INTISAAR COMPLETE BOOK 1 TO 4, HAUSA NOVEL WRITTEN BY KHALEESAT HAIDAR. Khaleesat haidar. *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** A gajiye ta shigo gidan hade da kullo gate, ta nufi sashin su ba tare da ta kula da mutanen dake tsakar gidan ba, bare ta gaishesu, "lallai yarinya nan kin rika... Ta juyo da sauri tare dadawowa da baya tace "kuyi hakuri ban kulabane wallahi, ina yinin ku?" wata farar mata mai matsakaicin jiki tana linke kayan shanya tayi tsaki hade dace "ai bamu ba, wataran mahakaxaki mance da uwarki, munafukar Allahkawai, bace mana da gani, ta tsunkuyar da kai takasa wucewa, don ita har ga Allah hankalinta nebayawajen amma tasan baxata iya fidda kantaba. Dan haka kawai sai ta kara maimaita "kuyihakuri" kawai. Tabe baki ta xaunen tayi tare da mikewa tace "banxa Agola kawai, tayi sashinta tashigetare da banko kofa, itama farar hakan tayimata hade da cemata shegiya tayi nata sashin. Jikintaa mace ta karasa palon nasu, momynta dake kwance tana karatun Adduo'i, ta dubeta bata ce komai ba ta kau da kanta, ta nemi guri taxauna tare dacewa " ina yini momy, momy ta mikexaune tana dubanta tace me ya faru Intisaar? Ta kirkiro murmushi tace bakomai momy, batasakecemata komai ba, sai ca tayi "ya mai jikin?" tacejiki da sauki sosai, hajiyarsu tace kila gobema asallamesu daga Asibitin, momy tace "to Allah yasauwake, kiyi sallah ga abincin ki can arufe," tace to sannan tashiga bathroom tayi alwala tafito, tana idar da sallan ta jawo abincintata fara ci, "momy ina ihsaan,? Momy tace taje kitso tare da mikewa tashiga bedroom dinta, Intisaar na gama cin abincin ta fita da kwanukan ta dawo, ta watsa ruwa, sannan tace wa momy ta tafi wajen Innah. A hanya suka hadu daZainab, Zainab ta dubeta tace "har kin dawo dagadubiyan?" eh na dawo daxun nan, ban madade dashigo wa gidan ba, tana magana ne tana tafiya, Xainab ta dan kwala mata kira hade dacewa "wajen innah xaki ne?" eh can xani me yafaru? Ok kice ta bani dambu na, dan daxu kursumtace min ta siyo mata dayawa, intisaar tace tokixomuje mana, "aa Hajiya ta aikeni ne " toshikenan idan ban manta ba xan karbo maki, xainab taharareta da wasa tace "xaki gane kuranki nekuwa idan kika manta" intisaar bata ce komai ba, ta wuce tana dariya. Cikin gidan innar tasutake, dan babban gida ne na gaske. Tana isasashin innar ta ganta xaune a bakin kofar falonta, tanakulla magunguna, intisaar ta hade rai tace"wai innah bakya gajiya da daure daurenmagungunada kunce kuncensu ne, innah ta hade raiitama tace "to dan gidanku ba duk dan saboda kunakeyiba" intisaar ta gyara xamanta tace "to ina dambuna da xainab innah? Da sauri ta juyotanaduban intisaar din tace "oh ni Rahmatu nashigauku, to yanxu uban wa yace maku na siyadambu,?" intisaar ta tabe baki tace "cinye kayanki innah, sannan ta mike ta shigepalon tayikwanciyarta." daga waje taji innah na cewa "inatakwarata?" ta yi shiru kamar baxata amsa ba, Saikuma tace "tana wajen kitso," to meyasabakikawota nayi mata ba.? "Ke har wani kitsokika iya innah.?" innah bata sake cewa komai bahartagama abinda takeyi ta shigo parlon. Sunjimasuna hira da inna, har aka kira maghrib ta yi salla, sannan ta diba abincin da fadila ta kawowainnahtaci. Ba ita ta bar sashin innah ba sai wajen karfe goma saura, bayan ta dibar wa xainabdambunta itama ta debi nata, tayi mata saidasafe ta kama hanyar sashinsu, duk da tsakargidan da haske sosai dan ko ina kwan fitila ne. amma gabanta faduwa yake yi sosai,da sauri ta karaso gida ta bude kofa ta shige tare dakullewa, momy ta dubeta tace " ke da waye haka,? Tayi dariya tace bakowa, momy tace to yayi. Washegari bayan sun karya ita da kanwarta Ihsaan suka je goudan Abba, yana xaune aparlonsa yana sauraren labarai suka shiga, kursum na xaune a kasa ta hade rai, daalamarabu take jira. Ya amsa masu yana murmushi, ya dauki ihsaan yace "mamata yau kin tashi da wurikenan, sannan ya dubi intisaar yace ke kikayimata kitso ko inna? Tayi dariya tace a’a saloonakayimata," to yayi kyau, ya dubi kursum yace"yauwa ina jinki, Tace dama Abba gyaran gashi xanje asaloon, yace nawa ne? Dubu biyu ne Abba, yaxaro ya bata, sannan ya dubi intisaar yaxaro dubu biyun ya mika mata yace "ke ma kigyaragashin naki, sai kuje tare," tayi murmushihade da godiya, kursum ta dubeta cikin tashin hnklidatakaici, sannan ta mike tace ngd Abba, ta fice. Intissar ta da da yi masa gdya sannan takamahannun kanwarta suka bar parlon. A hanyasukahadu da Hajiya tsaye suna jiranta, gabnta yyi mugun faduwa, ta daure ta karaso bakintanarawa tace "ina kwana hajiya.... Ido ta xaromata tace "ban kwana ba dan ubanki, da sauriIntissarta mika mata dubu biyun dake hannunta, takarbe kuwa, sannan tace "bnxa kawai, sukayigaba daita dasu kursum, kursum tayi mata gwalotare da fashewa da dariya, ita dai bata ce komai bata kama hannun kanwanta suka yi sashinsu. Ihsaantace, "amma anty ai ke Abba ya ba wa kudinkika basu?" intisaar tayi mata murmushi tace ai nasu ne dama, sannan ta ja ta suka shigepalor. Momy na shara ta karbe ta karasa sannan ta gyara gidan, ta kwaso kayanta tana guga. Ihsaan na jikin momy suna kallo, tace "momy,daddy yace kitso na yyi kyau wai, momy tayimurmushi tace "sosai ma kuwa" intisaartace "nima ae irin shi xanyi," to ba kin ba sumomynanty Xainab kudin ba, momy ta dube intisartace "wani kudin?" nima bn san mata ba. Ihsaan tace Abba ne ya bata two thousand yace tayikitso shine momynsu khadija ta karbe, momy tamikeba tare da tace komai ba ta dauki hijab tace"idan kin gama gugan ki dauki kudi ki siyogolden morn tun daxu ihsaan take so kuma bbu, ni xanje na gaida innah, ihsaan ta mike tace momynimaxan biki, eh dama tare xamu ae daukohijabin ki, suka fice tare. Intisaar ta cigaba da guganta. xainab ta shigo, ta dubeta tace inadambuna, saida ta ja mata rai sannan ta dauko ta bata tanadariya, xainab tace amma ke kka dibar minko? Eh nima ga nawa can, xainab tace shiyasanaganshi dan kadan, intisaar dai bata ce matakomai ba ta karasa guganta ta kashe dutsengugan ta kai kayan daki, ta dawo ta dubixainab tace yau baxa kiyi kwalliyan friday bne? Tace "uhum bari ma ki ga, aikena pa hajiya tayi. Tayi hanyar fita, intisaar tace ina xaki,? Supermarket! Tace ba tare da ta kalleta ba, tace jirani nimaxan siyo golden morn yanxu, ta daukokudin da hijab suka fita ta rufe kofa, xainab tacemomytana wajen innah ne, yea tana can, sukakamahanyar supermarket. Da kafa suka taka dan bawani nisa sosai, sai da intisaar ta rakatagidansukawarta dake Area din ta karbo litattafaisannan suka kama hanyar gida. Umma suka gani atsakar gidan ita da 'yar ta Rahmatu tanamatatsifa, intisaar ta gaida ta, bata ko kalla indatake ba bare ta amsa, ta dubi xainab tace ke danubanki ba aikenki hajiya tayi ba kika biwannangantalalliyar ku ka je gantali koh? Xainab tayatsine fuska ta danyi tsaki ba tare da tace matakomai ba ta nufa sashinsu, intisaar taisashinsuita ma da saurinta. ... Tana shiga parlonsu ta tar da ummanta tana shiri xata fita, tace "momy ina xaki?" momyba tare da ta kalleta ba tace "inda kikaaikeni" sai da ta gama shirinta tsaf sannan tacexasu je dubiya da innah... Wayan intisaar yyi kara tadauka tana cewa "kar dai har kun dawosamira?" daga can bangaren samira tace nace makiaetare xamu, ni ga ma ni a gate dinku kiyimaxa kishirya, tace mata "Allah karki ba kankiwahala ni bbu inda xani, ta kashe wayan. Momy tadubeta tace ina xaku, "wai dole tare xamu gidanMaryam kuma nace masu baxa ni ba, momy tace"waimaryam da akayi bikinta?" eh ita... Aa bakikyauta ba intisaar ayi bikinta ki ki xuwakumayanxun ma kuje gidanta kice ba xaki ba, ki dauredai ki shirya kuje, amman karki dde, ni natafi. innah tana jirana, ki tabbatar kin kulle minkofa, tace"to momy Allah ya kiyaye, a bakin kofatahadu dasu samiran suka gaisa sannan tawuce. Ba dan ranta ya so ba ta shirya suka bargidan, suna ta mata tsiyan bbu wanda xai xo bukinta, ita dai murmushi kawai take yi dan bata dalkcnsu, karfe sha biyu suka iso gidanmaryam, tayi murnar ganinsu sosai, amma sai tahade waintisaar rai, da kyar intisaar ta shawo kanta, tana dariya, dan tasan bata kyauta mata ba tundabata je bikinta ba. Ta cikasu da kayen ciyeciyeda soft drinks, lkcn sllh nayi suka yi gaba dayansu, sannan ta kawo masu abinci sunacisuna hira. Daga bisanni intisaar ta basuuxurintana cewar xata wuce gida dan momy batanan, maryam ta fahimce ta dan hka tayi matagdyanxuwan da tayi, intisaar ta hada ta da dubu biyu ta amsa da kyar sannan ta bar su samira agidanta wuce. A dai-dai gun da xata hau motaummi ta kirata, ta dauka tana cewa ummi ansallameku ne, ummi tace "eh yanxu ma xamu wucegida, cama nake xaki xo intisaar, intisaar tayimurmushi tace "to bari na taho ina hanya dan munjegidan maryam." tana isa hsptl ta gaida nurses dindakereception ta haye sama taje ward din daummin take, cak ta tsaya a stairs din gabanta na faduwa, kamr warce aka hankado ta juya dasauri ta fara sauka, da sauri ya bita har sukasauka kasa ya maxa ya shige gabanta yace"meye kika gudu 'yan mata, nayi laifi ne, fuskartaa daure tace a'a ta juya ta haye sama, jin ya biyota ne ya sa ta tsaya, ya karaso yace "yakika tsaya kuma, bata ce komai ba tayi hanyarward din kawarta yana biye da ita. Xaune tagaummi tana duba Novel, ta karaso, shima ya shigodakin, gefen ummi ta xauna tana ce mata ya jikin, taceda sauki ya su mummy? Ta daga kanta dasauri tace doctor dama ka shigo, yyi murmushi yace "yea, kin warware sosai yanxu ko? Tace "eh nagode Dr. Yace no probs wannan kawarkice, tadubi intisaar tace eh, yace hmm.., what's her name? Ta dubi intisaar da tayi kmr ma batasansuna yi ba tace "Intisaar sunanta" waww.. To menayi maki intisaar tun jiya kke guduna, itadaibata ce komai ba sai wayanta da take dannawa, yyi murmushin karfin hali yace o.k , am srrytoidan ina damunki, tace "o.k" sannan ta dubi ummi tace momy pa, ummi tace "sunje kirantaxi ita da su falmata yanxu xamu wuce dama." Shikam juyawa yyi ya bar dakin, intisaar ta danja tsaki, ita dai ummi bata ce komai ba. Karfeukusuka bar hsptl din, bayan ummi taje tayi maDrfaruuq godiya dan yana da kirki sosai, takuma maida masa Novels dinsa da ya bata takekarantawa, sannan ya nemi alfarman tabashinmbr intisaar bbu musu ta bashi yyi mata gdya. Har bakin taxin ya rako su, momy ta sakemasagdya sannan ta shiga motar, suka kamahanyargida. Yau wajen sati uku kenan, kullum sai Dr,faruuq ya kirata, wani lkcn ta dauka, wanilkcn taki dauka dan ko ta dauka bashi da watamgnar da ya wuce ta amince masa, ita kuma yanxukam ba abinda ke gabanta ba kenan. Ummi ba mata adalci ba da a bashi nmbrta, kuma taje har gidan nasu ta nuna mata bata ji ddin hknba. Suna xaune da momy suna kallo da daddareyakirata, ta mike ta shige daki da sauri danbatasan ta jawo hnkln momyn tata, ta daga, taji Yace"intisaar, tace ina jinka, murya can kasa yacemata " bni da lfya yau, sosai ki mani addu'akinji, tace "xan mka Allah ya sauwake, yacenagode. sai da safe, tace tam. Tana fita hanyar ktchen tayi taje ta wanke kwanukan da aka ci abinciagidan dan momynta ce tayi girki, ko da takomapalonsu ihsaan tayi bacci. momy kuwa,Abba yakirasu da su hajiya yana masumagana, tana kwantar da kanwarta tayi wanka ta kwantaitama. Washegari bayan sun dawo daga makaranta, taje tayo wa momynta cefanesukashigo gidan tare da xainab, ita ma an aiketa,kayanta da ta shanya taga fadila tanakwashewa tana xuba su a kasa, xainab tace "meye hkafadila, fadilar tace mele. Intisaar tace"meyasa