"" Mutallab ya yi furucin a daƙile a kuma fusge cikin ɓacin" "rai da zafin zuciya, domin gani yake kimiyya bango yake son kai shi, idan ya tuna maganganu mahaifin" "Safiyyerh ƙirjinsa zafi yake masa, shi ya sa ko da wasa baya buƙatar ya ji an ambaci sunan mahaifin nata." "Kimiyya yana ta dariya ya ce ""Kake zagina saboda ka ganka wani shirgege ko? Ni dai ba zan fasa fada" "maka gaskiya ba wallahi domin idan ban faɗa maka ba babu mai faɗa maka ba tunda ba wasu abokai gare ka ba, ni dai"" Mutallab bai ƙara tanka Kimiyya ba, suna cikin tafiya zuwa harabar makarantar Safiyyerh ta yi murmushi tana kallon Mutallab ta ce ""Na ɗauka ka tafi fa?"" Ya dube ta sai ya yi shiru ta ce ""Faɗa kuka yi ne naga yana muzurai kamar mara gaskiya?"" Kimiyya ya sake yin wata dariyar yana girgiza" kai a hankali yana ja baya ya ce. """Ce mini ya yi fa ya jima yana son ki ashe kullum da son ki yake kwana yake tashi a ran shi""" "Ta juya ta kalli Mutallab da yake dubanta ta ce ""Bestie da gaske wai? Don Allah haka ne?""" """Ƙarya yake"" Mutallab ya ce kai tsaye, ta yi murmushi kawai tana sunkuyar da kanta ƙasa tare da" "hawayen daya cika mata idanu sai ya ɗago kai ta ce ""Na sani daman"" ya juya idanunta tana ɗaga kafaɗa ta ce ""Ni dai ba ina son ka, idan na mutu ruhina ba zai barka ba, fatalwata zata dinga bibiyarka ne har sanda zaka dawo gare ni mu rayu a aljanna shikenan Ubangiji ya rama mini duk wani damuwa dana shiga" "ta hanyar sadani da kai a cikin jannatul-firdausi"" kallon tausayi kimiyya ya bita da shi sai ya juya ya kalli" "Mutallab shi bama su yake kallo ba, can kuma yaga ya ɗan cije lips kamar zai yi murmushi sai kuma ya" "tsuke fuska. ""Ni driver ya yi latti maybe na tari napep ko?""" """Aafiyyah ta rage miki hanya mana tunda a lifan dinta tazo""" """No, ai ba hanyar mu ɗaya ba""" "Suna tsaye shima kimiyya na jiran drivern gidansu, a hankali yaga wata lafiyayar mota ta shigo cikin" "makarantar da wani irin fitinanen gudun kamar zata tashi sama, Mutallab ya saki siririn tsaki, bayan motar ta shigo kuma sai ga ambulance na asibiti suma sun shigo da sauri. Wanda yake cikin baƙar motar ya fito, mutane biyu ne da MJ da wani fari tsayayye akan ƙafafuwansa, a ɗan gaggace Mj ya kalli Safiyyerh yana ƙarasawa wajan ya ce ""Safiyyerh ina Aafiyyah take? Fews minutes back ta kira ni bamu gama magana ba sai na ji ta yi shiru kuma a wayar bata katse ba, alamar numfashinta ya tsaya, so daman" "kin san bata da wani lafiya"" a rikice Safiyyerh ta fara rawa da murya ta ce" """Aafiyyah ɗin? Yanzu na fito ,""" "Wani sirrin tsaki aka je mai matuƙar ƙarfi, ta juya taga wanda suke tare da Mj ya zura wayarsa cikin aljihu" kai tsaye kuma ya fara takawa da ɗan sauri zuwa cikin class ɗin nasu Aafiyyah. """Yaya meke damun Aafiyyah ne don Allah"" Safiyyerh ta ce hawaye na sauka a cikin idanunta jikinta sai" rawa ya ke yi. """Ki yi mata addu'a, idan dokin rai ce tabbas zata rayu amma tana cikin halin jinya "" Mj ya ƙare maganar" "yana kallon Mutallab daya zuba hannunsa cikin aljihu kayan dake jikinsa yana kallon gate ɗin shigowa cikin makarantar fuskarsa a kame. Ganin ya fito da Aafiyyah rungume a jikinsa ga jini duk ya ɓata farar t.shirt ɗin daya saka ya saka cikin sauri ambulance ɗin suka fito da gadon marasa lafiya ""her bag, da sauran kayanta"" ya cewa Mj yana ɗora ta a gadon asibitin cikin sauri kuma ya tura ta ciki Mj ya dawo da sauri ya shiga cikin ambulance ɗin aka ja suka fita, shima motarsa ya shiga tare da yin reverse ya juya da" gudu ya bar cikin makarantar. "Kuka sosai Safiyyerh ke yi, Kimiyya idanunsa sukai jajur ya kasa cewa komai jin kukan na gundirarsa ya" "saka ya damƙi hannun Safiyyerh ya jata suka fice, napep ya tsara ya faɗi unguwar su Safiyyerh ya tura ciki ""Idan kika sake zuwa gidanmu sai na karya wannan sillan ƙafafuwan naki ok, kuma ki bashi kuɗin napep ɗinsa, kar ki sake kirana a waya kin ko?"" Ta kalle shi da jiƙaƙƙun idanunta sai ta yi murmushi ganin" "yadda lokaci ɗaya fuskarsa ta haɗe babu kyan gani ""E ɗin, ni dai ina son ka""" Ya yi kamar bai ji ba. """I love you, I love so much Bestien beastie, kuma sai na kira ka ɗin""" "Mai napep ɗin ya ja yana yin dariya shima, Mutallab ya bi napep din da kallo sai kuma ya shafa kansa, ya" juya ya sake kallon makarantar da kyau da kuma sunan dake zane raɗau na Federal college school FGC. * Safiyyerh na zuwa gida ta tarar da Uncle Musbah a parlo da shi da Wahee sai Ummeyh. Ta durƙusa har "ƙasa ta ce ""Uncle barka da yini"" ya yi mata murmushi ya ce ""Yawwa daughter, ya karatu""" """Allahamdulilah, uncle""" """Daman ke nake jira, amma ki fara shiga wajan mahafinki tun ki saman a nan parlo kin ji?""" "Ta jinjina kanta, jikinta ba kuzari ta ajjiye jakar hannunta ta miƙe zuwa part ɗin daddy a hankali ta tura" "ƙofar bakinta ɗauke da sallama, yana zaune akan kujera ya yi shiru idanunsa suna kallon sama ""shigo mana Safiyyerh Abdu"" ta shiga cike da tsoro ta nemi waje a ƙasa kusa da ƙafafuwansa ta zauna ta ce ""Daddy barka da hutawa"" ya yi shiru sai ta fashe da kuka ta ce ""ka yi haƙuri don Allah daddy ka yafe mini" "ka daina fushi da gudaliyarka""" """Gudaliyar dake ƙoƙarin haramta kanta dani?""" "Ta girgiza kai tana dafa ƙafarsa ta ce ""Ba zai taɓa jin daɗin rayuwa kana fushi dani ba, haka ba zan taɓa" "wanyewa lafiya ba idan ka wofitar dani, kar ka yi fushi dani daddy kai ne komai nawa, duk abin da na zama wallahi dalilinka ne, ina yi maka komai wajan kare hakƙin bibiyarka daddy don Allah don girman Allah ka bar ni da makaranta, bana so daddy wallahi bana fahimtar komai a karatun nan daddy ka bar ni na rayuwa da Bestie don Allah ka yi mini wannan alfarmar koda zai zama buƙata ta ƙarshe da zan nema" "wajanka, Safiyyerhrka ce daddy gudaliyarka, jaririyarka, ƴar gidan professor Abdu ɗin nan""" "Tunda ta fara magana daddy ke kallon ta, ya haɗe hannayensa biyu waje guda yana kaɗawa idanunsa" "sun yi jajur a hankali ya ce ""Tashi ki fita """ """Ba zan iya barin wajan nan, zuciyata zafi daddy ba zan iya jurewa ba, na kasa, na kasa""" """Safiyyerh wannan yaron yana baki abu a waje kina sha ko ci ko? Ya miki asiri kin shanye yanzu yake" "ɗawainiyya dake?""" """Daddy bestie bai mini asiri ba, koda ya yi mini na yafe masa wallahi duniya da lahira na yafe masa ai ina" "son shi, kuma babu kyau mace tana yi wa mijinta mummunan zato kar ka saka na ɗauki zunubi don Allah"" ta ce cikin fitar hayyaci ƙirjinta na ɗagawa sama-sama. A harzuƙe daddy ya miƙe tare da yin kanta zai daka Uncle Musbah ya yi saurin riƙe shi, ba tare ya ce komai ba ya kama Safiyyerh suka yi waje, kai tsaye upstarts suka nufa inda ɗakinta yake. Ganin sun fito haka ya saka Ummeyh miƙewa ta nufi wajan daddy ta same shi a tsaye idanuna jajur a kiɗime ta ce ""Prof ba dai Safiyyerh kakewa kuka ba? Ba dai" "wannan hawayen dominta yake zuba ba?""" """Ya kike so na yi idan ban yi kuka ba Dr? Wacce kalar jarrabawa ce wannan tsinannen yaron MUTALLAB," "tsakanina da shi Allah ya isa ban yafe masa ba wallahi, Allah ya isa"" ya zube saman kujera yana dafe kansa, Ummeyh ta ce ""Me zai hana ka aura mata shi? Ko dan samun nutsuwar zuciyarka Prof dani kai na wannan issues ɗin Safiyyerh gab yake da sawa zuciyata bugawa"" ta faɗa a raunace, tana zama kusa da shi cike da damuwar data gama addabar zuciyarta, ita yanzu tsoro abin ke bata wallahi ta gama dawowa" daga rakiyar yaran yanzu. """Dr, bawa Safiyyerh Mutallab idan bai zama sanadin barina duniya ba to zai zama silar mikin da zai iya" "ajalina komai jimawa, idan ya zama auren take so lallai sai na bata wannan yaron Captain da yake son ta, ko na bata auren Nahyan ɗan wajan Wasim""" """Kana ganin zata amince?""" """Innalillahi wacce kalar jarrabawa ce? Yaron nan anya ba wajan yan hisba zan kai shi a yi masa nasiha ya" "kunce asirin da ya yi wa Safiyyerh ba? I need my Safiyyerh back, wannan ba Safiyyerh ta bace, ba haka Safiyyerh ta ya kamata ta kasance ba"". Ummeyh ta girgiza kai ta ce ""I don't think hakan zai zama daidaito, idan ka kai shi hisba ko kana so ko baka so sai sun ɗaura mata aure da shi ai, saboda za su tuhumeka da laifin child abuse da physical violence a part from violence against women. Prof as a mother nake maka wannan maganar don Allah ka sakko da zafin kanka ka aurawa Safiyyerh yaron nan, let bygone be" "bygone don Allah bana son wani abu ya samu Safiyyerh at first na ɗauka iskanci ne""" """Na aura mata ɓaraho? Mai kashe ƴan'mata? Gawarta kike so a kawo mini ko mene Dr? Sau biyu fa yana" "zuwa state cid? Sau biyu""" "Ya girgiza kai ya ce ""I don't think, i am going to do this, ina son Safiyyerh I'm not ready to lose her""" """Ka san soyayya a zuciyar yaran yanzu? Ka san yadda suke ɗaukan al'amura da zafi?"" Cikin ɓacin rai" "daddy ya nunawa Ummeyh ƙofa ya ce ""Take your time, leave please wallahi gwara ta mutu dana aura mata Ɗan'malam kin ji na rantse miki da girman Allah""" "Miƙewa ta yi jiki a sanyaye, bata son yin jayaye da mijinta akan ƴar su, yin jayayya tsakanin yaro kan iya" zama silar da yaron kan koma wajan Ubangiji. "A can ɗakin Safiyyerh bayan Uncle Musbah ya rarrashe ta ya ce ""Daughter mu yi magana ya fahimta, da" "dai na san karatu kike yi of course, kuma kike fata ki zama abin da kike da muradin zama ya aka yi kika" "sauya ra'ayi lokaci guda bani labari"" Safiyyerh ta durƙusar da kanta ƙasa tana hawaye sosai ya kamo hannunta ya ce ""Ni ai abokinki ne tun ba yanzu ba, zan yi ƙoƙarin ganin na aura miki Mudallabin naki""" """Promise me uncle""" """How? Ta ya ya zan yi promise naki bayan ba ki faɗa mini ba? You first sai ni kuma """ "Ta yi jim, sai kuma ta ce ""Uncle ina son irin rayuwar da dady da Ummeyh suke yi nake gani, hakan yana" "mini daɗi ina jin nutsuwa a raina sosai, idan naga daddy yana kissing Ummeyh sai na ji dama ni ya kewa, idan na ga ya rungumeta sai na ji dama ni ce, kullum da daddare idan Ummeyh ta shiga ɗakin daddy bata fitowa, i heard her voice tana screaming all the day at the night, sai na dinga jin daɗin ihun da take thinking me daɗi yake mata haka take ihu, sai na ɗauka faɗa suke ko dukanta ya ke yi, na dinga kuka ina dama zan iya taimakon Ummeyh. Ranar daya zama ma fahimci cewa ba dukan Ummeyh ya ke yi ba wani abu nada ban, ranar da Ummeyh ke faɗawa Anty Maryam cewa kaya sun yi Prof yana ta murna idan akwai wani kayan for sex she need more. "" Kasa cigaba ta yi da maganar ta fashe da matsanancin kuka" "sosai, ta kasa kallon uncle Musbah saboda wani irin kallo da yake binta da shi with shocked." "Da ƙyar ya tattara nutsuwarsa wajan ƙarfafawa kansa qwwia ya ce ""Ina jinki"" ta ce ""I was thinking, mene" "sex da zai saka a dinga ihu? Sai na ɗauki wayar Ummeyh na fara searching na rubuta sex with daddy and Ummeyh, sai aka nuna babu, sai wasi bidiyos, na dinga searching domin a tunani iya su Ummeyh ke yi kawai shi ya sa ban amince na duba ba, daga baya ranar da bani da lafiya Ummeyh ta ce na ɗauka a ɗakin daddy saman kujera, cikin bacci na ji wannan ihun na farka ina dashi shine shine shine. ,"" jikinta" "ya dinga wata tsuma maganar ta tsaya mata da ƙyar ta ce ""I see them.... I see them Wallahi i see them" "uncle"" ta ce tana rushewa da wani irin firgitaccen kuka da ihu ta miƙe tana zabura za ta yi waje." Da sauri uncle Musbah ya riƙo ta ya janyota jikinsa ya rungumeta sosai idanunsa jajur hawaye na "sakkowa daga ciki, ashe sune suka lalata yarinyarsu sune suka bata damar yin abin da take yi. sune suka rusa ɗan ƙaramin tunaninta tare da gina mata sabon tunanin daya haifar mata da balagar zuciyar dake neman sawa ta kangare musu, daman shi yaro idan ya yi abu aka bi diddigi yana da dalilin yinsa. Hawaye" ya dinga zuba daga cikin idanunsa. Ba zai so ƙarasa jin wannan bayanin na Safiyyerh ba dake neman tarwatsa masa zuciyarsa a hankali ya "zaunar da ita ya ce ""Ki yi haƙuri, zan dawo gobe kin ji?""" Ummeyh dake laɓe a jikin ƙofar tana rusa kuka ta rufe bakinta da hannu alamar ta gama jin komai ta yi saurin barin wajan jin uncle Musbah zai fito. "Uncle Musbah ya dinga kallon Prof ya ce ""Zan wa Safiyyerh aure in sha Allah, in sha Allah""" """Ba dai Safiyyerh ƴar Professor Abdu ba, idan ita ce kada ma ka fara wallahi wallahi Musbah""" """Yaya, wallahi sai na aurar da Safiyyerh ka zuba idanu ka gani""" Yana cewa haka ya fice daga cikin gidan ransa a mugun ɓace. * "A gidan Malam Abdullahi, tunda Mutallab ya shiga da magariba ya fita sai yanzu na a shigo wajan ƙarfe" "tara, cak ya tsaya ganin ana zuba dambe tsakanin Mama Zaituna da kuma Inna Binta sun yi wa jikinsu ado da miyar kuka. Mama Zaituna tana nishi ta ce ""ai bake kaɗai bace mai rai a cikin gidan nan, gabaɗaya garin tuwon guda nawa yake? Da zaki mulmula sharɓeɓiyar kwasa ki kai ɗaki wato mu da" "ƴaƴanmu kuma yunwa ta kashe mu ko?""" """Ohho muku, ni dai ba zan yi zaman yunwa a cikin gidan nan ba wallahi tuwo kuma kowa ya ci da haƙuri""" "ta ce tana ƙoƙarin kwasar miya ta watsawa Mama Zaituna, cikin sauri Mama Zaituna ta kauce miyar ta" sauka a fuskar malam zuwa jikinsa gata da zafi a firgice ta ce. """Ba shakka Binta, ba ki san gidan Malam Abdullahi ba ko?"" Ya yi ƙwafa ya juya ya shiga ɗaki." """Ko na sani ko ban sani ba, wallahi ni dai ba zan zauna da yunwa ba daga zuwana na fara kwana da" "yunwa? Ban saba ba wallahi sam ba zan iya ba""" "Da gudu ta yi ɗaki ganin malam ya fito ɗauke da bulala, ta yi cikin ɗaki ta rufo Malam ya zararawa Mama" "Zaituna bulala a gadon baya, ta gantsare ta ce ""Washh bayana wayyoo bayana"" ta faɗa tana murza wajan ya ƙara cauɗa mata ta zurbaya tana sakin kwanan biyar ya kife a wajan ta yi ɗaki da sauri. Ya juya ya kalli Mutallab da yake tsaye idanunsa ya ƙanƙance wai akan abinci ake duka wannan tashin hankalin? Ya lumshe idanu idan yaga ana haka Muneeberh yake tunawa, ta mutu saboda yunwa saboda gazawa" "irin ta mahaifinsu. ""Kai fice ka bani waje ɗan asara haihuwar asara""" """Kun iya haihuwa Aby, tunda kun haifi irin Mutallab, kun haifi asararre irin Moh""" """Matsalarka ce, ai na gamawa sallamawa duniya kai, ka fice ka bar mini gidan nan ai na hanaka shigowa" "gidan nan muddin dare ya yi ka kusa daina shigowa gabaɗaya ma, in daina arba da baƙin cikinka"" Mutallab ya girgiza kansa cikin ɗacin rai, idan ya yunƙura sai kunamar hannunsa ta kumbura yana ɗaga hannunsa kuma tsaf zai iya cillawa Aby ita, don a fusace yake sosai. Da ƙyar ya ja numfashi ya tsaya masa" "a ƙirji ya ce ""Abinci zan amsa""" """Ba uwarka Ammo bace ta fita ta nemo kuma wallahi ba zaka ci ba koda kuwa nata ɗinne fita""" """Aby... Aby... Aby"" ya ce sai kawai ya juya ya fita daga cikin gidan." "A waje ya tarar da mutumin da yake jiransa, ya ce ""Ganinka sai an cike form yau dai finally gaka""" "Mutallab ya shafa kansa bai ce komai ba, shi kuma ya ce ""Allahamdulilah aikin da ka yi, ya yi kyau sosai kuma mun ji daɗinsa sosai ka ji? Yanzu ma wani aikin muke buƙata akwai kuɗi kimamin miliyan biyu da" "aka bani na baka kyauta ne kawai""" """Hmm""" """Yes, kuɗinka ne""" """Ban san yadda zan yi da kuɗin ba"" ya ce seriously." """Idan kana buƙata zan saka maka kuɗin a hannun jari duk sanda kake buƙata sai ka kira ni na baka su," kaga kafin nan kuɗin zai haɓaka sosai ko? And zanna kawo maka mutane tunda na gamsu da aikin naka "ƙwarai da gaske""" "Ya jinjina kai kawai, yana danna waya abinsa mutumin ya ce ""Ka bani numberka""" """No, faɗi taka""" "Ya fara faɗa masa ya ce ""To baka rubutawa ai?"" Ya zura wayarsa cikin aljihu ya ce ""Ba buƙata, Moh baya" "mantuwa na haddace, aikin idan na yi zan kira ka"" bai jira ya kammala magana ya shige shagon Goje ya" rufe ƙofa yana jin duk jikinsa wani iri. "Shirin kwanciya ya kammala, daga shi sai three qauter, ya tuna shekaranjiya Safiyyerh ta bashi abu a leda" "ashe kaya ne riga guda biyu, sai armless da wando na ya ji daɗinsu domin baya dasu amma ko godiya bai yi mata ba. Ya lumshe idanunsa sai ya ji tsigar jikinsa na tashi, sai bakin Aafiyyah ya dinga dawowa cikin idanunsa, shi bai san me ya yi ba, bai kuma san sunan abin da ya yi ba, kuma bai san ya aka yi ya yi, bai kuma san mene ya ja ra'ayin nasa ba, ya samu kansa kawai da sanya bakinsa cikin nata, ya samu kansa da tsotsar lips ɗinta. Ya takure waje guda ya rungume hannayensa a ƙirji saboda abin da yake ta dawo masa cikin ƙwaƙwalwarsa sai ya ji kuma mararsa ta kumbura kamar dai tana masa ciwo ""What is this" "please?"" Ya ce a cikin ƙirjinsa." "Again, secret love ɗin daya ƙara gani yau bai samu damar karantawa ba ita ya ɗakko ya buɗe a hankali ya" fara karanta zubin tsattsaren handwritten ɗin with style and passion ya jinjina iyayin Safiyyerh ainun. "“I LOVE YOU, FOREVER ”" Me ya sa? Why? Wannan magana ce daga idanun zuciyata zuwa ɗaya zuciyar tawa data sauka kai tsaya "zuwa cikin masarrafar tunanina. Tsaya ka ji abin dariya Yaa Muhammad, sunanka yana mini tsananin kwarjini da wahalar faɗa, kallon ka is my favourite thing, bana gajiyawa domin hakan shike samar mini da nutsuwa, irin nutsuwar dake riƙe ni zuwa kwana da wayewar gari kafin na ƙara tozali da kai. Ka ji" maganar da zuciyata ta yi; "My heart. Ta ce; dana ganshi sai na ji na kusa suma, daya sake murmushi yana kusanto ni sai na ji na" "sake mutuwa a kan shi, kullum ƙara mutuwa nake ina dawowa da muradin na yi rayuwa tare da inuwar Yaa Muhammad. Motsin da zuciyata ta yi sanda ya kira sunana na tuna ashe akwai halitta a ƙirjina bayan ni. Na dinga kallonsa ina jin gaɓɓan zuciyoyinmu na haɗe wa waje guda suna matse kan su, sai na tuna ba yanzu ba, akwai sauran dama, akwai sauran ƙalubale a tattara dani da Yaa Muhammad ɗina ɗan" baƙin Muɗallabina. "Yaa Muhammad, ka riƙe mini alƙawari i will come for you, zan bayyana a gare ka. Don Allah ka yi mini" "alƙawari da alfarmar gina kan ka, ai dai kaga zaka so na yi farinciki ko? To ka yi ƙoƙarin zame babban mutum, daman can Yaa Muhammad ɗina babban mutum ne, na hango zallar soyayyata a cikin idanunka sai hakan ya ƙarfafa mini qwwia wajan rayuwa dominka zan ta kokawa da numfashina, soyayyarka da numfashina za su zama maƙiyan juna a ƙirjina. The one thing you have to know is I will never stop loving you, no matter what happen, no matter how bad you treated me. Akwai wani abu game da son da nake maka da yake sani jin cewa da son ka aka halicce ni. Like, how could I be able to love someone so much non-stop? Yes! I love you Yaa Muhammad, Ubangiji ya kula da rayuwa ya ji ɓanci al'amuran rayuwarka" "ya haskaka zuciyarta, ka yi ta cin abinci ka zama ƙatoto yadda zaka iya goyani a bayanka, ka zama ƙatoto yadda zaka iya riƙe ni idan mun haɗu na samu damar yin kukan dana jima ina tara maka, ya baka haƙuri jure rigimata da shagwaɓata, Allah ya hure maka kuɗi na halak da zaka dinga siya mini chocolate, I love" "chocolate sosai Yaa Muhammad, laaa kalli bayanka"".." A firgice ya duba bayansa yaga babu komai sai ya ɓata fuskarsa irin bai ji daɗi ba yana duba wasiƙar daga "can ƙasa yaga ta saka alamar emojin na gwalo ta ce ""I jin daɗin tsokanarka sosai, ka duba bayan wasiƙar" "akwai certificate of birth ɗina ka ta ya ni murna ka mini addu'""" "“You are mine, and i am urs”" "Ya ajjiye paper ɗin ya ce ""If i catch you, ummmm, zan rama"" sai ya ji abin da yake ji game da saƙwannin" "yana ruɓanya kansa da kansa, wani abu mai kama da shiga soyayya wani abu kamar da kewa irin kewar da ya ji a lokacin da Muneeberh zata barsa, irin abin da ya ji a lokacin da yake rasa Jaanah, but; sai abun ya yi addition kansa a tsakiyar ƙirjinsa ya ninka sau duba akan yadda ya ji a kan nasu, bugun zuciyarsa ya" "ƙaru saboda wasiƙar nan, bugun zuciyarsa ya ƙaru saboda Safiyyerh ɗiyar Professor Abdu." * Fitowa ya yi da sauri ya ci karo da Ummi kamar ƙaramin yaro haka ya riƙe Ummi tare da fashewa da wani "irin kuka jikinsa na rawa, Ummi ta riƙe shi da kyau ita kanta nata jikin rawa yake yi ta ce ""Safiyyerh? Safiyyerh? Safiyyerh ko? Ya kasa cewa komai, ta sake shi tana cewa ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"" ta ce a rikice." "Da sauri kuma ya saki Ummi ya koma cikin room ɗin, a lokacin an jona mata wani machine an saka mata" "robar hanci ga wasu likitoci biyu a kanta ɗaya na danna mata abin da zai ɗago da numfashinta amma gabaɗaya abubuwan basa responding treatment ɗin, numfashin ya riga da ya tafi, dole sai an yi wata" "hikimar wajan motsa zuciyarta. Yana tsaye daman tunda suka shigo asibitin, ya durƙusa daidai kanta ya" "kama hannunta ya riƙe cikin nasa, a hankali kuma ya ɗora ɗaya hannun a saman sumarta ya dinga shafawa ya zubawa fuskarta idanu, sai kawai ya sake ta tare da barin room ɗin, suka ci karo da Mj, Paaah daman kamar statue haka ya zama dukkan jikinsu kuma sanye da green riga, da sauri Mj ya dawo kusa da ita ya riƙe hannunta can ƙasa daga shi sai ita ya fara mata magana ya ɗauki mintuna yana magana sai yaji ta motsa hannunta da suke cikin nasa, a hankali hawaye ya fara bin gefan fuskarta da hannu ya yi wa likitocin alama cikin saka suna sakawa ta ja wani numfashi mai ƙarfi ta sauke tana sake riƙe hannun Mj da sauri suka sanya mata oxgeyn nan suka buƙaci Mj ya tashi ya fita, Paaah yaƙi barin wajan gani yake yana fita Safiyyerh zata cika to kuma an ce mutuwa tana jin kunyar idanun iyaye zai jira har komai ya" daidaita. * "Washegari Aafiyyah babu ita a makaranta, har tsayin kwanaki biyu curr, suka ci-gaba da zuwa makaranta" har suka fara exam na frist term. Ranar ƙarshe suka shirya class party. "Kowa was happy, musamman Safiyyerh, Aafiyyah ta sake zama so silence kuwa ya san bata da cikakkar" lafiya an ce Limoniya ke damunta sai ta yi musu addition da tayfot. Students ne an cika sosai saboda class partyn da ake yi na kammala exam maza da mata babu teacher ko ɗaya tunda ta shigo hall ɗin makarantar tasu take duban inda zata ganshi. Cikin sa'a ta ganshi yana zaune saman window sanye da gajeren wando fari tas sai armless ɗin riga wacce duk aka yanke hannunta gashin kansa rabi a aske ya zubawa wani tafkeken gidan masu kuɗi idanu ta waje baya ko ƙiftawa kamar an ce ya juya ya ganta tsaye ta zuba masa idanu yaja tsaki kafin ta yi magana an shigo an "ce ""Mutallab, principal yana nemanka an kai ƙarar ka wai kana son Fiyya""" """Wacce Fiyya?""" """Aafiyyah, ka cire Aa da h na sunan zai baka Fiyya in short""" "Ya ware idanu abin da bai taɓa zuwa tunaninsa ba kenan sai kuma ya cije baki ""Shi principal ɗin ubana" "ne Malam Abdullahi kenan?"" Ya juya ya kalleta sosai ya ce ""Sai godiya, ni? Kuma ke hauka kenan"" ya ce yana dirowa" Aafiyyah ta dinga jin zafi a zuciyarta haka kawai daman ta ji bari ta tsoka ne shi kafin a tafi hutun makaranta ta ce. Ya dinga mamakin wannan sharrin har ina kuma? Yaushe aka yi? """Kai ne mahaukaci"" furucin ya fita daga bakin Aafiyyah ""Kuma na yi maka nisa, kasan yadda nake da" "masoya a makarantar nan amma ni ubana ba soyayya ya kawo ni ba, karatu zan yi ina da buri mai faɗi da zan cimma"" Ya miƙe tsaye yana kallonta daga sama har ƙasa a ransa yana ƙissima abu ""Shi uban naki can ta matse masa, karatun banza kawai ka zama mai iko shine"" ""Ba dai ubana sai dai "" Ta yi niyyar cewa," sai ta yi shiru. Ya buɗe idanu sai kuma ya fasa abin da ya yi niyya ganin hawaye a idanunta abin da bai taɓa gani ba. Da sauri ta fice daga hall ɗin ta zaga baya ta durƙushe a wajan tana fashewa da wani irin kuka kamar zata haɗiye zuciya a hankali ta yi magana wanda ita kaɗai ta ji me ta ce. Aka sauya musu tsarin cewa sai an dawo hutu kowa zai ga result nasa hakan yama Safiyyerh daɗi akai hutu ana kewar juna. * "Sun cimma sati biyu, Safiyyerh zaune a parlo ta rame sosai an hanata fita ko'ina ta shiga damuwa." "Wayarta ya fara ringing ta duba sai taga number Aafiyyah ta