baxaki kira ihsaan ta kai mun ciki ba fadila,"fadilar tace "sbda baki isa ba," intisaar tace"shikenan nagode," kursum ta fito da sauri tace"kar ma ki gode mana mahaukaciya kawai, intisaar tace "nagode" sannan ta kwashekayannata xata wuce ciki, fadila ta banke ta,cukumota xainab tayi tana cewa ke wacce irin dabbacefadila, wllh sai kin gya min me intisaar tatsaremaku a gidan na, kokuwa suka farayi, sai gauwarsu ta fito da gudunta, me ye hka?? Meya faru, kursum da sauri tace "wancan dabbarce tahada su fada, bata bi ta kansu ba ta cafkointisaar ta dinga xuba mata duka, tana kukatace" wllh momy ni banyi mata komae ba, ummabata saurareta ba ta dinga jibgar ta kamranaikota tana cewa "kaji min matsiyaciya, dan uwarki, nandin gidan ubanki ne da xaki hada manayara fada munafuka, tuni xainab ta cika fadila tana"waiumma me tayi maki ne, dan me baxa kitambayi munafukar yarki abinda tayi ba to.... Tanamagana ne tana kuka, sai ga hajiya ta fitodasauri ta cafke xainab tana cewa , danubankiintisaar kanwar uwarki ce ko ubanki, kukaxainabtake yi kawai, uwar ta watsa mata mari tajefarda ita sannan ta koma kan intisaar, daga itaharumma sukayi mata tatas, da kyar ta samusukabarta ta shige palonsu tana kuka sosai,momynta na xaune tana yanka alaiyahu. Xubewa kasatayitana kuka sosai, ihsaan ta xauna kusa da itatana share mata hawaye, momy bata ce komai ba, ta karbi cefanen ta wuce kitchen, tayi kukasosaihar barci ya dauketa. Da magrib momy tatasheta tayi sllh, ta bata abincin kowa ta kai masa sashinsa, hajiya ta fara kaiwa, xainabnabakin famfo tana alwala ta karaso da sauritakarba tana cewa kiyi hkuri intisaar Allah xaisakamaki, tayi murmushi bata ce komai ba tawuce. Ta dauki na umma ta kai mata, yusuf ta ganibakin kofa ta mika masa ya amsa sannan tadauki na inna ta kai mata. Tana xaune kandarduma, ta gaisheta, ta dubeta da kyautace "wa ya saki kuka intisaar,?" ta sunkuyar dakanta tace "ciki na ne ke mani ciwo, da sauri innatamike ta shige ciki ta dauko magani ta jika tabata tasha, batayi musu ba ta karba ta sha, innata xauna tana ta mita wai cikinta na ciwobaxa ta xo ta karba magani ba tana san ta kashekanta, da kyar ta samu ta barta ta wucesashinsu. Tasan dan inna bata nan neshiyasa sukayi mata hkn, dan da tana nan bbuwanda xaimata hka. Ko da tashiga parlonsu, momy takaiwa Abba abinci a sashinsa, ta dan ci abincitayiwanka sannan ta kwanta. Tana xaune tana sama ihsaan rani, momy kuwa na daki tajianyisallama, da sauri ta jawo hijab dinta ta sadanyar shimi kadaine jikinta da xani, sannan taamsasllmn tana mikewa, daga wajen yashigoyana murmushi yace ihsaan lalli ake yi, tace eh"unclesannu da xuwa," ya dubi intisaar yaceyauwa kanwas ya momy pa, sai ga ta ta fito taceHaisam yaushe a garin, yyi murmushi yadurkusaya gaisheta, yace "da safe naxo momy,amma bn dde da shigowa gida ba." ayya to ya hanya,? YaceAlhmdllh, ita kuwa intisaar ta mike ta kawomasaruwa ya amsa ya sha yana gdya, suna hiradamomy sai ga kursum, ta shigo ba ko sallama babu. Tace "yaya umma na kiranka, yace baki iya Gaisuwabne, ta yi tsaki tace ina yini ta fice, ya bita dakallo ya kasa cewa komai, ya mike yyi yakeyace"momy da daddare xan xo muyi hira, tace toHaisam Allah ya kaimu, ya dubi intisaar yace"kanwata naga sai kyau kika karawa meyesirrin, Tayi dariya tace "kai yaya bnda sharri, yyidariya yace, "da daddare kije wajen inna mushahira,tace "to yaya Allah ya kaimu, sannan ya fice dasauri dan ya riske Kursum amma har tashigegida. Yana shiga uwar tashi ta farabalbalesa damasifa, ita bata san shige shige da gantali, dagaxuwansa ko hutawa bai yi ba har yaje yawo,yyidariya yace "yau naga ikon Allah, bnda ikonxuwawajen matar ubana, A'a uwar ubanka, bamatarubanka ba, wllh ka fita harkana haisam. Mikewa yyi yace "to Allah ya kyauta sannanyyi sashinsa yana waige-waigen inda xai gaRahma amma bai ganta ba. Da daddaresukahadu da yaya Haisam a sashin inna, sunyi Hirasosai tun suna yi da inna har ta bingire awajentana barci, Intissar ta dinga dariya, yace "tokarki tasheta mana kanwa," tace to na daina yaya. Yace to yanxu samarinki nawa,? Tayi dariyasosai sannan tace "ko daya yaya," yace "kinmaidani wawa ko?" tace "lah, hava yayanawllh a'a," yace to gya min gskya, tace "Allah yayabana kulasu, yace "to ki daina hka, wataranAbbaxai ce ki fito da miji, idan kuma baki da, xai iyahadaki da wanda ransa yaso, dan hka, kidai-daita da mutum daya, kuma bance wai ki tarasamari ba, tayi dariya tace "to yayana," a hkaya rakota har sashinsu yyi mata sai da safe. Ta fitodaga wanka kenan wayanta yyi kara, sai dayakatse aka sake bugowa sannan ta dauka, "intisaar," taji ya kirata, ta amsa ba tare datakula ba, yace "ya gida"? Tace lau, yyimurmushi yace to yyi kyau, dama na kira ne na gaidaki,bye.. Ba shiri ta samu kanta da ce masa yajiki?Yyi jim, sannan yace "to da sauki, ammadaxunnan aka cire min drip, tace "to Allah yasauwake, yace ameen ngd, sannan yyi mata sallama yakatse wayan. Washegari da ta dawo dagamkrntasai ga mis cals dinsa, ta dauka tana kallonwayan, samun kanta tayi da send din nmbr,ba tare da ta shirya ba, ya dauka, suka gaisa,sannan da sauri ta fara kame-kame, "emmdama mis cals dinka na gani," yace hmm, yea nakiraki daxun, "ok naje mkranta ne," sai tayi da tasanin kiransa ma, ta dai dake dai tace "ya jikin,"yaceAlhmdllh, daxun ma naje karban treatment,tayishiru, can dai tace "to mene ya sameka?"yace hmm... Owwh bari na kiraki, na manta wllh, ........ Yana katse kiran nata ya kirata, "yi hkuriIntissaar, i 4got, tace o.k, sannan yace"idona keciwo," 4 d past 4 dayz yanxu,spec dina ya Bugeni a idon, Ayya, Allah ya sauwake.. Ameen ngd. A hankali taji ya kira sunan ta, ta amsa tana saurarensa, "ki bani ixini naxo gidankumana, dasauri tace "a'a karka damu, kaga bye.. Yanxu inaaiki ne, sai anjima, ta kashe wayan. Taxaunatayi jim tana tunanin abinda ya Haisam ya gyamata jiya, ihsaan ce ta shigo tace "Anty, innatace na kiraki, tace "to, tare da mikewa tadaukihijab, sai kuma ta tuna bata cire uniform ba, tacire, sannan taje kiran da innah ke mata.Rahma da khadija suna wankin uniform dinsu abakinfamfo, suna ganinta sai suka tare hanyarwucewa, ta dan yi jim a wajen, sannan tace "kugafara xan wuce, Rahmatu tace "idan anki pa?"khadija ta kara dacewa "ko gidan ku ne nan?" itadai bata ce komai ba sai kallonsu da ta tsaya yi,kumfar wankin Rahmatu ta debo da yawa ta yarfa mata a fuska, ihsaan ce ta xo da gudutana cewa me "me tayi maku?" khadija ta tura taharsai da ta fadi, intisaar ta kalleta cike datakaicitace "ita kuma me tayi maki khadija"? Ihsaan kuwa tuni ta mike tana kuka ta cire talkaminkafarta tana dukanta dashi, daukartakhadija tayia fusace ta tsoma ta cikin guttern dakewajen, intisaar bata san lkcn da ta fixgo khadija batadinga dukanta har ta jefata cikin kwatan itama,da gudu rahmatu na kuka da ihu taje ta kirahajiya da umma, dan suna kusa da gate axaune. Da gudu kuwa suka karaso wajen, hajiya tafara ciro 'yar tata daga ciki kwata tana salatitare da cewa "mai xan gani hka?" ummahkuwata cafko intisaar din da ta juya da gudu xatabarwajen, dukan fitar hnkli ta dinga yi mata dadukakarfinta, hajiya ma ta xo ta sa hannu, kukaihsaan ta dinga yi tana kwalawamommynsu kira,sai ko gata ta fito, ta kallesu bata ce komaiba,ta juya ta wuce abinta, su fadila da kursumduksun fito, hka aka dinga hayaniya, dukansunaxagin intisaar, "wllh sai naga bayan ku da uwarkua wannan gidan, shegu munafukai kawai,tunda Kuka shigo gidan nan muke.... Muryar inna dasuka ji na ya katse su, sai ummah dake tataunan cingam, "me xan gani hka Aisha?" cewarinna knan tana duban Hajiya baki bude,ummahtace cin halin ko in kula, gata nan kitambayetamana, hajiya ta maxa tace "kashe min 'ya xatayida har xata danneta tana duka?" innah tadubiintisaar dake ta faman rusa kuka ita daihsaan, tace "nashiga uku ni Rahmatu, yanxu me'yar nantayi maku da har xa kuyi mata taron dangi? Harda gore gore ina ji?" nan fa inna ta dingarusamasu kuka har da durkushewa a wajen,dagahajiyan har umma suka tabe baki, hajiya tace "toinna da yafi da ne?" sunan momyn intisaarinnata shiga kwalawa tana cewa "zainabu, zainabu,da sauri ta fito tana cewa "na'am inna?"inna tasharbe majina tace "ke wai wace irin sha-sha sha ce, ynxu kina ciki ana neman kashe makiya'ya kin ki fitowa? To Allah ya isa ban yafe ba, wllhtllhsai naci uban mutum yau, ta fadi tana kallonhajiya da 'ya yansu gaba daya, Zainab ce takaraso da sauri dan dama bata gidan, tanacewa "inna me ya faru,?" inna ta ciro wayarta dasauri ta mikawa xainab tace "maxa ki lallubo min number Abubakar, jikinta na rawa ta saka nmbrAbbansu ta mikawa inna, inna ta karbe da sauri tace"Abubakar maxa ka dawo gida yanxunnan,.. A'a idan kaxo ka gani, ta mikawa xainab wayantace"kashe min kayana, sannan ta kamo hannunintisaar din ta wuce sashinta da ita, ihsaan nabiye dasu. Tab! Hka hajiya tace cikin tashinhnkli, yanxu hadasu tayi da Alhaji sbdawannanAgolan, lallai akwai sake, nan xainab tabarsu atsaye ta wuce, momy kuwa tuni dama takomasashinta, ummah ta dinga gyada kai tanacewa "yau munga ikon Allah agola ta fi masu gida,nansuka dinga tsakar wa momy habaici damaganganu marasu dadi, ita dai bata tanka ba tana daki abinta, Haisam ya shigo yanadubansu, mamaki ya bayyana a fuskarsa yace "momymeyafaru, hajiya tace "agola ce tafi ya'yanmasu gida, yau munga ikon Allah, tsaki yyi ya barwajen kawai, ya samu xainab tana kwashekayanta, ta gya masa abinda ya faru, saikawaiyyi sashin inna, tana xaune sai rusa kukatake tana Allah wadai da matan Abubakar, danko itabasu ganin girmanta, kuma yau tasu ta kare agidan nan, intisaar na xaune ta xubawa TVido, dan ita bata ga abin kuka a nan ba da innaxatadinga yi, ihsaan kuwa na lullubeda towelalamar wanka tayi, haisam yyi sallama ya shigo,batajiraya xauna ba ta dinga jero masa abinda ya faru,sai ka rantse kace tana wajen, hkuri ya dingabata, amma kmr yana xugata, dan hka sai yajuya ya dubi intisaar yace "ki yi hkuri intisaaridan Abba ya dawo xasuyi bayani, da sauri innatace sake kira min Bukar din, ko abinda yke yiyafi kiran nawa ne, a lkcn Abba ya shigo gidandamotarsa, haisam yace to gashi can ma yadawo, tashi tayi da sauri taje ta samesa, haisam yagirgixa kai ya mike ya dauki ihsaan yace"srrykinji ko bby, yau nasan ai Abba sai yyi masubulala tunda suka tabo mamarsa, dariya kawaiihsaan tayi, sai ga Abba da inna sun shigo, haisam ya mike ya bar parlon bayan yagaidaabban nasa, intisaar a xata tashi inna tace"dawoki xauna, sannan inna ta fara jawabinta tanamatsar kwalla, ya ma rasa mai xai ce, kawaisaiya mike, yace "ina xuwa baba, ya fice, sashin hajiya ya nufa direct, ya dinga kwada matakira, Aisha, Aisha, tace na'am Alhaji sannan ta fitodasauri tana cewa lfya kke kwada min kirahka, yace "maxa ki bar gidan nan ki tafi gidanku,danban aure macen da xata sa mahaifiyatakuka ba,bai jira cewarta ba, yyi sashin Shafa, watoumma,ita ma ya gya mata hkn sannan yace dukwandaya dawo ya samu bai tafi ba to a bakinaurensa,ya juya ya koma wajen inna, hka ya dingabatahkuri sannan ya tabbatar mata da duk suntafigida, nan inna ta samu natsuwa dan itakadaitasan irin wlkcn da matan nasa suke mata,dakuma yanda suka sa xainabu da yaranta agaba, sai da ya tabbatar ta hkura sannan ya daukiihsaan yyi hanyar sashin su intisaar din,intisaar ta mike taje tayi wanka a bayin inna, ko datafitosina xaune da haisam tana tayi masa mita,intisaar tace inna wllh kin cika mita, inna tace"nayi