ɗauka ta kai kunne a hankali ta ce ""Ok gani nan""" """Ina zaki?""" """Aafiyyah ce take jira na a waje""" """Ita ba zata iya shigowa ba kenan?"" Cewar Ummeyh." """A'a Ummeyh, kin san ai tana zuwa ba'a fiya barinta fita bane, kuma yanzu ba ita kaɗai bace she told me" "cewa daga nan airport za su shige yanzu zan dawo""" """Five minutes""" "Da sauri ta ɗauki mayafin abayarta ta saka, ta jin cewa ta samu wata dama ta zuwa wajan mijinta, ta" "saka flat takalmi ta yi waje. Ta ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin ta fita, wata ash ɗin mota ta gani a ƙofar" "gidan can aka buɗe ƙofar bayan motar ƙafarta ko takalmi babu, haka Aafiyyah ta fito daga cikin motar." "Abin da ya bawa Safiyyerh, ganin robar hanci a cikin hancin Aafiyyah duka hannayenta biyu kanuna ce a" jiki ɗayan na ɗigar da jini da mamaki ta ce. """Aafiyyah daga ina kike haka?""" "A hankali ta ce ""Asibiti, an Please Safiyyerh alfarma za ki mini na san dai zai miki wahala kuma za su ki ji" "wani iri, duka mu biyun babu yadda muka iya ne"". Aafiyyah ta ce a hankali, numfashinta na yin sama." """Aafiyyah alfarma ta mece? Wacce irin alfarma ce da zata saka ki fito daga kan gadon asibiti a wannan" "halin da kike ciki?""" """Gidansu Yaa Muhammad za ki raka Ni, shine alfarmar""" Gaban Safiyyerh na faɗuwa sosai ƙirjinta na bugawa ganin da ƙyar Aafiyyah take iya magana ta ce """Wanne Muhammad? Waye Yaa Muhammad kuma Aafiyyah?""" """Ohh no, Mutallab nake nufi """ "Sai walwalar fuskar Safiyyerh ta ɗauke, wani abu ya tsaya mata a maƙoshi ta kasa magana sai kallon" "Aafiyyah da take yi cike da mamakin jin wai gidansu Mutallab take so ta raka ta, ko ta yi mata kwatance. ""Uhm Safiyyerh kenan, Kimiyya baya nan, wayarsa a kashe bana jin a nan ya yi hutu nima yau zan bar ƙasar, i will the country Safiyyerh, ki raka ni gidansu Yaa Muhammad ko ki bani address zan yi following map zuwa direction ɗin, i need to talk to him please"" Aafiyyah ta ce tana riƙe ƙirjinta sai kuma ta matsa" ta jingina da jikin bango saboda jirin da take ji. "Safiyyerh ta ce ""Gashi nima ban san gidan nasu ba"". A hankali Aafiyyah ta ce ""His number?""" """Shima babu kam""" "Aafiyyah ta yi murmushi ta san Safiyyerh is lying to her ta ce ""Safiyyerh idan kin ƙarya ina ganewa, me ya" "saka a rayuwa kika kasance me son kan ki ne? Me ya saka kika zama selfish ne all the time? Duk kara da kawaici da na yi miki akan Yaa Muhammad ba ki gani ba? Ba ki ji cewa kina yin ba daidai ba. Ni ba wannan ba, ki taimaka mini ki tausaya mini ki kai ni wajan yau Paaah zai ɗauke ni daga ƙasar nan, babu wanda ya san na fito daga cikin asibiti sai driver, ki duba ko takalmi babu a ƙafata, ki duba ko abinci bana ci sai ta cikin roba ake saka mini. Safiyyerh don't do this to me, kin san ina son Yaa Muhammad kin sani" "Safiyyerh kar ki raunata mini zuciya ki bar ni da jinyar da nake""" "Safiyyerh ta gyara tsaiwa ta ce ""Aafiyyah kenan, ni za ki duba ki cewa na kai ki wajan Mutallab? Bayan" "kin fi kowa sanin wahalar da nake sha a kan shi?""" "Aafiyyah ta ce ""Safiyyerh ai ban hanaki kula Yaa Muhammad ba, sai dai kiwa kan ki hisabi nima ki mini," "kafin ki fara ganin Yaa Muhammad ni na fara, ba wai a makaranta ba, i saw him, na ganshi yana ɗaukan bulo, na ganshi yana kwasar bulo da hannayensa, a lokacin har bidiyo na yi masa, if you like i will send it to you. Still, again kafin ki ganshi ko a makarantar nina fara ganinsa ranar weekend sun shigo da Kimiyya, sanda kikai mini maganar cewa kin faɗa soyayya i ask you waye? Wa kike so, kika ce mini not today not tomorrow za dai ki faɗa mini, i told you ina da abin da zan faɗa miki, kin tuna a washegari dana same ki na faɗa miki cewa nima na faɗa soyayya da wani? Kin tuna da na ce miki ba kowa nake so ba sai Yaa Muhammad, na ce miki Mutallab nake so? Kinga kenan na riga ki ganinsa kuma na riga ki fara son shi""" "muryar Aafiyyah har rawa take yi, ta sulale ƙasa ta zauna don bata ji zata iya ci-gaba da tsaiwa." """Safiyyerh kar ki mini haka, ba zan ji komai don ya kula ki ba, duk da ya kamata na jin, ina ɗauke miki kai" "ina miki kawaici ina avoiding kai na a duk inda yake a kuma duk inda zan iya ganinku, ya kike tunanin sanda zan ji da kika ce masa kina son shi bayan kin san ina son shi? Me ya saka ban miki complain ba, saboda bani da wani ikon yin hakan bai san ina son shi ba, kuma ban isa na hana zuciyarki son shi ba, shima ban isa na hana shi son ki ba, sai dai a kodayaushe kwafsawa kike, kina ta ɗaukan carryover wajan nuna masa soyayya. Still Safiyyerh kikai mini message na cin mutunci, ban ji haushi ba, still kuma kika nemi alfarma wajan na je wajan shi na ce masa ya so ki, wallahi Allah da zuciya ɗaya na ce masa ya so ki," "kuma ina da confidence ɗin cewar ya sauya miki kuma ya fara son ki""" "Wayar Aafiyyah ce ta fara ringing, ashe ta taho da ita number Paaah ta gani ta ce ""I told you ina son" "Mutallab, na faɗawa Kimiyya ma duka kun san komai, this is the right time daya kamata ya sani""" "Safiyyerh idanunta ya cika da hawaye ta ce ""Aafiyyah sunanki ko? Ban san gidansu Mutallab ba, kuma" "bani da numbersa me ya sa tun farko ba ki faɗa masa ba? Kuma a yanzu ba zai taɓa son ki ba wallahi domin ni da shi miji da mata ne"". Aafiyyah ta ce ""Ba za ki gane ba, ina da dalilin ɓoye masa, kuma wallahi zai so ni zai ƙauna ce ni, Safiyyerh kalli kiga, duk wata wasiƙa da kika gani a nan wajan yana da irinta a wajansa, nina yarda duka mu biyun mu yi soyayya da shi ya kuma aure mu, don Allah kar ki cutar dani Safiyyerh, idan na bar ƙasar nan ban san yaushe zan dawo ba, ina son yin magana da shi nasan idan na yi magana shi zai jira dawowata komai nisan shekarun da zan yi, amma za ki cutar da zuƙatanmu ni da Yaa" "Muhammad""" """Me kike so na miki Aafiyyah """ """ I can kneel down on my feet, zan roƙe ki da ki kai ni wajan shi ne""" """I am sorry ban sani ba""" """Ok, ok babu damuwa ga duka wasiƙar ki ce masa saƙo ne daga wajena ni Aafiyyah, ki bashi ki ce secret" "love message ɗin nan ni nake masa, wallahi wallahi kika faɗa nasa da kasa zai neme ni, na rubuta number waya a jiki""" "Jikin Aafiyyah na rawa tattare wasiƙun ta bawa Safiyyerh, ta ɗauki number waya daban ta sake bata, a" "lokacin wayar Aafiyyah sai ringing take daga nan kuma su kaga mota ta faka a gabansu Mj ya fito da sauri, ganin Aafiyyah na tari jini na fita ta cikin hancinta ta ce ""Safiyyerh Please, don girman Allah ki bawa Yaa Muhammad ki faɗa masa ni ƴar ce nake son shi, masoyi baya taɓa zama masoyi sai ya zama majanuji """ "Luu kuma ta tafi zata faɗi, Mj ya ɗauke ta cak ya saka ta a bayan mota yana kiran number Paaah, kai" tsaye kuma airport ya nufa da Aafiyyah. "Safiyyerh ta lumshe idanunta, hawaye na sauka idanunta da sauri kuma ta yaga number wayar da" "Aafiyyah ta bata tare da tura ta a baki ta taune. ""I am sorry Aafiyyah, goodbye Aafiyya""" "Kamar anjefo shi haka taga Mutallab tsaye a gabanta, sai taga kamar an ƙara masa girma hannunsa duk" "a cikin aljihu daga shi sai armless da gajeren wando. ""Daga ina kai kuma?""" """Gida""" """Wajan wa ka zo?""" "Ya miƙa mata chocolates ɗin hannunsa ya ce ""Na fara aiki domin siya miki chocolates"" ta dinga kallonsa" "sai kuma ta yi murmushi ta ce ""Nima ɗin wajanka zani ai, ƙila yau ka so ji na gaji da ajjiye copyn wasiƙun" "da nake maka kodayaushe""" "Da ɗan sauri ya buɗe ido, yana amsar takardun yana duba, exactly, the same iri guda ne dana wajansa ya" "ɗaga idanunsa ya duba ta, ya sake duban takardun muryarsa can ƙasa ya ce ""Are you sure about this" "fiyyya?""" """Very sure ma""" "Sai ya ajjiye su cikin aljihu yana binta da wani irin kallo can taga ya yi murmushi ta ce ""mene?""" """No more secrets, gani, gaki ba ɓoye ɓoye"" ya ce yana matsawa kusa da ita ""Ni ne baƙi ƙatoto ko?"" Ta yi" "saurin kallon shi kafin ta yi magana ya janyota da hannunsa kusa da shi ya ɗora bakinsa a kunnenta ya ce ""kin yi ƙoƙarin sato zuciyar Moh, na dai sha mamaki ba ki da halayyar zama matar Moh, amma Moh ya yaba da rubutun naki""" "Za ta yi magana ta ji ya rungumo mata jikinsa yana mata murmushi ya ce ""Matata""" Mu tara ranar talata. Akwai page 42-43 a Arewabooks. Paid book. 08164069385 "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 38: Deep Friendship" Not edited "Ganin ta manne da ƙirjinsa ya saka ya ɗan zame, zata faɗi ya ɗan tare ta yana tsattsare ta da manyan" "idanunsa, yana ƙoƙarin fahimtar ta, ya ɗage kafaɗa ya cije lips yana bin gidansu Safiyyerh da kallo, itama kalla take kafin ta ce." """Me kake kallo?""" "Ya ɓata fuska, sai ya ce ""Gidan jinin ƙaruna da hamana"" ya ce ba tare da shakka ko tsoro ba. Sai Safiyyerh" ta ji babu daɗi ta ce """Babana ne fa? Shi ɗin babana ne bestie ba kyau ka daina""" """Ok, ni daga sama na faɗu duniya kenan? And waye ya ce ba babanki bane, ubanki ne mana""" """Zagina kake yi? Duk saboda na ƙauna ce ka ne? Duk saboda ina son ka? Ka mini komai amma ka daina" "taɓa ƙimata ta hanyar aibata iyayena, ina son su, sune suka haifan, suka kula dani har na kawo yanzu da" "nake gabanka""" """Kuma suka ce kina bibiyar namiji?"" Ya ce yana ƙanƙance jirkitattun idanunsa, wanda suke mata tsananin" "nauyi a ƙirjinta, suka farraƙa duk wata ƙiyayar da ta yi niyyar yi masa, suke hana zuciyarta jin haushinsa all the time. Ta yi ƙasa da kanta idanunta na cika da hawaye, ta ji inama a yanzu farat guda ta ji zuciyarta" "ta yaye daga ƙaunar da take wa Mutallab, ta ji inama hijabin ƙaunarsa ta yi ƙaura daga cikin zuciyarta," "inama Ubangiji ya dasa mata ƙiyayyarsa mai tsananin zafi, but how? Sai tafi ci cutuwa, bata ƙaunar ko a" mafarki taga fushinsa balle ta ji sabon halitta a zuciyarta mai kama da ƙiyayya. "Jin ya yi shiru, ya saka ta yi murmushin nan nata mai kyau ta ce ""To bani wasiƙun""" """Uhmm""" """Please bani, ai kana da irin su""" """Ƙwaci, ki ƙwata Safiyyerh""" "Ta girgiza kai tana ta murmushi ta ce ""A'a yi haƙuri, Allah Ya baka haƙuri ka ji?"" Muryarta a raunace ta yi" "maganar, domin da gaske tana buƙatar wasiƙun tana son jin me Aafiyyah take faɗa masa da zafi haka" "har take da ƙarfin quiwa haka, har take da confidence ɗin cewa dole zai so ta, har take proud da kalamar tilas zai so ta, she want to know." "Ya miƙa mata hannu yana kallon fuskarta. Ta ce ""Me zan baka?""" """Abin da na ba ki""" """Ban san me ka ban ba"" ya yi mata shiru kawai ganin bata fahimtar yaran nasa." """A'a ka yi haƙuri, ai ban gane ba""" """Safiyyerh!"" Ya kira ta a dame, cikin wata karayayyiyar muryarsa. Ta ce ""Na'am "" ya dinga kallon ta sai" "kuma ya ce ""I hate this, I hate that, I hate it idan kika ce yi haƙuri, ke ba za ki faɗa mini magana mai zafi" "bane? Ba za ki iya ramawa bane? Haƙurin gundurata yake, damuna yake, ci mini zuciya yake, ki daina da" "gaske ki daina bana so""" "Ta kalle shi da damuwa ""yanzu haƙurin ne ya zama illa wajanka da abin assha? Kai ɗin ai mijina ne, idan" "ban baka haƙuri ba sai mene zan baka?"" Sai ta ji zuciyarta na rawa, irin rawar da jikinta ya ke yi, shakka da tsoran shi suka dinga dira a zuriyarta suka yaɗu tare da bin jini da jiyiyon jikinta, ya sauka a ƙwaƙwalwarta, ta hanyar gina mata sabon tunani, tunanin yadda zata rayu dashi, tunanin yadda zata" "zauna dashi matsayin mata da miji, tunanin yaushe ne zai so ta? Ko dai bata da wani rabo ne." """Bani""" """Me zan baka?""" """Ohhh!"" Ya ce kawai." "Chocolate ɗin hannunta ya ƙwace ya buɗe, a hankali ya gutsira ya tauna a hankali sai kuma ya jinjina," "hannunsa ya miƙa mata ta amsa, sai ya bita da kallo a hankali ta miƙa chocolate ɗin bakinta daidai inda ya gutsira, ta ɓata fuska ainun da ta ji kunnenta ya motsa, bata dame ta ba, bata son chocolates." """Bana ci"" ta ce tana miƙa masa." "Ya suɗe laɓɓansa yana fiddo harshe waje, ya jima kamar ba zai magana ba sai kuma ya ce ""Ba ki isa ba," "ko dai ki sha ko dai na ba ki ta cikin bakina"". Ta ɗan fara ja baya ta ce ""Da gaske bana ci, bana so, bata burgeni """ """Ji, zo nan"" ya ce." "Ta ƙarasa dab da shi, ya amshi chocolate ɗin ya sake gutsira, tare da kaiwa cikin bakinsa ya dinga" "taunawa, za ta juya ya damƙo hannunta, ya saka hannu ya figo ƙugunta ya dawo dab da ita ya damƙo fuskarta ya juye mata chocolate ɗin bakinsa a nata, ya kame bakin da hannunsa har sai da ya ji ƙut; alamar ya haɗiye a cikin cikinta kenan ya sake ta." "Safiyyerh sai ta ji nutsuwa, sai ta ji miƙewar gashin jikinta ta ji saukar abu duk da bata san mene ba, ta" "san dai hakan ya mata daɗi ta gamsu ɗari bisa ɗari. Ya mata shiru sai kallon da yake binta da shi, ta yi murmushi mai kyau ta ce" """Bestie""" "Ya yi shiru, ta shagwaɓe fuska tana diddira ƙafa ta ce ""Bestie"" ta faɗa cike da shagwaɓa mai saukar da" "nutsuwa a ƙirji, still ya sake mata shiru, bata karaya ba ta faɗa kiran sunansa ta ce ""Bestie""" "A daƙile cikin haɗe fuska ya ce ""Bana so, bana son wannan taɓe fuskar kamar kin yi arba da kashi, kamar" "kinga abin ƙyama na tsana haushi irin wannan abin suke bani, damuwa suke saka ni. Moh baya so ok?""" "Ya taka ya fara tafiya ta bisa da kallo ba ta yi magana ba har ya yi gaba abinsa, sai ta ji kamar da zuciyarta yake tafiya sai ta ji tsoro, tsoron rasa shi. A hankali ta sauke ajjiyar zuciya tare da komawa cikin gidan." A hankali Prof dake saman bene ya saki farin labulan ɗakin Safiyyerh wanda kuma ta nan ne yake hango "ta tare da Mutallab ɗin. Ya jingina a hankali yana jin wani rin ɓacin rai, yana jin damuwa da kuma takaici mai zafin gaske Safiyyerh na neman zame masa damuwa da kuma ciwon kai, Safiyyerh na neman zame masa jarrabawa. “Ya Allahu, Ya Rahmanu ka bani ikon cinye wannan jarrabwar ba zan iya aurar da Safiyyerh ga matsiyaci irin yaron nan ba, ina da mafarki a kan ta in sha Allah"". Ya nemi waje nan stool ya zauna yana sunkuyar da kansa, idan ya tuna yadda ya janyota sai ɓacin ransa ya ruɓanya kansa a zuciyarsa. Yana nan zaune ta buɗe ƙofa ta shigo ""Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"" Ta ce a kiɗime ganin" "daddy a ɗakin nata, zata juya ya ce ""Dawo ki zauna""" Jikinta a matuƙar sanyaye kamar an watsawa kaza gishiri haka ta ƙarasu wajan ta zauna a ƙasa ta ce """Gani Daddy"" ya ce ""Na ganki"" ya gyara zaman nasa da kyau yana kallon ta, ya jima kafin ya ce ""Kike sunkuyar da kai kamar mutuwar arziƙi? Kamar dai na isa dake, kamar kinga mutumin banza a gabanki a dole kina jin sai kin fi ƙarfina ko Safiyyerh? Haka kike tunani a ranki ko?"" Ya ce da damuwa a ransa kamar" "ya yi kuka haka yake ji, Safiyyerh na neman sama shi ciwon damuwa." """Safiyyerh Abdu.""" "Idan ya yi mata irin kiran nan sai ta ji tsoro da ƙyar tattara dukkan jarumtarta ta ce ""Na'am""" """Me kike so?""" """Ka aura mini shi""" """Lallai shi, zan miki auren amma banda shi kin fahimta, bashi da abin da zai riƙe ki kin ji?"" Ta yi shiru sai" "kuma ya ce ""Safiyyerh, abin da nake miki ba rashin ƙauna bace hakan soyayya ce, kowanne uba zai so ya aurar da ɗiyarsa ga mutumin ƙwarai, ya so haɗa zuri'a da zuri'ars ƙwarai, babu mai ƙaunar siyar da akuya ta dawo tana ci masa dunga. Batun aure ba wasa bane kuma ke tashan balaga ke damunki, ba ki san me kike so kike ra'ayi ba a yanzu, don Allah ki taya ni kula da tarbiyyarki, yaron nan ba ɗan arziƙi bane, ba" "mutumin kirki bane, yaron banza da wofi ne, yaron iska wulaƙantaccen yaro...,""" """Daddy don Allah "" Sai ta yi shiru. Ya ce ""Don Allah na daina zaginsa right? Safiyyerh akan saurayi mene" "ban miki ba a rayuwa? Alfarma ɗaya ce ba za ki iya yi mini ita ba ya miki kyau""" "Ya miƙe ""Ki shirya zan aura miki Nahyan, you'll get marry as soon as possible as far as ya amince""" "Ya yi waje zai fita sai kuma ya juyo ya kalle ta ya ce ""Za ki je gidan Hajia ba za ki dawo nan ba"" ya yi waje" "ta bisa da idanu. Sai kuma ta tuntsire da dariya har hawaye na sakko mata ta watsa hannunta ta ce ""Oh Safiyyerh ni da saurayin ma baya so na"" ta sake yin dariya mai ban tausayi da cin zuciya. Ta cure waje guda, ta fara tunanin Aafiyyah nan take kishi ya mamaye zuciyarta, me Aafiyyah ta mayar da ita ne? Duk wahala da fafutuƙar data sha one time ta zo ta ce mata wai ta raka ta gidansu Mutallab? How that be possible? Anya Aafiyyah nada hankali? Sai kuma ta yi shiru ta fara processing tunanin yadda suke da" Aafiyyah. “Deep friendship” "Tun playgroup alaƙarsu ta fara kuma duka sunansu Safiyyerh, haka sunan mahaifi Abdu, daga ita har" "Aafiyyah babu middle name ko family name a sunansu. Sanda suka kammala primary school Paaah ya yi yunƙurin ɗauke Aafiyyah zuwa ƙasar China domin yin karatu, Aafiyyah bata amince ba ta dinga kuka ita zata zauna a Nigeria ta yi karatu, me ya sa zata bar Safiyyerh alone? Ba zata tafiya ƙasar waje karatu without Safiyyerh ba, ta tubure ta nace Aafiyyah ta addabi kowa, ta saka rigima, tashin hankalin yau da ban na gobe daban, Aafiyyah idan tana son abu sai mutanen gidan sun san cewa tana buƙatar abu wajan" "Paaah, haka nan zata dinga birgima Paaah sai dai ya yi mata dariya kawai, a wannan lokaci har carbi ya" tsulawa Aafiyyah a jikinta amma ta rufe ido ita dai Safiyyerh. Paaah ya fuskanci akwai zumunci mai ƙarfi "a duka zuƙatan Safiyoyin, ya buƙaci Daddy ya bada Safiyyerh ya haɗata da Aafiyyah sai ya ce a'a baya da ra'ayi kawai, bashi da kuɗin karatun Safiyyerh a ƙasar waje. Bisa dole ya ce Aafiyyah ta zaɓi makaranta sai ta ce Fgc day inda Safiyyerh zata fara haka ya nema mata kuma suka samu aji guda da Safiyyerh a lokacin daman sabbin ɗalibai ake ɗauka, lokaci guda ita da Kimiyya suka shiga da Kinal, sai suka kasance" "group guda, Safiyyerh, Aafiyyah, Kimiyya, Kinal, Kimiyya." "Aafiyyah bata ɓoyewa Safiyyerh komai, likewise Safiyyerh Abdu." "Aafiyyah score ɗinta na fin na kowa, daga ita sai Safiyyerh kimiyya ke mara musu baya, bata da sauƙi" "wajan karatu kamar Safiyyerh sai zumunci ya sake faɗaɗa kan shi, Safiyyerh Wizzy na kai ta gidansu Aafiyyah ta yini amma Aafiyyah bata fita, daga makaranta sai makaranta, sai shopping ko wani waje shima tare da Mj shine best friend ɗinta. Har suka shiga matakin secondary school, wani lokaci Aafiyyah bata hutu a Naija. Idan ta dawo haka zata musu tsaraba tari guda, tsakaninta dasu wani lokacin murmushi ko ɗaga gira. Safiyyerh is so friendly to everyone da yaje wajanta itama bata shiga sabgar" mutane she is nothing but a blessing. "A haka Mutallab ya shigo cikin makarantar, ya shigo ciki da rashin tunanin zai shiga zuƙatan duka" "Safiyoyin. Ranar data zama bad ga Safiyyerh shine a class a cikin aji, a makarantar Fgc. A daren ta faɗawa Aafiyyah cewa ta faɗa soyayya ta ce.""I think i am in love, na ji kamar na faɗa cikin soyayya Aafiyyah"" suka dinga magana har suka zo inda Aafiyyah ta cewa Safiyyerh." """This is what we call love and romantic. Ga amsar ki nan""" """Amma wa kike so haka?"" Aafiyyah ta ɗora da tambayar." "Ita kuma ta cewa Aafiyyah ""Secret crush, zan faɗa miki not today not tomorrow ƙila watarana"" cewar" "Safiyyerh, ita kuma Aafiyyah a lokacin da suke wayar ta cewa Safiyyerh ""Za mu yi magana gobe idan muna raye a makaranta, and i will tell you something"". Ashe something ɗin da zai iya tarwatsa kansu da zuƙatan su ne, Safiyyerh taƙi faɗawa Aafiyyah Mutallab shine wanda take so, ita kuma tunanin Aafiyyah bai kawo taɓa kawowa kai ba. Don haka washegari bayan sun je makaranta, Aafiyyah ta riga su zuwa har" "suka tattauna akan birthday ɗin Safiyyerh, a haka Aafiyyah ta ƙarasu wajan.." "Safiyyerh ta ce ""You came early today, akwai magana ne?"" Gira Aafiyyah ta ɗaga mata, sai kuma ta yi" ƙasa da murya ta fara mata magana secretly a ɗan raunace. The open conversation; "Aafiyyah a lokacin da ta faɗawa Safiyyerh magana a kunne zuciyarta har rawa take yi ta ce ""Safiyyerh kin" "san bana miki maganar wasa, I'm always serious akan kalamaina right, ina son Mutallab ɗin nan sosai, ranar wata juma'a na ganshi tsakanin asabar da juma'a na ganshi ni da Yaya Mj, ni kawai na ji ina son shi, ban san hujja ko dalili ba, amma ƙarfin zuciyarsa ya mini, jajircewar shi ya mini, kawai completely ya yi wa zuciyar Aafiyyah. Na dinga tunanin ina zan ganshi, dake ni mai sa'a ce a rayuwa sai na ganshi ranar wata Sunday na shigo Extra lessons, a nan mukai magana da Kimiyya, na ce kar ya faɗa masa, kema Please kar ki faɗa masa, Safiyyerh ban taɓa jin tsoron rasa abu ba irin yadda nake jin tsoron rasa Mutallab, Safiyyerh ban taɓa jin cewa na shirya amsar ƙalubale ba sai yanzu, idan na faɗa masa yanzu da matsala dukkan mu yara ne, ina buƙatar ya tsaya da ƙafafuwansa amma zan wa Paaah magana, ko farkon sunansa “M” na ji zuciyata girgiza take, i love Mutallab so much, i love everything nasa, i like his anger komai, ki riƙe haka, saboda shi zan zo birthday naki, zan lallaɓa Paaah, Safiyyerh ina son Mutallab, Safiyyerh ina ƙaunar Yaa Muhammad, ni na faɗa miki damuwata tunda ke kin ƙi faɗa mini wa kike so," "shikenan """ "Safiyyerh ta dinga kallon Aafiyyah a tsorace, wani irin kallo na dama na faɗawa Aafiyyah tun jiya a waya" "cewa nima Mutallab nake so, haka ta dinga bin Aafiyyah da ta kasa cewa komai, ta sunkuyar da kanta" "ƙasa, ta sake kallon Aafiyyah sai ta ce ""Ok, dear""" Aafiyyah ta ɗaga kafaɗa tana murmushi ta fice ta nufi cafeteria. "*Kuka Safiyyerh ta fashe da shi tana wani irin ƙanƙame jikinta a lokacin data gama tuna komai, nan take" "zazzaɓi ya rufe ta, ta dinga girgiza kan ta ta faɗa saman carpet tana birgima ta ce ""I am sorry Aafiyyah, i am sorry, ba zan iya ba, ba zan iya ba, nima ina son shi, shi kaɗai, only him""" """Aafiyyah is not my fault, it's urs, me ya sa za ki ƙi faɗa masa? Shin ni ba kiga wahalar da nake sha ba?" "Wani irin uzuri ne da zai saka kiƙi faɗa masa? I love Mutallab too, ba zan iya jingina shi da kowacce mace ba, idan soyayyarsa jarrabawa ce lallai na amince da hakan, amma ko a matsayin kishiyar soyayya balle kishiya a matsayin matar Mutallab, ki mini afuwa, zan miji Addu'ar Allah ya haɗaki sa wanda sa ya fi Mutallab, zan yi addu'ar Allah kar ya ƙara dawo dake Nigeria har abada, idan mutuwarki hutu ce, zan yi" "addu'ar Allah ya kai ruhikinki aljanna, ya sadaki da mala'ikunsa masu rahama, soyayyar Mutallab azaba" "ce nima a zuciyata"" ta dinga kuka har numfashinta na tsayawa ta ji a yanzu MUTALLAB ɗin kawai take so, tana tsananin buƙatarsa a kusa da ita, tana son ta jita a jikinsa kamar dai yadda take yawan ganin daddy da Ummeyh. A haka bacci ya ɗauke ta saman carpet ɗin, baccin wahala, bacci mai cike da mafarkan" "Aafiyyah saboda da ita ta kwanta a cikin ranta, bacci mai tsananin takaici da tsananin azaba ga ruhinta." * A gidan Malam Abdullahi kuwa yana zaune a saman tabarma bayan ya fatattaki yaran ɗaki wasu kuma "sun yi waje, aka duka sallama ""Wai Malam ya zo a waje"" cewar wani ɗaya daga cikin almajiransa. Malam" ya miƙe tare da saka takalma ya ce. """Kai in jiwa?""" """Wani ne a waje a cikin babbar mota, ya ce Malam Abdullahi yake nema"" faɗin yaron, bai jira malam ba" ya saka takalma ya yi waje jin cewa mai neman nasa a mota yake tafe ƙilan wata zakkar ce domin azumi ya gabato. "Yana fita yaga mutumin ya fito, cikin wata dakakkiyar shadda mai ruwan ƙasa sai buga sheƙi take yi, kana" "ganinsa ka san yana cikin rufin asiri ƙwarai da gaske, Malam ya miƙa hannu suka gaisa da mutumin cikin jin daɗi Malam ya ce ""Ka yi mini afuwa ban wayeka ba ranka bawan Allah"" ya ce da alamar rashin fahimta." "Ya jinjina kai ya ce ""Gaskiya ne, baƙon arziƙi ne in sha Allah." """To, to ba damuwa Allah Sallallahu a jisshe mu alheri"" cikin malam har rawa yake yi, ta inda kuɗi za su" fito kawai yake baza idon gani. "Ya gyara tsaiwa ya ce ""Sunana Engineer Musbah, na so ne akan batun yaron ka Mutallab"" uncle Musbah" "ya faɗa yana murmushi, tare da kallon fuskar Malam sai ya hango ɓacin rai, damuwa, tsana, ladama, tsoro, razani duka ya hango a lokaci ɗaya." "Malam ya kame fuska ya ce ""Wata rashin ɗa'ar ya yi maka? Ba dai sata kai ma ya yi maka ba? Ni dai sisi" "na biya bani da shi, kana kaiwa hukuma ƙara su kama ka"" uncle Musbah ya yi murmushi ya ce ""Ko kaɗan, muhimmiyar magana ta kawo ni kuma ne daɗi da alheri ka bani dama mu nemi wajan zama ko?"". Malam ya ce ""Mu yi magana a nan"" uncle Musbah ya jinjina kai sai ya ce ""Kasan labarin Safiyyerh a wajan shi?" "Ba haka bama ina neman haɗin aure da ƴar ɗan'uwana Safiyyerh. Malam Abdullahi, Safiyyerh tana son Mutallab ban san shi ma, soyayyar dake neman lalata tarbiyyar da muka bata, soyayyar dake sawa ta biyo shi tun daga makaranta har zuwa gidan nan naka, soyayyar data saka ta cikin damuwa har ta saka bata fahimta a makaranta, shekarar Safiyyerh goma sha biyar da watanni ta nufi 16 years yanzu, ban san shekarun yaronka ba babu mamaki ya fita, koda bai fita ba hakan ba haramcin. Suna cikin mataki mai hatsari gaske a matsayin Adolescencet stage, bana son wata fitina ta biyo baya, saboda akwai gigi da giyar balaga dake ɗawainiyya dasu, ina son tushe wannan ɓarakar ta hanyar yi musu aure, a cikin satin" "nan""" """Kana son ganin gawar ƴarka kenan?"" Cewar Malam Abdullahi." """Subuhanallahi, kamarya zan so ganin gawar jinina idan ba wa'adinta ne ya cika ba?"" Cewar uncle" Musbah yana barin jikin motar tasa da mamaki. """Amincewa ka aurawa Muɗallabi auran ɗiyarka shine wa'adin mutuwarta da ganin gawarta ta, zata mutu" "ne kamar yadda Diyna da Jaanah suka mutu ya kashe su""" """Still, i don't understand you, ka yi mini bayani yadda zan fuskanta""" "Malam Abdullahi ya jinjina kai sai kuma ya ce ""Musbahu sunanka ko? Bari ka ji da kyau, yaron da kake" "magana a kansa Muɗallabi, tabbas ɗana ne amma ba ruwana da sabgar shi, nima ido nake zuba masa domin ya fi ƙarfina, ɗan ta'adda ne shi, a baya na yunƙurin aura masa wata yarinya saboda ina ganin fitinarsa ta yi yawa, wataƙila zai shiryu idan na yi masa auren, ashe na kashe maciji ne ban sare kan ba, ashe na tuno wuƙar kashe kai na ne, ya zame mini gobara a daga cikin kogi maganinta Allah. Da farko dai Mutallab yaron nan bashi da lafiyar ƙwaƙwalwa, ma'ana yana da taɓin hankali, abu na biyu duk yarinyar da aka nemi aura masa sai ya bi dare ya cinna mata huta ya kashe ta wallahi, ya kashe Diyna da Jaanah," "kenan yarinya ta gaba ɗiyarka zai kashe ina tabbatar maka da hakan""." "Ya ja numfashi ya ce ""Dabara ta rage ga mai shiga rijiya, idan ka amince zaka aura masa ita a hakan to" "shikenan, amma kar a yi kuka da Malam Abdullahi, kar a zo mini idan ya yi mata aika-aika. Kuma bani da sisin yi masa aure""" """Ikon Allah """ """Ikon gaske"" cewar Malam." "Uncle Musbah ya ce ""Ta ya ya zaka haifi ɗa yafi ƙarfinka? Ka taɓa zama da shi ka ji dalilin mutuwar Diyna" "da Jaanah? Al'amarin yara akwai saka idon mahaifa, makami ka taɓa ganinsa da shi da zaka ce masa ɗan ta'adda?"" Ya yi tambayar da shakku a ransa ya ji yana son ganin yaron kuma." """Ku tambayi ƴar taku, ai har makami ya zaka mata"" sai kuma ya ce ""Gashi can, ku yi magana da nasan" "cewa akan shi ne ma ba zan fito ba"" ya nuna Mutallab da yake tsaye da wani almajiri jikinsa duka kayan farauta ne jibga-jibgan karnukansa sun baibaye shi ya karkatar da hular saƙin kansa zuwa gefe." """Mutallab""" "Uncle Musbah ya kira shi, ya ji kuma ya gansu, sai ya ƙi juyawa sai da uncle Musbah ya yi masa kira uku" "ya juya ya buɗe ido, da hannu uncle Musbah ya yi masa alamar ya zo, kafaɗunsa sama yake tafiya yana bubbuɗawa idanunsa rambaɗe da kwalli." """Sannu "" cewar Mutallab, ya faɗa a daƙile kuma a gajarce." """Ɗan albarka, ka yini lafiya? Madallah amma abin da ka yi ba daidai bane zunubi ne ba haka akewa" "manya ba ka ji?"" Kawai ya jinjina kan shi, domin shi bai ga rashin daidai ba daga cewa sannu." """Ka san Safiyyerh Abdu?""" """E.""" """Ka san tana son ka?""" """Na sani""" """Kai kana son ta?""" "Yana kallon gefe, yana jin motsin da aljihunsa yake yi da zillo amma ya yi shiru. Uncle Musbah ya sake" "cewa ""Kana son ta""" """Bana ce ba""" """Me ya sa?""" """Saboda haka ne, ban sani ba""" "Ya dinga kallon Mutallab, ya fahimci da iyakar gaskiyar shi yake magana, ba wasa ko ƙarya cikin" "maganarsa. ""to ita tana son ka, na kuma tabbatar da hakan, zan kuma ɗaura muku aure da ita in sha" "Allah, zaka zama babban mutum, sai ka dai na wannan shigar kamar ƙauraye, ko da yake sune zan zo a" "koya mini shiga dawa, amma ka daina yawo da karnuka ka ji?""" """Ƴar ka zaka aura mini? Idan na kashe ta fa? Idan taɓin hankalina ya motsa a kan ta ba? Kar ka yi haka" "kar ka yi, da gaske"". Ya ce yana girgiza kan shi kawai." """Zan yi, ka shirya inda zata zauna""" """Bani da wani wajan zama daya shige jeji, ni ban iya kulawa da mutane bafa""" "Uncle Musbah ya dinga dariya, daman tuni malam ya bar wajan. Ya buɗe motarsa ya ce ""Na barka lafiya" "Bestien beastie "" ya shiga motar ya bar wajan Mutallab ya bisa da kallo." * "Uncle Musbah ya yi parking motar a harabar gidan Professor Abdu, ya fito sai ya dinga mamaki ganin" "motar Nasim a cikin gidan, a haka dai ya shiga cikin gidan, ai kuwa shine, shi ɗinne ya hakimce samam kujera ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya kan ɗaya jikinsa sanye da voyel mai taushi kamanninsa da Nahyan ya fito sak. Uncle Musbah ya nemi waje ya zauna ya ce ""Yaushe ka dawo kai kuma?"" Ya yi murmushi ya ce ""Jiya, ban samu shigowa gidanka bane sai yanzu, sai kuma Professor ya ce yana buƙatar ganina ni da" "Nahyan, gash nan ma"" ya faɗa yana nuna Nahyan, cikin ladabi Nahyan ya ce ""Evening uncle""" """Evening son, ya hutu?""" """Mun kusa komawa ai, sati mai zuwa ai""" """Ma sha Allah, Allah ya yi wa rayuwa da karatu albarka""" "Prof, ya gyara murya bayan an gaisa ya ce ""Nasim, kai ne baka san komai akan abin da yake faruwa don" "gane da Safiyyerh""" """Haka ne Yaya"" cewar Nasim." "Professor, ya kwashe komai ya faɗawa Nasim, sai ya ɗora da ""Na yi shawara tunda har yanzu visar" "Safiyyerh yaƙi samuwa, zan mata aure kamar yadda take so, na yanke shawarar aura mata Nahyan domin ba amince da Ɗan'malam ba""" "Da wani irin firgice Nahyan ya kalli Prof sai ya ce ""A'a uncle Prof, ba haka tsakanina da Safiyyerh kuma ai" "Safiyyerh tana da aure an yi musu aure a cikin ajinmu, a class ɗinmu"". Gabaɗaya suka kalli Nahyan da mamaki ""An ɗaura musu aure dawa? Wane ya yi auren, wane ya walicci kuma?""" """Da Mutallab, ni ne kuma na zama waliyin Safiyyerh, Allah uncle Prof Safiyyerh matar aure ce""" """Ka yi hauka dai ba aure ba, daman haka auren yake, ai kuwa a banza domin bai yi ba auren nan"" Prof ya" "faɗa yana miƙewa tsaye sai kuma ya shiga kiran sunan Safiyyerh, yama manta bata cikin gidan tana" gidan Hajiya. "Uncle Musbah ya dinga murmushi da dariya ya ce ""Allahamdulilah """ """Alhamd for what? Wallahi aure bai ba, kuma banza wallahi""" """Aure fa sai wani, ba dai auren Safiyyerh da Mutallab ba, kuma zata tare a cikin gidanta in sha""" """Ka yi kaɗan Musbah, wallahi ka yi kaɗan ka ce aure ya yi""" """Uncle kaga auren fa"" Nahyan ya ce yana bawa uncle wayar hannunsa, ya kunna bidiyon suka kalli komai," "Abba Nasim, kallon bidiyon yake kawai bai ce komai, sai uncle Musbah ya ce ""Wallahi wallahi auren Safiyyerh ya yi, kuma baka isa ka kashewa Safiyyerh aure ba, idan kuma na cika na isa sai na yi abin da ya dace, idan kai ka shirya ganin abin kunya wajan Safiyyerh ni dai ban shirya ba, ina mai tabbatar maka auren nan shine rufin asirin mu gabaɗaya, Nahyan ɗan wajan Nasim ne, Nasim ƙaninka ne Prof, idan" "Nasim nada ikon auran ɗiyarka, kamar yadda" "Shima Nahyan ke da iko, muddin Safiyyerh ta amince ya zama waliyinta, to zai iya yi mata aure a ko'ina" "ma wallahi, kuma Allahamdulilah na ji daɗi ta amince, me ake buƙata? Tsayayyen waliyi to Nahyan" "tsayayye ne ina da tabbacin zai tsayawa Safiyyerh a ko'ina kuma ga alama nan, Nahyan ya kai munzalin" "zama waliyi, don haka aure ya yi, shi kuma Mutallab nada ikon karɓawa kan shi aure. An samu waliyi," "shaidu, saɗaki, yaran da Safiyyerh zata aura, to ba zaka zama ƙaddarar da zai saka yaran su zo a wulaƙantattu ba""." """Musbah, ni kake furtawa haka?""" """Prof, na faɗa maka ka yi komai idan ka ji zaka iya yin haka, wallahi idan ka kafe sai ka hana auren nan," "ko ka saka ya sake ta sai na kai ka ƙara wajan VAWA""" "The Violence Against Women Act (VAWA) is a federal law that, in part, provides housing protections for" people applying for or living in units subsidized by the federal government and who have experienced "domestic violence, dating violence, sexual assault, or stalking, to help keep them safe and reduce their likelihood." """Shikenan, ya shirya kira ga hisba ko hukuma wallahi sai ya sake ta""" "Professor ya fice yana nufar wajan hisbah, ya faɗa musu komai, ya ce yana buƙatar a duba masa halaccin" "auren a musulunci, idan aure ya yi kuma a saka Mutallab ya saki Safiyyerh ko nawa ne zai bashi. Malamin" "hisba ɗin ya dinga murmushi ya ce ""Ka je ka taho mana da yarinyar taka, mu zamu aika a zo da yaron da mahaifinsa""" * "Malam Abdullahi ya samu kiran hukumar hisba kuma aka buƙata ya je har da Mutallab, cikin sa'a kuma" "Mutallab bai jima da zuwa ba, ya tisa ƙeyarsa zuwa office ɗin hisba. Suka tarar da Professor, uncle" "Musbah da Abba Nasim, Safiyyerh na durƙushe a wajan kusa da uncle Musbah tana kuka." "Ɗan hisba ɗin, ya dinga kallon Mutallab sai ya ce ""Ka ajjiye mana karnukan nan a waje""" """Na kai su ina? Bayan karnuka tsada suke, a tsahirta mini su zauna a nan ba wanda za su ciza""" "Jin muryar Mutallab ya saka Safiyyerh ɗago kai, suka haɗa idanu ya ɗage mata girarsa. Malamin hisbar" "ya sauke numfashi ya ce ""Ki ne Mutallab ɗin? Kai ne mai son Safiyyerh?""" """Ni ne Mutallab, Ɗan'malam Abdullahi gashi a zaune"" Mutallab ya nuna malam. Sai kuma ya ce ""Zan" "maka kyara Allah gafarta, ita ce mai son ɗan gidan Malam Abdullahi dai"". Ya ce yana ɓata fuska ainun" "wato Safiyyerh ƙararsa ta kawo? Kamar bata san ya shirya zama da ita ba?""" "Malamin hisbar ya ce ""To afuwan, na yi kuskure, amma matarka ce ko?"" Ya tambaye shi, haka kawai ya ji" yaron ya masa yadda yake tsage gaskiyar dake ƙirjinsa. """E, matata ce""" """Zaka iya sakinta?""" "Prof ya ce ""Wanne zai iya? Dole ma ya sake ta, kalli jibga-jibgan karnukan da yake yawo da su fa?""" """To zan sake ta""" "A firgice Safiyyerh ta girgiza kai, ta rarrafo ta riƙe ƙafar Mutallab ta ce ""Dom Allah bestie kar ka sake ni," "ka rabu da daddyna ni ina son ka, don Allah ka bari mu yi rayuwa tare don Allah"" wani ɓarin makauniyya daddy ya yi Safiyyerh, ya hantsila ta kifa ya miƙe ya sake marinta ta kifa, zata faɗi Mutallab ya yi saurin riƙota ta faɗa jikinsa,tana sakin wani gigitaccen kuka tare da ƙanƙame Mutallab. Ya ƙara saka hannu ya kifa mata wasu marukan bai sauke hannunsa ba ya ji uncle Musbah ya sauke masa wasu tagwayen" maruka a fuska. "Uncle Musbah ya ce ""Mutallab kana da inda zaka ajjiye Safiyyerh?""" "Ya yi shiru, uncle Musbah ya daka masa tsawa ya ce ""ina maka magana, kana da inda zaka ajjiye" "Safiyyerh matsayin matarka""" "Cikin sauri Malam Abdullahi ya ce ""Ba'a gidana ba, domin nima ya yi mini kaɗan, shima a shago yake" "kwana"" Malam ya faɗa yana miƙewa tsaye, office ɗin hisbar ya hargitse. Uncle Musbah ya ce ""Thank God akwai shagon su dinga kwana a can, ya je na bashi Safiyyerh, na amince masa""" "Mutallab ya ce ""Kuma zan iya kwana a jeji ma"". Ya faɗa yana riƙe hannun Safiyyerh dake ta kuka. Uncle" "Musbah ya ce ""Ko a saman kan ke ne tana kwana, riƙe hannunta, riƙe hannun matarka kuje Allah ya" "tsare ya kiyaye""" "Murmushi Safiyyerh ta saki, idanun Prof ya cika da hawaye ya zubawa Safiyyerh idanu, Mutallab ya" "damƙe hannun Safiyyerh ya yi waje tare da fita daga office ɗin da ita, karnukansa suka bi bayansa. Fitar su ke da wahala Prof ya yanke jiki ya faɗi a wajan." Mu haɗu asabar Mutallab paid book 08164069385 "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 39: My new home" "Cak Safiyyerh ta tsaya jin Abba Nasim ya kira sunanta, Mutallab bai juya ba sai sake riƙe hannunta kawai" "da ya yi. Ta juya ta kalle shi taga ba ita yake kallo ba, ta yi ƙoƙarin cire hannunta zuwa ga kiran Abba Nasim,Mutallab ya hanata, a hakan kuma Abba Nasim ya ruske su yana kallon Mutallab sai kuma ya kalli Safiyyerh ya ce ""Mu je daddynki na kira"" ya faɗa babu wasa a fuskarsa shi saɓanin uncle Musbah ne." Idanunta na rawa tare da cikowa da hawaye ta ce """Abba, amma ba raba ni zai yi da bestie ba ko?"" Ta yi furucin." """Da abin da ya fi bestie zai raba ki, za ki shige muje ko sai na kifar dake na tattaka ki a nan wajan""" "Ta juya ta kalli Mutallab, shi kuma yaƙi kallon ta, yana jin dai yadda hannunta ke rawa cikin nasa, ta kasa" "motsi zuciyarta cike da fargaba da zullumin abin da zata tarar a wajan daddy. Takaicin Safiyyerh ya kusa saka Abba Nasim yin shigewarsa, domin idan ya cigaba da tsayawa zai iya saka ƙafa ya yi ƙwallo da ita, tamkar yadda ake cilla ƙwallo cikin raga. Safiyyerh ta fara shassheƙar kuka, kukan da yake ƙara tunzura" "zuciyar Mutallab, ta dube shi ta ce" """Me ya sa kowa ya kasa fahimta ta? Ummeyh ta kasa fahimtar halin da yarinyarta je ciki, Abba Nasim ya" "kasa, Wahee ta kasa ita da nake mata kallon yayata wacce zata iya bani shawara, kuma zata iya" "fuskantar halin da zuciyata take ciki, uncle Musbah ne yake gane shi kaɗai, only him, shi kaɗai ya san ciwon da nake ji a cikin nan ɗina bestie, a nan ɗina nake jin zafin komai a cikin nan ɗina""" "Ta nuna masa tsakiyar ƙirjinta, wajan saitin zuciyarta. ""Hatta kai ka kasa fahimtar halin da nake ciki," "saboda kai na shiga wannan halin saboda kai ne Mutallab"" sai ta durƙushewa a wajan tana fashewa da kuka shi kuma yaƙi tankata ta yi mai isarta idanunta jiƙe da hawaye ta ce." """Ba zaka rarrashe ni ba?""" """Hmmm""" """Ka rarrashe ni ko zan ji daɗi""" """Ban iya ba"" ya ce without a manners in his speech." """To ai riƙe ni za ka yi,ka rarrashe ni ka dinga cewa na yi haƙuri har sai na haƙura haka ake yi""" "Ya cije lips ɗinsa, ya dube ta yana fiddo mata da manyan idanunsa farare tas sai taga ya ɗage kafaɗa" "ɗaya tare da yi mata shiru. Safiyyerh ta ji rauni, wani irin rauni da tunanin cewa ta rasa komai sai shi, shi ɗin da bai ɗauki feelings da emotions ɗinta a bakin komai ba, shi ɗin da yake kallon ta matsayin da ita da babu duka ɗaya ne. ""Please bestie, i need ur care mana, ka daina wulaƙanta ni Allah ba kyau ni fa" "matarka ce sirrinka, hijabinka, tsaraicinka, al'aurarka ni Safiyyerh""" "Ya dinga kallon ta a mamakance wani irin kallo da zata iya ɗaukarsa da manufofi da yawa, ya girgiza kai" yana matsawa dab da ita a daƙile daidai kunnenta ya ce """Bangane ma'anar ni al'aurarki bace, ni ɗin? Ni ne al'aurar taki""" """E, ni Safiyyerh matarka ce, sirrinka, kuma tsaraicinka""" "Ya nuna kan shi, da babban yatsarsa yana buɗe ido ya ce ""Wuuuhh, ni ne al'aurar, nuna mini al'aurata a" "jikin ki, Fiyya gaggauta nuna mini na gani""" "Ta fara ja baya ta ce ""Hausa ce, Hausa na yi maka ba wani abu nake nufi ba, ai akwai sirri tsakanin" "ma'aurata""" """Oh""" "Ta yi saurin cewa ""Wallahi tallahi""" "Ya wani suɗe gefen bakinsa, wanda most of the time sai ya ji an raina masa wayo ya ke yi, ya dinga" "kallon ta from head to toe. Da ƙyar muryarsa a cikin ƙirjinsa yana jin tana masa amsa kuwwa a kunne ya ce ""Ai sai kin nuna mini, ko dai ki nuna mini ko ki mini bayanin yadda na zama al'aurarki"" ya ce yana miƙa hannu zai damƙo ta, ganin Abba Nasim ya sake fitowa a karo na biyu yayo kan Safiyyerh ya saka ta yi" bayan Mutallab da sauri ta ce """Innalillahi, wallahi na manta""" "hannu Abba Nasim ya tattare ya ce ""Ke, nima yanzu zan nuna miki ɗan zamani ne, wacce irin yarinya ce" "ke? Na shaida miki ubanki yana kira amma ki manne jikin mutum kamar wata gaska, wanda ma na ji" labarin baya ta taki? Za ki shige ki je kiran ko sai na yi miki bugun shekararriyar dawa a wajan nan hankali "kwance?""" "Abba Nasim, damuwa biyu ya dame shi, ya so haɗin auren Safiyyerh da Nahyan, sai abu na biyu yadda" "shegiyar yarinyar ta kafe akan faƙiri ɗan talakawa, ya yadda bata damu da damuwar iyayenta ba, sai abu na gaba shegen yaron da take naci a kansa ko darajar iyayenta da danginta bai sani ba, tun ɗazo Abba Nasim yake zarya amma kallo wannan bai haɗasu da Mutallab ba, balle ya saka ran jin sannu ko gaisuwa, Mutallab ba ya yarda ya kalli direction ɗin Abba Nasim ɗin. Sai ran Abba Nasim ya soso ainu ya kaiwa Safiyyerh duka cikin sa'a Mutallab ya tare dukan da hannunsa guda ɗaya, ɗaya hannun kuma ya riƙe" Safiyyerh da shi still kuma bai kalli Abba Nasim ba kamar yadda shi kuma yake buƙatar hakan ido rufe. "Cikin ɓacin rai ya ce ""Ko ɗan gidan uban waye? Dame kake taƙama? Ba shakka""" """Ɗan gidan babana malam Abdullahi ne mai rufar almajirai""" "Cewar Mutallab, sai kuma a lokacin ya juyo suka haɗa ido da Abba Nasim, cikin sauri Abba Nasim ya" "haɗiye sauran maganganun, saboda wani irin abu daya gitta a cikin zuciyarsa, mai kama da tsoro da kuma kwarjinin idanun Mutallab ɗin, a shekaru dai, yana da ƙanƙantar su, a kamanni da tsare girarsa ya" ninka ruɓin shekarunsa. "Ya tura Safiyyerh gaban Abba Nasim, ya gyara tsaiwa sai ya ji kamar ya cinnawa Abba Nasim su tiger sai" kawai ya karkatar da kai ya tsuke bakinsa ya yi feɗuwar data saka Abba Nasim rufe kunnuwansa a hankali yake kallon shi kamar ba zai magana ba sai kuma ya shagiɗar da bakinsa da suke masu kyau "madaidaita musamman laɓɓansa ya ce. ""Dake ta, idan kana so""" """Dake ta, amma ba akan idanuna ba, kuma ƙwarza ne na gani a jikinta sai an biyani jikin matata""" """Bestie. ,""" """Quiet Fiyya!"" Ya ce a dame." """Ke jaka ce da za'a dinga dukan ki? A faɗawa Mutallab haramcin abin da kika aikata, a faɗa mini in ji ko" "zaɓar jinin talaka faƙiri mara gata wanda cin yau ke masa wahala balle na gobe shine kuskuren ki, da har" "suke miki haka?. Tell me, Safiyyerh answer my question right now""" "Jikinta ya fara rawa ta kasa magana, ya ƙarasa gabanta ya daka mata wata razananniyar tsawa data saka" "ta kusa sakin fitsari a wando, hatta Abba Nasim sai da tsawar ta girgiza masa zuciya. Idanun Mutallab ya" "jirkice ya sauya launi ƙwarai. Baki ya buɗe zai mata magana sai ya kasa ya yi ƙwafa kawai, ya sake trying" yin magana a wannan lokacin har tsartuwa harshensa ke yi yana alamta zafin zuciyarsa ya ce. """Yes, Safiyyerh. Ni mahaukaci ne, mai taɓin hankali, mai rangwamen gata, mara dukiya da arziƙi, wanda" "bashi da wadatacciyar sutturar sawa, ɗan gidan Malam Abdullahi mai alamjirai. Yes, Safiyyerh, na kashe mata biyu Diyna da Jaanah, of course Safiyyerh ni ɓaraho ne, na haura gidan Alhaji Wada na saci garin kwaki da biredi domin na bawa Muneeberh, satar da bata mini rana ba, na je a lokacin da Muneeberh ke shaƙar numfashinta na ƙarshe. Yes, Safiyyerh, na shiga state cid har sau biyu wanda a nan mahafinki mai taƙama da arziƙi, wanda kuma duk arziƙinsa bai kai ƙaruna ba, a nan ya gani, and i saw him too. Yes, Safiyyerh ni mafarauci ne, ni mai shiga jeji da kuma dawa ne, mai yawo da karnuka,kuma yake jin daɗin mu'amala da su, wannan shine MUTALLAB TAHHB SCORPION, ko ki ce mini Mai dawa, wannan shine" "zahirin wanda kike gani""" "Safiyyerh sai ta ji rauni ya kamata, rauni irin na miji da mata, ta ji raunin Mutallab a cikin idanun" zuciyarta ta ji kuma ba zata jure ganin wannan raunin ba. "Ya damƙo kaɗunta ya ce ""Amma fa, wannan talakan ya san me yake yi, wannan mahaukacin ya san me" "yake, ina da zuciya, zuciyar da ba zata iya bari naga kin wulaƙanta ba, ina son ko ko bana son ki, wannan matsalar Moh ne, damuwar Moh ne, kina so na wannan kuma jin daɗina, i promise ba zan bar ki da yunwa kamar yadda suke tunani ba, zan nemo halak wajan kula dake""" """Fiyyya, ban miki alƙawarin soyayya iya tsayin rayuwa ba, domin rayuwar Moh, ba'a hannun Moh take" "ba, ba zan ce ina jin soyayyarki ba a raina, domin ban taɓa nutsuwa da tunanin hakan ba, ke dai ki cigaba da so na, ki so ni, love me, ki so Moh Safiyyerh"" duk ya hargitsa kan shi, ya kuma har gitsa baiwar Allah, Safiyyerh kallon shi kawai take da jiƙaƙƙun idanunta da sukai laushi." "Ya sake ta, yana ɗaga shoulders" """And i promise you, you'll never regret it, kin ji?""