din, sannan taci gaba daga inda tatsaya," da kyar haisam ya samu ya lallabata ya barmatadakin, Abba kuwa ya kira su kursum dakhadijagaba dayansu yyi masu ta tas, sannan yasasukneel down a tsakar gidan, ya tabbatarmahaifiyarsa ta sakko sannan ya komaoffice, Su Aisha da Shafa kuwa tuni suka bar gidandansunsan Alhaji baya magana biyu. Washegarin ranar suna xaune ita da xainab Dr faruuq ya kirata, taki daga wa har sabiyu xainab tayi mata mgna sannan ta daga, Sukagaisa, tayi masa ya jiki, yace "jiki da saukiintisaar, ya su momy?" tace "lau suke" ohk..Inakofar gidanku... A dan firgice tace "me?"yace "eh".. Kaga bna san hka malam ka rabu danidanAllah, ta katse wayan da sauri. Xainab taceb"waye?" intisaar tayi tsaki tace "oho nimaina nasani, wai wani gashi a kofar gidanmu saikace nagayyato sa, wllh xan bata ma ummi rai ne, ni Tadaina min shisshigi," xainab ta mike hadeda tabebaki ta dauki hijab, intisaar tace "ina xaki?"ba tace komai ba har sai da ta isa bakin kofasannan tace "am cummin" sannan ta fice. KofarKofargida ta nufa, bakin gate ta tsaya tana waige-waigen inda xata hango bakon intisaar din,hardai ta hangosa jikin wani flower yana tsayeyanadanna wayarsa, ya daga kai yana kallonta....Nan ta gane shine bakon, dan da alama waniyakejira, tace "kai ne faruuq wai?" ya dubeta dakyauyace eh nine, tace "bisimillah wai ka shigo,"yace"to ngd sosai," tare da binta har cikin gidannasu, tayi masa iso har sashin inna. Tana xaunetasaTV a gaba wai tana kallo, xainab tayisallamahtashiga tana cewa "inna kinyi bako," innatace"waye?" xainab ta xauna gefenta tana yardariyatace "saurayin intisaar ne, wai kunyar kawomaki shi take yi," da fara'a sosai inna ta tarbesa,tabude fridge ta kawo masa ruwa da lemotana samasa albarka, hkn yyi ma faruuq ddi sosai yadinga gdya, nan dai inna ta dinga jan sa dahiratana basa lbrin Intisaar, xainab kam saidariyatake yi, ta mike da sauri ta barsu tayisashinsuintisaar, intisaar tana xaune tayi shiru,alamar tana cikin damuwa, xainab tace mata "meyafaru?" tace "wllh xainab ni bna sanwalakantawannan mutumin amma yasani gaba... Xainabtace "to kuma meye abin damuwa bayan kinkoresa?" intisaar ta tabe baki tace bbu! Xainabtace gskya kam, inna dai tace na kiraki tanajiranki, xainab na kai wa nan ta fice ta barmata parlon. Jikinta a sanyayye ta dauki hijab tayisashin inna, tayi sallamah, inna ta amsa dakarfinta har abin ya ba intisaar dariya, koyaufarin cikin me inna take yi hka? Duk da takalminda ta gani bakin kofar inna bata kawokomai a kaba, dan a tunaninta ya Haisam na ciki ne, tanashiga palon tace "ya Haisam ka min promise ndfail ko? Cak ta tsaya ganin faruuq xaune aparlon, kanta ya dinga mata wani irin juyi takasafahimtar komai, ya dago kai yana dubantakawaiba tare da yyi mgna ba, dakin inna ta shigedasauri, inna tace "yo kunyar me xaki ji kuma?Saikawai ta fashe da dariya" intisaar taji wani irintakaici ya lullubeta, yanxu xainab ta kyautamataknan? Sa ta tayi taje wajensa bare har tashigodashi gidansu kuma ma wajen innarta, Sallamanya haisam da taji ne ya sanya ta kararudewa,inna kuwa sai xuba take ta wa faruuq, shima yabiyeta suna ta yi, inna ta amsa wa haisamsllmaya shigo, tana wangale baki tace "haisamwannan saurayin intisaar ne yaxo gaisheni,haisam ya kallesa da mamaki suka gaisa dafara'arsa, sannan yace "to ina intisaar dininna?" inna tayi dariya tace "wai ita kunya tun daxuta shige daki," haisam ya kirata ta fito gabantana faduwa ta nemi gefen inna ta durkusa tanagaishesa, ya amsa yana daria yace "wayewannan?" ta kalli faruuq tace "nima ban san shiba " dariya haisam yyi yana kallon inna, shi kuwafaruuq yyi murmushi ya dukar da kansakawai, hka Haisam ya ci gabada xolayarta amma itahnkalinta na waje daban, tunani kala kala yakasu a ranta, da daga kai ta dan saci kallonfaruuq din suka hada ido ta kauda kanta da sauri,hka suka ci gaba da hira gaba dayansu ammabnda ita da ta kurawa plasma ido. Wayan haisamda yyi ringin ne yasa inna ta dakatar dasurutunta tana tambayansa waye, salanta knan,da taji wayarka yyi ring xata tambayekawaye dasaurinta, yace mata mijinki ne, sannan yadaga,bai jima yana mgna ba sukayi sallamah yakashewayan. Inna tace Aliyu ne ko wa? Yace "eh shine" inna ta girgixa kai tace "oh yaronnan baida kirki, halinku ba daya ba da nashi, bai dakirkiko kadan, bai yo halin Bukar ba, halinsa saknauwarsa... Haisam ya maxa ya katse ta yace "toxabiya, ni xanje GRA ne ynxu sai na dawo"tace to... Amma me Aliyun yace mka yanxu,? Yausheyace xai dawo,? yana ina ne yace mka? Kode yana hanya ne? Cike da kufula Haisam yacekaini inna ban sani ba, ca yyi na gaida innaRahmatu kawai, sannan ya mike sukayixchange din nmbr da faruuq, yyi masu sallama yafice, intisaar ta mike da sauri tace "inna bari narakasa gate ina xuwa"inna tace to kiyi maxamaxa ki dawo, tace to. Sannan tabi bayanhaisam da sauri. Haisam ya dubeta yace "saurayin naki yahadu intisaar, ta ce "bna so yayana, ni ba ninakawosa gidan nan ba, yyi dariya yace "bndakarya dai kanwata" nan ta marairaice masa Tayimasa bayanin yanda suka hadu da faruuq Harxuwa yau da ya xo, yyi dariya sosai sannanyace "to amma kanwata naga ai bai da aibukumayanada hankali, ki dan basa dama mana."ita daibata ce komai ba har suka iso gate sannan Yadubeta da kyau yace "kar fa ki ki komawakanwata, kinsan dai walakanci bai da kyau,kibasa dama ku saba, tace "to yaya baxangudu baxan koma" yauwa kanwata gud of you. Nan sukayi sallama ya wuce ita kuma ta koma Sashininna. Suna hira har ynxu, ta nemi gefe taxauna,tana jinsu kawai sai dai tayi murmushi. Sai Wajenkarfe shidda yyi sallama da inna, ya batakudimai yawa, ta karba tana godya, hkn yyimugunbata wa intisaar rai, kamr warce ke jiramaimakon tace ya barshi, har bakin kofainna tarakosu sannan ta koma ciki tana masa Allahyakiyaye hanya. Suna tafe ne bbu wanda yacekomai, can dai ya dubeta yace "ngdintisaar,"bani ce da gdya ba, ta fadi ba tare da takallesaba. Yace to waye? Bata kallesa ba tace xainab,yyi murmushi yace gskya ne, bbu wanda yasake mgna a cikinsu har suka isa gate sannan yadubeta ita ma ta kallesa, sai ya sakar matamurmushi , ta sunkuyar da kai da sauri,bata sanlkcn da itama tayi murmushin ba. Yyi ajiyar xuciya yace "to kira min xainab din muyisallama," aa dare yyi ka bari sai wani lkcin, yaceba nan gidan take bane?" eh nan takeamma ynxu ta shiga gidansu. Yace gskya ne. Tointisaar i am vry grateful, ngd sosai, tagyadamasa kai kawai sannan ya juya ya fice, ta bisa da kallo, ya juya suka hada ido kunya yakamatatayi saurin rufe gate din sannan tayisashinsu. Gabanta yyi mugun faduwa ganin su Kursum labe ta windo suna kallonsu, da sauri tayisashinsu tabude kofa ta shige. Ko da tashiga ta tarar Momybata ciki, tayi hanyar kitchen, ta ganta daxainab Suna raba abinci, taimaka masu tayi sukagama A tare, ita ta kai ma inna nata, xainab kuwa takaima su kursum nasu, intisaar bata ce daxainab komai ba, itama xainab din haka.su hajiya kamyau kwanansu uku basa gidan, xainab batadamuba, hka ma haisam ko a jikinsa, su kursum dai nehankalinsu a tashe, momyn intisaar tayikkrinshawo kan Alhajin amma hkn bai yiwu ba,innakam ko a gyalenta, dan gidan ma sai yyi mataddi. A kwana a tashi intisaar suka shaku dafaruuq sosai, fiye da tunaninta, faruuqmutum ne mai kirki da fara'a, duk gidansu an sanshidanduk jumm'ah sai yaxo gaida inna sannan yashigaya gaida momy. Su fadila da su kursum kambakin ciki kmr xai kashesu, gashi yau wajensatiuku knan Alhaji yaki barin iyayensu su Dawo. Intisaar ta samu kwanciyar hnkli sosai agidandan bbu mai takura mata ynxu, yawanciIdanfaruuq yaxo gidan tare suke xaunawa har Daxainab suyi ta hira, a wajen ummanta kuwabatada hiran da ya wuce na faruuq, hka ma awajen inna. Abba kadai ne bai san dashi ba a gida,amma har su Hajiya da umma da basa gidan 'yayansu su kirasu sun fesa masu. Yau ma kmr kullum faruuq yaxo gidansu da yake Friday ce, wajen karfe shidda ta rakosa xai wuce sukaiskefadila da khadija a kusa da gate a tsaye, dukdasun gansu amma basu yi kkrin matsawa dagagate din ba, faruuq dai bai ce komai ba dantundayake shigowa gidan basu taba bude baki sungaishesa ba, shima bai taba masu maganabadukda ba ma ganesu yke yi ba, bayan ga xainab. Dakyar intisaar ta iya cewa ku gafara dan Allah,ganin sun kusa minti uku a tsaye kuma sun Kibarin hanyar, ke din a su wa? Khadija ta jefomata tambayr, tayi shiru bata ce komai ba,khadija ta kara da cewa "nan gidan ubanmu Nedan hka ba ki isa kixo ki mana iko dashi ba"saiki bari idan kin samo ubanki sai kiyi iko dagidansa idan ma yana da" fadila ta fadi awalakance tana girgixa kafa, kuka ta sakar Masua wajen, faruuq kam kansa ya daure, ya ma Rasame xai ce, khadija ta dubesa "bawan Allahkanabani tausayi wllh, ga ka kyakkyawa maiasali, amma ka rasa warce xaka bige da nema saiwarce har yau ba a san ko yar gidan uban wayebace, sai yar tsintuwar innarmu, da sauriintisaarta juya da gudu ta bar wajen, ya bita dakallo, bakinsa yyi masa nauyin kiran sunan natama, fadila taci gaba tana kallonsa, "ita ba yarkowabace, sannan ta samu wajen fakewa agidanmuita da uwarta sai su dinga mana isa, yauwatadaya da sati biyu knan da suka sa Alhaji yakoreiyayenmu a gidan nan sbda ita da uwarta,kadijatayi tsaki tace "ai basu ga komai ba matukunna,sai suma sun bar gidan nan kmr yanda sukasaaka kore uwata." fadila tace "nima hka," sannan suka bar wajen gate din suka shige cikingidaxuciyarsu pal da murna. Sai da faruuq yyikusanminti biyar a wajen a tsaye, sannan ya bargidanjikinsa a sanyayye.. Momy ta dube Intisaar dake ta famankuka tun da tashigo a karo na farko tayimatamgna "me ya faru?" ta girgixa kai tana gogehawaye, cikin kuka tace "momy wai ni kigya minranda xan ga abbana, na gaji da gorin daakemani," hawaye ya ciko idon mahaifiyar tata. Tayi kokarin gogewa da sauri tace "me kuma yafaru?" cikin kuka me tsuma xuciya intisaar ta koromataduk abinda ya faru, momy ta goge hawayenidonta tace "kiyi hkuri intisaar, watarana sai lbri, na sha gya maki" sannan ta mike tana cewa"saikiyi ma faruuq din bayanin komai, sannan tashiga dakinta." bayan faruwan hkn da wajenkwana uku faruuq bai ce mata komai ba,iyakadai ya kirata suyi hira sosai. Ranar watalarabayake ce mata yana so su hadu gobe da daddarea kofar gidansu, bata yi masa musu ba taceAllahya kai mu, amma gabanta na faduwa dan tasanbaya xuwa gidansu sai ranar juma'ah. Washegarin ranar alhamis ta gyawa Ummantayanda suka yi dashi, tace "shikenan, ammakarkiboye masa komai intisaar," tace "to momy." sannan ta wuce sashin inna ta taya ta hira. Koda wasa bata gayawa inna abinda su fadilasukayi mata ba, ta barshi a xuciyarta kawai. Da yammacin ranar wajen karfe bakwai damintigoma faruuq ya iso gidan nasu, ta nemiixini gunmomynta ta fita da cewar ba ddewa xatayiba. KarKar Abba ya sameta a waje. Yana xauna kanwani dakali, ta karaso wajensa, ya tare ta damurmushi, tun kan ta karaso wajen Kamshinturarensa mai ddi ya doki hancinta, takallesahade da sunkuyar da kai, ya mike yana matasannu da xuwa. A hankali ta gaishesa, ya Amsayana cewa "ya momy da inna?" tace sunalfya. Sannan ya xauna ya nuna mata gefensa, ta Dan yi jim, kmr mai naxari sannan ta xauna. ShiruShirubbu wanda yace komai, can dai ya katse shirunyace "i luv yhu my Intisaar," ta rufe fuskartakawaibata ce komai ba, ya kalli fingers dinta yace "ringdin waye wannan?" tace na xainab ne, yace Ok, ita ta baki? Uhm ko kana so ne? "yace aa da Dainaki ne" tayi murmushi kawai. 