." "A hankali ta ce ""Thank you"" sai kuma ta fashe da kuka sosai." "Ya sake dubanta, sai sakawa take ran shi yana ɓaci for no reason. Ya kama fuskarta sai ta kalli cikin" "tsakiyar idanunsa, ta ji zuciyarta na rawa ainu tana rawa da soyayyarsa, ta ji tana buƙatar jinta a tsakiyar ƙirjin nan nasa. Mutallab tunani ya faɗo masa, tunanin da bai ci a ce ya wanzu cikin ƙwaƙwalwarsa ba, tunanin Aafiyyah. Ya wanzu da tunanin Aafiyyah ba zata taɓa kallon tsakiyar idanunsa ba, bata da ƙwarin" "zuciyar yin haka, sai ya ji sanyi ya sauka akan gaɓbansa." """Je ki, zan jira""" """Ba zaka tafi ba?""" "Ya mata shiru sai ta juya tana waiwayo shi ganin ya sunkuyar da kansa zuwa ƙasa kamar mai tunani, sai" ta ji tsoron tunanin nasa har ƙasan zuciyarta sosai. "A jingine jikin bango Safiyyerh ta ruski daddy idanunsa ya kaɗa ya yi jawur, uncle Musbah yana gefe sai" "Abba Nasim daya shigo tare da biyo bayan Safiyyerh. Malamin hisbar kam an kasa jin ta bakinsa har zuwa lokacin. Safiyyerh ta ƙarasa wajan daddy ta zube a ƙasa tana riƙe hannunsa ta ce ""I am sorry daddy, I am sorry, ka yafe mini don Allah kar ka yi fushi dani don Allah kar ka yi mini haka"" daddy ya zuba mata" ido sai kuma ya yi murmushi mara sauti yana riƙe hannunta da kyau. """Fushi? Why should i?""" """Ka yi haƙuri, ka yafe mini ban zama yarinyar arziƙi a. ,""" """Stop saying this gudaliya"" ya faɗa a hankali. Ya yi shiru sai kuma ya sake sauke ajjiyar zuciya mai nauyi" "yana jin zafi a ran shi, da ƙyar ya tattaro kalaman dake cikin bakinsa yana ƙarfafa zuciyarsa wajan kallon" "Safiyyerh da faɗin cewa. ""Safiyyerh!""" """Daddy""" """I am sorry Safiyyerh, ki yafe mini Safiyyerh Abdu, ki yafewa Professor ɗin ki, ki mini alfama""" """Daddy please, why are you saying this to me? Ba ka mini komai ba ni ce mai laifi na maka laifi na bijire" "maka, na kasa yi maka abin da kake so, daddy ba yin kai na bane, soyayya ce daddy, abin da nake so ne ya haifar mini da hakan?""" """I knew, na sani""" "Ya ja numfashi ya ce ""Kina son aure, kuma shi Ɗan'malam ɗin kike so right Safiyyerh?""" """E, haka ne daddy""" """Bani da nutsuwar fahimtar auren ya yi ko bai yi ba, za'a duba hakan daga baya. Safiyyerh ni na ja miki" "balagar zuciyar dake wahalar da zuciyata a yanzu, sai yanzu na san dalilin son auren ki, shi ya saka mahaifiyarka ke ta kuka ashe mu ne sila, we are the reason behind all this, ban ɗauka hakan matsala bane, ban ɗauka kina lura damu ba, ban ɗauka za ki ji wani abu a zuciyarki ba, bai ɗaukan kaifin tunaninki zai kai ga abin da muke aikatawa ba. Safiyyerh da nake cewa ba zan aurar dake ba, ba hakan ne bana so ba, mu iyaye muna tsoron dukkan abin da zai taɓa yaranmu, ni ne mahaifinki Safiyyerh,tun kina ciki, cikin uwa mahaifiya nake kulawa dake, har kika zo duniya kika kawo yanzu har kika kai munzalin bijire mini, na ji daɗi dana fahimta tun wuri domin idan Ubangiji ya ƙaddara akwai zuri'a tsakaninku ke da Ɗan'malam to ko na hana auren tabbas za'a haife su ne a tsakiyar titi, bana buƙata hakan ko a mafarki. Na ji kawai ina son na sama miki rayuwa mai inganci ne amma ke bakya fatan hakan, soyayyar kike hangowa, auren kike buƙata, ba ki san damuwar dake cikin aurar ba, daɗin auren da abubuwan ƙawatarwar cikin su kike hangowa, Safiyyerh ko kin yi aurar a yanzu ba za ki samu abin da" "kike kwaɗayi ba""" """Zan samu daddy, I promise zan samu ka mini addu'a """ """Hmmm shikenan, zan miki yadda kike so, damar visa naki ya tsayar damu, In sha Allah a gobe zamu bar" "ƙasar nan, na amince ki auri yaron ki zauna da shi matsayin miji, amma ko da wasa Safiyyerh kar ki wajena da buƙatar wani abu, na zame hannuna daga cikin lamuranki, haka ban amince ki je wajan yan'uwana da zummar neman taimakon su ba, ki je tunda shi kika ɗauka, Allah ya tsare ki ya kuma" "kiyaye ki a duk inda kike, zan saka a aiko miki da kayanki ko ta hannun uncle naki ne""" """Kar ka mini baki daddy, ka saka mini albarka don Allah""" """Na saka miki, na jima da saka miki wish you a happy marriage dear, ki bi mijinki kamar yadda ki kaga Dr" "na yi mini biyayya"" kuka kawai Safiyyerh ke yi, ta ji dama zata iya haƙura da soyayyar Mutallab, ta ji dama zata ita haƙura da auren, but she couldn't tana jin wata dauwamammiyar soyayyar bestie a ƙasan" zuciyarta. "Malamin hisbar ya ce ""Amma ina da magana mai muhimmanci ,""" """Na janye, ba sai ka ce komai ba, jeki wajan mijinki Safiyyerh yana waje daman albarkacin shi na ci kika" "zo nan ɗin"" cewar daddy, bayan ya katse malamin hisbar wanda shima bisa dole ya yi shiru ya zubawa sarautar Allah ido kawai. Safiyyerh ta yi ta kuka aka rasa mai rarrashinta, uncle Musbah kan shi a ƙasa. Abba Nasim ne ya dakawa Safiyyerh tsawa ya ce ""Bar nan don ubanki"" da sauri ta miƙe jikinta na rawa ta fita kai tsaye wajan Mutallab ta nufa tana zuwa wajansa ta zube a wajan ta haɗe kanta da qwwia ta dinga rusa masa ihu, shi kam ko a jikinsa ko a kwalar jikinsa ya dinga girgiza ƙafarsa is like yana enjoying" kukan nata ya nuna. * "Ammo na zaune a tsakar gida tana kaɗa miyar yauƙi wacce za'a haɗa aci tuwon dawar da ta yi, gefe guda" "kuma man ja ne data ɗaura saboda masu siya. Bata ji sallama ba sai tsaiwar mutane ta gani a kanta, ta kalli malam ganin ya shige ciki abinsa, sai kuma ta kalli Mutallab da yake kallon ta, irin kallon ki taimaka mini da yake mata tun yana yaro sai kuma ta kalli Safiyyerh dake raɓewa a bayan Mutallab, a hankali ta" sauke ajjiyar zuciya daman tunda aka ce ana kiran su a ofishin hisba gabanta ke faɗuwa ta miƙe ta ce """To da kuka yi tsaye gidan ne baƙin ku ko yaya?"" Ta ɗora da faɗin ""Kama marasa gaskiya""" "Da ƙyar Safiyyerh ta ce ""Ina yini""" """Lafiya lou Safiyyerh shige ki rabu da shi, daman shi zaman gidan ba wani damunsa ya yi ba""" "Safiyyerh ta kalli Mutallab, sai taga ya ɗage gira sai kawai ta yi murmushi ta bi gefensa ta shige zata" "zauna a tsakar gidan Ammo ta ce ""A'a shige ciki mana""" "Ta yi jim, sai kuma ta shige ɗakin Ammo bakinta ɗauke da sallama, ta dinga kallon ɗakin tsaf yake yana" "ƙamshi amma bashi da wani girma katifa ɗaya ce tal a ƙasan ɗakin, sai kwanoka da kayan miya da sauran tarkace ta nemi waje ta zauna bata ma lura da Sa'adah ba sai da ta ji alamar kamar ana kallon ta ta juya cikin sauri ta ce ""Anty ina yini?"" Ta ce muryarta na rawa sosai tana bayyana tsoran daya shige ta sosai." """Yaya za ki ce ba Anty ba, shima Tayo haka yake ce mini yaya""" "“Tayo” it seems like ta taɓa jin sunan nan Tayo, a ina? A wajan wa yaushe kuma? Da sauri zuciyarta ta ce" mata “Aafiyyah” So Aafiyyah ta san komai akan Mutallab ta san everything na rayuwarsa ko mene? Ta yi shiru tana tunanin wanne hali yanzu Aafiyyah ke ciki? Ya jikin nata? Allah ya sa soyayyar Mutallab ba zata kassara "ta ba. Safiyyerh sai ta ji hawaye na neman cika mata idanu, tabbas ta san cewa Aafiyyah na son Mutallab, ta faɗa mata, Aafiyyah bata taɓa nuna tana son abu ko da wasa idan har ba son take ba, she is always serious bata ma fiye wasa ba, komai zata faɗa sak take faɗa. Sai dai ita ta rasa ya aka yi idanun zuciyarta ya manta cewa Aafiyyah na son Mutallab ɗin? Ya akai zuciya ta kwashe ta zuwa ga soyayyar abin da Aafiyyah ke so? Bata sani ba, ta ji kawai itama tana son shi kuma data san cewa something ɗin da Aafiyyah ke cewa zata faɗa mata da tun a lokacin a wannan daren a cikin wayar zata faɗa mata cewa tana son Mutallab. Aafiyyah ta saba haƙuri a kodayaushe, ta saba yi wa Safiyyerh uzuri ta saba haƙura da komai ta bar Safiyyerh, sai hakan ya ƙarfafawa Safiyyerh zuciya tare da bata tabbacin a wannan karon ba, Aafiyyah za ta yi sadaukarwa, za ta iya sacrifice na soyayyar Mutallab ga Safiyyerh, sai ta ji cewa Aafiyyah ba za kuma neman Mutallab ba, sai dai shi ya neme ta, kuma ta san Aafiyyah ta yarda da ita, ta yi" "trusting cewa zata bawa Mutallab duka tarkacan wasiƙun ta ce masa Aafiyyah ce ke yi masa, da wannan" "tunanin da kuma yardar Aafiyyah ta bata za ta yi amfani da ita ta rayu da Mutallab, ba zai taɓa sanin" cewa Aafiyyah na son shi ba har abada. """I am sorry Aafiyyah!""" """Wace Aafiyyah?""" "Da sauri Safiyyerh ta dawo tunaninta ta ce ""To yaya zanna cewa nima as from today""" """Me kika ce?"" Cewar Sa'adah." "Murmushin yaƙe kawai Safiyyerh ta yi, a haka Ammo ta shigo ta zauna ta ce ""An yi kiran magariba""" """Ayya bamu ji ba"" Sa'adah ta ce tana yin waje. Safiyyerh sai ta kasa haɗa idanu da Ammo, ita kuma" "Ammo sai kallon Safiyyerh take yi, kallon mamaki kyakkyawar yarinya mai gata da nutsuwa amma" ƙaddarar soyayya ta afka mata sai kuma ta yi murmushi ba tare data san ta yi ba saboda wani shuɗaɗɗan abu data tuna years back. """Ki je ki yi alwala""" """To"" ta miƙe ta fita, tana kallon yadda Inna Binta da Mama Zaituna ke binta da kallo ganin jar fata sharr" "da ita cikakkiyar yarinya kuma girarta luff. Ganin kallon ya yi yawa sai ta durƙusa ta ce ""Ina yininku?""" """Lafiya"" cewar Mama Zaituna." """Baƙuwa muka yi ne?""" """E, baƙuwa ce. Safiyyerh zo ki yi alwalar kin ji"" Sa'adah ta faɗa tana nuna mata buta, ɗauka ta yi ta shiga" "banɗakin da yake da tsananin duhu jikinta ya ɗauki rawa, ga banɗakin duk zarni ga duhu gashi duk ruwa tsigar jikinta ta fara tashi, ta saba shiga banɗaki haske ko'ina har ma ta tanƙwashe ƙafafuwanta ta yi karatu. ""Ya Allah"" ta ce tana tsugunawa jikinta duka rawa yake yi, tana ɗora hannunta ta ji hannun ya sauka akan wani ƙaton abu mai numfashi mai laushi kuma, wani ihu ta kurma tana yin tsalle tare da fitowa a guje, da sauri Ammo ta fito haka Sa'adah wacce ke shirin tayar da sallah, Mutallab ma shigowarsa kenan ya yi tsaye a bakin ƙofa yana kallon ikon Allah, a zuciyarsa kuma ya ji kamar ya tuntsira" saboda yadda Safiyyerh ta bashi dariya ya riga da ya san abin data gani. "Ammo ta ce ""Lafiya mene ya baki tsoro Safiyyerh?"" Safiyyerh ta kasa magana sai hawaye jikinta duka" rawa yake yi. """Wani abu ne, there is something inside the toilet, na taɓa wani abu""" "Ya ƙarasu ciki, ya zauna kan kujera ya dinga kallon su. Ammo ta ce ""Wani abu ne kuma? Anya akwai abin" "tsoro a banɗakin nan?"" Kai tsaye Mutallab ya ce." """Akwai""" """Mene to? Babu komai fa tas na wanke banɗakin nan""" """Ba lallai ki gani ba, ita za ta gani matar Moh ce ai""" """Muhammad""" "Ya miƙe tsaye kawai yana girgiza kai can ya nisa ya ce ""Na ajjiye maciji ciki, maciji ta taɓa"" ya ce yana" "shige cikin banɗakin sai gashi ya fito ɗauke da ƙaton maciji ya yi gammo da shi, idanun Ammo ne bai hana Mutallab maƙalawa Safiyyerh macijin a wuya ba. Inna Binta da Mama Zaituna ɗuwawu suka haɗa suka kifa baya, suka ƙara miƙewa zasu gudu ganin macijin na fasa kai, nan ma suka sake faɗuwa a tare" sai kawai suka rungume juna tare da fasa ihu a tare. "Ammo ta bi Mutallab da kallo har ya fice daga cikin gidan ""Sa'adah tsaya a nan ta yi fitsarin a bakin rariya" "sai ta yi alwalar ta tsorata da yawa wallahi"". Sa'adah ta ce ""To Ammo"" haka Safiyyerh ta yi fitsari da alwala a nan wajan. Har ta yi sallah ta idar dana matsalar hawaye, sai dai ta samu kanta da addu'a akan Aafiyyah, addu'a akan Allah ya ƙara nisanta Aafiyyah da ƙasar Nigeria ko mutuwa ce Allah ya ɗauki ranta" a ƙasar da take a yanzu haka ya wanzu da wannan addu'ar. """Ga abinci nan""" "Safiyyerh ta dinga kallon tuwan, bata son taƙi ce ace ƙyamar tuwon take yi haka ta ci lauma ɗaya ta ce ta" "ƙoshi, tana ta zaune har wajan ƙarfe tara amma Mutallab bai shigo ba sai ta ji zaman ya dame ta, ga sauro nata ciwon farar fatar jikinta ga babu wayarta zaman ya gundire ta sosai. Cikin dare sama-sama ta ji Mutallab yana cewa ""E matata ce"" ta dube shi sosai ta ce ""Haka mahaifinka ya ce, amma aure yanzu Muhammad ba ka yi gaggawa me kake dashi ina zaka saka yarinyar nan? Ba zata iya zama a nan ba," "kuma ba zata iya cimar mu ba""" """Hmmm"" ya ce yana miƙewa tsaye ya ce ""Mu kwana lafiya""" "Safiyyerh sai ta ji kamar ta miƙe ta bi bayansa, amma ba zata iya ba. Yana barin gidan kuma cikinta ya" "fara ciwo tun tana daurewa har ta ce ""Wassh"" ta miƙe zaune taga duka bacci suke a lokacin kuma an kawo wutar nepa, tana ta yarfe hannunta wani irin matsanancin ciwon cike ke addabar ta, da ƙyar ta miƙe a durƙushewa ta nufi hanyar waje a hankali ta zare sakata ta fice daga cikin gidan. Ta duba hasken gari dana wuta, ga almajirai duk sun kwanta, a zaune ta hango shi ya saka gabansa gabas yana zaune saman ladduma shi kaɗai kaf unguwar idanunsa biyu, ta rarrafa ta je wajansa ta kasa magana sai" "hannunta data saka ta taɓa ƙafarsa, ya juyo kaɗan ya dinga kallon ta sai taga idanunsa a ɗan juye." """Cikina, bestie cikina zan mutu""" "Sai ta fashe da kuka, ya yi ta kallon ta kuma bai motsa ba, a hankali ya juya ya mayar da kan shi gabas" "kawai, ta ƙara taɓa shi ta ce ""Baka ji ne? Cikina ke mini ciwo amai nake ji, wayyo ni"" ya sake juyawa ya kalle ta, sai ya ɗauke kan shi ya miƙe tsaye kawai yana saka hannunsa ya ɗago ta, ta miƙe da taimakonsa ta ce ""Ba zan iya tafiya ba sosai yake mini ciwo"" hannu ya saka ya ɗauke ta, ya nufi cikin shagon da yake da ita. Shi kaɗai ne ciki, Goje sunje farauta can wani gari, ya kwantar da ita da ita ya je ya kashe hasken" "ɗakin ta yi zumbur ta miƙe ta ce ""Ya kuma ka kashe hasken ɗakin ka kunna""" "Ya yi mata shiru. Ta sake cewa ""Bana son duhu tsoro nake ji""" Bata san yana dab da ita ba sai data ji hucin numfashinsa a fuskarta murya kamar ba shi ba da ƙyar ya ce """Shhhh, shittt """ "Baki ta buɗe za ta yi magana sai kuma ta ji ya rufe mata bakin ya ce ""Shiru, ke bakya ganewa ba ki san" "lokacin da za ki addabi mutum ba, ki nutsu ki kwanta ba daidai nake jin kai na ba yanzu ok"" sai ya sake ta," "ya kuma kunna hasken. Tana ta murƙususun ciwon ciki idanunta na cika da ƙwalla taga ya kwaso wasiƙun Aafiyyah yana ta dubawa, ya jima yana dubawa sai kuma ya jingina da jikin bango ya ja numfashi ya sauke ya ce ""Safiyyerh, kalamanki na zahiri daban, kuma na wasiƙun daban"" ya sake" dubawa. """Yaa Muhammad""" "Ya ce a fili, sai kuma ya ce ""Na ji kin mini kamar wasiƙun nan, ba zan ƙara duba su tunda dai gaki""" "Ta fara ƙifta idanu sai ta wayance ta ce ""Cikina ke mini ciwo fa""" "Bai kalle ta ba, kuma bai tanka ta ba sai wasiƙun daya ɓoye cikin aljihunsa ya kwanta tare da juya mata" "ba, ta cikin idanunta ya hango ciwon cikin nata, kamar yadda ta yatsun ƙafarta ya san ajin da take a cikin ajin yaran soyayya dana ma'aurata. Safiyyerh ta zubawa faffaɗan bayansa idanu, da yake ta sheƙin baƙin ta ji dai abu na janta, ta ji kuma ciwon cikin nata ya ƙaru sai ta fashe da kuka tana gangarawa zuwa inda yake, yana jin ta bai motsa ba, a hankali ta shige jikinsa tana wani irin kuka tare da ɓoye fuskarta a" ƙirjinta. "Ya buɗe ido, sai ya girgiza kai yana buɗe hannunsa data takure shi sosai, a hankali ta sake tura kanta a" "cikin ƙirjinsa ya yi maza ya buɗe ido ya ce ""Kika cije ni sai na rama, kuma ba ki da tabbacin inda zan rama Fiyya""" "Ta marairace fuska ta ce ""Kai baka iya rarrashi bane? Cikina ke mini ciwo, da gaske nake maka""" """To ɗauki abin da kike ƙulafuci""" """Meee?""" """Mele""" """Kai ko?""" """Ke ko?""" """Uhmmm""" """Nima ummmm ɗin""" """Ina son ka sosai, ina kishin ka sosai, ina jinka a raina sosai """ """Hmmm""" """Wai me hmm ɗin ke nufi ne?"" Ta ce tana jan karan hancinsa da ɗan gemun data fara gani a ƙasan" "haɓarsa, sai ta fara tunanin topic ɗin da aka yi musu a subject ɗin basic science. Developmental Changes sai ta wanzu da tunanin topic ɗin a daidai lokacin da take cin gemun Mutallab a hannunta." Past tense.... "A lokacin suna zaune ita da Mutallab cikin sabon ajinsu na Jss 3, hira take masa amma ya yi shiru yana" "kallon gefe. A daidai lokacin kuma Aafiyyah ta shigo ciki,. domin da sun yi tunanin ba zata zo bama, bisa" mamaki sai Safiyyerh taga Aafiyyah ta ja kujera ta zauna gabansu musamman Mutallab fuskarta ɗauke "da murmushi ta ce ""Namesake iyayen ƙauna"" ta ce with smile on her face. Safiyyerh ta ce ""Aafiyyah to" "ya ranki""" """Kamarya?""" """Da kiga ganni ina ƙauna da bestie nake nufi mana?""" "Sai Aafiyyah ta ɗaga kafaɗa duka biyun ta ce ""Alhamd, na san kina sane ai so ba zan damu ba, kina dai" "tuna maganata""" """Hmmm"" kawai Safiyyerh ta ce. Mutallab na jinsu ya yi shiru domin baya wani fahimta, tunda Aafiyyah" "ta shigo ya sunkuyar da kansa ƙasa, ya zubawa yatsun ƙafarta idanu, takaici duk ya cika masa zuciya," "bata san cewa tamkar tsirara take yawo bane da ƴan tsunta a bayyane, yana hango tsayin kowanne da ajin da ko wanne yatsa yake da kuma ma'anar zurfin ƙafarta da tudun dunduniyarta. Ya ja tsiririn tsaki." "Safiyyerh ta kalle shi ta ce ""Wannan tsakin fa?"" Ta tambaya da mamaki a fuskarta, kafin ya yi magana" "Aafiyyah ta kalli Safiyyerh ta ce ""I am sorry """ """Sorry for what """ """Na dame ku"" cewar Aafiyyah. Ta faɗa tana zubawa gefe guda ido, a hankali kuma ta sunkuyar da kanta" "ƙasa, sai ta ji ya take mata yatsun ƙafarta sai ta yi murmushi kawai ta miƙe tsaye ""Ga basic science" "teacher nan, bye""" "Sai a lokacin Mutallab ya ɗago kan shi ya dubi Aafiyyah, duban da hargaban abada ba zai manta da shi ba," "memoryn da ba zai taɓa gushewa daga cikin tunaninsa ba, kallon daya zame masa abin tunawa. Maimakon ya ga Aafiyyah cikin uniform ɗinta sai ya hangota tsirara, ba uniform ɗin yake kallo fa, farar fatarta yake kallo, babu wani abu da yake jikin Aafiyyah wanda Mutallab bai haddace shi a lokacin ba, mistakenly ya sunkuya ya murza kwallin daya jima da haɗawa sai yanzu ya saka domin gwadawa, gwajin" "ashe akan Aafiyyah sai sauka, sai a lokacin ya lura da ɓoyayyiyar baiwar dake tattare da jikin Aafiyyah, ya" "ji ya kasa shan iska, numfashi ya yi masa ƙaura ""Auuuuhhh"" ya furta da ƙyar, a lokacin da Aafiyyah ta" "juya ya ji kansa ya sara lokaci guda, a firgice kuma ya saka hannunsa ya murje kwallin cikin idanunsa tas ji ya yi wani abu na fusgarsa, sanyi na ratsa shi da kyau yana jin kamar zai yi zazzaɓi a lokacin." Basic science teacher ɗin na zuwa ya fara musu revision akan Developmental Changes da kuma "Characteristics features of Developmental Changes irin su, childhood stage, puberty stage, adolescence stage, and adulthood stage. A haka ya ce ""Ok class, our today topic is Temporary and permanent" "changes in growth and development"". Sai ya umarci yin shiru duk wanda ya yi masa dariya kuma zai gani." "Ya ɗora da faɗin ""Wanann stage ɗin shine mai matuƙar wahala akan na bayan, tun farko na yi muku" "bayanin yadda maza ke jin feelings akan mata, haka suma maza. Da zarar girma ya fara zuwar wa namiji ko mace, akwai abubuwan da suke nuna wannan girman a bayyane kuma a ilimance, wanda kuma kai tsaye ke nuna mutum ya shirya zama father or mother ok. Baby age yana farawa daga 2-years, childhood age 11-years. Adolescence age 11-18 years, Adulthood age 18- and above. Daga ɓangaren mata akwai daɗin murya, muryarsu zata sauya wacce zata iya attracting feelings ga maza su ji suna sha'awar muryar wance, sai maƙerin budurci za kaga yarinya ta ƙara kyau sosai, sai bayyanar mama a" "ƙirjin budurwa...,""" "Sai ya yi shiru, Safiyyerh ta yi ta murmushi like ta shige wajan ita, Aafiyyah kuma ta haɗe fuska tamau ta" harɗe hannunta a ƙirji ta zubawa teacher ɗin ido. """Bayan fitowar mama, akwai fara al'ada ga mace wanda kuma da zarar mace ta fara al'ada alamu ne" "dake nuna ta shirya ɗaukan ciki, rounded buttocks in girls, appearance of breast in girls, public hair in both boys and girls, breken voice in boys, well formed bones and become stronger very active boy, zai haifar da emotions da feelings, anan kuma ake bambanci sex and romance. Maza akwai buɗewar murya, gashin hammata, da kuma gashin gaba haka ma mata, idan an zo wannan stage ɗin kowa ɗari ɗari yake" "da ɗan'uwanasa. Time up sai kuma next topic""" Aafiyyah ce ta fara miƙewa ta fice jin ƴan class ɗin nata dariya kamar mahaukata. Mutallab ma ya miƙe "ya yi waje jin Nahyan na cewa ""Thank God, yanzu zamu gane ƙwailayen aji da wanda suka shiga" "matakin """ """Dalla ɗan iska"" cewar Kimiyya." Safiyyerh ta miƙe ta fice tana murmushi ta fara duba inda zata hango shi. Present continues.... "Safiyyerh sai ta sake yin murmushi tana cigaba da jan ɗan gemun Mutallab, ya yinda shi kuma yake" "tunanin wasu ƙalamai da Safiyyerh ta yi masa a wata wasiƙa, lokaci ɗaya suka kalli idanun juna ya kasa magana ya kuma zuba mata ido a hankali ya ce ""Kin ce kina son chocolates?""" "Sai ta yi shiru can ta ce ""Eh""" """Ok wace?""" "Sai ta nuna masa lips ɗinsa ta ce ""Wannan chocolates ɗin, ita miji ke bawa matarsa as a love""" """You are impossible Fiyya""" """Ko? Impossible ko?"" Ta ce tana shafa ƙirjinsa, ya runtse idanunsa, maimakon ya ji emotions akan" "Safiyyerh sai ya dinga hango suffar Aafiyyah cikin yanayin daya kasa juyawa. Ya juya muryarsa a dame ya ce ""uhmm Fiyya, ni......ni... I am no ready, ban so ban iya ba muna da sauran time fiy "" Sai sauran" "maganganun suka tsaya masa ganin ta sauke masa numfashinta a ƙirji, ta fashe masa da wani irin kuka ta ƙanƙamesa ta ce ""Don't you trust me? Idan ka amince da wasiƙuna me ya sa ba zaka amince mini ba? Ni ko? Ni bestie, shikenan ka bani wasiƙuna zai koma wajan iyayena ka riƙe soyayyar taka na fasa"" sai ya ji" "rabuwa da wasiƙun shine abin da ba zai iya ba kuma. Ya dube ta da ƙyar ya ce ""Me kike so?""" Mu haɗu litinin. Mutallab paid book 08164069385 """You""" """Gani to""" """Kiss me""" """I don't know how to do it """ "Sai ta yi murmushi ta ce ""Nina iya ai, come bari kaga yadda ake yi"" ta faɗa tana kai bakinta zuwa ga nasa" a daidai lokacin kuma aka ɗauka wutar nepa sai ta ji daɗin hakan a ranta ta sake matsar da fuskarta zuwa ga tashi. "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 40: My love for him." "Zame fuskarsa ya yi a hankali ya ce ""Kama ta nan"" ta yi saurin ɗauke fuskarta tare da fasa yin abin da ta" "yi niyya na daga sumbatar sai ta yi shiru, thinking how Aafiyyah feel a zuciyarta idan ta ganta tare da Mutallab a koyaushe? Da sauri kuma ta ɗauke tunanin Aafiyyah a ranta ta kwantar da kanta a jikin hannunsa tana jin ciwon ckin na sanɗarta a hankali a haka kuma bacci ya ɗauke ta sosai, bacci cike da mafarkai wai ga Aafiyyah a gadon asibiti, ga a Aafiyyah cikin makara, still ga Aafiyyah na mata magiya, magiyar da bata san ta mece ba. A haka har aka fara kiran sallar farko na shigowar asuba sai baccinta ya" sake nauyi. "A hankali ta ji yana ɗan zungurinta ta miƙe zaune tana kiran sunan Allah, ta kalle shi ta ce ""Shine ka" "tashe ni ko?""" """To wani daren za'a sake miki?"" Ya ce yana ɗan gyara rigar jikinsa, sai ta dubi kayan jikinsa taga uniform" "ne a jikinsa ta ce ""What, ba dai lokacin makaranta ya yi ba?"" Ya jinjina mata kai kawai sai ɓata fuska ta ce ""Sallah, ban yi sallah ba ai subuhanallahi""" """Ok, kina yi kenan""" """Bangane ba ina yi ba""" """Wai ba ki fara abin da teacher basic ya ce something al'ada"" ya ce seriously." """Ban sani ba, ido kake saka mini kenan? Ni ba wannan ba kunyar Ammo nake ji ba zan iya shiga ba, kuma" "ban zo da kayan makaranta ta ba, ko na saka sportswear ɗinka sai na je da su tunda nrml ne ai?""" "Ya yi mata shiru ya cigaba da shiryawa, ta zuba masa ido kamar zata haɗiye shi, saboda wani irin kyau da" "taga ya yi mata ainun, bata taɓa lura da yadda uniform ke masa kyau ba sai yau, wani irin murmushi mai sauti ya suɓuce mata ta ce ""Ka san wani abu? An taɓa faɗa maka kana da kyau? Kalar fatarka baƙa haka tana da wahalar samu, kuma an ce baƙaƙen maza ko a aure sun fi qualities right? I am very lucky dana sameka matsayin mijina"" yana ta jinta dai, bai kula ta sai da ta ce ""Ba zan iya haɗa soyayyarka da kuwa" "ba a zuciyata, kai ma Please kar ka mini kishiya ko a mafarki ne balle gaske""" """Hmmm, Safiyyerh Indomie generation ke damun ki, da addu'a kikai Allah ya bani kuɗi na kula dake, na" "yi miki haɗaɗɗan gida mai kyau, ki samu nutsuwa a zuciya yadda ya kamata, amma kin zauna kina wani imagination""" """Ai ni son ka a zuciyata ba ruwan shi da wani babban gida, ko garin kwaki a jiƙa ka gani zan sha""" """Sallah Safiyyerh!""" """Ohhh""" "Ta miƙe da sauri tana gyara jikinta har yanzu rigar abaya ce a jikinta tun ta jiya, ta ɗauki hijjabinta ta saka," "sai ta fara rarraba idanunta domin bata san ta yadda zata shiga cikin gidan ba, ta sake duban Mutallab taga yana zaune ya tanƙwashe ƙafarsa ɗaya saman ɗaya yana duba wani littafi a nutse, tafin ƙafarsa fari tas kuma jajur, yatsun ƙafarsa dugwaye faratan farare dasu, ta zubawa sumar kansa idanu baƙa ce sosai" "kuma ta ɗan cuccure waje guda sai ta yi kyau. A hankali ta ji ya ce ""Ina girma ina sauya kala da kama ne" "Safiyyerh, ki ɗauki sallah da muhimmanci ok?"" Sai ta sauke ajjiyar zuciya ta ce ""ai kunyar zuwa wajan" "Ammo nake bata san na fito ba wallahi sam""" "Ya ɗaga kan shi ya yi mata kallo ɗaya, sai ya ɗauke kai yana miƙewa tsaye ya yi waje ta bi bayansa da" "sauri, duk yadda taso cimmasa bai tsaya ta ba, a tsakar gida ta tarar dashi tsaye yana kallon Sa'adah dake masa magana... ""Ba dai ba ki yi sallah ba?"" Cewar Sa'adah ta faɗa tana miƙewa ta ɗauki buta ta bawa Safiyyerh, da sauri ta amsa ta shiga banɗaki, a tsaye ta yi fitsarin ta ɗaura alwala don ko wanka bata jin zata iya yi a cikin banɗakin. Har kuma ta idar da sallah bata jin tarin Mutallab ba, kuma yan tsaye a tsakar" gidan. "A sanyaya ta ce ""Ina kwana?""" """Lafiya, ya kwanan baƙun ta kuma Safiyyerh?"" Cewar Ammo." "Murmushi kawai ta yi, sai kuma ta shafa kai ta ce ""Daman jiya. "" Da sauri Ammo ta dakatar da ita da" "faɗin ""A'a ba sai kin faɗa ba kin ji? Fatan dai bai miki komai ba, domin na san halinsa ƙwarai""" """A'a, hira ma mukai""" """A'a ki daina wani goyan bayansa, Kodayake ai miji ne, shi kuma miji haka yake zuma ga daɗi ga harbi" "watarana zan ji kan ku ne ai"" Ammo ta ce, cike da fara'a a fuskarta da ƙoƙarin ganin ta saka Safiyyerh ta saki jikinta. Murmushi kawai Safiyyerh ta yi, a hankali ta ga ya ɗago labulen ɗakin daga bakin ƙofa ya tsaya, yana ta ƙissima abin da zai ce kwana biyu bakinsa har ciwo yake kuma duk Safiyyerh ta ja masa" "yawan yin surutu haka kawai. ""Sakar mini labule, idan ba wani abu ya kawo ka ba malam""" """Hmm, ta je a waje"" ya ce so clam." """Ita wa?""" """Safiyyerh, ur uncle is here"" yana cewa haka ya saki labulen ya juya abin shi yana duba agogon dake jikin" "wayar hannunsa. Safiyyerh sai ta ji gabanta ya faɗi, ba dai zuwa akai tafiya da ita ba? Ba dai daddy shawara kuma ya sauya ba daga baya? Innalillahi in sha Allah ba haka bane. Sai da Ammo ta nanata mata" "sannan ta miƙe a hankali tare da fita, sai Mama Zaituna da Inna Binta suka bi bayan Safiyyerh da kwallo." """Kwaɗayi maɓuɗin wahala, ashe ƴar gidan masu kuɗi aka hango masa shine ya kashe waɗancan?"" Mama" Zaituna ta faɗa tana riƙe haɓarta cike da mamakin kyawun Safiyyerh ga jikinta so ma sha Allah. Inna Binta ta ce. """Bana jin cewa iyayenta sun san yana kashe mata fa, kuma basu da labarin ya taɓa yin sata ko?""