'intisaar' taji Yakirata a hankli, tace "na'am" a sanyaye. Lbrinrayuwarki nke so ki bni yau, kinga am vrybusybut na ajiye komai aside, dan naji tarihinintisaardita. Ta kirkiro murmushi kawai bata ce komai ba. Bismillah if u re ready, tace "uhm to ta Inaxan fara?" yace "ko ta ina ma Intisaar," nan da nan taji hawaye ya ciko idonta sannan tafara batare da bata lokaciba. Ni sunana Fateemah Umar faruuq, Ya xuba mata ido yana kallonta, can dai yasakarmata murmushi ya gyada mata kai alamartacigaba, ta cigaba ba tare da ta kallesa ba, ninataso ne a Zoo road nan kano da mahaifiyata,tana yi ma wata aiki lkcn ina da shekarahudu, momy tace min a nan gidan ta haifeni in datakeyin aiki, dan ta fara aiki da sati biyu ne tahaifeni. Inna ita ce warce ummata ke yi maaiki,da farko dai ni na taso a tunanin inna ce tahaifeni, amma ita da bakinta ta kan ceminnadaina damunta ga mamata can, a hankli dainagano wacece mahaifiyar tawa, inna mutumcemai kirki sosai, ko sau daya bata tabawalakantamu ba, ta dauki ummata kmr ita ta haifeta,nikuma ta daukeni jikarta. A kwana a tashi inna tasani a sch, lkcn har na isa primary 5,watarana asch aka ce mana kowa yaxo da babansaxa'ayimeetin, ni ban kawo komai a ka ba dannasanummata xata xo min, amma muna shiga ajisaiwata classmate dita maimuna tace min"intisaarke kina da Abba ma kuwa? Bamu sanbabanki ba,mu babanmu xai xo gobe. Tun da nake bantabakawo mahaifi a rai ba sai rannan, sai naji ba ddi ganin yanda kowa ke dokin babansa xai xo,nakagu mu tashi naje gida a gya min inda babanayake, dan ba'a taba min mgnarsa ba, ina isagida Kuwa da tambayar da na tari mamata knantanawanke wanke, naga tashin hnkli ya bayyana a fuskarta sosai, inna ta fito da sauri tanacewa,waye ya aiko ki? Nace gobe akace mu kawobabanmu a makaranta, inna ta ja ni tashigardanidakinta tace "ki kwantar da hankalinki yarlele ta,gobe uwarki xata je, nan na fashe mata dakukanace ni dai babana ne xai je ba mamata ba. Innata hassala tace "to dan ubanki xauna ki ji,babanki bamu san inda yake ba,mahaifiyarki natsince ta a titi ne ranar na dawo daga gidanaminiyata, tana da cikinki lkcn, a sume mukakaita asibiti mu da bayin Allahn dake wajen, bayan kwana biyu ta farfado, cikin bayinAllahnda muka kawota asibiti ni da wata baiwarAllahkadai muka rage, dan sauran duk sun tsere dawashegarin ranar. Ana sallamota na kawotagidana. Ita kuwa talatu, sunan matar knandamuke ta sintiri da ita a asibiti, a haife dai nahaifeta, na nuna mata xan kula da mahaifiyarkixainab, dan itama ta damu kwarai da gaske, tokinji dalilin ganin ki nan gidan da kikayi, inna tacigaba tana kallona, bayan satinta daya nagatawarware sosai, nake tambayrta ita wacece. Nanmomy tabawa inna tarihinta, tace daga Misrataxo nan Nigeria, mijinta ne ya barta wajenwatatara knan bata san in da yake ba, sbda Bakincikin hkn ne ya sanya ta kasa gano yandaakayita baro Egypt, kawai ta ganta a nan Nigeria, sannan tace ma inna tana da kishiya kuma ataresuke, to bayan sati daya inna tace ummatatahaifeni a nan gidan nata, danta tasa yayankamin rago aka sa min fateemah, Sauran bayanandai ne duk na manta. Da yake lkcn ba wani wayogareni sosai sosai ba ban wani nunadamuwanada yawa ba, washegarin ranar inna ta kiradantamuka je meetn din mkrantar tare. Inna tamanaabinda ko na jininmu baxai mana ba, innatatausayawa mahaifiyata sosai, duk da dailkcn dukwannan abun da take ba da san ran dannatabne, dan baya san yanda inna ta makalemanadaga ganinmu ba wai saninmu tayi bakuma tayrda damu, amma ta nuna masa bai isa yahanata abinda tayi niya ba. Lkcn ina da 3 yrs inna ta tilasta ma danta yyi mana visa mukajeegypt nemo mahaifina, har da ita. Da kyarummata ta iya gane gidan abban nawa,amma koda suka je, sai suka ga wai stepmum dita tasaida gidan, hka muka sake dawowaNigeria. hankalin momyna a tashe, inna ta dingakwantar mata da hankali tana cewa wataranaabbana xaixo gareta, wannan ba komai bne illa aikinasiri damuguwar abokiyar xaman tata tayi kawai. Tundaga lkcn inna ta dauki ummata kmr yar ta, Ta nemo wata yar aikin daban dan yanxu waimunxama yan gida.sai abinda baxa a rasa bakaidaimomy ke mata, inna da ta tashi sani amkrnatsai ta sani a mkrntar kudi, Abba na biya,ummata gani tayi kmr inna ta daurawa dan natanauyinmune, dan shima yana da nasa iyalin, dan lkcnmatansa biyu da ya'ya shidda, dan hkamomytace wa inna ta barta dan Allah ta nemiwanidan aikin da xata dinga yi, inna ta nunabacinranta sosai, tace momy kar ta sake matahka, bbu ruwanta da lamarinta da na danta dantsakaninsu ne, sau dayawa duk bayan satibiyusai jikokin inna sun xo gidanta, ba karamintsanata sukayi ba baya ga xainab dake sonasosai, kuma dama sa'a ta ce, na sha hantarawajensu da na iyayensu, basa sona damomyna,sun tsanemu, bn san ko dan muna cin arxikinsu bne, Abban nasu kuwa tun yana dauremana da,har ya sake mana sbda yanda yagamahaifiyarsake sanmu sosai. Ya maida ni kmr yarsa, komaiyyi ma yayansa sai yyi min nima. Tun asalidama yaya haisam yana ji dani sosai, ya daukeni kmrkanwarsa kuma yana girmama mahaifiyata. Inada shekara 12 lkcn ina jss2 inna ta hadaaurenmahaifiyata da danta, wato AbbansuHaisam. Ba karamin tashin hnkli momyna tashigaba dan babana bai sake ta ba ai, inna tadingamata jaraban wai ynxu kusan shekara 13 knan tana jiran wanda kila yanxu ya mace, kumama aia musulince ta halatta tayi aure tunda yadderabon da ta gansa ko sanin inda yake. Hkananinna tasa Alhaji Abubakar ya aure ummata, Shibai nuna abin ya damesa ba, dan dukabindamahaifiyarsa take so shi yke yi. A hka ni damomyna muka koma gidansu dake shagariqtres, wato wannan gidan na yanxu... Uhum tadanyishiru sannan taci gaba ganin yanda faruuqkekallonta a raunane, tun daga ranar har yauni daummata bamu samu farinciki ba gidan nan,saiwajen Abba da inna, sai kuma xainab dastepbrother dinta Haisam, sun tsane mu,basason mu, sun takura mana, kumahar yau basutaba shiri da ummata ba, ita kuma tundatakebasu taba mata abu ta tanka masu ba,shiyasahar gobe Abba ke alfahari da ita kuma yanaji daita, momyna tana da hkuri sosai, da kau dakaiakan abu. Ihsaan kadai momyna ta haifa anangidan, bayan nan bata sake haihuwa ba, Yanxu ihsaan shekaranta kusan 6 knan. Sbda irinyandasuka samu gaba ne ya sanya inna ta sa abba Yagyara mata sashinta na nan gidan ta dawo,dandama can yayi-yayi da ita ta dawo nan daxamadan ya kula da ita da kyau amma taki dan bagirmamata matan nasa ke yi ba. Hkn yakarawamomyna tsana a wajensu hajiya, dan innatafififfitata a kansu, kuma tafi son ni da ihsaanakanya'yansu, a makaranta daya muka gama secsch da xainab, fadila da kursum, khadija darahmakuwa suna ss2 ne ynxu hka. Hajiya Aisha itace matar Alhaji ta farko, ya'yanta uku, yayaAliyu,xainab da khadija, ita kuma umma shafaya'yanta hudu, yaya haisam, fadila,kursum da rahma,saijikanta yusuf dan fadila ta taba aure ammasunrabu da mijin. Faruuq yyi ajiyar xuciya yace "toshi yaya Aliyun yana ina?" ta dan xaro ido tace "nima ban sani ba wllh," amma baya gidanynxuhka, ok xainab ce kanwartasa knan, eh...tacekanta a sunkuye, to meye na kuka intisaar, Wllhnaji na kara sonki ne ma, ya ciro handkercief yagoge mata fuskarta. "i luv you my intisaar," tagyada kai kawai ta kasa cewa komai, ki baniixinina turo gidanku plss, ta danyi jim, sannantace tosai nayi shawara da innata, yace o.k gobemaxan xo ai wajen innar, da kyar ya bartatashigaciki dan duk ya birkice mata ta amince masakarta ya dashi, shi din mai sonta ne da gskya,harbakin gate ya rakota ta shiga sannan yawuce, Taji ranta yyi fari sosai, taji ta kara sonfaruuq……. Washegarin ranar da magrib faruuq ya bargidansu, sun dde suna hira da inna dagabisannitace idan tayi shawara da danta xatagayamasalkcn da xai turo, har gate ta rakosa, yaya haisamya shigo suka gaisa da faruuq, ya danxolayeta Sannan ya wuce, faruuq ya dubeta yace "yanaaiki ne haisam,?" tayi dariya tace kaibarrister nehka pa da ka gansa, a Abuja yake aiki kila hu2yaxo nake ga, yace " to shi da Aliyun wayebabba?" ta danyi jim sannan tace "ya Aliyunemana" o.k shi kuma Aliyun wani aikin yakeyi? Ko bai fara ba? Tace "wllh nima bn sani ba,"ya dubeta da tuhuma yace "baku interact dashine?" tayi murmushi tace aa ni bamu san junasosaiba, o.k... Duk xamanki gidan nan baya nan ne? Tadan xaro ido tace "a'a yana nan mana," Faruuqyyi murmushi yace "ko bae sake maki bne?" Tadanyi shiru sannan tace uhm, dan ita batamasan ana tuna mata ya Aliyu ko kadan, duk takagu ya rabu da ita da xancen Aliyu, shi kammurmushi yyi yace "to shknan intisaar, nixan tafi,ya ciro kudi mai yawa ya bata," tace hava na Mene yaya, yace yau juma'ah shi yasa, tace a'a nagode,ka barshi kawai, ya bata rai yace "tundamukedake na taba baki abu intisaar? Wllh nasanabinda nakeyi, ki karba nace, da kyar takarbatayi masa gdya sosai, sannan tayi sashinsudasaurinta. Xaune take a kasan parlon Abbayanaduba jarida, can dai ya dubeta yace "me ya Faruintisaar ya akayi ne?" a hankli ta faramaganamuryarta na rawa, Abba dan Allah danannabikayi hkuri ka bar su Hajiya da umma sudawo,Abba ya katse ta da sauri yace "to ai ni bnida tacewa a nan, sai abinda kakarku tace, dan itakeda iko dani, kinga kuwa bni da laifi a nan." Tayishiru, sannan ta mike tace "to Abba shknan"ta Fice ta bar palon. Yyi murmushi dan yasanuwarta ce ta turo ta, dan ya nuna mata kartasake masa mgnarsu Aisha kwanaki uku da Sukawuce tana basa hkuri. Intisaar na fita sashininnata nufa, ko da tayi mata mgna ma bata rai Tayisosai, tace "maxa fice ki bni waje ka finraina yabaci, idan ma uwarki ce ta turo ki kije kicematanace tashiga hankalinta, idan ba naci ba mamutanen da ba sonta suke ba ta wani damukanta a kansu" intisaar ta fice mata dagapalonnata a fusace dan ita bata san me inna take Nufiba, to don me baxa su ci darajar ya'yansuba maa barsu su dawo gidan. Ita kam tausayinxainabdasu kursum take yi sosai, shi kam haisam ko ajikinsa dan ko xancen ma baya so. Tana tafetana waya da faruuq, ynxu kam shakuwarsuyawuce misali, dan inna kadai yake jira tayi maabba magana dan shi a shirye yake, kuma yace xai dauke mata nauyin kara2n ta gaba daya,dariya tayi sosai tace "kai ya faruuq wajeninnapa xani ba wani gun ba, yace "ohk ai nayi xaton fita xakiyi ne shiyasa nace hkan," a hka takarasosashin inna tana ce masa "yayana ko sllh mapabn yi ba" yace "hva de kanwata gashi harwajenkarfe takwas, to kiyi alwala a bakin tap, nanwajen kafin ki shiga mana," tace "dama hknxanyi yayana, bn gama abinda nkeyi bnedaxunshiyasa lkcn sllhn ya wuceni" ko da ta isabakintap din ma sai ta tarar ana alwala, tace "kgayaya haisam ma na alwala a wajen," yahaisam,yayana yana gaisheka wai, hka nan suka ci gabada hira da faruuq tana jiran haisam itamatayialwalan sai ta shiga ciki, "hmm to shknankanwata yi alwalarki anjima mayi magana,"faruuq ya fadi yana kkrin kashe wayan, tacea’a ai ya haisam bai gama ba, dariya faruuq yyiyace "baki gajiya da jin muryata ko bbynah?" kunya yakamata tace "lalle ma yayana to bye" oh srry myintisaar wasa nke maki, a dai-dai lkcn maialwalan ya dago, sukayi ido hudu da yaAliyu,wani irin muguwar faduwar gaba yaxomata,bakinta ya fara karkarwa ta ma rasa nemomgnar da xatayi masa, kallo daya yyi matayadauke kai ya shige parlon inna. Faruuq kamyakira sunanta yafi sau biyar, duk da wayanna karea kunnanta amma ta kasa cewa komai, haryagaji dan kansa ya kashe. Kasa koda motsitayidaga gun da take, ta dai dake a hnkli ta juyaxata koma sashinsu taji inna ta kwado mata kira, da sauri ta dawo amma ta kasa amsawa, tajiinna nacewa "Aliyu ba muryar intisaar nake jidaxu a waje ba?" shi dai baice mata komaiba illadardumar da ya dauko ya shimfida, a'a baxakamasallaci bne, yace eh... Ya tada sallansakawai. Sai da inna ta leko tayi ma intisaar mgnasannantayi alwala tashigo palon, gabanta namugun Faduwa. Sai yanxu kika ga daman xuwan knan, intisaar ta dube innar tace "aiki nke yi ne" tokeda faruqu kke waya ko wa? Tayi shiru batace Komai ba sai hararan innar da takeyi, innatatabe baki taci gaba da dama furar da takeyi, Aliyu ya idar ya mike, inna ta dubi intisaartace "ba ki ga yayan naki bne ba ke," ta dubesa dasauri tace "ina yini yaya," lfya kadai yace ba Tareda ya kula ba ya nemi guri ya xauna, inna ta Nunamata dardumar da ya mike daga kai tace "kijekiyi sllh ga shimfida can, ta mike take ta tadasallah tana dan satan kallon Aliyun. Har taidar. inna bata daina mitan da takewa Aliyu ba narashin son xuwa gida ba, don ynxu ma badanubanshi ya kirasa ba, ba xuwa xai yi ba, shi kamhankalinsa na wajen news din da yke kallogabadaya, hka tayi ta surutu intisaar na kallonsukmrtayi dariya, inna tace "iyye!! Gamahaukaciya namagana ko? Shi kam bai ma san tana yi ba, innatace "ba mgna nke mka ba Aliyu," ganin baisantana yi ba yasa ta daka masa tsawa ya dawodaga kallon a dan firgice, "wai meye ne hkainnarahma?" ya tambayeta a fusace, ta mike takashe TVn, kan ta juyo shima har ya mikexai fita, ta juya tana dubansa tace "ynxu Aliyu ni ka maida mahaukaciya," to hva inna news pankekallo kke takurani hka, ta tura kofarta ta rufe,tana cewa "sai ka tambayi haisam yandaakayi anews din" yyi murmushi ya xauna yace toinajinki tsohuwa, ta koma ta xauna ta dinga masabnasiha ya daina abubuwan da yake yi, yagirgixa kai yace "to menake yi inna?" kusan kullumsaiBukar ya kawo min kwamplan a kanka,dariya yyisosai yace "to ayi hkuri Hajiya" ta hade raitaceka tsaya ka saurareni ni dai," nan tacigabadabatunta, shi kam wayarsa ya fito da ya na tadanne danne. Ganin wannan nasihar ba maikarewa bane yasa intisaar ta mike tace"inna niguga xanyi, xan tafi," ehh dama tsifa xakiyi minkuma xainab da kursum sun min daxu,gobe dasafe dai ki xo, tace "to inna, amma baki bnifurarba," inna ta dubi furar dake gaban Aliyun tace"ga na Aliyu bai sha ba ki dauka kije dashi"intisaar ta dago kai ta dubi Aliyun ta gakallonta yake yi, suna hada ido yyi murmushin da takasa gne ko na mene, amma dai tasan bna arxikibne , ya kalli inna a fusace yace "to sai nace makibaxan sha bane" inna ta tabe baki tace "je ki kidauko kofi ki diba," kai dai ban san waniirinmutum bne, har yau baxaka canxa halinkaba ko, wae ma dan meyasa baxakayi koyi daHaisam bane, nan kuma ta fara sabon fadan, intisaardai tadeba wanda xata deba tace "to inna sai da safeni na wuce" Allah ya kaimu. Inna ta fadi batareda ta kalleta ba. Ta dan saci kallon Aliyun dayamike tsaye yana duban inna kawae kmr yamareta, intisaar ta bude kofar ta fice, ya juyashima ya fice, inna tana baxaka sha furarbnekuma, bai ce komai ba ya fice abinsa. Intisaar natafe tana waige-waige, can ta hangosa daganisashima ya fito ta xuba a guje, taji taci karo damutum, ta daga kai a tsorace sukayi idohudu daHaisam, yana kallonta yace lfya? Tana mai danumfashi tace tsoro nke ji ne, Aliyu yakaraso, haisam ya dubesa ya dubeta, yace "ina yinibro,"ya amsa hanklinsa baya wajen, sannan ya dubiintisaar yace "wllh wllh ki ka sake ganinakkakwasa a guje kmr kinga uwarki to sai naciubanki,na maki dukan fitar hankali, kanta a kasa tace "nisauri nke yi ne shiyasa nke gudu," bai bi takantaba yyi gaba abinsa yana cewa "ko ma uban mekke yi ni dai na gya maki" haisam ya dubetayace "ki daina gudu idan kin gansa, shima aiyasan koyyi hauka ne baxai taba ki ba," bata cekomai batayi ma Haisam sai da safe sannan tayihanyar sashinsu. Tana isa ta tarda rahmatu daxainab aparlonsu, ba abin mamaki bne don tagarahmatua sashinsu don duk fitsararta ita da kursumsunashigowa khadija da fadila dai ne basashigowa, wajen karfe tara da rabi ta rakasu sashinsu, xainab na mata dariya tace " kinga babankidaxua wajen inna," tayi murmushi kawai dansbdayanda take mugun tsoran Aliyu suke cemasababanta, don ko momy da Abba batabtsoransubhka, ita kam duk duniya bbu wanda taketsorokmr Aliyu, baxata taba iya mantawa da Aliyuba arayuwarta.. Inteesar Tana xaune a balcony tana ferewa momydankali, momy na wanke-wanke a bakintap, tadubi momyn tata tace "momy yaushe yaAliyu yadawo?" momy ta juya ta watsa mata harara Tace "ya xa'ayi na sani ni kuwa, kinga yaxo Gaishenihar ynxu, bare nasan ya dawo ko kumayausheya dawo?" intisaar bata sake cewa komai ba Tacigaba da abinda take yi. Xainab ce ta karasodasauri, tayi ma momy sannu da aiki sannan tadubi intisaar tace "inna tace na kiraki" takammala abinda take yi da sauri, sannan tanemiixini wajen momynta, tace "to amma kiyimaxa kidawo xaki min abu ne" to! kadai tace sukawuce. A hanya take tambayar xainab me xata yiwainnar, xainab tace "aikenmu xatayi wai" abakinkofar inna suka tarda ya Aliyu tsaye, yana taxuba, xainab tace "kai yaya har ynxu bakaragewannan surutun naka ba sai ma....." da sauriyajuya yana kokarin cafkota yaga tare suke daintisaar, nan da nan ya hade rai, ya lekaparloninna yace "inna ni na tafi," tace aa har mungama hirar mai gidana,? Bai ce komai ba yabarwajen, xainab tace kai! Yaya kaga yandakayiwani irin fresh kayi kyau? Tab! Inna ce tafito dasaurinta tana cewa "Aliyu xo dan Allah." har Yyinisa ya juyo tare da cewa ya akayi? Xo danAllahnace. Yace "aa ni baxan iya dawo wa ba."sannan yyi gaba abinsa, inna tayi tsaki tacegantalalle kawae, dama hanya nke son yaragemaku wllh, intisaar tace "aa bama so inna, Da mayaya Haisam ne." dole ta basu kudin motardaaiken da xasu kai wa kawarta hajiya maimuna. Sun isa gidan suka bata sakon, tayi ta samasualbarka sannan ta basu dari biyar su haumota, Jikarta murja ta rakosu har inda xasu haumota,sannan ta koma. Xainab ta dubi intisaar tace "kk muyi save din kudin mu, mu taka kawaitunda bawani nisa, da kyar ta lallaba intisaar sukafaratrekkin don da kin yrda tayi. A dai-dai wanikatonpharmacy faruuq ya fito rike da leda ahannunsa,xainab ce ta fara hangosa, tace "lah..Intisaarkinga faruuq," da sauri intisaar ta juya suka Hadaido, ya sakar mata murmushi ya karaso dasauriyace "daga ina hka?" suka gaya masa dagaindasuke, bayan sun gaisa ya bukaci da ya rage Masuhanya, bbu musu suka shiga, yyi drop dinsuakofar gidansu, suka fito suka yi masa gdya sannan ya kashe wa intisaar ido, ya ja motaryawuce hade da cewa sai munyi waya, kugaidamin da inna." Aliyu suka ci karo da a gateyanatsaya, cak suka tsaya ganinsa a wajen,xainabtayi karfin halin cewa "yaya me kke yi anan?" yaxura wayarsa cikin aljihu sannan ya ddubet dakyau yace "motar uban waye kika shiga?" tahade rai tace "saurayin intisaar," ya bude bakiyana kallonta, ganin yanda tayi mgnar kotsorobbu,kika ce me? Ya sake tambayarta, tamaimaita ranta a hade, mari ya watsa matamairai da lfya, tuni intisaar ta fara karkarwa,xainabkuwa ta fashe da kuka, ya fixgota , ta turasadakarfinta, ta xuba a guje sai bangaren suintisaar,bin ta yyi da saurinsa, intisaar kuwa naganin hkatayi wajen inna da gudu gabanta nafaduwa. Parlonsu intisaar xainab ta afka, ya bita harcikiyana cewa "dan ubanki yaushe na farawasadake xainab," tayi bayan momy da gudu Tanahakitare da goge hawayen fuskrta tana kumahararansa, momy ta dubeta tace "me ya faruxainab," ta fashe da kuka tana cewa " marina yyimomy banyi masa komai ba, kuma Allah yaisaban yafe masa ba," dan uwarki xo ki fita, yadakamata tsawa a fusace, xainab ta wasa mashiharara tace "anki din, kuma ka sake mamutanekofar su ka bar wajen, tunda a gidanku ba akoyamka kayi respect ba, bare har kayi gaisuwa." Tuniidonsa yyi jajir yana kallonta kamr wanixaki. Momy ta dubi xainab tace "shiga daki xainab," tashige da sauri, ita kuma taci gaba da abindatakeyi," da kyar ya iya sake kofar parlon yaja dabaya kmr ya hadiyi xuciya, tsaye yaga sukhadija,kursum, da rahmatu suna kallon abinda yafaru, wani irin wawan kallo yyi masu da yasasukakwasa a guje suna dariya. Kmr ance ya juya tagefensa ya ga intisaar a tsaye, duk a birkicetake, yana juyowa sukayi ido hudu, ta budo kofaratsorace xata shige parlonsu ya cafkota, kuka tasaka tana cewa "nashiga uku yaya, wllh kayihkuri bni bace ba..... Bai ko kulata ba ya cire takalmin dake kafarsa ya dinga xuba matadakarfinsa kmr an aikosa, kuka takeyi tana kiranmomynta, yace "don uwarki an gya maki inada lkcnki ne bare na lamarinki,to ba a mota ba,ko ajirgi ne akayi park dinki a kofar gidan nanbburuwana, na dai ce maki ni ba dodonki bne,idankka sake ganina kika gudu sai na babbalaki jakarbnxa kawai mahaukaciya, ya turata cike datsanayana huci, haisam ne ya iso wajen da sauri yanacewa "hava Aliyu, me tayi mka hka xakabiyotahar kofar daki kana dukanta, Aliyun yahararesayace to sai ka rama mata .. Haisam ya tambayesu me kuka yi masa,xainab ta fito tana goge hawayenta tace"inna ceta aikemu, shine don yaga Faruuq ya ajiyemusai yake xagina har da duka," ta dubi Intisaartace "kema meyasa bakiyi wajen inna bakika xonan," ta goge hawayen idonta tace bata nanne, adai-dai lkcn inna ta bullo, ta karaso dasaurintatana dubansu tace "me ya faru, hatsarikukayi,ne? Nan da nan ta rude masu, haisam yyidariya,xainab kuwa ta kwashe duk abinda ya faru Tasanar da inna, nan inna ta dinga bala'i tanamasifa tayi dakin Aliyun tana cewa Allah ya isar masu. Haisam ya dubi don intisaar ta rigatashiga ciki yace "momy bata nan ne?" Xainabtace tana ciki, ya girgixa kai yace ammaAliyubashi da kunya ko kadan. Ya shiga sukagaisa da momy, sannan ya basu hkuriya bar sashinnasu. Suna xaune su uku suna hadawa yaya Haisamkayansa don anjima xai komai Abuja, xainabtalinke wa, intisaar na gyarasu cikin jaka,rahma dakursum na kwance da yake a dakinsa suke,sunakallo Xainab ta dubi intisaar tace "jiya faruuqsaewajen karfe goma ya bar wajen inna," intisaar tace "hva" ba tare da ta kula ba,xainab taceehmana, ai can na kwana, kursum ta dubixainabdin tace kai xainab tara da rabi fa naga yabargidan nan. Xainab ta dubeta a fusace tace"jakabki ji abinda nace bne?" ca nayi har wajenkarfegoma, bnce karfe goma ba, ita dai intisaarhankalinta na wajen abinda takeyi bata cemasukomai ba. Ya haisam ya shigo yace idan sungama su rufe masa dakin, xai je wajenummarsayyi mata sallama, kursum tace "ayya yayaxanbika don Allah, abba baya bari muje wllh" yadubeta yace to xo muje, nan rahma ma tacexatabisa, yace duk su xo su tafi, ya tambayi xainabko tana da sako dan xai je wajen hajiyarsuma,tace aa kawai dae ya gaisheta. Nan yakwashekanninnasa sukayi gidanmahaifiyarsu donyasansunyi kewarta sosai barin Rahma autar ta. Bayansun tafi ne intisaar take tambayr xainab inakhadija, tace mata sun fita tare da ya Aliyu,batasake cewa komai ba don tasan yana ji dakanwarnan tasa khadija duk cikin kanninsa saekumarahma da kursum. Jiya maganar aurenkufaruuqyyi da inna pa.. Intisaar dai bata ce matakomaiba ita kuma taci gaba da maganarta " tace Yabata sati biyu don akwae wani shawara dasukeyida Abba ne," intisaar tace "uhmm" ta cigaba dabinda takeyi kawae. Basu bar dakin ba saiwajen karfe biyar na yamma, sannan sukakullomasa kofar sukayi sashin inna, hirar daxainabtayi mata, shi innar ma tayi mata, ta kara dacewa "ynxu dai nace masa ya dawo bayansatibiyu kafin lkcn mun gama shawarar dababanku" ita kam intisaar binta tayi da uhm kawai. Suna cin abinci da daddare