." """Ko shakka babu, domin duk mai hankali ba zai bawa Muɗallabi auren yarinya tsaleliyya kamar wannan" "ba, duk yadda aka yi an rufe su, ni banda kar ace sokar aure wallahi tallahi da gidan su yarinyar zan nema na faɗa musu komai, idan ya so a raba auren ya je ya auri daidai da shi, domin wannan yarinyar idan ya kashe musu ita wallahi tallahi har ya mutu yana gidan ɗan'kande"" Mama Zaituna ta yi furucin da mamaki da takaici kuma, tana ƙara jinjina kyan Safiyyerh a fili. Inna Binta ta ce ""Au ke jira za ki yi? Ai a yau ɗin nan zan nemo gidan iyayenta na labarta musu komai, ba mamaki na dawo da tukuici mai girman gaske, suna sane suka nema masa aurenta ai saboda sunga ƴar masu kuɗi ce zakka ba zata shige su ba"" Inna" Binta ta ce tana miƙewa. """Ke Binta sokar aure za ki je yi kenan ko? Ba kyau ba""" """Zauna nan Zaituna, da sanyin safe ake kama fara wallahi """ "Safiyyerh, kanta a ƙas ta ƙarasa wajan motar uncle Musbah, shima yana ganinta ya buɗe motar ya fito" "cikin sauri ta ce ""Good morning uncle"" ya yi murmushi ya ce ""Morning daughter, ya kwanan amarci kuma? Hankalinki ya kwanta ko? Kin samu Mutallab"" a hankali ta ce ""Uncle ka fahimce ni"" ya jinjina mata kai ya ce ""Na fahimta ai, na jima da fahimtarki Safiyyerh fahimtar ce ma ta saka na ce haka, kuma na miki uzuri hakan kuma ya faru ne saboda lack of parent guidance and careless, iyayenki sune silar komai, sai ƙuruciya da balagar zuciya dake ɗawainiyya dake, ina miki addu'ar kar bijirewar Prof da kika wani abu ya shafe ki, domin na karaya ainun da yadda naga ya amince kuma hawaye na fita daga cikin idanunsa. Safiyyerh hawayen iyaye masifa ne, ba zan yi mata ya zama masifa a gare ki ba domin bayin kan ki bane sakacin tarbiyyarki aka samu, wanda kuma ance icce tun yana ɗanye ake tanƙwara shi," "amma su sun yi sake ya bushe har yana neman karye musu, wannan shine kuskure na wasu iyayen," "yanzu duk abin da suke buƙata ki yi ba za ki iya yi ba, saboda kin yi nisa ba za ki taɓa jin muryarsu ba," "balle sunanki da suke kira""" """I am sorry uncle""" """Sorry for yourself Safiyyerh, kawai na ji ina jin tausayin ki da kuma auren naki, daka ke har mijin naki" "kuna buƙatar kulawar iyaye sosai. Safiyyerh ki gane da gidan mahaifinka Professor da nan gidan surukanki akwai bambanci, kar ki yi tsammanin samun abin da kike samu a gida, ki zama mai haƙuri da ɗauke kai, mai jajircewa akan mijinta, ki zama mai taimaka masa a kodayaushe kin ji ko?"" Ta jinjina kanta, hawaye na cika mata cikin idanunta sai ta samu kanta da tambayar ""uncle daddy, Ummeyh?"" Ya dinga" kallon ta da tausayi a fuskarsa sai kuma ya kalli sama jin ƙarar jirgi ya ce """Idan wannan bai zama jirginsu ba, to jirgi na gaba nasu ne, daga airport na zo nan, nima ɗin zan yi tafiya" "shima Abba Nasim ya shige""" "Safiyyerh sai ta ji kamar ita kaɗai ta rage, wata kewa ta mamaye jikinta so da ƙaunar iyayenta na" "girmama kansu a zuciyarta ta dinga kuka ita ɗaya tana ajjiyar zuciya ""Kukan mene? Kin samu abin da kike so ai, no more crying"" sai ta ji zuciyarta na cewa ""Yes uncle, I'm not alone Mutallab is here"" a fili kuma ta" "ce ""Yaushe za su dawo to uncle?""" """I don't know"" ya ce yana ɗaga kafaɗarsa. Bayan mota ya buɗe ya sakko da jakar kayanta, da uniform da" "komai, amma banda takardun makaranta, takalma da bags ɗinta da duk tarkacan kayanta na mata har ma da wayarta. Ya ce ""Ga kayanki nan""" """Thank you uncle"" ta faɗa a hankali, sai kuma wani ɗan murmushi ya suɓuce mata ashe haka ake kai" "amarya? So ko wacce amarya haka ake aurenta dama? Shikenan ta zama matar Mutallab? Allah," "Allahamdulilah! ""Ga wannan"" ya miƙa mata zoben gold ɗinta,ta amsa ta saka a hannunta ya ce ""Zan tafi, Allah Ya sanya albarka kin ji gudaliya""" "Ta yi shiru, sai ya ce ""Akwai wani abu da kike buƙata ne Safiyyerh? Faɗi kafin na shige nima""" """Uncle ka bani kuɗi na siyawa bestie kaya shima, please uncle"" ta ji ta samu kanta da cewa haka. Uncle" "Musbah ya dinga kallon Safiyyerh sai kuma ya ce ""Ai na san mijinki, na taɓa masa kyautar kuɗi yaƙi amsa, yana da zuciyar nema na yarda da shi, zan aiko miki da kayan ok? Ga kuɗi sai ki riƙe a hannunki ko? Kinga ba gida ne dake ba balle a yi maganar shirgin kayan mata furnitures, ko gara sai sanda kukai gidan kan ku"" ta yi murmushi ya miƙa mata bandir ɗin kuɗi masu yawan gaske ta amsa tana masa godiya, da hannu ya kira Mutallab da yake shirin tafiyarsa makaranta hankali ƙwance. Mutallab ya ɗan yi sak kamar ba za shi ba, sai kuma ya ƙarasa yana ɗan sunkuyar da kan shi kansa ""Mutallab ga kayan matarka nan, ka shigar mata dasu ciki?"" Ya jinjina kai kawai, sai uncle Musbah ya ɗora da faɗin ""Safiyyerh ta zama Mutallab, Mutallab ya zama na Safiyyerh, Bestien beastie. Ina neman alfarma daka tsayawa Safiyyerh" "don Allah ka ji yaron arziƙi?""" "Mutallab ya kalli uncle Musbah, can ya nisa ya ce ""Uncle, idan kana ce mini yaro sai na ji ba zan iya ba" "kuma"" ya faɗa yana yin kicin-kicin da fuska. Uncle Musbah ya ce ""Waye mutum, ai kai babban mutum ne" "irin ku basu da yawa, ina da mata kana da mata kaga babu batun yaro ko?"" Bai ce komai ba, ya ɗauki kayan Safiyyerh ya yi cikin gidan dasu a hannunsa biyu." """Na gode sosai uncle""" "Ya jinjina mata kai, ya dinga kallon ta sai ya ji gabansa na faɗuwa haka kawai musamman murmushi da" "kuma hawayen da yake gani at the same time. ""Safiyyerh"" ya kira sunanta, sai ya miƙa mata hannu bayan ta ɗago kanta da sauri ta ƙarasa ya rungumeta a jikinsa yana jin wani iri, yana jin kamar yana rabuwa da tsaginsa ne, ya ji tsoron barin Safiyyerh da gaske, amma bashi da wani zaɓi haka ta nema kuma ta samu da ƙyar ya zame ta a jikinsa ya ce ""Allah Ya yi miki Albarka"" ya ce a hankali har ya shiga mota tana tsaye, sai kuma ta fashe da kuka tana juya da sauri zuwa cikin gidan a zaure sukai karo da Mutallab zai fito, tana ganinsa taga bata da wanda ya shige shi, ba kuma da wanda zata iya tisawa a gaba ta yi wa kuka sai shi ɗin, only him ya rage mata, da sauri ta faɗa jikinsa tana fashe masa da kuka ta ƙanƙamesa da kyau tana gunjin kuka, bai hanata ba, kuma bai mata shamaki da jikinsa ba, tunda ya fahimci jikinsa na ɗaya daga cikin abubuwan dake sanya zuciyarta nutsuwa ya daina hanata hakan. Suna" "tsaye har ya gaji ya yi ɗan gyaran murya, sannan ta ɗago kan ta a hankali daga jikinsa" """He lefted"" ta ce." """Hmm""" """Ya tafi, ba zai dawo ba""" """And? Ki bi shi mana""" "Sai ta yi murmushi ta ce ""Ai ba zan iya ba ka sani, salon ka auri wata ko? Bayan yanzu kai kawai nake da" "shi, kai nawa ne ka ji?""" "Komawa ya yi ciki, ta bi bayansa, cikin sauri ta shirya tsaf kayan sun mata kyau sosai, ya jingina da jikin" "bango yana zuba mata idanu har ta gama shiryawa ta ce ""Na yi kyau ko? Ka ce na yi kyau, nima ai na faɗa maka cewa ka yi kyau"" ya ƙanƙantar da idanu yaƙi magana, s haka Ammo ta shigo ta ce ""Ba za ki karya ba, zauna ki sha kunu da ƙosai kafin a kammala ɗumame"" Safiyyerh ta yi shiru ""Zauna mana"" ƙoƙarin zama ta fara sai suka ji ya ce ""zan ta fi, ta fito kawai"" ya ce yana yin waje." Da sauri kuma ta bi bayansa. * "Kamar yadda yake a ɗabi'ar makarantar sai da aka yi assembly kana aka fara shiga class, Safiyyerh ta" "dinga rarraba idanun ganin Aafiyyah amma babu ko inuwar Aafiyyah, haka babu Kimiyya. Kinal ta ce ""Safiyyerh wai ya jikin Aafiyyah ne? Na yi ta ƙoƙarin kiran numberta amma bata shiga, har ya yayanta na kira amma baya tafiya is she ok? Lafiya take?""" """Safiyyerh!"" Kinal ta sake kirata fuskarta ɗauke da damuwa, domin tana da tabbacin Safiyyerh ta san" "komai ta san inda zata samu Aafiyyah, domin ko a school idan Aafiyyah ta ɓoye ana nemanta Safiyyerh ke nemo inda take kodayaushe. A hankali Safiyyerh ta kalli Kinal ta ce" """Me kika ce?""" """I asked you Aafiyyah, where she is?"" Ta faɗa loudly." """An yi mata aure, kamar yadda aka yi mini kuma ba'a ƙasar zata zauna ba, Aafiyyah da Nigeria har abada," "nima ɗin na nemi numberta bana samu kullum""" """Safiyyerh?""" """Kinal""" """Ita Aafiyyah a kaiwa aure? Kin san Aafiyyah da karatu?""" "Safiyyerh ta watsa hannunta ta ce ""Ohh Kinal, ba za ki fini sanin Aafiyyah ba dai ko? Kawo wayarki na" "saka miki wata number ƙila ki same ta ko?"" Cikin jin daɗi Kinal ta bawa Safiyyerh wayarta itama Safiyyerh ta amsa." "In few minutes, ta goje number kimiyya tas, ta goge ta Aafiyyah haka ta goge da Mj daga wayar Kinal, sai" ta saka mata wasu fake ta kuma saka mata wata as Aafiyyah's new number kana ta bata number. Haka ma ta amshi wayar Nahyan ta goge komai. Mutallab dai hankalinsa na kan littafi gabansa duk da yana jin conversation ɗin su. """Safiyyerh ana kira a office na principle"" cewar Class captain na su Safiyyerh. Sai ta yi sak can kuma ta" "miƙe ta fice ta jima har aka tashi daga makarantar bata dawo ba. Mutallab sai ransa ya ɓaci sosai, ya yi gaba zai tafi sai ya hangota zaune ita ɗaya ta ci kuka idanunta ya kumbura sosai gently ya ƙarasa wajan, madadin ya yi magana sai ya cake mata aka ta ɗago ta kalle shi, sai ta miƙa masa envelop ɗin hannunta ya saka hannunsa ya amsa, muryarta a rarrabe ta ce ""An kore ni, na yi failed exam har sau uku"" sai ta sake fashewa da kuka sosai fuskarta ta yi jajur, ta miƙe tsaye tana mustsika fuska sosai sai kuma ta kalli Mutallab tana dariya while hawaye na zuba cikin idanunta ta ce ""Na zama drop out, ko out of school wanne, sun kore ni daga makarantar innalillahi, bestie ba zan sake zuwa makaranta ba"" ta faɗa tana sakin raunataccen kuka jikinta har wani kakkarwa yake sosai. Mutallab ya kasa ce mata komai, ta dinga" "kuka ita ɗaya yana tsaye a gabanta sai data gaji da kuka ta ce ""Mu je""" "Yana tafiyar nan tasa majestically, a zuciyarsa yana nanata ""Ke kika ja komai, ke ce Safiyyerh"" a wannan" "tafiyar kuma tunanin Mutallab ya sauya, tunanin kula da Safiyyerh, tunanin yadda zata samu wata makarantar, ko kuma ya yi musu karatu duk abin da ya zama ai kamar ita ce, a wannan tafiyar ya ji ya yi believing na duka wasiƙun wajansa, ya ji ya gamsu da su, ya kuma yarda cewa Yes, yana son wasiƙun" "yana kuma son mai wasiƙun he trust Safiyyerh so much a lokacin, ya amince he loves Safiyyerh, without" "knowing yadda love ɗin yake, ba tare da sanin mene gaskiyar abin da ke zuciyarsa ba, bai kuma ya yarda" "ya zauna ba, ya ji cewa duka wasiƙun is belong to Safiyyerh's. Har suka fita yana nanata sunan FGC a" zuciyarsa. "A cikin napep ya same ta zaune yana shiga ta ce ""Kai ta tafiya kana bubbuɗawa haba bestie""" "Ya cije lips, yana kallon ta." """Uhm, i feel like crying""" "Ya yi shiru ""Na kwanta a cinyarka? Bacci nake ki kai na ciwo yake mini sosai""" """Uhmmm"" ya ce." "Sai ta zame ta ɗora kanta a gefen kafaɗarsa, shi kuma ya gyara hannunsa yana yin game a wayarsa suna" "tafe bacci ya ɗauke ta. A hankali ya kama hannunta yana kallo, tare da zoben dake jikin madaidacin hannunta sai a lokacin kuma ya ji jikinta zafi ga cikin na ƙogi ashe fa ko karyawa ba ta yi ba. Ji ta yi yana taɓa kumatunta ta miƙe bakinta ɗauke da addu'a sai ta yi murmushi ta ce ""Thank you da auron wajan" "bacci""" "Zata ɗakko kuɗi cikin jakarta sai taga ya miƙawa mai napep ɗin kuɗi ta ɗan tsaya ta ce ""Kabar naka zan" "ba yar fa"" ko kallon ta bai yi ba. Maimakon ya shiga cikin gidan sai ya yi gaba abinsa, bata kula shi ba ta shige cikin gidan, wannan karan tarin yaran da suke zaune a tsakar gidanne suka zaba mata na mujiya sai" "kuma Malam ta durƙusa ta ce ""Ina yini Aby""" """Safiyyerh ko?""" """E, Aby""" """Ke kin zaɓi zama da wannan tantirin yaron ko? Kin zaɓi bijirewa iyayenki saboda wannan yaron da bashi" "da wata makoma mai kyau ko? Wannan yaron ko kinwa iyayenki adalci kenan yanzu idan ya kashe ki me za ki cewa iyayenki eh?"" A hankali Safiyyerh ta ce ""In sha Allah Aby ba zai kashe ni ba, in sha Allah"" ran Aby ya ɓaci ya ce ""Saboda ke nake magana idan don tashi ne wallahi ko a jikina, tashi ki je duk abin da kika jawa iyayenki shikenan ai"" ta miƙe jiki a sanyaye ta shiga ɗakin Ammo ta sameta zaune tana ɗaura" man ƙuli Sa'adah kuma na yanka alawar madara lokacin bikin Sa'adah saura kwana biyar ciff. """Barka da gida Ammo, Yaya""" """Sannu Safiyyerh, ya makarantar?"" Ammo ta tambaya da kulawa tana ajjiye abin hannunta ta ce ""Ki fara" "yin wanka sai ki yi alwala tunda magariba ya kusa sai kici abinci ko"". Safiyyerh ta ce ""To Ammo"" uniform ɗin ta cire ta saka towel ta saka hijab, sabon soson wanka ta gani an bata da sabulu ta amsa, da ƙyar ta yi wankan a tsaye tsigar jikinta na tashi a haka ta yi ta fito. Sanda ta shiga ɗakin ba kuwa a ciki haka ta sutale kayan jikinta tana shafa mai a jikinta, ganin tana ƙoƙarin cire towel ɗin gabaɗaya ya yi gyara murya, ta juyo da sauri a ƙoƙarin ɗaukan riga sai towel ɗin ya faɗi ƙasa, shi kuma ya ɗago kai ganin ta fasa ƙara tana ƙanƙame jikinta ta rasa inda za ta yi, ko inda take bai sake kallo ba ya mayar da hankalinsa kan alawar madarar da yake kwasa yana dannawa a cikin bakinsa hankali kwance. Ganin ba kulata zai ba" "ta saki kuka ta ce ""Ba zaka tashi ka fita ba, kaya zan saka fa, ni ka tashi"" ta ce tana yarfa hannunta." "Ta fara diddire masa ƙafa ""Please mana, ka tashi"" ta ce silently." """Bestie""" "Ya yi iska da ita, ta sake cewa ""Bestie kaya zan saka ka fita""" "Ya ɗago kan shi, suna haɗa ido ta rufe idanunta sai ya tsuke fuska ya mayar da kan shi akan bokitin" alawar madarar hankali ƙwance. """Bestie. ,""" """Damn it..!""" "Ya ce yana miƙewa, ya yi kamar zai fita sai ya dawo baya idanunsa sun nutsa ciki yana mata wani irin" "numfashi, harshensa na yin tsartuwa ya dunƙule hannunsa da yake jin kunama na yawo a ciki. Sai kawai ya girgiza kai ya ce ""Shhh"" numfashinta na fita da ƙyar bata taɓa jin tsoron shi irin yau ba, sai taga kamar ba shi ba, jikinta ya ɗauki rawa sosai a hankali ta ga ya yi baya yana cillo mata rigar data yar a ƙasa." "Ɗauka ta yi ta zura da sauri ko halpvest ɗin bata saka ba, tana gama sakawa ta ɗauki hijjabi ta yar da sallah, har kuma ta idar bai kalle ta ba. Ta juya taga ya juye gurasa irin ta wajan masu balangon nan ta sha romo a faranti, taga hadda nama da kuma awara mai kyau sau turiri da ƙamshi suke yi. Tunda taga ya ɗan kalle ta kaɗan ta san magana yake son yi mata amma kuma bai san ne zai ce ba, sai taga ya share ta ya fara cin gurasar murmushi ta yi ta ƙarasa gabansa tare da tanƙwashe ƙafarta, juyawa ta yi zata" ɗauki cokali sai taga babu hannunta ta saka cikin farantin ta fara cin naman. "Suna cikin cin abincin Ammo ta shiga, ta kalle su ta jima tana kallon su musamman yadda Safiyyerh ke ta" "yi masa hira shi kuma kamar baya wajan, sai ta juya ta bar musu ɗakin kawai. Shi ya fara ɗauke hannunsa ya miƙe ya fice yana fita itama ta fice ta wanke hannunta." "Cikin ɗakin ya dawo ya zauna, Ammo ta ce ""An kawo kaya naka ne Muhammad?"" Da sauri Safiyyerh ta" "ce ""E, nasa ne""" """Tom""." """Yau zaman gida kake da shi kenan? Ba zaka fita ba?""" """Ammo ki na fita ne?"" Cewar Mutallab yana kame fuska" """Ban sani ba don gidanku"" ta ce tana miƙewa, saman katifa ya samu ya kwanta yana ware ƙafa ɗaiɗai" "bacci ya ke ji sosai, yana kwanciya bacci ya ɗauke shi, Safiyyerh ma kusa da shi ta samu ta kwanta, bacci ya ɗauke ta lokacin data gama shigewa jikinsa yayinda shi kuma ya zagaye ta da hannunsa gabaɗaya ba tare daya sani ba, sau biyu Ammo na shigowa tana ganinsu rungume suna bacci ta rasa kunya ke kamata ko mene? Ita dai ba zata jure wannan abin ba, duk da tana da yaƙinin basu gama sanin mene auren ba yanzu. A dawowa ta uku kuma sai taga gabaɗaya Safiyyerh ta haye ruwan cikin Mutallab tana bacci" hankali kwance ta ƙanƙamesa kamar ta samu filo cikin sauri ta saki labulen ta fita. * Switzerland/ Bern "Yanayin ƙasar tana matakin hadari ne, sama-sama mizanin saukar ruwan sama 5% sai laimar iska 93%" daIska km/s 6 sai hakan ya saka gabaɗaya yanakin ɗaukan wani irin sanyi mai rasa jiki da ƙasasuwan "mutane, kowa ka gani da rigar sanyi jikinsa da kuma takalmi babba snow nata sauka a jikin mutane da kyau kamar yayyafin ruwan sama domin ita ke sauka madadin ruwan da ake saka ran samu a yau ɗin." "A cikin haɗaɗɗan gidan ma hakanne, sai ya zama gidan shiru kamar ba kowa. A hankali ya murɗa handle" "ɗin ƙofar ɗakin da hannunsa da yake cikin safa ya shiga, idanunsa ya dinga rarrabawa ta cikin baƙin glasses ɗin daya saka, gano ta ya yi tsakiyar gadon da rufe jikinta sosai tana bacci peacefully. A hankali ya ƙarasa ya tsaya sai kuma ya nemi waje ya zauna ya saka hannunsa mai ɗan sauran sanyi duk da safar hannun ya zame duvet ɗin data rufe kanta da shi, ko ya ce aka rufe mata. Farar fuskarta ta bayyana, ya zuba mata ido ta yi wata ramewa ta ban mamaki, ya sake haske sai siririn hancinta da ya sake yin tsayi ƙwarai, hannunta ɗaya cikin bakinta ta ƙanƙame teddy ɗin dake kusa da ita, ga azkar ɗin dake kuma gefe, ya miƙa hannunsa ya kama hannunta ya riƙe cikin nasa, ya jima zaune sai kuma ya tashi ya fice daga cikin" ɗakin gabaɗaya yana rufe ƙofar without making any sounds. "Bayan wasu mintuna aka sake buɗe ƙofar tare da shigowa, daidai nan itama ta buɗe idanunta da ƙyar" "suka haɗa ido da Mj ya yi mata murmushi ya ce ""bacci daɗi favourite"" ta ɗan ɓata fuska sai ta ce ""He is here?""" """Yes, he is here, but he already lefted"" ta yi shiru kawai tana mirginawa gefe. Mj ya nemi waje ya zauna" "ya ce ""Ya kika sani?""" """Me fa?""" """Yazo""" """Kamarya?""" "Ya watsa mata harara ya ce ""Aafiyyah ki rage tunanin nan please kin ji, tunda Paaah ya yanke hukunci" "shikenan babu sauyi kin sani, ki yi addu'a idan akwai rabo sai kiga komai ya zama labari da tarihi ko?""" """Labari? Tarihi?"" Aafiyyah repeat the words tana kallon Mj tana kame fuska sosai ba wasa." """Yes mana, Aafiyyah amma kina da tabbacin Safiyyerh zata bawa yaron wasiƙun nan?"" Mj ya tambaya" "yana kama hannun Aafiyyah ya riƙe cikin nasa, a hankali ta langwaɓe a jikinsa tana jan numfashi, tunda suka zo ƙasar aka je asibiti da ita, bata san meke faruwa ba, da zuwan da komai sai farfaɗuwa ta yi taga ana maƙala mata jini a jika, satinta uku kuma aka sallame ta zuwa dawo gidan Paaah da yake ƙasar. Bata taɓa fita ba, ko parlo bata fita kodayaushe tana ɗakin al'amarin kuma daya damu duka ƴan gidan kenan, sun san Aafiyyah bata barin kowa ya zauna lafiya ko ba zata kula mutum ba sai ta yi tsokana ta nemi faɗa" ga tsinannen bada labari kamar ƴar jarida. "A hankali ta ce ""Yaya, i trust Safiyyerh zata bashi in sha Allah"" ta ce ƙirjinta na ɗagawa da ƙarfi sai kuma" ta kalli Mj kamar za ta yi magana tai shiru. "Mj ya ce ""Allah ya sa, at least da wayarta ya shiga shine kuma kinga an sauya miki sim an yi deleting" "komai, i am sorry Aafiyyah, ki fahimci Paaah""" """He is my father, my father yana da iko dani ko ka manta?""" """Ban manta ba, ina tsoran ki furta kina son abu, na san yadda kike son Mutallab, na sani Aafiyyah,na ji" "ban kyauta ba da na yi supporting naki wajan faɗa masa a wajan karan amma na hana ki, it's all my fault, fault ɗina ne Aafiyyah, laifi na ne"" shassheƙar kuka ta fara tana girgiza kanta" "Mj ya ce yana matse hannunta, ƙara shigewa jikinsa ta yi kamar mage hawayenta na sauka a jikinsa sosai" "ta ce ""But they promised me, sun mini alƙawari yaya, sun mini yanzu me ya saka suka karya al'ƙawarin" "nasu? They break the promises""" """Sun miki alƙawari tabbas, kin cika naki al'ƙawarin tabbas, kin kuma yi biyayya tabbas, ban san ya aka yi" "reshe ya juye ba""" """Kamarya?""" """I don't know, amma dai yanzu tunanin Paaah na amincewa da Mutallab bana karatunki bane, ya sauya" "shawara you can ask him """ "Aafiyyah ta yi cak, tana kallon Mj idanunta ya yi jajur ƙirjinta na bugawa da ƙyar take fusgar numfashi, ta" "ji iskar wajan na neman yi mata kaɗan a hankali kuma ta fara tuna ranar data ganshi, ranar da ta yi wa zuciyarta alƙawari, ranar da Paaah ya yi mata alƙawari, ranar data ji ta fara rayuwa domin shi, ranar data ƙara samun ƙwarin zuciya da confidence ɗin yin karatu domin ta same shi as her husband,domin ta rayuwa da MUTALLAB. Ranar asabar ce na fito da sauri jikina sanye da blue black ɗin abaya cikin sauri kamar zan faɗi, ina tafe ina faɗin ""Yaya zan ranka ka please, ina son siyan chocolates a hanya,kaga da muka dawo ban fita ko'ina ba, please yaya"" a hankali naga ya juyo ya kalle ni sai ya mini alama nazo, ina ƙoƙarin shiga motar Yaya Mj sai motarsa ta shigo ya fito cikin sauri, wata uwar harara ya doka mini da sauri na ɗauke kaina a raina ina faɗin ya ci kansa, na shiga gaban motar Mj ya ja. A lokacin sai na ji i feels comfortable na ji zuciyata wasai na ɗauki wayata na dinga yin bidiyo a hanya ina yi wa yaya Mj gwalo, sai" ya yi mini murmushi. """Oh Allah"" na ce daidai lokacin da muka tsaya a danja, sai dai me tsayuwar tamu ya yi daidai da ƙarin" "gudun zuciyata, irin gudun da take mini a duk sanda zan haɗu da abin alheri ko na tsiya, na lumshe idanuwana ina shaƙar iskar ƙasata Nigeria da na yi missed nata, buɗe idanun da zan yi na buɗe akan ƙaddarata, when my destiny started, i saw him, i just saw him da wasu kaya a jikinsa duk datti da gajeren wando hannayensa ɗauke da bulo, yana ɗauka daga right side zuwa left side. ""My future husband"" na ce" "a fili ina binsa da wani irin kallo, kamar ban taɓa ganin wata halitta ba a lokacin sai shi." """Who?"" Mj ya tambaye ni, ba tare dana ɗauke idanuna ba na ce ""Gashi can yaya, ɗan matsa na yi masa" "bidiyo na ajjiye"" ya zame kafaɗarsa ya bani damar zura wayata na dinga masa bidiyo, ina murmushi ina kallon shi ina cewa ""Aafiyyah's husband, til-janna, ina son shi yaya, ina son shi i love him"" na ce soundly da wani irin farinciki a fuskata a lokacin." "Mj ya dube ni sai naga ya juya yana kallon shi ya ce ""Waye mijin naki? Yaushe kuma aka ɗaura?""" "I see the tsokana in his eyes, na gano tsokana a cikin idanun Yaya mj, but i don't think cewa tsokanar ta" "gaskiya ce. Sai na ce ""Yes, zai zama mijin Aafiyyah wallahi ina son shi, za ku aura masa ni?""" """Ask Paaah first, ki tambayi Paaah ki ji"" na ɗaga kafaɗa na ce ""Zan iya"" daga nan na fara ƙoƙarin buɗe" "ƙofa, trying to out of the car, sai Mj ya yi saurin sakawa motar key ya ce mini ""Ina za ki Aafiyyah?"" Ina yarfa hannuna na ce ""Wajan shi, Yaya zani gunsa ne don Allah"" sai kawai ya ja motar ya yi gaba, ganin da gaske ƙoƙarin fita nake son yi, a lokacin na ji zafin Mj na ji kamar kuma zuciyata ta buɗe ne, na ji wani irin damuwa a cikin raina sai na fara tunanin ta ina zan sake ganinsa? I don't know, ban sani ba, san ina zan sake ganin Blackman ba. Sai na fara kuka hakan ya saka naƙi siyan chocolates ɗin har muka koma gida. Was the first abin da na fara zuwa wajan Paaah a lokacin kuma ya dawi gida, na same shi zaune akan kujera yana duba jarida cikin jin daɗi na ƙarasa na ce ""My Paaah, my handsome father, the great" "and greatness father, good evening """ """My talkative and smartness daughter in the world"" Ya ce yana mini wani irin murmushi cike da soyayya." "Muka rungume juna, sai kuma na yi shiru na ji abin da zan faɗa kamar ya yi girma, sai kuma na tuna" "Paaah ya ce mini shi ɗin abokina ne dukkan matsalata aboki ake faɗawa, sai na gyara zama na shirya faɗa masa cewa naga mijin aure." """Ya aka yi kuma? Wannan bakin gulma ya ɗakko mini ko hira?""" """Dad, i love him""" """Who? Waye? Wa kike so?"" Na ji ya tambaya a yanayi na ruɗewa, domin i can see the fear in his face. Na" "ce ""Daddy, wani na gani kuma ina da tabbacin zaka yarda, kai abokina