khadija ta shigo, innatacesae ynxu? Tace eh, ta nemi kujera takwanta, inna tace " to ina Aliyun?" tace oho! Kamr yaknan oho? To ni da kafa na dawo don ban Sakeganinsa ba, xainab ta fashe da dariya tace "Allahya kara," intisaar dai jinsu kawae take yi, tamiketace inna ni sae da safe don barci nke ji. Tana tafe a hnkli cikin sassarfa kmr mara gskyatajikamshin turaren Aliyu, gabanta yyi mugunfaduwa, tasan duk yanda akayi yana nan wajajen,nan da nan ta fara neman wajen da xatabuya,har wani rawa jikinta yke yi sbda tsoro, jikinwataflower dake wajajen ta labe xuciyarta nabugawa, yana ko karaso wa dae-dae wajen sai yatsaya kmr mai tunani, ganin hka ya sa ta fasa ihudona tunaninta ya ganta ne, ba karamin firgitayyi bada karar da tayi, ya koma baya da sauri yanasallati, da sauri ta fito daga flowern ta nakokaringudu, yyi hanxarin cafkota, ta kara fasa masawani ihun, muryar Abba sukaji, yana cewa"fateemah me yafaru?" ba shiri ya cikata tare dadurkushewa yana kallon kafarta yace "subhanallaimae kika taka?" Abba yakaraso da sauri wajen,me kka taka fateema, me ya faru, ta ma rasa mexata ce, amma har ynxu jikinta bari yake,Aliyun yyi maxa yace "ina jin abu ta taka naxowucewane naji tana ihu," tambayar Abba ya sake jefomata muryarta na karkarwa tace "Abbanima bnsan meye ba" Abba ya ciro da torch yana haskakafar, Aliyu ya karba yana duba mata kafaryace"sannu, amma ai ba komai a kafar, yana makiciwo ne," tace aa da sauri, Abba yace "toAllahya kiyaye dai, me ya hanaki kwana wajeninna,? Tace bakomai, yace "to Aliyu dan rakatacikingida," yace to Abba, tashiga gaba yana biyedaita a baya, Abba kuma yyi nasa parlon. Tana gaba yana biye da ita a baya, yanadan waige-waige yana duban kofan palonabbannasa, har dai yaga ya kashe wutan parlonalamarxai shiga bedroom dinsa knan, ya ji ddinhknsosai, ya juya da hanxari xai shige gabantaamma yaga wajen wayam bbu kowa, itakam abba na shigewa palonsa tayi ta kanta dantasan sauran bayanin, cikin rashin sa'a ta tarda momy ta kulle kofa, a rude ta shiga jijjiga kofartana kwalawa momyn nata kira, momyn tatamaa tsorace ta iso xata bude kofar tana cewa"lfya, menene,?" amma tuni ya karaso wajen, taxabgaihu tana "wayyo momy ki....." bugun da yakaiwabakinta ne ya hanata karasawa, a dai-dainan Momy ta bude kofar, hkn kuma bai hanasariketakmr wata 'yar shi yana duka ba, momy tajuya takoma ciki ba tare da tace komai ba, "donAllahyaya kayi hkuri wani abu ne ke bina shi yasanayi ihu," dukanta ya dinga yi ba sassaucihar daidaga karshe yyi wani irin juyi da ita yawurgar,sannan ya bar wajen yana huci kmr xaki,kuka tadinga yi tana kiran ummanta, can dae ganinmomy ba fitowa xatayi ba yasa ta mike da kyarta shiga palon nasu. Ita dai har tayi barcimomybata ce mata komai ba, sai ma ca mata datayixata kara mata idan bata rufe mata baki ba, doletasa ta hadiye kukan nata har bacci yyi gabadaita. Da safe ita da kanwarta suka gamabreakfst,ta kwashi kwanukan xata je ta wankemomy tagatana dingishi, "xo nan intisaar", ta dawotanakallon momyn tace na'am, me ya samikafarki, "yaya Aliyu ne ya buge min kafar" to yyikyau, Jeki. Haushi ya cikata sosai amma bata cekomaiba ta gama wanke-wanken ta ja kanwarta Sukayisashin Abba su gaidashi. Inna na palon nasa A xaune rahma na kusa da ita a xaune, a taresukashiga parlon da xainab da ita ma taxo gaida Abba, abba ya dubi intisaar da ta nemi guritaxauna yace "ya naga kina dingishi,?" innatace"me ya samu kafar," tace "bugewa nayi"garinyaya? Inna ta tambaya tana kallonta, abbayace"ko dae jiya kin ji ciwo ne?" eh kadai tacesannanta fara gaida abba, ya amsa, xainab ma tagaidashi, ya dubi intisaar yace "to bari Aliyu Yaxo ya duba maki kafan ko?" bata ce komaiba, sai TV da ta kurawa ido. Anjima xaku jegidannafisa ku taya ta gyare-gyare ta dawo jiyadadaddare, Nafisa kanwarsa ce, kuma autawajeninna, shekaransu goma knan aiki ya kai mijintagermany, xainab taji ddisosai, intisaarkuwa batawani santa sosai ba, xainab tace "to abba wa xaikai mu ne, bamu san gidan ba ai, abba yace "ehAliyu xai kai ku dama ai," a dai-dai lkcn Aliyuyashigo palon da sallamarsa , yana sanye da Fararshirt da bakar wando, kamshin turarensa yagauraye ko ina, ya nemi gefe ya tsugunna yagaida inna, ta amsa tana cewa sai ina? Baikulata ba ya gaida abbansa ya amsa yana Cewaka tashi lfya? Bai ce komai ba ya maidawayarsaaljihu ya xauna. Xainab ta dubesa tace "inakwana yaya?" yace "lfya lau" intisaar ma tagaishesa ya amsa da lfya! Abba yace "yauwaxaka kaisu jan bulo gidan Nafisa ina fatan Kasanta dawo, ya hade rai bai ce komai ba, xainabtace"ki tashi muje mu shirya intisaar," abba yace "kugyawa fadila ma, har da ita xaku." suka ce to, sannan suka mike xasu bar palon. YauwaAliyuka dubawa fatimah kafarta dingishi take yiwaijiya bugewa tayi, ya dago da sauri yana Kallonkafartata, ita kam da sauri tace "lah Abba wllh bawani ciwo yke min ba ya ma daina." inna tacemunafuka a hkn ya daina maki ciwon? Batatanka mata ba ta fice da sauri xainab ta bibayanta. Fadila xainab taje ta sanarwaabindaAbba yace, ta kama hanya abinta ta wuce. Dakyar xainab ta lallaba intisaar ta shirya donkukata dinga mata wai bbu inda xata Aliyu kashe Taxai yi a hanya, tun xainab na dariya har ta daina,tace "wllh bai isa yyi maki komai ba.. Ba don ta yarda da maganar Xainab ba tagama shirinta, don tasan kila ma ya damketaxainab din ba tsayawa xatayi ba. Su ka yiwamomy sallama, ta hada su da ihsaan suje, a Canbangaren inna suka sami Aliyun, inna tace"maxaka kai su Aliyu, bai ce komai ba ya mike yaficesuna biye dashi a baya, intisaar duk a Tsoracetake, kofar gida suka yi gaba daya, xainab dai saikallon ikon Allah takeyi, suna fita ya cirodububiyu ya mikawa xainab yace "gashi ku haubike,ni ina da waje mai important da xa ni," bani wayarki na sa maki nmbr Nafisan idan kinjecanki kirata..... Ta mika masa yasa mata nmbrsannan ya mika mata wayanta, yyi wajen motarsa dake parke a gurin, ya bude knan ihsaan tace "uncle amma kai dady yace ka kai mu,"yajuya yana kallonta sannan yace "xo nan," intisaarta ruko ta da sauri dan xuwa xatayi, waniirinkallo yyi mata ba shiri ta sake kanwartata, tatafi kuwa da saurinta, "me kika ce?" ta sakemaimaitawa tana kallonsa, rankwashi ya kaimata a ka har sau uku, ta fashe da kuka, yace"na taba wasa dake ne?" nan da nanhawaye yaciko idon intisaar, xainab ma ta hade raiammabata ce komai ba.... Daga ta yyi sama ya sako gaban motar sannan ya kulle motar ya ja tasukayi gaba, intisaar ta xaro ido tace "ya tafi daitaxainab," xainab tace "mu tafi kawae ae xai dawoda ita," ba don ran intisaar ya so ba xainabta jata suka yi busstop, don duk hankalinta na wajenkanwarta, kuma taso taje ta sanar da momyamma xainab ta hanata, wae ai ba gudu xai yi daita ba. Anty nafisa tayi farin cikin ganinsusosai barin yanda taga sun xa ma yan mata gabadaya. 'ya'yanta biyar suma duk sun girma, Antynafisa tana da kirki sosai, aiki suka je taya taamma bata bari sunyi komai ba sai hirar dasukadinga yi, basu bar gidan ba sai wajen karfetakwas mijinta ya mai dasu gida, ta cika sudatsaraba sosai, sannan tace ita ma xata xogobe. Amma abinda ya daure masu kai bai wucerashinganin fadila a gidan ba amma basu cekomai basuka ja bakinsu sukayi shiru. Ko da suka Koma gida Aliyu bai dawo ba, hnklinta ya tashisosai, ta gyawa momynta da ihsaan ya fita tun dasafe,momy bata ce komai ba tana ta harkargabanta, ganin hka ne yasa tayi sashin inna ta gyamataita da xainab, inna tace "duk inda suka jexasudawo, meye abun damuwa, ba kanwarsa bace," ita dae hnklinta bai kwanta ba. Xainab tabajewainna tsarabar da nafisa ta basu, tana ta saalbarka. Karfe tara da minti hudu Aliyu ya shigopalon, yana rungume da ita tayi bacci... Inakukaje hka Aliyu, yace "in da kka aikeni," batasakecewa komai ba, ya kwantar da ita sannanyace"sae da safe" ya fice. Da sauri intisaar ta Miketaje kusa da ita da durkusa tana tada ta, Innatace "ya haka tana barci xaki tashe ta, je kishinfide ta a daki" ta dauketa tashiga daki Takwantar, sannan ta fara duddubata don ita Batayarda da Aliyu ba kilama cutar ta yaje yayi, sai Da inna ta kirata sannan ta dawo parlon, inna Tace"Aliyun ya shiga ya gaida nafisa,?" duka suka yiwuri-wuri suna kallon inna, intisaar ta maxa taceeh," to meyasa fadila baku dawo tare ba? Tun takwas ta dawo ita, xainab tace "ohonmata," nandae inna ta dinga yi masu surutu, harintisaar ta mike tace "inna ni dae sai da safe bacci na keji," kamar warce ta tuna abu kuma tayi saurincewa "au na manta a nan xan kwana, sannan tashigedakin inna," sae da tayi wanka tayi shirin Baccifaruuq ya kirata, sun jima sosai suna waya daga bisani sukayi sallama ta kwanta. . .... Yau wajen watan su Hajiya uku basagidan, bbu yanda momyn intisaar bata yi daAlhaji ba amma yaki hucewa, inna kuwaidan kana son ganin bacin ranta kayi matamaganansu, ko kayi nuni da cewar tayihkuri tabar Abba ya dawo dasu, nan da nan xaku Batada ita. Yau Aliyu ya cika sati hudu da dawo wa,har ya gaji da yi ma Abbansu magiyan yabaruwarsa ta dawo gidan, Anty nafisa ma taxo tayima inna magana da ta fuskanci abinda akeciki,amma tace lallai sai sunyi shekara daya agidaniyayensu, abun yana damun Aliyu sosai,xainab ma harta fara damuwa, ita kuwa fadila daman satan hanya take yi taje wajen mahaifiyar ta suyi ta sake sake da kwance kwance. Yaukam abin ya ishe Aliyu yaje suyi tata kare da inna,tana xaune gaban akwatin talabijin waetanakallo, intisaar tana daki lkcn tana kwance, Aliyuya nemi gefe ya xauna yace "inna wajen kinaxo," tace "to sannu da xuwa" ya danyi tsaki yace “nifa inna na gaji da rashin uwata a wannangidan, ke waye ya raba ki da danki da harxakirabamu da uwarmu sbda wani dalilinbanxa, toni de na gaji wllh, idan xaki kira danki kiyimasamagana ya maido min da hajiya ta gidannan to,idan kuma ba hka ba wllh na bar gidan nansaekun sake ganina, ta juya tana kallonsa tace"kwantar da hankalinka, uwartaka tacidarajarintisaar xan sa a maido ta, amma ba donhka bawllh sai na nuna masu ni na haife Abubakar, yace "darajar wa?" inna tace "intisaar," dondaxun nantaxo ta sani gaba tana kuka, kuma don hkaxansa a maido Aisha da shafa, wani irin bakin Cikida takaici ya mamayesa, ita intisaar dinwaceceda har xa aci darajar ta, lalle inna, ya dubetayace " intisaar din banxa, ai sae daimahaifiyatataci darajarmu ba ta wata intisaar ba,wayanintisaar dake palon ya fara kara, inna takwalomata kira taxo ta dauki wayarta kuma wayeyakirata," ba karamin tashin hnkli Aliyu yashiga bada ya gano intisaar na dakin, a sanyaye tafito tadauki wayartata ta koma ciki, ya mike a fusace yana duban inna, "wllh idan kika sake Takuramauwata a gidan nan hajiya Rahmatu sai na...... Kamin duka ko? Inna ta karasa masa, danbnxanyaro fitsararre, mai halin bnxa kawae, yajuyayana dubanta yace ni? Tace a'a uwarkaAisha, yyihuci yace shknan mu xuba dake, ya juya yaficea fusace, a gaban wannan jakar inna kexaginsa,tab lallae, inna ta fashe da dariya tana "donubanka ya ka wuce, ka tsaya mana muga ni Dakai waye tatattce, bai tanka mata ba yyigaba, Yaron bnxa kawae, kai Allah dae ya shimaHaisam Albarka yaro mai kirki, mai hankalidabiyayya, intisaar ta fito tace "hva inna donAllah ki dena biye yaya Aliyu, inna tace "mantadashi dai dai nke dashi dan uwarsa, kuma bariuban nasa ya dawo, kece shaidata kinga daiyanda yaxaxxageni, intisaar ta xaro ido a tsoracetace "A'a wallahi ni ba shai'dar ki... Tana kwance a palon momyn ta suna kallon tashar Kidscov ita da ihsaan, momy kuma tana bedroom kursum tashigo, "intisaar ana kiranki," ta dubeta da sauri tace "wa?" Kursum tace "inna" ta mike da sauri kmr dama jira take tace "momy inna tana kirana," momy tace "sai kin dawo" kursum tace "ina kwana," lfya lau, momy ta amsa daga ciki sannan suka fice, a hanya intisaar ke tambayarta ko aiki inna xata sa ta, kursum tace "oho tana dai palon abba," su ka shiga da sallamarsu palon, inna na xaune kan carpet xainab na kusa da ita, Abba na xaune yana kallon Aliyu dake durkushe a gefensa kamar me neman gafara, fuskar nan tasa a hade, nan da nan taji gabanta ya fadi, ta daure ta nemi gefen xainab ta xauna, ta gaidasu.... "ehe , ki gayawa babanku abinda Aliyu yyi min jiya, don ya karyatani ynxu," inna ta fadi tana kallon intisaar ranta a hade. Abba yace "intisaar ki gaya min me ya faru jiya, me Aliyu yyi ma Inna? Intisaar tuni ta firfito da idanuwa a tsorace tace "ni?" inna tace "kwarai kuwa ke kadai ce shai'data a nan don ya karyatani," Ni Hajiya ki daina cewa na karya taki don.... Abba ne ya katse shi da tsawa "wllh ka sake bude bakin ka a nan Ali xan watsa maka mari," Abba ya dubi intisaar yace "ina jin ki fateema," ita kam tuni ta fara rawan dari, ta juya ta sace kallon Aliyun, ta ga kallonta yake yi, idon nan nasa yyi jajur. Ta girgixa kai muryarta na rawa tace "wllh Abba ni ban san komai......" inna ta daka mata tsawa tace "to ke din ma karyatani xaki yi, bayan nace kina wajen kuma kece shai'data,?" aa inna, ta fadi tana kokarin maida kwallar da ta taru a idonta, xan fadi gaskiya. Ta juya ta kara sacen kallon Aliyu, har yanxu kallonta yake yi, ta ma rasa wani irin kallo yake mata, can dai tace "Abba dama yaxo ya same inna ne akan maganar dawowarsu Hajiya, shine sae inna ta fara masa masifa......" fashewar dariyar xainab ne ya katse ta, Abba yace "meye haka,? get out" da sauri xainab ta mike ta fice tana dariya. Inna kam tuni ta Bude baki tana kallon intisaar, Abba yace "ina jin ki fateema" ta dan gyara xama tana kallon Aliyun sannan taci gaba " shine sai bai ce mata komai ba, tana ta fada har......" murmushin da taga Abba yayi ne yasa tayi shiru. Sai a lokacin inna Ta saka salati tana tape hannu baki a bude, Abba ya dube intisaar yace "je ki fateema" ta mike da sauri ta bar falon ba tare da ta kalle kowa ba. Da sauri ta shige palonsu, momy dake xaune ta dubeta tace "lafiya?" ta kirkiro murmushi tace Ba komai. To ranar dai Intisaar ko nan da kofa bata fita ba, tana palo a xaune har da yamma, Xainab ta shigo tana ta tuntsirar dariya, ita dai bata Ko kalleta ba ma, ta dae gama dariyar ta ta fita. Wajen karfe biyar taji muryar inna da alamar sashinsu xata yo, da sauri ta figi hijabinta ta fice, momy tana ina xaki amma tuni ta fice, ta canxa hanya don ma kar su hade da innar, Ta sashinsu xainab ta bullo, xainab tace "daga ina haka? Ina xaki" ko kallonta ma bata yi ba tayi gaba abinta, dariya xainab tayi tace "yau yarinya ta watsa ma innar ta kasa a ido," hanyar gate intisaar tayi har wani xaxxabi ma take ji, xaune taga Aliyun a kusa da gate yana waya...... .. Yana ganin ta kuwa ya mike, ta tsorata sosai ta juya xata gudu, yayi hanxarin fixgo ta, Ta saki kuka tace "na shiga uku me nayi....." tura ta da yayi ne ya sanya ta hadiye sauran Maganar tata, "Allah ya taimake ki yau da sai nayi gunduwa gunduwa da ke" ita kam babu baki Sai gyada masa kai kawai takeyi, tashi a gaba kar nayi ball dake, da sauri ta fice daga gate din Ba tare da tasan inda xata ba. Gidan wata kawar xainab dake nan layin ta shiga, farida tayi mamakin ganinta don tasan baxuwa gidansu intisaar take ba, nan dai ta tsaya har tayi maghrib sannan ta kama hanyar gida, yanxu tsoranta daya gamuwar ta da momynta don tasan inna ta gya mata. Tana isa gate tayi jigum a bakin gate din ta kasa shiga, can dae sai ta fara leke-leken cikin gidan, taji an kirata, da sauri ta juya a dan firgice suka yi ido hudu da faruuq, "lah.. Ya faruuq yaushe kaxo?" yace "hmm” leken me kike yi a cikin?" no xainab nake jirane, mu shiga ciki," tayi saurin shigewa gidan, ya bita a baya yana murmushi, yasan ba gaskiya ta fadi ba. Ta juya ta dubesa tace kaje can wajen inna gani nan xuwa dama momy ce ta aikeni," to bari Na fara gaida momyn mana," da sauri tace "a’a kadai je gun inna idan xaka tafi sae ku gaisa," yace ok sannan yayi sashin inna. Tana isa kofan parlonsu sae da tayi kusan minti biyar sannan ta shiga, momy da ihsaan na cin abinci, ta nemi gefe ta rakube, momy ta harareta bata ce komai ba. A haka suka gama cin abinsu. momy taje tama ihsaan wanka, ita dae tana nan a bakin kofa A xaune. Xainab ta shigo da sallama tace "ke yar walakanci ce pa yarinyar nan, shine xaki bar bawan Allah tun daxu yana jiranki," ta mike da sauri tace "bari nayi wanka na manta ne," sannan ta shige bathroom tana satan kallon momy dake shafawa kanwar tata powder. Ta saka kayan barcinta sannan ta dora dogon hijab har kasa ta fito, ta dubi momy tace "ina xuwa momy," ko kallonta ma bata yi ba ta fice a sanyaye, ko me inna ta tsara mata oho. Tana isa sashin inna ta nemi gefe ta tsaya sannan ta fara kiransa, bugu daya ya dauka tace "ka fito ya faruuq ina nan waje," yace "baxaki shigo....." da sauri ta katse sa ta hanyar cewa "aa ka dai fito ina jiranka sannan ta kashe wayan" ya dubi inna yace "inna ni xan tafi sai wni lkcn," aa to ina intisaar dinm baxa ta xo bane, yace "aa tana nan waje tana jirana. Yana fitowa ya kalleta yayi murmushi yace "sae yanxu?" bata ce komai ba sae gyada Masa kai da tayi, sae da ya fara shiga suka gaisa da momy sannan ta rakosa gate, ya dubeta yayi Yar dariya yace "me ya hadaki da innar taki baki San shiga wajenta?" tayi yake tace "aiki xata sani ne shi yasa" yyi dariya yana kallonta yace "ke dae fadi gaskiya kanwata," ta kauda kai bata ce komai ba sae hmm. To bara na wuce kar Abbanki yaxo ya same mu a nan ko?" da sauri tace "wa?" ya kashe mata ido yace "Aliyu mana" tace "uhum kaga sai da safe ya faruuq yau ba hira kake san min ba" yayi dariya yace "dama ae wuce wa Xanyi bayan kinsan kin wa inna laifi xaki turani can" bata ce komai ba sai murmushin da tayi, ya Ciro kudi mai yawa yace taba ihsaan, don yasan ita ba karba xata yi ba, shima din da kyar ta Karba, suka yi sallamah ya wuce, sannan tayi sashinsu. Tun faruwar abin suke wasar 'yar buya da inna, yau dae kam har dakinsu inna taxo ta sameta, tayi mata tatas, ita dariya ma abun ya bata, can dae ganin ba kyaleta inna xatayi ba tace "to naga dae inna ba sharri nayi......" dundun da inna ta kai mata ne yasa ta fashe da dariya, tace "kai ni inna ki kyaleni, haka kawae ban ji ba ban gani ba ya Aliyu ya min duka," da kyar inna ta kalleta Ta bar sashin nasu, momy dae bata ce masu komai ba, sai gashi da daddare wae xata wajen inna, momy tace "amma baki da kunya wallahi" tayi dariya tace "to momy ae dae inna ta ce." A hanya suka hadu da xainab, ta bude baki tace yau kuma wajen inna xa a? Har an manta... Duka ta kai mata ta bar wajen da sauri, xainab ta bita ita ma tana cewa "tab ae wllh sae na rama" da sauri ta bude kofar palon ta afka ciki tana dariya, Inna tace "lafiya ke da wa?" ta juya da sauri xatayi magana sae kuma tayi shiru ganin Aliyu xaune a parlon yana cin abinci... Xainab ta shigo ta da'da mata duka ita ma sannan tace "na rama" intisaar dae bata ko kalleta ba sae kame-kamen da ta fara yi, inna tace "ku dae ban san randa xaku girma ba," Aliyu ya mike yayi tsaki ya dube xainab yace "get out kar na fasa maki kai," ta harare sa tace "saboda kan nawa......" da gudu ta fice ganin ya yo kanta, ae intisaar na ganin haka ita ma ta fice a guje, inna tace "kai wallahi mugu ne yaro nan" kofar ya rufe ya dawo yaci gaba da cin abincinsa yana kallo. Suna xaune a palon inna, xainab na daddanna mata kafa, intisaar kuwa kallo takeyi sae kursum dake kwance ita ma tana kallon, inna tace "wannan yaron yace xae xo da bakuwa yau ko me xamu girka mata?" xainab ta yatsine fuska tace wai Aliyu? Inna tace "eh," ta tabe baki tace abinda muka dafa a gidan xamu bata mana. Khadija dake dakin inna tace "kamar ya abinda muka dafa xamu bata? Ita bakuwar xa a ba wa dafa duka?" xainab tace "shi kuma dafa dukan ba abinci bane ba koh?" khadija tayi tsaki tace oho. Kar ki min rashin kunya wallahi don xan fasa maki baki, xainab ta fadi tana kokarin mikewa, inna ta fixgota tace rabu da ita. kursum je ki ki kira min Zainabu, da gunguninta ta fice wae ita ta gaji. Ba a jima ba momy ta iso, inna tace "zainabu shinkafa da miya xaki girka min, wae Aliyu xai xo da bakuwa, wannan gantalallun 'ya yan sai yawo suke da hankalina. Ta ce "to inna sannan ta fita." xainab tace "inna budurwarshi ce?" inna tace kya barni budurwa," kursum tace yau akwae buduri kenan. Nan inna aka tashi aka fara gyare gyare su xainab na tayi mata dariya kuma suka ki taya ta, intisaar kadai ce ta kama mata aikin don wae bayan la'asar xasu iso. Momy ta gama girki ta kira xainab taxo ta dauka ta kawo sashin inna. Karfe hudu da rabi ya shigo parlon da sallama, yana sanye da kananan kaya yayi kyau sosai, inna ta amsa da fara'arta tana cewa "ina yarinya," yace tare muke, sannan ya dubi su xainab yace "ku kuma uban me kuke yi a nan, da sauri intisaar ta shige dakin inna, xainab ma ta bita kursum kadae ce taki tashi, har yarinyar tayi sallama da siriyar murya, inna ta amsa da karfinta tana wangale baki, yarinyar ta shigo palon. ... Tana shigowa palon ya nuna mata kujera ta xauna, kursum dake kwance dama tuni ta mike tana karewa yarinyar kallo, doguwa ce kyakkyawa fara amma da ganinta kasan ta hada da mai, tana sanye da atamfar Holland an mata shegen riga da skirt dinkin ya dameta sosae, sannan ta sakale wani dan guntun mayafi kalar atamfar tata yellow a wuya, make up kuwa har da na hauka don har da su blusher, sae wani yatsine fuska take, inna dama tuni bakinta a bude yake... Kursum ta dan sa kafa ta bugi inna alamar ta rufe bakin, ba shiri kuwa ta rufe hade da cewa "ikon Allah! Ina yini? Yarinyar ta kalle innar tace "sannu baba" tana taunar cingam hade da karewa parlon kallo, inna tace "yauwa pa" Aliyun kuwa tuni yayi hanyar fridge xae dauko mata lemo da ruwa. Inna dae ta dage sae kallonta take daga sama xuwa kasa, can sae ta fashe da dariya, kursum ta rufe fuskarta cikin kujera dan ita ma kar tayi, don shi ke cinta, daga yarinyar har Aliyu juyawa sukayi suna kallon inna, inna dae ta kasa daena dariya, Aliyu yace "wae meye haka ne Hajiya?" tayi kokarin shanye dariyar tace "wallahi wani abu na tuna ne" sae kuma ta kwalo wa xainab kira, "xainab ku xo gu gaisa da Antyn taku mana" xainab dama kamar jira take tafito da sauri don tuntuni take son lekowa amma tana tsoran kar Aliyu ya ganta, intisaar ma ta fito don tana san ganin budurwar tashi, gefe suka nema suka xauna, xainab ta kalle yarinyar sannan ta kalle intisaar da ta sunkuyar da kai saboda dariyar dake cinta, ita kanta xainab daurewa take amma da tuni ta fashe da ita. Inna ta sake kwashewa da dariya tana kallonsu xainab din, tace "ku kawo ma antyn taku abinci “No”a barshi kawae naci a gidanmu kafin na fito," Aliyu sae kallon inna yake cike da takaici. Inna ta kara dacewa "to ai bamu ma san sunanki ba" sunanta safeeyna, Aliyu ya taya ta fadi. "ayya amma wannan telan naki bai maki adalci ba, atamfa har atamfa amma ya tashi yayi maki dinki kamar 'yar babyn roba, ae wannan riga taki ko ihsaan jikin ta baxae shigeta ba, amma wannan anyi dan banxan tela," inna ta fadi tsakaninta da Allah babu ko dar. Xainab bata