ne, na gani wani ina so daddy, shi nake son aura, shi nake so ka aura mini don Allah, don Allah, don Allah"" na faɗa ina haɗa hannaye biyu wajan yi masa magiya. Paaah ya zubawa Aafiyyah zuciyarsa na tsananta faɗuwa, shekarar Aafiyyah nawa a duniya har ta san aure? Wanne irin girma ne haka, a hankali kuma yanayinsa ya fara sauyawa sai naga" "ya yi mini murmushi ya ce ""Waye wannan kuma?""" """Ban san shi ba, ban kuma san sunansa ba, ban san inda zan ganshi ba, ina da tabbacin zan sake ganinsa" "in sha Allah""" """Accepting, na amsa amma da sharaɗi biyu zuwa uku""" """Na amince daddy, idan zaka mini al'ƙawarin aura mini shi""" """Kar ki kuskura ki faɗa masa kina son shi, babu kyau haramun ne a cikin addinin musulunci yarinya" "ƙarama ta ce tana son namiji sai ta girma, kuma Allah yana yin azaba ga duk wanda ya yi hakan, ni da kaina zan aura miki shi idan lokacin ya yi, kawai ki san waye shi ok? Na biyu ki mayar da hankali a karatunki, ki nutsu kar ki sake mini zancen shi sai ranar da kika kammala secondary school ok? Idan kika mini wannan alfarmar to kin cinye zan kuma aura miki shi, yanzu karatunki nake buƙata fiye da komai ina da buri akan karatunki?"" Sai na ji daɗi duk da ina fargabar ina zan sake ganinsa? ""Daddy ina son zama" "kamar ka ai""" """Da gaske?""" """In sha Allah, kuma na maka al'ƙawari"" ya jinjina mini kai ya ce ""Za ki zama kamar ni ɗin, tabbas za ki" "zama darling""" "Na miƙe na fita, a daren na kasa bacci burina na faɗawa Safiyyerh na yi saurayi, mijin aure naga wanda" "nake so, sai na tuna Safiyyerh bata da waya, kuma bani da number Ummeyh dole na yi haƙuri. Juyi kaɗan kuma shi nake gani cikin idanuna. Washegari weekend na shirya zuwa Fgc, babban abin da ya bani mamaki ganin abokina kimiyya tare da wanda zuciyata ke bugawa a yanzu domin shi, na yi yunƙurin masa magana sai na zubawa yanayinsa ido, nan take na gano waye shi, sai na share maybe shariyata" zata janyo attention nasa zuwa kai na. """Kimiyya waye wannan?""" """Muhammad Mutallab Abdullahi""" """Uhmm, bani labarinsa""" """Me ya sa?""" """Ina son shi, na faɗawa Paaah, Mj ya sani amma kar ka faɗa masa, zan sanar masa da kaina, alƙawari na" "yi wa Paaah ba zan masa magana ba, kaga idan ina son gamawa da duniya dole na bi umarnin daddy. Amma zuciyata zafi take a yanzu, na ji ina son masa magana wallahi ina son shi""" """Sunansa Mutallab a nan unguwar Birget yake, mahaifinsa kuma shine mai makarantar almajirai sunansa" "Malam Abdullahi. Mutallab an taɓa yunƙurin yi masa aure amma Allah bai yi ba, ƴan matan na mutuwa" "Diyna da Jaanah, kuma ya taɓa shiga state cid da laifin sata, wannan makarantar da kike gani Jeddah ce ga saka shi, rayuwarku ba zata yi ɗaya data Mutallab Aafiyyah """ """Shi ba mutum bane?"" I ask Kimiyya. Ya ce mini ""Tsarinku ne ba ɗaya ba, kuma mahafinki ba zai amince" "ba Aafiyyah""" """Uhmm, Kimiyya kenan na faɗa maka dai, kar ka faɗa masa ina ta neman Safiyyerh saboda na mata" "albishir sai na tuna bata da waya. Ganin Mutallab na neman zuwa wajan namu na yi sauri na bar wajan zuciyata na rawa da yadda naga fuskarsa a cunkushe da sauri na faɗa mota. Tun daga ranar kullum da tunaninsa nake kwana nake yi ne, na ji ba wanda nake tausayi a duniya sai shi, na fara saka shi cikin jerin wanda nakewa addu'ina. Ranar da Safiyyerh ke faɗa mini ta faɗa soyayya sai na yi tunanin ko Captain take nufi? Na buƙaci ta faɗa mini taƙi, sai na share domin ta saba yi mini irin haka, na yi yunƙurin faɗa mata cewa nima ina son wani sai Paaah ya buɗe ƙofa ya shigo hakan ya tilasta mini cewa “I will tell you something” sanda na faɗawa Safiyyerh da dukkan yarda ta na faɗa mata, kuma na ji sauƙin zuciyata" daman na riga na jima da iya rubutun Safiyyerh. Sai na fara yi masa wasiƙun da Safiyyerh's handwriting. Ina son karatun English novels hakan ya saka na "iya wasu abubuwa da yawa, kuma ina jin yadda Ummi ke yawan yi wa Paaah addu'a sai na yi addition" addu'a ta akan Mutallab a cikin wasiƙun. "Duk wata exam da zan yi ina yini da tunanin ina gamawa zan cika muradin Paaah, bana gazawa na" "amince yin karatun shine zai bani damar amsa sunan matar Mutallab. Sanda na ji Safiyyerh na cewa bestie ko a jikina domin na yarda da ita, kuma na ji zata iya mu'amala da Mutallab ba wani abune, tsoro ne ya kama ni don ba zan manta cafeteria ba sanda take cewa what if I tell you I love you? Na hango soyayyar Mutallab a cikin idanun Safiyyerh. Fargaba ta kama ni na fara saka tunani wanda ya haifar mini" "da ciwo, naƙi faɗawa kowa dalilin wannan ciwon domin na yi alƙawarin ba zan sake maganar Mutallab a" "wajan Paaah ba amma Yaya Mj ya san komai, na fara saka shade glasses domin kallon Mutallab is my" favourite thing. What a blind love! """Aafiyyah"" na firgigit ta dawo cikin hayyacitaa da sauri ta hantsila ta sakko duk da jikinta ba ƙwari," idanunta rufe ruf. Tun daga cikin ɗaki take kiran sunan Paaah har ta isa cikin bedroom ɗinsa. """Aafiyyah""" """Ummi, ina daddy""" """Gani, ya aka yi ne?""" "Cikin sauri Aafiyyah ta zube a gaban Paaah tana riƙe ƙafafuwansa ta ce ""Paaah ka mini al'ƙawarin aura" "mini Mutallab, daddy na yi maka al'ƙawarin yin karatu, ka ɗauke ni daga ƙasar ba tare dana faɗa masa ina son shi ba, daddy ka ce yanzu ba zan koma ƙasar ba, zuciyata daddy, daddy zuciyata ina son Mutallab Ka mini al'ƙawari kar ku karya, kamar yadda nima ban saɓa sharuɗan daddy ba"" Aafiyyah ta faɗa tana" sakin wani irin kuka tare da riƙe ƙafar Paaah. """Ummi ba har dake a yi mini al'ƙawarin ba? Don Allah ku mayar dani Naija, ina son komawa Nigeria don" "Allah """ "A hankali Paaah ya ajjiye jaridar hannunsa, ya juya ya kalli Aafiyyah sai kuma ya ce ""Yes, i promised you," "e, na miki al'ƙawari zan aura miki shi, amma na sauya al'ƙawarina a ranar dana fahimci kin yi zurfi a soyayyarsa, ban san waye shi ba,ko sunansa ban riƙe ba, ban kuma taɓa ganinsa ba, talaka ne mai kuɗi ne yaya yake i don't know, i really really don't know. Buɗe kunnenki da kyau Aafiyyah, kina da mijin aure, kina da wanda za ki aura, ki cire wannan yaron a ranki, ki daina wani mafarkin da kike na soyayyarsa...""" "Ya miƙe tsaye, Aafiyyah ta tsaya da kukan cak da ƙyar ta ce ""Me ya sa?""" """Saboda na yi miki mijin aure tun kina zanin goyo, kina yi al'ƙawarin bada auren ki, kina da wanda za ki" "aura, not him..." Akwai update a arewa bayan page ɗin nan keep reading and following. "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 41: No Options" "Gaban Aafiyyah ya tsananta faɗuwa ta dinga kallon Paaah da yake cewa ""Ba zan aura miki shi ba, ba shi" "nake da ra'ayin ki aura ba kin ji ko?"" Ta jinjina kai kawai ta kasa cewa komai sai ajjiyar zuciya da take saukewa." """Kar kuma ki ji kamar auren dole ne, bana dole bane, za ki so ɗayan ma, kamar yadda kike son wannan""" Paaah ya ce yana kallon Aafiyyah sai kuma ya nemi waje ya zauna tare da harɗe ƙafafuwansa waje guda ya cigaba da kallon Aafiyyah kafin ya ce. """Safiyyerh!""" "Aafiyyah, ta kasa amsawa sai kanta data ɗago ta zubawa Paaah jajayen idanunta da suke buɗewa da" "ƙyar. Ya ja numfashi ya ce ""Buɗe bakinki ki amsa ni Safiyyerh, buɗe baki ki yi mini magana domin na tabbatar da abin da nake faɗa miki ko kina fahimta ok?"" A hankali ta ce ""Na'am, ina ji daddy"" Ummi ta zauna, Mj ya nemi waje ya tsaya yana mai jin tausayin Aafiyyah a cikin ransa, domin an gama saka mata" "rai, an yi mata al'ƙawari." "Paaah ya ce ""Safiyyerh, nagartattun yara sune masu bin umarnin iyayensu, kuma baza su taɓa taɓewa ba" "idan sun yi biyayya. Ina da wanda na zaɓa miki a matsayin mijin aure, ba dan wancan da kike so ba cancanta ba, ba kuma don bashi da nagartar da zan iya ɗaukan ki na bashi bane, da ace ban yi al'ƙawari akan ki ba, wallahi wallahi wallahi Allah kenan a yau zan koma Nigeria na nema miki auren shi, ko halin" "riƙe ki ne bashi da shi ni mai iya yi masa komai ne, wanda zai riƙe maka yarinya har tsayin rayuwa ai ba" "abin wulaƙanta wa bane. Kar ki ji a ranki ko wani dalili ne, a'a, sunan auren ki AL'ƘAWARIN AURE. kuma" "in sha Allah mutuwa ce kawai zata hana hakan faruwa""" "Ya yi shiru yana fahimtar Aafiyyah, sai ya ɗora da ""Daman kuma ita yarinya budurwa ba ita ke da hakƙin" "zaɓawa kan ta mijin aure ba, yau da ke bazawara ce to ba ruwan kallo da gajiya, Safiyyerh kina da miji, idan yanzu ma kika ji kina son auren in sha Allah a satin nan zan miki shi, domin da wata matsalar gwara wata, ke yarinyar kirki ce na san za ki fahimce ni ba zan cutar dake ko cutar da rayuwarki ba""" "Kai ta fara girgizawa ta riƙe ƙafafuwansa da kyau ta ce ""Na roƙe ka don Allah, kar ka mini auren dole" "Paaah, kar ka haɗa ni da wanda bana so, an ce mace na iya mutuwa ko ta kashe mijin idan aka yi mata auren dole, Paaah kai ka mini al'ƙawari, ka nanata mini, na yi yadda kake so, na jure kar ka zo mini da wata buƙata ta auren wanin Mutallab don Allah Paaah, don Allah ,"" ta kasa cigaba da maganar sai ta" ɗora kanta a saman cinyar Paaah tana shassheƙar kuka. """Don't do this to me""" "Ta ce very slowly. Mj ya ce ""Paaah don Allah, ka janye maganar nan""" """Get out my friend""" "Paaah ya cewa Mj yana nuna masa hanyar waje fuska a kame babu alamar wasa, Ummi ta buɗe baki za" "ta yi magana nan ma ya yi mata alamar ta yi masa shiru. Aafiyyah ta dinga rusawa Paaah kuka da birgima kar a yi mata auren dole, fuskarta ta yi jajur ya tanƙwashe ƙafafuwansa yana kallon ta kawai, idan tashin hankali ne irin wannan ai ya saba gani wajan Aafiyyah, kuma ya san at the end dole za ta yi haƙuri ta bar maganar yana da wannan tabbacin. Sai data gama kukan ta yi bacci saman carpet ɗin parlon Paaah daman kuma ba wani kuzari gare ta ba, ya miƙe a hankali ya ƙarasa wajanta yana duƙawa ya ɗauke ta, kai tsaye bedroom ɗinta ya shige da ita. A hankali ya kwantar da ita saman bed yana gyara mata" kwanciya da rufe ta da duvet. """I am sorry Safiyyerh"" ya ce a nutse domin ya san ya yi mata laifin, ya yi wasa da tunaninta tun farko," wataƙila da ya ce mata tana da wanda zata aura a sanda dazo masa da tata buƙatar da tuni ta mance da wannan babin. """Ki yi mini afuwa, ki wa mahafinki afuwa, ki fahimci mahaifinki Safiyyerh. Stay strong my darling"" ya ce" yana shafa kanta sai kuma ya fara mata addu'a kamar kodayaushe idan tana bacci bayan ya kammala ya miƙe ya fice daga cikin ɗakin. "Mj ya samu Paaah a ɗakin hutawa, kallo ɗaya kuma Paaah ya yi wa Mj ya ce ""Idan akan batun Safiyyerh" "ne kar ka mini magana""" """Paaah, dole zan maka don Allah, ka saurare ni""" """To Ubana""" """A'a ka yi haƙuri, ba haka nake nufi ba wallahi""" """Ok, ya kake nufi Mj?""" """Paaah, Aafiyyah yarinya ce mai sauƙin kai duk da rigimarta da karaɗinta da iyayinta, tana da faɗa na" "sani kuma tana da haƙuri, duk wanda zai san haƙurinta to baya na zai bi. Tun tana ƙarama ake raba faɗa" "da ita, domin bata yarda aci zalinta kuma bata yarda taci zalin wani, amma ana ce ta yi haƙuri an gama. Amma tana da ƙulafuci da saka abu a rai, ban san me wannan zai haifar ba""." """Ok, kana tunanin shawarar dana yanke zai haifar da wani abu ne?""" """A'a, alheri kawai nake hangowa Dad. Amma wannan zamanin da muke ciki an daina auren dole saboda" "fitun-tun da hakan ke haifar wa, ana shiga haƙƙin yara ne kuma kasan auren yanzu da soyayya ma yaya aka ƙare balle wanda iyaye suka ƙulla? Sau nawa ana bada labarin an yi wa yarinya auren dole ta kashe mijin da abokansa, ko ta kashe kanta, ko ta fara yawon bin maza. Astagafirulla; ba haka muke fata ba, lokaci bai bar komai ba, zamaninku daban na yanzu daban don Allah Paaah ka janye, a bar Aafiyyah ta yi" "karatun kamar yadda aka yi al'ƙawari ta koma ta auri wancan yaron shikenan""" """Ina Mj""" """See me here Paaahh """ """Wannan maganar mu bar ta iya nan, koda wasa na ji kuma ka yi hanya ko zama sanadin haɗuwar" Aafiyyah da yaron zaka gane cewa ni ne ubanka kuma nine na kawo ka duniya. Kuma daga yau ka zama "idanunta, ka ajjiye tunaninka a kan ta, motsinta da duk abin da take yi duk da na yi yaƙinin ba zata" "bijirewa umarnina ba, amma she is smart girl, bana son maganar ta yi tsayi""" """Yadda ka ce haka za'a yi ranka ya daɗe, Allah Ya ƙara girma""" """You can leave""" "A daddafe Aafiyyah ta yi baccin mai cike da wahala, da wani irin mafarki mai ban tsoro, tun kuma daga" "sanda ta farka wani abu ya tsaya mata a maƙoshi, ga wan irin ciwon kai daya saukar mata mai tsananin zafi da ƙyar take buɗe idanunta. A hankali ta sakko daga kan gadon tana dafe bango, ruwan zafi ta haɗa ta yi wanka tare da yin brush saboda bakinta babu daɗi, tana gamawa ta ɗauki alimon ta shafa a jikinta kamar yadda Ummi ta nuna mata saboda tsane jiki da kare kai daga tashin wari saboda shigowar lokacin girma daya gama bayyana muraren a tattare da Aafiyyah ɗin. Sallar issha ta yi, sai ta samu kan ta da yin addu'a, addu'ar zaɓin alheri tsakaninta da Mutallab, da kuma wanda Paaah ya zaɓa mata a matsayin wanda zata aura ɗin. Babban tashin hankalin Aafiyyah bai shige yadda bata san waye zata aura ba, ita tana da kalar zaɓin ba kowanne namiji ne zai iya zama kalar ta ba, zaɓin ta ba, ba kuma kowanne namiji" ne zai iya zama test ɗin ta ba. "Ummi ce ta buɗe ƙofa ta shigo, da sauri Aafiyyah ta yi murmushi tana sakin fuskarta kamar ba ita ba," "Ummi ta nemi waje ta zauna tana duban ta kafin ta ce ""Ki fito ki yi dinner, sai na rasa zaman da kike cikin" "ɗaki kwana biyu""" """Bana jin yunwa""" """Me kika ci""" """Kawai, na ji i am ok""" """Safiyyerh""" """Na'am Ummi"" Aafiyyah ta amsa, tana jingina da jikin gadon idanunta rufe tana jin yadda ake mata ihu a" "cikin ƙwaƙwalwarta. A tausashe Ummi ta ce ""Wallahi ba za ki taɓa wulaƙanta ba a wajan yi wa iyaye" "biyayya, ki ci-gaba ki jure ai ke jaruma ce, ki yi ta addu'a dare ta rana Allah ne kaɗai ya san wanda zai zama mijinki""" """Ummi ku ne kukai mini al'ƙawari fa? Me ya sa tun farko ba'a faɗa mini gaskiya ba? Ai kun san kuna da" "hakƙi akai na, wajibi ne a matsayina na ɗiya a wajanku na sauke hakƙin iyayena. Da ba ku yi mini al'ƙawari ba, kun san yadda duk maganarku ke zama hadda a cikin tunanina bana wasa da kowanne furucinku, i trust you, me ya sa Ummi?"" A hankali Ummi ta ce ""Saboda mun san mun isa dake ne, shine kawai"" murmushi Aafiyyah ta yi, tana goge idanunta ta ce ""You are right, kin yi gaskiya ni ikon ku ce ai, na amince da zaɓin Paaah, na amince"" ta ce a hankali tana jin ƙofofin zuriyarta na tushe kansu da kansu" ta rasa iskar shaƙa ko kaɗan ta rasa kuma yadda za ta yi ta daina jin zafi a cikin ƙirjinta. """Da gaske kin amince da zaɓin mahafinki?""" """E, na yarda""" "Ummi ta ɗago Aafiyyah ta rungumeta a ƙirji tana ta mata addu'a, sai Aafiyyah ta kyalkyale da dariya ta ce" """Ke uwa ce, you are the best mom ever Ummi""" """Ma sha Allah, Allah Ya yi miki Albarka ya shiga cikin lamuranki""" """Amin""" "Ummi ta jima tana yi wa Aafiyyah hira kana ta miƙe ta fita, tana fita Aafiyyah ta sulale ƙafa tare da" "durƙushewa ta saki wani irin gunjin kuka tana fige hijjabin jikinta tare da farke gaban rigarta, ji take kamar kayan jikinta ne suka hanata shaƙar iska yadda ya kamata, bata san cewa gabaɗaya zuciyarta ta ce a cunkushe kuma a ƙuntacce ba, duk yadda Aafiyyah taso amincewa tare da kawar da batun Paaah kuma ta yi accepting amma zuciyarta taƙi bata damar hakan, tunaninta ya tsaya ƙwaƙwalwata ta yi hooking ta daina fahimtar komai. Ta yi shiru tana zubawa wani waje idanu, sai kuma ta zabura ta ɗauki wayarta tare da shiga wani waje data ɓoye pictures, bidiyon data fara yi masa a ranar data fara ganinsa ta shiga ta fara gani, sai murmushi ya suɓuce mata ta dinga kallon bidiyon tana murmushi da hawaye at the same time. Sai ta harare shi kamar yana gabanta ta ce ""Ka dinga fushi dani for no reason, kana fushi dani ni, ni ko?"" Ta tambayi bidiyon tana nuna kanta, sai ta yi baya ta zauna zaman dirshen a hankali kuma ta shiga ɗaya picture ɗin ranar da ta yi masa shi da Safiyyerh suna zaune, ya jingina da jikin bishiya ya kafe Safiyyerh da kallo fuskarsa ba walwala sai lips ɗinsa da sukai jajur, Aafiyyah ta yi zooming photon ta saka yatsa ta shafi fuskarsa tana murmushi ta ce ""Stay strong my, kar ka manta ni ko sauya, ko a dramar da" "mukai ne kar ka manta ni don Allah"" sai ta sake shafa fuskar ta ce" """Na san kana so na"" sai kuma ta yi shiru ta ce ""Zaka kira ni? Ka kira ni don Allah zan ta jiran kiran ka, a" "sanda Safiyyerh ta faɗa maka saƙona a sannan zaka fara nemana ido rufe"" Aafiyyah ta kwaɓe fuska ta ce ""Amma ina jin tsoron haɗuwa da kai, kuma ina son ganinka ka zo mini a mafarki ka ji? Za ka zo?"" Ta" tambayi photon Mutallab kamar yana gabanta. Haka ta wanzu ta ce Wannan ta ce wancan. """Ya Allah make it easy for me, for him Allah ka sadani da shi a duniya kafin na koma gare ka"" ta ƙanƙame" "jikinta waje guda, sai yau dinga jin wani iri a lokaci na farko, ta rufe idanunta kamar a lokacin yake kissing lips ɗinta. Bata taɓa tunanin tana jin tsoron wani abu a rayuwa ba, irin yadda take jin tsoron ganin cikin ƙwayar idanunsa, a duk sanda zata kalle shi ta cikin glasses ɗinta, tana hango wutar faɗa sosai a cikin jirkitattun idanun nasa, tana hango kamar yana mata kallon mai laifi, kallon jin haushi, abu ɗaya ne ke mata daɗi idan ta hango abu mai sanyin a cikin idanun nasa. ""Innalillahi, i love him so much, i love you so much Tayo, i love you today, tomorrow and always forever. Allah Ya tsare ka ya kare ka, ko aure ka tashi" "yi ka auri Safiyyerh kafin na zo gare ka, don Allah ka neme ni, ka ji ɗan baƙin Muɗallabina? Ka ji masoyi""" Har dare ya raba tana zaune. Sai dai har aka yi kiran farko na asuba idanunta ko motsi bai yi ba da "zummar yin bacci, bata ma jin baccin kuma tana jin daɗin zama ita ɗaya, sai ta ji bata son ganin kowa da komai, ta ji kamar sabuwar duniya akai mata ita ɗaya wacce zata dinga rayuwa a cikinta, sai kuma ta dinga hira ita ɗaya ko ta dinga jin kamar ana kiran sunanta." * "Yamma ce lis amma a haka ya kammala abin da yake yi ya nufo gida, fuskarsa a kame kamar wani" "babban mutum a kodayaushe tunda ya jima gina kan shi akan cewa ya kai munzalin kowanne namiji da yake kawai. Yana yi yana sosai tsakiyar goshinsa a haka ya tsallake almajiran da suke faman karatu ya shigo cikin gidan, shi shaf ya manta da wani bikin Sa'adah da ake shirin yi a kwanakin nan. ""Ya zaka dinga faɗo mana babu sallama ne? Ni sam banga ma'anar da zaka dinga zarya a tsakaninmu ba tunda ka mallaki hankalinka ka tunda har mata ka mallaka"" Inna Binta ta faɗa cike da masifa da kumfar baki. Bai" kulata ba ya tsallake ya shige ɗakin Ammo yana ajjiye ledar dake hannunsa. "Sai Mama Zaituna ta yi shewa ta ce ""Wannan fanɗararren yaron ne kike tunanin zai mana sallama?" "Dama dai ba jinin yarabawa bane"" ta ce tana miƙewa." """Ko jinin waye shi ta shafa kuma zan ɗauki mataki a kan shi wallahi idan gidan ubansa ne ni kuma gidan" "mijina ne ehhe"" Inna Binta ta bada raddi." "Sai kuma Mama Zaituna ta girgiza kai kawai kamar za ta yi shiru sai kuma ta ce ""Kee iya bakinki ɗan" "masu gida ne, kada kuma ki saka ya miki kiranye ki zura da gudu har haɗeja wallahi""" Mutallab na jinsu ya yi shiru domin ya lura Ammo da Sa'adah bata nan. Yana shiga ɗakin suka haɗa idanu "da sauri ta sunkuyar da kanta idanunta ya yi jajur alamar ta ci kuka, bai kula ta ba ya tsaya daga tsayen Safiyyerh ta miƙe tana murmushi domin wata jarrabawa data faɗa data ganshi dukkan wani damuwarta ke yayewa ta ce ""Shine sai yanzu zaka dawo? Babu daɗi gidan"" ta ce tana ƙarasawa inda yake sai kuma" "ta yi sauri ta ce ""yen yen ƙazami warin dauɗa kake yi, sai gumi kake haɗawa bestie ƙazami""" "Ya yi mitsi-mitsi da idanunsa ta ce ""ba zan taɓa ka ba, kar ka shafa mini dauɗa, dama Ammo ta ji ƙan ka" "ta yi maka wanka yau""" "Ya zuba mata idanu, sai ya cije lips ɗinsa ya fara takawa zuwa cikin ɗakin ita kuma ta yi baya tana cewa" """Mai dawa ya zama ƙazami, mijin Safiyyerh mai warin dauɗa"" idanunta ya faka ya damƙo ta, tare da janyo ta kusa da shi idanunsa da suka ƙanƙance a kanta da ƙyar ya ce ""Kika ce me?"" Sai ta fara inda-inda tana ƙifta idanunta sosai ta ce ""Ba magana na yi bafa, don Allah ka je ka yi wanka sai ka dawo mu yi fira" "ko?""" """Ƙazami ne ni?"" Ya faɗa a daƙile yana jin muryarsa a ƙirjinsa saboda yadda furucin ya fito kamar an masa" "dole. Ta girgiza kai kai ta ce ""Yaushe na ce haka?""" """Ni kike cewa ƙazami?""" """Ka yi haƙuri to""" """Ni ne ƙazami? Kwaɗo kike so na zama? Na dinga rayuwa a cikin ruwa ƙarewar wanka ko""" "Ta tura masa bakinta tana kawar da kai gefe ta ce ""Ai wanka cikon imani ne, don na ce ka yi wanka bai" "zama haramci ba ai"" ta ce a shagwaɓe tana sake matsawa baya, ganin yadda yake nishi da numfashi a" gaggauce yana sake matsawa inda take yaƙi ce mata komai kuma. "fuskarta ya dinga bi da kallo, da ɗan mitsitsin bakinta da laɓɓanta da suke motsawa. A sama ta ji" "maganarsa ya ce ""Zo ki mini wankan, yau sai kin mini wanka""" """Wallahi ba zan iya ba""" """Hmmm"" ya ce kawai yana cire rigar jikinsa ya yar a tsakiyar tsakar ɗakin, ta yi saurin rufe idanunta, sai" "kuma ta buɗe su da ƙyar saboda ganin suma ƙwance a ƙirjinsa baƙa suɗik. ""Don Allah na zuba maka ruwanka, ka je ka yi """ """Wari nake ko?""" "Ta girgiza kai ta ce ""Ni ban ce ba""" """Kin ce mana, ko dai ki mini wankan nan, ko na kashe ki da warin, ke ko na yi niyyar yin wankan ba zan" "ba"" ya yi maganar yana sake tunkaro ta. Safiyyerh ta ce ""Haba mana, idan ka kashe ni kuma yaya kenan? Ni dai don Allah na zuba maka ruwa ka yi?""" """Nawa za ki biya na yi?""" """Sai na baka kuɗi""" "Ya ɗaɗɗage girarsa biyun da suke a cunkushe, sai ya yi baya ya kwanta a kan katifa alamar bashi da" "niyyar yin wankan. ""To yanzu idan na baka kuɗi za ka yi?"" Ya jinjina kai ba tare daya kalleta ba, ita dai haka kawai yau ta ji tana jin shakkarsa. Ta je cikin kayanta kuɗin da bai san dasu ba ta ɗakko dubu ɗaya ta ce ""To gashi a yi mini wankan dubu ɗaya, daga jeji kake fa ƙila wata dabbar ka farauta shine zaka kwanta haka?"" Yana daga kwancan ya mirgina idanunsa suka nutsa ya miƙa mata hannu alamar ta bashi kuɗin, cikin rashin sanin dabara ya yi mata sai ta matsa daga tsayen ta miƙa masa kuɗin ta ce ""Yawwa gwanin na iya mijina"" maimakon ya amshi kuɗin sai ya cafko hannunta ya cillota kan shi, ya mirgina ƙasa ya danne ta yana sakar mata nauyi, Surayyerh ta runtse idanunta tana jin warin rana na dukanta cikinta" "na juyawa tana nishi ta ce ""ƙirjina, cikina, cikina"" ya sake danne ta ya ce ""Wa kike cewa ƙazami?""" """Da kaina nake""" """Kan naki na waye?""" "Ta yi shiru, sai ta fara masa shagwaɓa ta ce ""amai nake ji, cikina juyawa yake ka yi yawo a raina da yawa" "bestie"" wani irin miskilin shagiɗar da baki ya yi zuwa gefe yana sake tura kanta tsakiyar ƙirjinsa yana da zata shaƙi warin da kyau idan ma shi ɗin yake yi, Safiyyerh ta dinga muruzai idanunta ya yi jajur saboda yadda ya yi mata nauyi a ƙirji, ganin tana kakarin aman da gaske ya saka ya sake ta, ai kuwa ta gudu ta miƙe tsaye ta yi waje tana sheƙa uban amai kamar kayan cikinta zai fita. Mama Zaituna ta bita da idanu, sai suka kalli juna da Inna Binta ta ce ""kin san Allah muna zaune a gidan nan sai dai mu ji kukan jariri, ba dai auren gata da son garta akai masa ba? Ɗan mitsitsin yaro a bashi yarinya haka? Amai take yi fa ki" "duba?"" Ta ce hankali tashe tana leƙa Safiyyerh dake bakin rariya." """E, to. Abin kunya ne dai an yi an zuba masa ido yana danne ƴar mutane a ɗaki saboda ta ƙamar shi auta" "ne, yaro sai ƙifaɗi da ɗan iskan faɗin ran tsiya kuma a ɗakin uwar saboda wani kalar jin daɗi, ana sake masa yana yin yadda ya so"" Inna Binta ta faɗa tana ɗan kyaɓe bakinta." "Da sauri kuma suka sauya zancen ganin Safiyyerh tana shigewa ɗakin Ammo, Mama Zaituna ta ce ""Sannu" "ƴar masu kuɗi, Allah ya raba ki da kayan nauyi lafiya""" """Amin"" Safiyyerh ta amsa, ba tare data san abin da suke nufi ba." "Safiyyerh na shiga ɗakin shi kuma yana miƙewa fuskarsa ba wasani, kamar daren ashirin da bakwai" "saboda duhu. Ya fice ba tare daya kalleta ba, sai ta ji a ranta bata kyauta masa ba, ai mijinta ne taya" kuma zata ce masa yana warin rana? Sai ta ji ta muzanta kuma ta ji zata bashi haƙuri. Tana ta zaune bai "shigo ba, har su Ammo suka dawo daga kasuwa siyayyar bikin Sa'adah data gabatuwar azumi." """Safiyyerh sannu da zaman waje guda, amma mene ya same ki haka kikai zuru-zuru haka?""" "Murmushi ta yi ta ce ""Ba komai, bacci na yi fa"" ta ce a hankali." """Ban yarda ba, ko Muhammad ya miki wani abu ne? Na san halinsa""" "Sai ta yi ƙasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta, dokawar da ƙirjinta ya yi da ƙarfi ya saka ta" "fahimci zuciyarsa ke kusantuwa izuwa tata zuciyar. Ta ɗaga kanta suna haɗa idanu ya watsa mata harara ta yi saurin ɗauke kanta gefe tana kawar da hawayen idanunta, da kuma hana zuriyarta jin zafinsa da gaske. Ya nemi waje ya zauna yana tanƙwashe ƙafafuwansa ya fi ƙarfin mintuna goma sha biyar da zama" "da ƙyar ya cira kan shi ya ce ""Sannu Ammo"" ya ce bisa dole yana kame fuskarsa sosai da kyau kuma." "Wani irin kallo take masa kafin ta ce ""Me ka yi mata?""" """Ita wa?"" Ya bi ba'asi tambayar." """Safiyyerh, kuka take""" "A cikin kansa ya nanata sunan Safiyyerh yana jinjina ƙarfin halinta a ran shi. ""Ina tambayarka mai ka yi" "mata ne?""" """Nima ɗin ai na shirya kawo ƙararta ai, zuwa ta yi tana shinshina ni wai ina wari, ni nake wari ni zata" "cewa ina wari"" ya faɗa a daƙile yana nuna kan shi da yatsarsa tare da nutsar da idanunsa zuwa ciki sai ya yi ƙwafa yana tsuke fuska. Safiyyerh ta girgiza kai ta ce ""Ammo wanka fa kawai na ce ya yi, daga cewa ya yi wanka shine ya danne ni na shaƙi duka zufar jikinsa""" "Ya juya ya kalli Safiyyerh sai ya ce ""Bana ce ki mini wankan ba, ban ce ki mini ba? Kin zo kin mini ne""" "Ammo ta hangame bakinta ta ce ""Na ga abin da ya dame ni, yanzu ita ce zata maka wankan don Allah," "kai baka ji kunyar maganar nan akan idanuna ba yanzu?""" """Ita bata ji nauyin kallar cikin idanun mijinta ta ce masa yana wari ba? Naga dama sai na yi sati ban" "wanka ba kuma wallahi tare zamu shanye warin dauɗar"" ya miƙe tsaye yana doka ƙofar ɗakin ya yi waje ƙirjinsa har rawa yake yi saboda tsananin zafin zuciya. Sa'adah ta bi bayansa da kallo ta ce ""Yau autar ta motsa, masifaffe yaro kawai"" Ammo ta girgiza kai kawai ta ce ""Allah ya shirya""" "Safiyyerh sai ta fashe da kuka, ganin kamar bata kyauta ba kuma ta yi zunubi mai girman gaske. Sai da ta" "yi kuka son ranta sannan Ammo ta ce ""Ki yi haƙuri, zuwa anjima ya manta kin ji ko?"" Ta jinjina kanta Ammo ta ce ""Murɗaɗɗen yaro ne, abin da kake ganin shi ne daidai shi a kuskure yake gano shi. Ki ko yi riƙe sirri Safiyyerh, dana shigo bai dace ki ce ya danne ki ba,ai mijinki shi, sirrinki ki koyi iya zama da shi, idan ya yi niyya yana da sauƙin kai a lokacin da bai niyyar magana ba kar ki kula shi, a sanda ya yi niyyar maganar ma kar ki kula shi kin ji? Sannan kina yin fitsari a tsaye idan ba ki yarda da banɗakin ba, kuma kina tsarkake jikinki, idan za ki yi tsarki ki fara wanke ƙasanki sosai kana gabanki kowanne daban daban, da kin fito wanka ga alimon ki jika ki shafa jikinki yana tsane zufa da hana tashi, ki dinga yawaita addu'a" "cikin lamuranki shima kina yi masa, Allah yana amsar addu'ar mata ga mijinta""" "Ta jinjina kai a sanyaye ta ce ""In sha Allah. Na gode sosai Ammo""" "Yana ƙwance wajejen ƙarfe goma na dare, tunaninta ne a ran shi, yana son yi mata magana sai dai bai" san mene zai ce sai ya share ta kawai ya cigaba da kwanciya yana jin gajiya na saukar masa. "Ƙofa ya ji an buɗe ta cikin shagon, bai juya ba domin ya san ba Goje bane, ya kuma fahimci ita ce," "Safiyyerh ce sai ya rufe idanunsa pretending yana bacci. Ta ƙarasu tare da zama kusa da kan shi, tana hango fuskarsa ta cikin wutar nefar da aka kawo, asalin kyawun fuskar Mutallab yana da shi tabbas, duhun fatarsa ba mai muni bane oval face a zagaye take irin zagayayyiyar fuskarsa da ƙasumba ke cika ta, yana da madaidaitan laɓɓa kuma jajur dasu sai manyan idanu, kamar mace girarsa a cunkushe baƙa ƙirin haka sumar kan shi. Safiyyerh ta samu kanta da taɓa girarsa wacce ta mata kyau, yana jin ta ya yi shiru" "ita kuma ta ɗauka bacci yake yi, a hankali ta kama hannunsa ta riƙe cikin nasa." """Zafi nake ji a nan ɗina, a nan ɗina nake jin zafi idan ka ci zalina amma na yafe maka bestie""" "Ta ce, muryarta na rawa maganganun na rarrabe kan su da kan su. Hawaye ya cika idanunta ya sauka har" "ƙirjinsa ta ce ""Ai kai ba mugu bane, ko kana mugunta ba za ka yi wa Safiyyerka ba, ka duba yanzu bani da kowa sai Allah da Manzonsa sai kai mijina"" sai ta fashe da kuka, a lokacin kuma kewar su daddy ce gabaɗaya ya addaba ta, ta dinga kuka kamar zata haɗiye zuciya bayan ta gama ta yi yunƙurin miƙewa ta fita ta ji ya riƙo hannunta ya dawo da ita baya, sai ta fara inda-inda domin bata san idanunsa biyu ba. Ya" "buɗe idanunsa ya zuba mata su bakinta na rawa ta ce ""Uhm am ashe idanunka biyu""" "Ya mirgina ya ce ""Idanun kina son ganina a cikin aljihu za ji ajjiye ni, so that kina tare dani always Deer""" ya miƙe zaune. """Uhm"" ya ce." "Ta yi shiru, sai ya saka ƙafa ya zungure ta, ta ɗago kai idanunta jiƙe da hawaye ta ce ""Ka yi fushi ɗazo, an" "ce ba kyau fushin miji""" """Za ki kyau da wasan kwaikwayo, kina da iya ƙirƙirar hawaye""" "Da wani irin mamaki da takaici take duban Mutallab, sai ta shanye ɗacin zuciyar ta ce ""Haka ne""" """Deer""" "Ta yi shiru, ya saka ƙafa ya zungure ta, ta ɗago ta kalle shi ya ɗage rigar alamar ya? Ta sunkuyar da kai" "kawai. ""Deer""" """Wai waye Deer?""" """Barewa""" """Ohh dabba ka mayar dani?""" "Ya ɗaga kafaɗa ya ce ""Mai lasisi ma, a cikin dabbobin ta musamman"" ta maƙale kafaɗa ta ce ""Ni special" "name nake so, sunan masoya ba kaga ni har sweetheart nake cewa ba? Shine zaka haɗani da dabba? Ni ko?""" "Ya yi mursisin, bata tsammaci zai sake magana ba sai da ya ji saukar muryarsa ya ce ""Ni ma'abocin jeji ne" "da namomin dawa, duk wacce zan bawa special nane to apart from animals ne, You are a Deer""" """Waye tiger?""" "Ya yi mata shiru ta ce ""Ni tiger nake so, na fi son tiger""" """Hmm"" ya juya mata baya, sai ta lallaɓa bayansa ta ɗora kanta tana sauke ajjiyar zuciya ""Safiyyerh"" ta" "amsa ya ce ""Maganar gaskiya ina da gundira, bana da halin ƙwarai a duk sanda kika ji ba za ki iya ba tell me, i will give you a chance to go, a freedom. Ki je wajan iyayenki daman nima ba auren na isa ba, ba zan miki yadda kike so ba, ina da gundira. Moh halinsa daban ne ok"" ta girgiza kai tana shafa sumar kansa ta ce ""Ko zaka gundiri kowa ban da ni, i never get tired of you, saboda ina son ka, na san baka so na, ba" "lallai ka so ni ba amma mu amshi ƙaddara kuma ka yafe mini""" "Ya juya ya ce ""Me kikai mini?""" """Kawai ka yafe mini, na san na maka laifi mai girma Mai dawa""" """Gaskiya ba zan iya yafe miki ba, kar a cuce ni kamar yadda bana cuta ok?""" """Ka cuce ni nima, ka cutar da zuciyata ina son ka, zuciyata na son ka kai baka gani, ko kana so na? Kana" "so na?"" Ya juya ya kalle ta sai ya ce ""Friends Safiyyerh, mu yi abota ta amana ki zama babbar abokiyata, mu jingine batun aure don bana jinsa a kaina kin ji?"" Ta yi shiru tana kallon shi, wani irin kalla na ban fahimta ba, wani irin kallo na what do you mean by this, wani irin kallo na i am nothing to you, wani irin kallo na You never love me, ba za ka taɓa so na ba. Sai ta yi ƙasa da kanta kawai tana haɗiye hawayen" idanunta da suka tarar mata. "Ya saka yatsu biyu ya ɗago fuskarta ya ce ""Bana jin auren nan a kaina, mu ajjiye batun auren mu a gefe," "mu yi abota, ki zame mini babbar ƙawa kuma animiyata, zanna goyaki da safe, da rana har dare amma duk goyo ɗaya naira ɗari biyu, kinga ɗari shida a rana, sai kina tara mini kuɗin a wajanki, kin ga fa har ce mini kikai ina wari? Wai wari nake kar na taɓa ki, da ban kai zuciya nesa ba da tuni kin samu karaya biyar har wannan tsukakken ƙugun naki zan ƙarya, ni ina da gundira ne, gwara zama abota da zamowarki" "matata""" "Sai ta yi murmushi ta ce ""Shikenan, idan hakan ya yi maka"" ya ɗaga shoulders ya ce ""Moh, baya da wani" "zaɓi sai abin da zuciyarsa ta ƙissima masa""" "Ya miƙa mata hannu ya ce ""Friends"" ta miƙa masa nata ƙaramin hannun ya kama yana jin kamar ya riƙe" "sillan kara. A hankali ta ce ""Friends""" "A karo na farko taga ya ɗan faɗaɗa fuskarsa sai ya saki hannun ya ce ""To zo na zauna a cinyarka ki mini" "hira har na yi bacci"" ya figota zuwa kusa dashi kamar zai ɗora kansa a cinyarta sai kuma ya janyota jikinsa" "saman ƙirjinsa ya rungumo ta sosai, ajjiyar zuciya ta sauke a hankali." * An yi bikin Sa'adah lafiya an kuma kaita gidan mijinta lafiya. Koda Anty Hameeda ta zo babu wanda ya "faɗa mata abin da yake faruwa, haka ta dinga bin Safiyyerh da idanu, Bafullatana kawai aka faɗawa saboda an san ita kurma ce. Azumi ya zo ya shuɗe, sana'ar Ammo na garawa tana kula da Surayyerh sosai. Malam kallo ne kawai nasa da Mutallab sai muguwar magana ta aibatawa wanda idan da sabo ya saba da hakan. A hankali kuma ɗabi'un Mutallab suka sauya, duk inda shiga dawa yake da jeji yana kan gaba ko farauta za'a yana daga kan gaba. Mutane suka san shi matsayin mai dawa a ɓoye kuma ake" zuwa wajen shi neman taimako. Tsakaninsa da Safiyyerh mutunci duk da sai ta yi kwana biyu bata gansa ba. Suna yin waya dai ta dinga "tsokanarta, rabin hirar duk ita ke yi. Daga ita har shi suka shiga shekara ta goma sha bakwai. 17 years. A lokacin kuma yana Ss2 sai aka yi masa jumping zuwa Ss 3 zangon karatu na farko. Kuma yana ajin Q ne science class. Sai makarantar ta fara damunsa, ba Kimiyya hatta Nahyan ya sauya makaranta shi kawai ya rage, a hutun da aka yi ne kuma aka shirya tafiya dawa domin farauta wanda suka shafe wata guda a can, amma Malam bai taɓa cewa don me, Safiyyerh iyayenta basu taɓa cigiyarta ba a cikin wannan" shekaru buyun da watanni. "Tana tsaye ta juya baya a tsakiyar ɗakin Ammo taga inuwar mutum, a lokacin kuma daga ita sai guntun" "zani ta fito daga wanka, bata shi bane, bata san zai dawo ba, domin tunda suka tafi farauta bai taɓa nemanta ba. Hucin numfashi ta ji a bayanta ta juya da sauri suka haɗa ido, sai gabanta ya faɗi ganin yana binta da wani irin kallo, a jerin shekaru biyun da suka zo tare da shuɗewa da kuma wata guda da ya yi bai ganta ba, sai yaga ta ƙara girma a cikin idanunsa ainun ta zama cikakkiyar budurwa mai shekaru 17 da" watanni a duniya. "Bunjimar rigar farauta ce a jikinsa, sai hular saƙi, hannunsa duka goro da layoyi, gashi tubarakallah a" tsaye mai faɗi gemu duk ya fito masa ya sake buɗewa daman gashi da faffaɗan jiki. Sai ya yi mata kwarjini a cikin idanunta da shakkarsa kuma. "A daddafe ta ce ""Sannu da zuwa""" "Ya yi shiru. Ta ce ""Ya hanya? Ya jeji kuma mai dawa?""" """Kece?""" "Ya ce, yana binta da wani irin miskilin kallo ganin ta sauya completely ta sake kyau, diri da cikar ƙirji" "gabaɗaya. Ta harare shi ta ce ""Daman na san ka manta dani ai, ai shikenan ka zauna na kawo maka abinci""" "Ya shafa kai kawai ta saka hijabi ta fita sai ya bita da kallo a makake, ya sauka numfashi a ƙirji a lokacin" "duk wani kaifafar tunani Allah ya bawa Mutallab, ya gama gamsuwa Safiyyerh matarsa ce, ya kuma" shirya rayuwa da ita zai mata halacci kwatankwacin yadda ta yi masa zai bata abin da take ƙulafuci tsayin shekaru. "Ya yi baya ya kwanta, a lokacin akwai ƙaramin gado a ɗakin Ammo, ya rufe ido daidai nan ga shigo ta" "matsa gefe ta ce ""Ka yi wanka ko? Kafin abincin""" """Yau ma warin nake?""" "Ta ji ya tambaya, sai ta yi shiru ya miƙa mata hannunsa ya ce ""help me"" ta kasa fahimta,ya buɗe" "idanunsa ta suka ƙanƙance ta ce ""Me ka ce?"" Ya yi shiru yana miƙewa zaune ta juya zuwa ɗaukan kayanta, daidai nan kuma aka ɗauke wuta bata san ya aka yi ba sai jin saukar jikinta ta yi a cinyarsa da sauri ta ce ""abota, abota, ka manta cewa abokiyarka ce ni ba mata ba?"" Bai kulata ba, sai zabura da ta yi ganin ya yaye hijjabin jikinta da sauri kuma ta ƙanƙamesa jikinta na rawa jin hannunsa inda bata taɓa" tunanin ji ba a karo a farko a rayuwarta. "[1/7, 9:36 PM] Sis Fauzy: Chapter 42: My love is back" Not edited "Ta cikin hijjabin ta fara ture shi ta ce ""mene haka, me kake yi....,"" ta haɗiye sauran maganganun a cikin" "maƙoshinta, bisa tilas sai rarraba idanunta take ta cikin duhun ɗakin. A wata guda da ya yi a cikin daji yana farauta bata jin muryarsa ba, balle ganinsa, shiyasa yanzu daya faɗo kamar daga sama ta ji faɗuwar gaba, kamar irin wanda ya shekara haka taga sauyi tattare da shi, yanayinsa sun jirkice, banda ƙamshi ciyayi da warin jeji babu abin da yake yi, girmansa na lokacin ɗaya kuma ya sake tsoratar da ita ya saka" "mata jin shakkarsa da kwarjininsa akan dole, ta lura kuma bai fahimta ba." "Da ƙyar ta ce ""Mai dawa""" """Hmmm"" ya ce yana ɗan buɗe idanunsa, tare da kunna hasken wayar hannunsa ya haske fuskarta da ita." A hankali ta ce """Me kake yi haka ne?""" """Abin da ya dace""" """To hakan bai dace ba ai, mene haɗin namiji da hijabi? Namijin mai Mai dawa gwarzon maza?""" """Uhm""" "Ta ce ""wai mene wani uhm, kamar mai ciwon baki don Allah? Ni ka sake ni wanka na yi fa, ƙilama da" "sauran ƙurar jeji a jikinka"" ta ce tana marairace fuska, tare da ƙoƙarin ƙwace kanta ganin idanunsa a lumshe kuma a jirkice. Zata zame ta gudu ya saka mata ƙafa ya danne ta, yana jan numfashi ta cikin" "ƙirjinsa ya yi kuma kamar ba ita yake kallo ba can ya nisa ya ce ""hmm""" """Sake ni na fita, ba zaka kashe ni da wannan hmm ba, mu je ka yi wanka sai ka ci abinci na maka tausasa" "ko? Meka kamo mana ne?"" Ta ce tana murmushi fafaren haƙoranta a bayyane, ya fahimci haƙurin Safiyyerh a bayyane, ya fahimci sauƙin kanta a zahirance, ya fahimci sanyin halinta a ɗabi'ance ya fahimci baiwar fara'a da Ubangiji ya wadata zuciyarta da ita, wacce ita ke sawa ta manta da abubuwa da" "yawa, she is nothing but a simple, silly girl." "Ya kamo hannayenta biyu a daƙile ya ce ""So still deer yarinya ce""" """Ban fahimta ba?""" """Deer, ke yarinya ce"" ya ce yana cure girarsa guda, ɗayar kuma yana matsar da ita can gefe guda. Cikin" "rashin fahimta ta ce ""Uhm'uhm ni dai ban gane ba""" """Tuna mini"" ta ce ganin ya yi mata shiru, kuma yaƙi sakinta idanunsa kuma a rufe amma tana da" "tabbacin yana kallon ta. Ya cije lips ɗinsa ""Moh baya manta abu"" sai ta harare shi ta ce ""Ni na manta, ka tuna mini kawai"" ya mirgina gefe ya tashi zaune ita kuma tana daga kwancan ya hanata tashi ya danne ta da ƙafarsa. Bata ɗauka zai sake magana ba sai da ta ji ya ce ""Zan miki abu idan na tuna miki fa?"" Ta ce" """Kai baka abu saboda Allah ne? Kamar kai ka fi kowa son kuɗi bestie? Ba kyau son kuɗi""" """Idan ban so kuɗi ba, ke zan so""" "Ta yi jim, sai ta ce ""A'a, ban ce ka so ni ba ai ban isa ka so ni ba""" """Good"" ya ce without care." """Tuna mini""" "Ya buɗe gajiyayyun idanunsa a lokacin ya zuba a kanta, to make sure ita ɗin ce, a zuciyarsa mamakin" "sauyinta ya yi, girman jikinta, kyan fuskarta nacin da take masa duka sai ya ragu, irin raguwa da musamman, sai kuma ya hakan ya ɗan sosa ranshi, don me zata rage yi masa naci? Shi ya saba da nacinta yana jin daɗin nacin. A fili kuma ba wani kallon arziƙi yake mata ba, gani yake zata iya raina shi tana ganin shekarunsu ɗaya shi ya tsani raini bai so ko kaɗan shi ya sa baya wasa. Kamar daga sama ta ji" ya ce """Yarinya ita ce wacce bata. ,"" da sauri Safiyyerh ta hantsila gefe tare da mirginawa har towel ɗin na" "zamewa bata sani ba, ta saka tafin hannunta ta rufe masa bakinsa da shi tana zazzare idanunta wanda suka tara ruwa, kamar ya yi dariya sai kuma ya tsuke fuska yana sakar mata cizo ta ɗauke hannun tana yarfewa ta ce ""Auchhh, my hand"" sai kuma ta fashe da kuka sosai kamar daman jira take yi irin ta tara kukan sosai, ya zuba mata idanu sosai yana kallon ta yana jinjina kai kamar yana jin daɗin kukan nata. ""Ba zaka bani haƙuri ba? Cizo na ka yi fa? Ka bani haƙuri"" ya yi shiru ya zubawa waje guda ido, da sauri ta kalli inda yake kalla innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, ashe ilahirin ƙirjinta a bayyane yake hijjabin ya cire, towel ɗin hakan, ta kasa motsi ta kuma kasa rufe jikinta, idan ta ɗago kai sai taga wajan yake kallo," "jiyiyon kansa duk sun fito sai cije lips ɗinsa yake yi. Sai kawai ta cure waje guda ta fara wani irin kuka," "ganin yaƙi kulata ta matsa kusa dashi ta fara kai masa duka a ƙirji da iyakar ƙarfinta, shi dai bai motsa ba" kamar statue ita kuma bata fasa dukan ƙirjinsa ba. "Jikinsa ta faɗa, irin i need a shoulder to cry on." """Bestie""" """Hmm""" """Mai dawa, mijina mijin Safiyyerh"" ta ce tana shassheƙar kuka da dukkan ƙarfinta, kan ta kuma a" "kafaɗarsa hannunta ɗaya a ƙirjinsa. ""Na yi kewar su daddy, ina kewar Ummeyh, ina kewar babban abokina, ina jin kewa,ina jin kamar ni ɗaya ce, don Allah abokina ya kasance dani, ina son abokina ina son shi"" ta ce a raunace muryarta na sarƙewa hawayenta na fita kamar famfo." """Kina jin daɗin kuka, kuka na miki daɗi Deer"" ya ce yana yin ƙasa da kansa suka haɗa ido." """Au bama zaka rarrshe ni ba?""" """A saboda na miki wani abu? Jin daɗi ne ya miki yawa Safiyyerh""" "Ƙoƙarin tashi ta fara daga jikinsa ba tare da ta ce komai ba, ganin ba zai kulata ba ta ce ""Kai kullum kafi" "gane ka yi ta haɗe fuska, ka yi ta fushi murmushi fa ni'ima ne yana wanke zuciya wallahi"" ta ce hawaye na sake gangaro mata." """Ji"" ya ce mata." "Ta juya ta kalle shi. Sai ya ce ""Kina da matsala da yanayin da Ubangiji ya yi mini ne?"" Ta ce ""Kana yin" "murmushi dai don Allah"" ta yi furucin a raunace jikinta kuma a sanyaye, ganin bata ji daɗi ba ya kamo hannunta ya ce ""To nawa za ki bani na rarrashe ki? Kin ga lokacina zan ɓarnatar a iska""" """Saboda ka rarrashi matarka ya zamana ka ɓarnatar a iska? Baka son Manzon Sallallahu alaihi Wasallama" "ya umarci mazaje da su zama abokan wasan matayensu ba? Lada fa zaka samu Mai dawa, ladan ne baka so? Ni dai ina maka kwaɗayinsa""" "Ya dube ta, yana zame bunjimar rigar jikinsa, sai ta lura hatta ƙugunsa wasu manyan layoyi ne, a ƙirjinsa" "ta lura da zane, zanen da bata san na mene ba kuma da alama ya jima a jikin nasa." """Ai sai kice rarrashi kike so daga wajan mafaraucin mijinki""" """Ni yaushe na ce haka?"" Ta faɗa tana ƙifa idanu ganin ya ajjiye askira a gefe ya cire hular saƙin ma. Baƙin" "jikinsa ya bayyana a fili, ya taune harshe yana ajjiye guttun busar hayaƙin ƙarfe na tsari ya ce ""Yarinya" "kenan"" ta ɗauke kai ta ce ""Whatever, ni ban ce mijina ba, yaushe zan ce maka mijina akan me to?""" "Yanayin maganar tata a ƙufule ya fito. Sai ya ɗaga kafaɗa ya ce ""Kin ma ƙaton kan ki ai, kin wa kan ki""" """Ni yanzu bani da wata alfarma a wajanka? Shiga cikin jeji kayi rayuwa da dabbobi yafi maka?""" """E, ina jin daɗin hakan, jeji shi ne ni, jeji na Allah, Mai dawa na jeji""" """To ai shikenan""" "Ta faɗa tana juyawa, sai ta sake tsayawa ta ce ""Wai ba zaka ce ya nake ba a matsayina na matarka? Ba" "kyau, ba kyau abin da kake""" "Ya yi mata wani irin miskilin kallo ya ce ""Sai ki ce mijinki kike buƙata, idan ya kike ne na abota na miki ai," "ki ce mijinki kike buƙata kawai ki daina nunƙufarci ba zan gane ba, uhm"" ya ce yana miƙewa tsaye sosai akan ƙafafuwansa ya kere mata a tsayi ta yi ƙasa da kai ta ce ""Ni bana buƙatar wani miji"" sai ya ɗaga kafaɗa kawai, ya nemi hanyar fita cikin sauri ta ce ""I need my husband, I need my bestie, ina son mijina," "ina son Mai dawa na""" """Yarinya kin yi kyan kai, kina da minti biyar ki faɗa mini komai""" "Sai Safiyyerh ta samu kanta da yin shiru, ta rasa me zata ce masa, ta ji tana son faɗa masa nauyin saƙon" "Aafiyyah da yake kanta tsayin shekaru biyu, da shi take kwana da shi kuma take tashi a rai, sai kuma ta fara tunanin mene makomarta a wajansa idan ta faɗa masa cewa the message is not belong to her, is for Aafiyyah, ya matsayinta yake a zuciyarsa? ""Think Safiyyerh"" zuciyarta ta ce mata, ya yi accepting nata a lokacin data nuna masa wasiƙun, ya sauya mata a wannan lokacin, what if ya goje mata idan kuma ta ce" "ba ita bace? Mene matsayar ta?"" Ta fara tunanin zuci." """Barewata"" ta ji ya kiranye ta, cikin taushin murya duk da a daƙile ya yi maganar amma akwai laushi cikin" furucin nasa. """Safiyyerh"" he called her gain." """Na'am"" ta amsa a firgice, bata san zuwansa ba sai ganinsa ta yi tsaye a gabanta ya zuba mata gajiyayyun" "idanunsa da sukai laushi cike kuma da gajiya. Safiyyerh ta yi ƙasa da kanta taƙi magana sai kuma ta ji nauyinsa, ta san kuma ba lallai bane ya ce mata komai ba. ""Hmmm, five minutes left"" yana cewa haka ya fice daga cikin ɗakin da sauri. Sai ta ji kamar ya tafi da ruhinta ne, kamar ya tafi da tunaninta da nutsuwarta ne gabaɗaya, a hankali ta sulale ta zauna daɓas a jikin gado ta cure tana sakin wani irin kuka mai cin zuciya a fili kuma ta ce ""I am sorry Aafiyyah, ki yi mini alfarma kina da komai, kin fini ƙarfin zuciya" "za ki iya haƙuri i am sorry, i am sorry Aafii"" ta dinga kuka ita kaɗai zuciyarta na yi mata zafi sosai." "Da ƙyar ta tashi, ta saka kayanta duguwar riga mai ɗan kauri wacce ta zauna a jikinta das ta saka hula" daman kanta ba wani kitso har yanzu tana da sauran mayuka fatatar jikinta tas take. "Saman gado ta hau ta zauna, ganin har yanzu Ammo bata dawo ba, ta jima tana tunanin yadda zata iya" "rayuwa da Mutallab da wannan botsararren halin nasa, shi komai a baibai yake ganinsa, taga bata da wani zaɓi daya shiga yin addu'a da neman zaɓin Ubangiji wanda tun farko ya kamata ace ta yi. A hankali ta ja numfashi ta sauke cikin rauni murya ta ce ""Ya Allah kai ne ka ɗora mini soyayyar bawanka a cikin zuciyata, Allah kai ka dasa mini ƙaunarsa a cikin ƙirjina, ka wanzar da tausayi a cikin nawa ƙirjin nake jin so da ƙaunarsa na yi yaɗo da gina kansu, kullum ina rayuwa da soyayyar mijina, ina rayuwa da ƙaunarsa, ina shaƙar numfashin da tausayinsa a zuciyata, duk shuɗewa da ƙiƙa da gittawar lokaci basa tafiya ba tare da sun tunatar dani begen shi ba. Idan soyayyar da nake masa kuskure ce Allah kai ka ɗora mini, idan ƙaunar da nake masa wawta ce Allah kai ka dasa mini ita, rayuwa da nake dominsa ne Allah kai ka" kawo numfashi ne a ƙirjina kawo war haka. Idan bari iyayena da na yi da nazaɓe masa shine laifina Allah "na tuba, idan wonfitar da aminiyata da na yi shine abin da nake girba Allah bani na sawa kai na ba," "zuciyata ce. Idan ina da rabo na alheri Allah ka kar kato da hankalinsa izuwa gare ni, Allah ka shirya mini mijina Mai dawa, ubangiji ka sanya masa hannu cikin lamuransa ka bani ikon cinye dukkan wata" "jarabbawa da zaka sadar da matsala tsakanina da shi, Ya Allahu Yaa Rahmanu""" "Sai ta ji nutsuwa a ranta, ta ji damuwar ta kau har ta manta." "Mai dawa na fita kuma wanka ya yi ya shirya cikin wasu ƙananun kaya, ɗaya daga cikin kayan da uncle" "Musbah ya kawo, wando ne three qauter mai duhu sai riga Jessy wacce ta kama jikinsa, ya saka wata hular angara ya karkatar da ita zuwa gefe. Yana zaune saman buzu ya saka ƙwarya a gabansa daya zuba ruwa a ciki da wasu allurai ya yi shiru idanunsa rufe, da sauri kuma ya buɗe idanunsa a ɗan firgice ya ce ""Safiyyerh!"" Ya faɗa yana jin kiran sunan yana nanata kansa ta cikin ƙirjinsa, ya yi shiru sai kuma ya sake rufe idanunsa ji ya yi kansa na masa girma yana juyawa bisa dole ya ajjiye tare da miƙewa hannunsa" "zube cikin aljihu ya fita, tunanin kimiyya ya dirar masa amma gabaɗaya baya samunsa a waya." * Suna zaune cikin ɗaya daga cikin manyan gidansa a sashi na musamman a ɗaya daga cikin manyan parlors dake gidan. A hankali ya gyara zama da ya yi a saman kujera cikin shigar alfarma sai kuma ya ajjiye abin hannunsa da yake juyawa kamar game. yaja gwauron numfashi a hankali ya ce """Jaa'afar""" """Ranka ya daɗe"" Jaa'afar ya amsa cikin girmamawa. ""Bana son wasa, da kai ɗaya na amince na kuma" "yarda Jaa'afar, lokaci ya yi da zaka nutsu ka tsayar da hankalinka waje guda ok?""" """In sha Allah ranka ya daɗe""" """Good"" mutumin ya yi shiru sai kuma ya ce ""Akwai magana ne?""" "Jaa'afar ya ce ""Kusan hakan, amma ga wannan ka fara gani"" Ja'afar ya miƙawa mutumin wayar hannunsa," "a hankali ya dinga bin screen ɗin wayar da kallo ya ɗauki a ƙalla 10 minutes yana kalla kafin ya ce ""And" "what is this Jaa'afar?"" ya tambaya yana juyawa Jaa'afar fuskar wayar shima ɗin fuskarsa da alamar" "tambaya domin bai fahimci kurman baƙin na Jaa'afar ba. ""Ranka ya daɗe ina ganin kamar. ,"" ya katse" "Jaa'afar da faɗin ""Ba wannan ne a gabana ba tukun ka ji ko?""" """Amma yana da kyau ka tsaya ka ji me zan ce ne""" """Na ji me? I am not ready """ """Shikenan sir""" """Ja'afar, aikin yaron nan Ɗan'malam i appreciate it, ban ɗauka muna da malamai a cikin gari irin haka ba," "nake ta wahalar da kaina a iska da ɓarnatar da kuɗi ba tare da buƙata kuma ta biya ba, na ji daɗin aikin sosai, zan ƙara masa kuɗi mai yawan gaske ka kai masa"" cewar mutumin. ""Sir, ai shi ba wai boka bane kuma ba sananne bane kawai dai Allah ya bashi baiwar abinne sama taka duba da cewa ɗangado ne, shi" "aikin yake yi kawai wallahi""." """Ko ma dai yaya ne, bana son ka yi mentioning sunana a wajansa, ya yi maka aiki ba tare daya san asalin" "wanda ya kewa aikin ba ka ji? Ka fahimta?"" Jaa'afar ya ce ""Kar ka ji wani ɗar bai san komai ba, aiki kawai yake yi mana, kuma zai cigaba da ya yi mana in sha Allah, kuɗin daman yake da buƙata""" """Kuɗi wajan ya tarar zai kuma samu, as far as buƙatuna suna biya shikenan. Ka je za mu yi magana zuwa" "dare"" cikin girmamawa Jaa'afar ya miƙe tare da ficewa daga cikin parlon. Yana fita mutumin ya ɗauki wayarsa ta sirri ya kira wata waya da sauri kuma ya ce ""bana son kuskuren da aka samu na baya, a ƙara sakawa gidan idanu da kyau don Allah, a sake nema yara sosai masu cikakkiyar lafiya da kuzari ko nawa ne a dinga biyansu suna tarayya da yaran kun ji?"" Yana kammala wayar ya kashe ya ajjiye. Waya ce" "wacce sai time to time yake buɗe ta, kuma yake amfani da ita kamar dai yanzu." "Cikin isa da izza yake takawa har zuwa cikin wani haɗaɗɗan ɗaki, a takure ya hangota can ƙuryar gado ya" nemi waje ya zauna. """Laylerh"" ya kira ta." "A firgice ta ɗago kanta ta zuba masa idanunta da sukai jajur taƙi cewa komai jikinta sai rawa yake yi, ya" "miƙa hannunsa zai riƙota ta sake matsawa a tsorace ""Laylerh"" ya kira sunanta da ƙarfi, ƙarfin daya sakata" "magantuwa bisa dole kamar doluwa haka take binsa da idanu ta ce ""Laylerh me?"" Ta faɗa cikin sigar tambaya." """I want you, ina nufin ina buƙatar ki, ina buƙatar ki Laylerh""" """Uhm, kana buƙatar Laylerh?"" Ta girgiza kai ta ce ""Wanne irin mutum ne kai wai don Allah? Wanne irin" "zuciya gare ka ne? Bana so bana so na gaji, abin da Ubangiji ya haramta shi ka mayar ado? Neman mace ta baya? Macen ma matarka ta sunna? Neman mace ta dubura? Me kake nufi? Tsafi ka fara ko ƙungiyar mafia ka shiga? To wallahi wallahi wallahi akan wannan sai dai duk abin da zai faru ya faru I'm tired, na" "gaji na gaji i am tired of this married""" """Me kike nufi?""" """Ina nufin abin da duk kake nufi, ina jin abin da duk kake ji, kai duk abin da zuciyarsa ta ƙissima maka shi" "nake nufi, i am ready for you""" "Ya nufeta, ta yi saurin direwa ta gadon ta miƙe tsaye da kyau samar kanta duk ta sakko, ya yi wani irin" "miskilin murmushi ya ce ""kin san mene? Ki daina wahalar da kan ki, aurena dake dole ne, zamana dani dake wajibi ne, rayuwa a cikin gidan nan tilasta ne, and and nemanki ta baya dole ne, ko da za kina mutuwa kina dawowa ne Laylerh, kin san waye ni, kar ki tsaya jayayya"" ya ce yana cire babbar rigarsa ya" "wular saman gado. Idanunta ya yi jajur ta ce ""Idan kai, kai ne nima Laylerh ni ce ɗan halak ka fasa""" """Yanzu idan ke kin fasa kece ba ƴar halak ba Laylerh? Ke fa ɗiya macace ba ki da wata power a cikin" "gidana, ba ki da wannan freedom ɗin Laylerh""" "Ta ɗaga kafaɗa ta ce ""Za mu gani""" "Yatsu biyu na hannunsa ya kaɗa suka bada wani sauti, cikin sauri wani garjejen mutum ya fito daga cikin" "wani ɗaki hannunsa riƙe da sirinji, kai tsaye wuyan Laylerh ya nufa ya faki idanunta tare da soka mata sirinjin a wuyanta, gigitaccen ihu ta saki tana dafe wajan, bata iya juyawa taga waye ba, idanunta daya cika da hawaye ta zubawa mijin nata, tana yi masa wani irin kallo mai kama da zargi, tuhuma kallo na me ka yi mini? Kallo na ka ji tsoron girman Allah, kallo na ka tuna ni matarka ce, kallo na ka tuna akwai tashin alƙiyama. A hankali idanunta ya fara lumshe hawaye masu zafi na sauka daga cikinsu ta yi gaba zata kifa saboda gabaɗaya jijiyoyin kanta dana jikinta sun saki, ta ji duniyar na juya mata, ta jita kamar matacciyya hatta yatsun hannunta ji take kamar ba'a jikinta ba, sauran hawayen suka ƙarasa sauka saman farar fuskarta a lokacin da yake taro ta jikinsa ta faɗo, ya saka hannayensa duka biyun ya rungumeta da kyau ya ce ""wannan shine girman iko na, wannan shine bambancin dake tsakanin mace da namiji, wannan shine jinkimata kin kasa gane cewa i love you Laylerh, dole zan yi amfani dake wajan" "cimma buƙatata, afuwa za ki mini""" "Ɗaukan ta ya yi, ya shige cikin ɗaki da ita yana mai yin murmushi mai sauti cike da gamsuwa." * "Shigowa cikin gidan ya yi karnuka na biye dashi hannunsa ɗaya riƙe da leda, ya ja ya cake ganinta zaune" "tsakiyar tsakar gidan tana yin wanki, ya juya idanunsa ya ga babu kowa hakan ya sake tabbatar masa cewa Ammo ta fita zuwa kasuwa, sai ya ji ransa ya ɓaci ganin duk suna ƙuryar ɗaka sai ita, tana yin wahalar da bai san ta mece ba, ya kuma kasa yi mata magana sai gadon bayanta daya zubawa idanu." "Ganin karnukan Mai dawa suna zagaye ta ya saka Safiyyerh sakin zanin hannunta, ta tsame hannun daga" "cikin bokicin wankin ta juya kaɗan sai suka haɗa idanu, da wannan mikislin kallon nasa na tuhuma kuma" a sheƙe. "Murmushi ta yi ta ce ""Idan an ji motsin karnuka to Mai dawa is on the way, ranka ya daɗe""" """Wa kike wa wanki?"" Ya tambaya yana zubawa kayan idanu sai ta sake yin wani murmushin ta ce" """kayana nake wankewa, sun yi datti shine"" yanayin maganar tata akwai ƙarya a ciki kuma nan take ya" "gano hakan tun kafin ta yi furucin, ya jinjina kai" """Maƙaryaciya kika zama?""" """Bangane ba?""" """I asked you, wa kikewa wanki""" """Uhmm ni fa, ni kayana. ,""" "A dame yana ɗaga mata hannu ya ce ""Quiet Deer"" dole ta yi shiru, ya taka a hankali zuwa wajan, ya fara" "ɗaɗɗaga kayan sai yaga kayan Inna Binta ne, ya ɗago ya kalli Safiyyerh sai ya ajjiye kayan ya ce ""Ya miki kyau Deer"" yana cewa haka ya juya zuwa ɗakin Inna Binta, Safiyyerh ta ce ""Don Allah kar ka ce komai""" kallon da ya yi mata ne ya saka kayan cikinta juyawa ta yi saurin shigewa cikin ɗakin Ammo. "Inna Binta na kishingiɗe tana gyangyaɗi ta ji an banko ƙofar ɗakin ta miƙe zumbur tana faɗin ""Auzubillahi," "mugun ji da mugun gani Ubangiji ya kare, waye a nan?"" Cikin buɗaɗɗiyar murya ya ce ""Mai dawa"" zuciyarta ta harba, ya zuro kan shi cikin ɗakin yana ƙare mata kallo ya ce." """Me ya sa za ki saka matata wanki? Hannu ne ba ki dashi?""" """Daga cin albarkacin yarinya sai ya zama tsiya? Na ga ita ta ce na kawo ta wanke mini""" "Ya jinjina kai ya ce ""Ok""" "Ta yi saurin cewa ""Wallahi ita ce, kuma ai lada zata samu ma ko?""" """Matata ce ita, ni nake da alhakƙun sata wanki, nima kuma bana yi. Ki dai na ganinta hakan nan ɗiyar" "arziƙi ce, ina sane da ita da duk motsinta, ba yau kuma kika saba sakawa ta yi miki aiki ba, ita zuciyar Mai dawa ce, halaliyyarsa zan jure komai a karan kaina amma banda a kan ta. Ita ƴar aljanna ce kina ji? Ya zama na farko kuma na ƙarshe da za ki saka mini mata aiki, ita ba baiwa bace, wabillahillazi zan miki abin da ban taɓa wani ba, zan saka ki a cikin duhu zan saka su tiger cinye mini namanki ɗanye, idanu a rufe" "suke banda a kan matata ok?""" """A cinye nama ne ɗanye kuma?""" """Idan kina da waufi, just continue""" """Allah Ya baka haƙuri""" """Da haƙurin ya mutu sadaƙar nawa kika bayar eh?"" Ya ce cikin hargagi yana doka ƙafarsa jikin ƙofa. Inna" "Binta ta buɗe baki sai kuma ta ji saukar abu cikin rigarta, ta zumduma ihu tana karkaɗe jikinta tana wani irin kururuwa na tsananin zafin da azaba, da azama ya fice daga cikin gidan jin muryar malam ya fito yana tambayar ko lafiya?. Malam ya tsaye jin Inna Binta na cewa ""Shegen yaronka ne zai kassara ni wallahi ba zan yadda ba idan ya yi wa rayuwata illa, daga saka matarsa yi mini wanki shine zai zo yana mini azaba? kunama ya saka mini a cikin riga na daɗe ina faɗa maka ƙulafucina yake yi banda haka duk" "jikina bai masa inda zai saka kunama ba sai saman ƙirjina sai a ƙirjina?""" "A ruɗe Aby ya ce ""Ƙirjina kuma? Mene haɗinsa da kunama?""" "A sheƙe Inna Binta ta ce ""Kana nufin baka san yana bokanci ba ko? Kaga irin layoyin dana tsinta a cikin" "ɗakin nan? Wallahi bokanci yake yi wallahi da ƙyar idan ba jinina yake zuƙa da kunamar ba""" "Malam ya yi jigum sai kuma ya ce ""bokanci fa kika ce Binta?""" """Idan ƙarya zan maka shikenan""" "A fusace Malam ya fita, daidai lokacin kuma Ammo ta shigo sukai kiciɓus ya ce ""Madallah, gwara da kika" "dawo na gaji da halin wannan mugun yaron naki mai baƙin hali da mummunar ɗabi'a, wallahi ba zai kashe ni kwana na bai ƙare a duniya ba, ban kuma haifi yaron da zai lalace akan idanuna ba, abin da ya saka kika ji na magantu matata ya taɓa saboda ta saka matarsa aiki, to mata ai bata fi mata ba, ya gaggauta neman gida ya ɗauke mini yarinyar mutane da cikin gidana, ya je can waje ya yi tsafi ma idan ya so babu saka hannuna kuma ba'a cikin gidana ba"" ya ƙare maganar cikin korari. Ammo ta yi tsaye sai kuma ta ce ""Yanzu me ya yi kuma?"" Ya ce ""Ba lallai ke kiga laifinsa ba, tunda daman shi laifi tudu ne," "kuma ina gaf da shata miki layi tsakanin ke da shi, zan saka muku hijabi. Na faɗa nan da wata guda ya" "nemi gidan da zai ajjiye matarsa ba gidana ba, ba zai yiwu iyan shiga ɗakin matata ba na ƙure a ɗaki" "shima yana shiga cikin ɗaki da yarinya ba, sam sam ba zan lamunta ba, tsinannen yaro mai mugun nufi" "da ƙyar idan ba shaye-shaye ya fara ba"" Ammo ta ji zafin maganar sosai ta dake ta ce ""Ko ma dai yaya ne hannunka ba zai taɓa ruɓewa ka yanke ka yar ba, duk abin da Muhammad zai zama silar ka ne," "kai ne sadani Abdullahi, kuma ita dauɗar gora ciki kan shata, kuma daina ganin ina maka shiru duk" "lalacewa jikina Muhammad ya tsaga ya fito, ka bar raina allura domin ƙarfe ce""" """Kike da ƙwarin zuciyar tsayawa gabana kika faɗa mini haka, tuni kike buƙata ko mene da za ki ce duk" "abin da ya zama nine bayan kin fi kowa sani?""" """Ban san komai ba, iya mugun bakin da kake jifansa da shi ya isa ya lalata shi, kuma in sha Allah Mutallab" "ba zai taɓa zama dalilin mutuwarka ba, ko hawan jininka""" "Ya kaɗa babbar riga ya ce ""Can miki, ni dai ya gaggauta neman gida ya bar mini nawa duk abin da zai" "zama ya jima bai zama ba""" "Cikin sauri Mama Zaituna ta fito ta ce ""Da ƙyar idan ba ciki ya ɗirkawa ƴar mutane ba"" Ammo ta juya" "suka haɗa idanu da Mama Zaituna, sai ta shige ɗaki tana shera hawayen daya taro a cikin idanunta. Malam ya fita yana sababi duk abin dake faruwa kuma Safiyyerh na ɗaki tana ji, sai kuma yanzu ta sake fahimtar abubuwa da yawa akan Mutallab, a iya rashin maganarsa hadda tasirin iyaye na rashin kwaɓa" "kamar yadda itama tata rayuwar ta jirkice dalilin iyayenta, her parents course everything." * "Harabar wajan ta ɗauki shiru sai kukan tsuntsaye da sanyin wajan, da ƙamshin furanni da suke tashi," "gabanta coke ne da pizza tun da mutuncinsu har vacteria ta shiga without knowing. Fararen idanunta zube a kan pizza ɗin duk maganar da ake mata ji tunaninta ya rabauta da wajan. ""Aafiyyah""" "Shiru ba amsa aka buga teburin gabanta da ƙarfi aka ce ""Aafiyyah""" """Blackman"" ta ce a fili ba tare da sanin kalmar ta fito daga cikin bakinta ba, sanyin muryarta ya ƙazanta" "har ba'a iya jin me take cewa sosai. Wace take gaban Aafiyyah ta ce ""Waye Blackman""" """Kamarya?"" Aafiyyah said, tana juya idanunta akan Shila." """You just said it""" """Say what Shila?""" """Blackman"" cewar Shila tana murmushi kana ta ce ""Kin san me Aafiyyah, ai kin yi zurfin da ba ki isa kin" "hana a gano matsalarki ba, kawai ki faɗa mini waye Blackman a shige wajan""" "Aafiyyah ta share Shila ta yi kamar tana taɓa wayar hannunta, amma ya sake tafiya duniyar tunani gani" "take kamar mutuwa za ta yi, kamar ba zata yi rayuwa mai tsayi ba, bawai mutuwar take tsoro ba, kullum zuciyarta ke raya mata cewa Aafiyyah you most die, sai ta ji gabaɗaya duniya ta yi mata zafi ta yi mata ɗaurin huhun goro wani irin baƙin ciki take ji a ranta da kuma ɗaukewar tsammani mai kama da hopelessness, ta ji rayuwarta bata da wata ma'ana ga zafin zuciya da Ubangiji ya ɗarsa mata a yanzu da saurin fushi. Duk yadda ake ƙoƙarin sama mata farinciki musamman Mj sai ta ji bata buƙatar wannan pleasure ɗin, ta ji kamar bata da wani amfani a duniya yanayinta ya yi mata kama da worthlessness ta ji" kamar ta yi laifi mai girma mai kama da guilt. """Aafiyyah"" Shila ta sake kiran sunanta, sai ta yatsuna baki ta ce" """Ina da kune Shila""" """Na san kina da shi, amma tunaninki baya nan wajan idanunki ya yi kama da wacce bata samun bacci" "wallahi""" "Aafiyyah ta yi baya kaɗan ta ce ""Haba?"" Cikin damuwa Shila ta ce ""Wallahi, kin rame da yawa""" """Ok"" kawai Aafiyyah ta ce. Tana kallon pizza ɗin, duk ƙaunarta da pizza amma yau ta kasa kai ta cikin" "bakinta. Sai ta yi murmushi a fili ta ce ""So it's true?"" Ta tambayi kan ta, ta samu kan nata da tunanin message ɗin da ta yi wa Mutallab inda take cewa “I love you more than pizza” murmushi kawai ta sake yi tare da yin shiru. Shila ce ta fito da baƙin coke a cikin jakarta ta tsiyayawa Aafiyyah a cikin cup ta ce ""Sha lemon nan za ki ji daɗi, kuma za ki yi bacci"" ta ce tana turawa Aafiyyah, ta kalli lemon baƙi ne zubin cokacola, a hankali ta ɗauki cup ɗin ta shanye, shila ta sake zuba mata lemon ta shanye sai ya ɓata fuska" "ta ce ""Shila ɓarnar kuɗi, kina da lemon kika samu siya?"" Shila ta ce ""Nawa ai special one don kiji""" "Aafiyyah ta duba agogon hannunta, sai ta miƙe jikinta sanye da Black ɗin abaya three pieces, ta yi rolling" "kanta da brown ɗin vail, sai wani brown neck data saka, idanunta cikin shade glasses ko jakar hannunta ta kamfanin Arɗos group bata ɗakko ba. ""Baza ki jira Mj ba""" """Zan iya driving, thanks Shila""" "Ta ce, tana nufar wata ƙaramar baƙar mota sai sheƙi take yi, buɗe motar ta yi ta shiga, key ta yi tare da" "yin reverse ta fita daga cikin restaurant, tun a hanya wani irin bacci yake cin idanunta motar na juya mata daidai sanda mai gadi ya buɗe mata gate daidai sanda su biyun suka fito, kallon ta yake cikin rasa da mamaki yadda kamar ta sauya halayye da ɗabi'a, hannunsa biyu zube cikin aljihu kunnensa ɗaya ya saka bluetooth fuskarsa a kame, ya juya a hankali jin Paaah na cewa ""Rayuwarka sai a hankali"" ya ɗan" "cire hannunsa yana shafa kansa bai ce komai ba ""Daga nan sai ina kuma?""" "A nutse ya ce ""Airport""" "Sai kuma ya sake buɗe idanunsa ta cikin baƙin glasses yana ƙarewa Aafiyyah kallo tas, ya kalli Paaah" "kamar zai yi tambaya sai ya share. Da murmushi ta ce ""Paaahh"" ya jinjina kai yana ƙarewa mata kallo kamar mai nazarin ta sai ta yi saurin washe fararen haƙoranta tana buɗe idanunta da ƙyar ta ce ""shine ina ta kiran numberka ana cewa a kashe fa"" ya ɗaga mata gira ya ce ""Saboda wayar bata da wayo irin" "naki safiyyerh, bata da halin Safiyyerh"" ta marairace fuska sosai ta ce ""Haba mana""" """Ina cikin jirgi time ɗin""" "Ta rungume shi ta ce ""Na yi zaton haka ai, you look great Daddy""" "Sai kuma ta juya ta ce ""Welcome Yaya"" ya yi shiru. Paaah ya ce ""Ana magana"" sai ya yi gaba abinsa ya ce" """Zan yi missing jirgi"" cikin sauri ya shige mota abinsa driver ya ja suka fice. Aafiyyah ta bi bayansa da" "harara. Paaah ya ce ""Laa la harara"" ta yi murmushi ta ce ""Kai Daddy idona ke rawa kamar ƙwaro""" hannunta ya kama ya ce """As always, kina da kalman kare kai Safiyyerh""" "Tunda Aafiyyah ta kwanta take bacci, baccin rabon da ta yi sa tun tana Naija, ko motsi ba ta yi a cikin" "baccin take jin nutsuwa na saukar mata damuwarta na yayewa baƙincikin zuriyarta na tafiya, ta shafe" sama da awa biyar cif tana bacci ba tare da shirin tashi ba tamkar bata da rai. * "Tunda ya shigo ya gama sababin faɗa Safiyyerh bata sake ganinsa ba, har dare ya yi gari ya waye wani" "daren ya sake yi. Ta ji ta kasa jurewa a hankali ta ɗauki wayarta sai ta shiga WhatsApp ta yi log-in da numberta, message suka fara shigowa ta samu ta yi lefted daga group nasu na FGC. Saƙon Nahyan ta gani dana Captain sai ta share hankalinta ta tafi akan wata number wacce bata ƙasar bace, tarin messages ne sun kusa guda ashirin idan ka ɗauke emojis ga voice note. Safiyyerh ta shiga saƙon, sai ta duba username taga empty ta duba dp taga babu sai ta yi murmushi ta ce ""Aafiyyah"" ta san ita ce kawai," bata son kayan wahala da tarkace. “Hy Safiyyerh” shine maganar farko sai magana ta biyu da aka ce """How are you dear, kina lou??""" "“Are you okay?""" """Ok, i won't disturb you”" “Safiyyerh” “Safiyyerh” “Safiyyerh” "“I so much miss you Safiyyerh, fatan alheri Safiyyerh”" Safiyyerh ta cigaba da duba saƙwannin Aafiyyah wanda suka shigo cikin mabanbanta lokaci. Ta yi murmushin takaici kawai tana lumshe idanunta da hawaye ta taro a cikinsu. "“Ina jin kunyar tambayarki, na san kina sane dani da zaman jira da nake shekaru biyu, na san za ki bawa" "Yaa Muhammad saƙona""" Sai voice note ɗin. Ta buɗe sai ta ji muryar Aafiyyah na fita da ƙyar very slowly muryarta ta juye cikin harshen German language a hankali ta fara saurara; """Kuna lafiya duka, to good. Safiyyerh Paaahh yana son haɗa ni aure da wanda bana so, ba zan iya ce" "masa a'a ba, bani da wani zaɓi Safiyyerh i love Muhammad so much and i meant it, billahi ina son shi don Allah ki daure ko bidiyo na fuskarsa ki mini idan ba zan iya jin muryarsa ba, na san watarana zai neme ni, i missed you Safiyyerh and i missed Muhammad, my stubborn boy, na san yanzu ya sake girma" "zafin zuciya zai ƙaro, help me please""" "Ɗago kai Safiyyerh ta yi suka haɗa idanu da Mutallab sai ta yi saurin ajjiye wayarta ta ce ""Yaushe ka" "shigo?"" Ya ce ""Kina aikin wofi""" """Na ji dai""" Ta ce a ruɗe. Sai ya juya ya fita abinsa miƙewa ta yi tabi bayansa tana shiga shagon suka haɗa idanu da "Jaa'afar, cikin sauri ta yi baya domin har ta buɗe baki za ta yi magana, Jaa'afar ya bita da wani irin kallo yana son sake ɗaukan picture nata a karo na babu adadi. Cikin gida ta koma ta jima kafin taga wayarta" "na haske ashe yana da numberta? Ɗauka ta yi ta kai kunne ya jima kafin ya ce ""Zo"" ya ce yana kashe" wayar. "Sanda ta shiga ta same shi kwance ya yi rufda ciki a hankali ta shiga bakinta ɗauke da sallama, bai juya" "ba sai ma sake rufe idanu da ya yi, ta matsa ta ce ""Gani"" ya yi shiru ta sake cewa ""Gani""" """Mai dawa""" "Ya juyo yana ƙura mata idanu fuskarsa babu walwala ya ce ""Waya kira ki?"" Ta buɗe ido ta ce ""Yanzu fa ka" "kira ni a waya"" ya cije lips ya ce ""Muga"" har ta miƙa masa wayar sai ta ɗauke ta ce ""Ba sai ka gani ba," "amma dai ka kira ni"" ya dinga kallon ta da ƙyar ya ce ""Ba ki da gaskiya"". ""Da gaskiyata Allah kai ka kira ni""" """Uhmm""" "Sai ya miƙe kawai ya nufi hanyar fita, sai taga ya tura ƙofar ya rufe ya kuma saki windows ɗakin ya yi" "duhu, ta miƙe da sauri zata gudu ya cafko ƙugunta ya dawo da ita baya, ya saka hannunsa biyu ya riƙe ƙugun nata ya ce ""Kike mini zirga-zirga ina aiki, kin ji daɗi wani ya ganki kin burge shi ko?"" Ya faɗa a" daƙile """Waya ya ganni? Wana birge ohh ni ashe zan iya birge wani?""" "Ta cikin duhun taga ya bubbuɗe idanunsa alamar mamaki sai ya yi ƙwafa ya ce ""Oh, a saboda ba ki san" "darajar aure da kuma darajar kan ki ba? Ko an ce miki ba'a kishinki ba'a son ki ne? Yaushe kikai lalacewar haka?"" Safiyyerh sai ta kwakkwaɓe fuska ta fara yarfe hannunta, ta yi kamar zata faɗi sai ta juya wayarta ta shiga WhatsApp wajan contact ɗin Aafiyyah ta danna voice. Gabaɗaya bai san me take yi ba sai da ya ji ta ce ""To ni mene laifina don wani ya ce na burge shi, ba shi zakai wa faɗa ba? Ni ka sake ni na tafi" "tunda faɗa ka kira ka yi mini, ba ruwana da kai""" """Safiyyerh!""" "Ya ce cike da mamaki ""Anya kina son wanyewa lafiya? Daɗi kike ji kin burge wani bayan zunubi ne a kan" "ki?"" Ta yi shiru." """Answer me"" ya faɗa a tsawace." Tsoro a kamata sai ta fashe da wani irin kuka tana bubbuga ƙafarta ta yi waje zata fita ta manta ƙofar a "rufe yake, still recording ɗin na ci-gaba da ɗauka." """Kina fita za ki gane baki da wayo, dole yau naga abin da ya saka sakarancan cewa kin yi masa, dole ki" "nuna mini abin da kike ta ɓoyewa, dole ki nuna mini iyakar iyawarki Safiyyerh"" shi sam bai san kishi yake ba, tunaninsa faɗa kawai yake mata ganin tana da kuka kamar ranta zai fita ya ce ""Zo"" sai ta maƙale kafaɗa. ""Rungume ki fa zan yi, idan kikai asara shikenan, ki zo mu yi sallama ina da farautar da zani"" ya" "taka zuwa gabanta, ba ta" "yi tunanin hakan ba, sai ji ta yi ya kusantota, ya damƙo kafaɗunta a hankali kuma ya ɗora kanta a saman" "ƙirjinsa da yake a buɗe, ta lura yana jin daɗin zama ba riga ko duk zaman jeji ne?. A hankali kuma ya" "zagaye hannayensa biyu a bayanta ya ce ""Shhhh"" sai ta ƙanƙamesa ta rasa wani irin kukan farinciki za ta" "yi, ko bai ce yana son ta yau kaɗai ya gama mata komai muryarta na rawa ta ce ""My love is back """ "A hankali ya ce ""Kuma forever""" "Sun jima yana rungume da ita, kafin ya ɗago kanta suka haɗa idanu ta ce ""Na ji me ka ce""" """What?""" """I love you too Safiyyerh"" cikin sauri ta danna voice ɗin tare da danna send ya tafi sai ta cilla wayar can" "gefe. ""You not serious""" """Ina son ka Bestie""" """Thank you Barewata""" "Sai ta dinga kallon bakinsa, musamman lips ɗin a hankali shi kuma ya ɗora goshinsa a nata bai ce komai" "suna sake haɗa ido taga kawai ya yi mata murmushi sai ta lura ashe har wushirya yana da shi he keep smiling ""me kake wa dariya wai?"" Ya girgiza kai ta ce ""Don Allah dariyar me ce"" yana ta murmushi ya ce" """Ba ki da gaskiya Safiyyerh, Allah ba ki da gaskiya""" """Rashin gaskiyar me na yi?""" """Kina son sumbatar mijinki""" """Uhm, oh ni nake so?""" "Ya ɗage mata gira ya ce ""E, ni ban niyya ba ai, ki yi kawai Barewa""" "Sai ta ji zuciyarta na harbawa, wani abu na janta zuwa gare shi musamman saman laɓɓansa, ta ji tsigar" "jikinta na tashi, bata san ta manne da jikinsa sosai ba sai daya ƙara matse ƙugunsa da nata da kyau yana riƙe ta, bata san kuma ya aka yi ba sai gani ta yi ta ɗora bakinta a saman nasa kuma ta samu kanta da" riƙe kansa ta fara kissing ɗinsa... MUTALLAB. PAID BOOK 08164069385 "[1/7, 9:37 PM] Sis Fauzy: Chapter 43: Soulmates"