san sanda dariyar da take ta hadiyewa ya kubce mata ba, ta Xube jikin intisaar tana dariya kyal kyal kyal, intisaar ta daure iya daurewa amma ta kasa rike nata dariyan, nan ita ma ta fashe ta har da xubewa kasa, kursum ma yi take har da bingirowa daga kan kujera, inna ta bude baki tana kallonsu da mamaki can ita ma dae ta fashe da dariyar suka taru suka dinga yi, "ni wallahi ca nake xabiya ce ma ta shigo don hasken yayi yawa, tsoro ma ne ya kamani...." inna ta sake jefo masu. Xainab har da hawayenta don dariya, intisaar cikin hijab din xainab tashige ta dinga yi kamar wasu sababbin kamu. Aliyu kam kasa cewa komae yayi sae kallonsu da yake yi daya bayan daya. Safeenah kam iya kan kulewa tayi shi, ta mike tsam tana kallon Aliyun a nutse tace "Haidar help me out of dis forsaken house plss" inna tace "lah har xata wuce?, ko me take cewa?" tuni safennar ta fice daga palon innar da takalminta me kamar tsani, inna ta tafe hannu tace "ohh yanxu idan ta fadi da tsautsayi ba karyewa xatayi ba da wannan tsanin dake kafarta" ya mike da sauri duk a rikice yake ya fice ya bita yana kiran sunanta, inna ta bude baki tace "ikon Allah ko sallamah babu ni Rahmatu" sae kuma ta mike da sauri tayi bakin kofa tana cewa "Aliyu kakai ta, ta gaida xainabu tana ciki" amma tuni har sun ma isa gate. Ta dawo tana cewa "inda ranka xaka sha kallo" ta kallesu xainab da har yanxu dariya suke kamar mahaukata, ta hade rai tace "kai ni fa bana son iskanci dariyar meye haka?" kursum ta mike tace "na tafi wajen momy ni kam kun ga tafiyata, don yau idan ya Aliyu......" shigowar khadija ce ta sa tayin shiru, don dama taje wanke gashi, ta dubesu idonnan na ta a xare, tace "kai!! me kuka yi wa yaya Aliyu? Naji yace wallahi sai ya sumar da mutum daya a gidan nan " tana fadin haka, kursum ta bar falon a guje xa ta sashinsu intisaar, nan da nan hawaye ya fara sintiri a idon intisaar, cikin kuka tace"xainab wallahi ke ce kika....." wani axababben ihu can ciki ciki suka ji kursum ta saki... Sallati inna ta saki ta fice a guje tana cewa shikenan ya kashe ta!! Intisaar ta daura hannu biyu aka tace wayyoo nashiga uku na lalace, xainab tuni ta firfito da ido cike da tsoro tace "mun shiga uku!!!" Aliyu ya kauda kanshi ba tare da yace mata komai ba, sai da Abba ya bari tayi mai isarta tayi shiru sannan ya nisa yana duban Aliyun da kyau yace "ka gya min meye Matsalar ka a gidan nan, me ke damunka?" kansa kawae ya sunkuyar ba tare da yace komai ba, "why is it alwayz you in this house? Don me ba a kawo min karar haisam sae taka? Look.. Wallahi ka sake taba min wani a gidan nan sae nayi mugun saba maka, mutumin banxa kawae, tunda ka dawo gidan nan hankalina bae kwanta ba" ya dago kai da kyar yana duban Abban nasa yace "to Abba ka gyawa inna ta fita harkata ta daina min...." shut up! Abba ya katse sa a fusace, " dama duk cikin 'ya yana kai ne baka da manner, amma xanyi maganinka" Abba ya mike ya shige Bedroom sakamakon kiransa da akayi a waya, sae a sannan Aliyun ya dago ya fara kallonsu daya bayan daya a palon, ya mike yana duban innar dake kallonsa yace "ba wata tsiya bace idan na bar maku gidan, amma sae kun sake gani na " sannan ya juya xae fice, inna ta mike da sauri tana cewa "to Bukar sae kafito gashi nan ya hada kaya xae bar gidan wae" ido Aliyu ya xaro yana kallonta, ya koma inda yake da sauri, Abba ya fito yana kallonsa yace "to tashi ka wuce" bae ce komai ba sae tiles din palon da ya xubawa ido, Nan Abba ya dinga masa fada kamar xae ari baki, inna na ta xuga sa, har dae daga karshe Abba yace ya fice masa a palo, ya mike ransa a bace kamar ya hadiyi xuciya ya bar palon. Da Yammar ranan intisaar da xainab suna tsakar gida tare da inna dake yi ma ihsaan tsifa take tambayar su Ko sun ga Aliyu tun daxu don tun bayar barinsa palon abba basu sake ganinsa ba khadija ma ta kai masa abinci daxu da rana ta gama bubbuga kofarta ta dawo bae bude ba, xaenab tace "kila tafiyar yayi," inna ta dan marairaice fuska tace "Allah dae yasa ba tafiya yayi ba...." Budewar gate din da akayi ne ya sanya su duka suka maida hankalinsu wajen, Aliyun ne ya shigo, yayi Sashinsa ba tare da ya kalle su ba, sae ga Hajiya ma tashigo rike da jaka, umma na biye da ita a baya, sannan khadija ma tashigo da wani jakar a hannunta, da gudu xainab taje ta rungume uwartata, kursum ma dake kusa da wani flower a xaune taje da gudu ta rungume ummarta harda kuka, nan da nan inna ta hade rai kamar bata taba dariya ba, intisaar ma ta mike da sauri ta karbi kayan dake hannun hajiyar tana masu sannu da xuwa, har kasa suka durkusa suka gaida inna, ta amsa masu can ciki-ciki ba tare da ta kallesu ba, momyn intisaar ma ta fito tayi masu sannu da xuwa da fara'arta, sannan duka sukayi sashinsu, tsakar gidan ya rage daga inna sae intisaar da ihsaan, inna ta tabe baki tace "shegu munafukai, wallahi ni banyi farin ciki da xuwansu ba tsinannuna mutane." intisaar cike da jin haushi tace "ni bana son wannan abinda kike yi inna wallahi," sannan ta bar mata wajen ta koma sashinsu. .. Tun ranar da Hajiya da umma suka dawo gidan suka shiga taitayinsu, don ba karamin tashin hankali suka shiga ba kwanakin baya don a nasu tunanin Alhaji ya sake su ne basu sani ba. Kullum da sassafe suke xuwa gaida inna. Abinda basa yi da, har wani shiri suka tsiri yi da Momy duk da na munafurci ne. Yau kam intisaar na xaune gaban inna tana mata hira, inna tace "yauwa wannan yaron faruuq yaxo ya sameni jiya da daddare wae yana so ke da xainab kuje Gaida mahaifiyarsa," intisaar ta firfito da ido tace "kai; inna sae kika ce masa me?" eh nace ranar juma'a ya xo ya kai ku, gobe kenan." intisaar ta hade Rai tace a’a ni babu inda xanje inna, ke kinga hakan ya dace? Saboda gantali kawae sae na kwashi jiki Naje gidansu" nan da nan inna ta hade rai tace "to idan yaxo goben karki bisa" intisaar ta mike Ta fice daga palon tana cewa "ni kam babu inda xanje." tana komawa sashinsu ta fadi ma momynta, momy tace "A'a ko da ma xaki je gidan nasu ba yanxu ba sae lokacin da ya dace," da yamman ranar faruuq din ya kirata, da kamar baxata dauka ba sae kuma ta dauka don taji haushinsa sosae, anata tunanin it’s not decent yace xae kai ta gidansu bayan ba ayi maganar komai ba tukun. Bayan sun gaisa yake ce mata inna tayi mata magana, tace "eh amma babu inda xani" yayi murmushi yace "to shikenan kanwata." nan dae ya dinga mata hira har yace mata xae je masallaci don lokacin sallah ya kusa. Da daddare xainab ta shigo palonso intisaar din tace "ke wae inna tace gobe faruuq xai kai mu wajen momynsa" intisaar tace "eh amma babu inda xani" xainab tace saboda me? Ke kinga hakan ya dace? Intisaar ta tambayeta tana jiran amsa" Xainab tace "to meye a ciki don munje gaida mamarsa? Ni dae banga rashin dacewar hakan ba wallahi" intisaar ta mike tace "ke kya iya xuwa, amma ni baxan je ba." sannan ta shige daki, xainab ta tabe baki ta yi gaba abinta. Washegarin ranar juma'a inna ta xo sashinsu wajen karfe sha daya, tana kwance tana kallo, momy kuwa na bedroom, inna tashigo palon tana cewa "ke wai wace irin yarinya ce xaki bar bawan Allah tun daxu yana jiranki, wannan wani irin wulkanci ne, na aiko a kiraki yafi sau hamsin sae kice min kina xuwa?" intisaar tabe baki tace "ko ma de sauna nawa ne ni dae ki rabu dani inna babu inda xani pa" au uwar taki ta hura maki kunne kice min baxaki ba kenan?" da sauri momy ta fito tace "maxa ki shirya kuje, ni ban hanata ba inna" dolenta ta shirya cikin atamfa java red colour an mata dinki riga da skirt dama gata fara sosae sae ya amsheta, ta danyi kwalliya tayi kyau sosai sannan ta dauki hijab dinta har kasa, ta fito palo tace "momy na tafi" momy tace "ki kama kanki, kuma ku tafi da ihsaan, sannan ki turo min xainab" ae da ita xamu momy, momy tace "eh nasani," tana fita tayi sashin su xainab, ta hadu da khadija a bakin kofa tana dauraye cup, tayi mata wani irin kallon banxa sannan tace "amma de kinyi batan hanya ne ko?" tayi jim sannan tace momyna ke kiran xainab. Aliyu ne ya fito yana dubanta yace "get out" cikin tsawa, xainab ta fito da sauri ita ma ta shirya cikin wani material ja, tace gani nan xuwa intisaar. Gidan uban wa xaki? Aliyu ya tambaya yana kallon xainab din, "inna ce xata aike mu gidan kawarta wae," bae sake cewa komai ba ya shige ciki kawae, hajiyarsu kuwa tana sashin umma suna tseguminsu da suka saba. A tare suka je sashin inna da xainab din bayan taje kiran da momy ke mata, ita dinma ta ja mata kunne ne akan su kula da kansu, ashe faruuq din ma bae xo ba inna duk tabi ta axalxalesu. Sha daya da rabi ya shigo gidan, suka gaisa sannan, inna tace, "amma dei da wuri xaka maido su ko?" yace in'sha Allah inna. Ita dae intisaaar hade rai ko kallonsa ma bata yi ba. Har bakin kofa ta rakosu sannan ta koma. Sae da suka hau kan kwalta sannan ya fara hira da xainab, ita dae jinsu kawae takeyi sae wayanta da take ta daddannawa. Tafiyar kusan minti talatin sukayi sannan suka iso gidan nasu, yayi horn aka Bude gate ya shiga yayi park, sannan ya bude masu kofa suka fito, da ganin gidan kasan lallai mahaifinsa mai kudi ne sosai. Kanwarsa ya kira ta fito,da ganinta baxata wuce su ba, tayi masu sannu da xuwa tashiga dasu ciki da fara'arta Har palon mahaifiyarsu tayi masu iso, sannan ta nuna masu kujera su xauna ta cika su da drinks da kayan ciye ciye, ba a dau lokaci ba mahaifiyar tasu ta shigo palon, suka sauka har kasa suka gaisheta ta amsa da fara'arta tanai masu sannu da xuwa sannan tace suyi xamansu a kan kujerar, xainab tace nan ma yayi momy, "a’a don Allah kuyi xamanku nan ba bakon waje bane," da kyar dai xainab ta xauna kan Kujerar amma intisaar taki xama, hakan yasa momyn Ta gano ita ce fateemar. Nan dae ta tambayesu ya mutanan gidan suka amsa mata da duk Suna lafiya. Ba a jima ba faruuq ya shigo yace xae wuce masallaci tayi masa Allah ya kiyaye hanya sannan ya wuce yana kallon intisaar amma bata bari sun hada ido ba, sae da suka fara yin sallah, sannan aka cika su da abinci kusan kala hudu, Ita dae intisaar ta kasa sakin jikinta ga kunyar momyn da take ji, ganin hakan yasa momyn ta basu waje tashiga ciki, a tare da kanwarsa ummi suka ci abinci, yarinyar na da kirki sosai, suka dinga hira kamar da can sun san juna. Karfe biyu faruuq ya shigo gidan ummi ta kai masa abincinsa dakinsa sannan ta dawo suka ci gaba da hirarsu akan makaranta da sukeyi, sae da faruuq ya dawo parlon sannan momy ma ta fito, nan dae aka dinga hira amma ban da intisaar da sae dae tayi murmushi, karfe uku da rabi yace xae maidasu gida saboda traffic, momy tashiga ciki ta hado masu tsaraba mai yawa tun daga kan atamfa har xuwa sabulai da omo da jeweries na fashion masu kyau, da after dresses, ummi ma tashiga ta hado masu nata tsarabar na kayan make-up da turarruka kala-kala, intisaar tace "mun shiga uku xainab, don Allah kice ma faruuq yace su rage sunyi yawa wllh. Xainab tayi banxa da ita ta dinga godiya kawae, har kusa da motar suka rakosu sannan ya ja motar suka bar gidan. Ganin yayi park a wani supermarket ne ya sanya intisaar tace masa "me xamuyi a nan, yace wannan ba matsalarki bace. Sannan ya shiga ciki, wani tsarabar ya kara hado masu, sannan ya siya ma inna malt carton daya, da peak milks holland, aka xo aka xuba kayan cikin booth sannan suka bar wajen. Ana gama sallar la'asar suka iso gida, ya fiffito masu da tsarabar tasu xainab ta bude baki tana kallonsa tace "me yasa xaka daurawa kanka nauyi haka ya faruuq," yace ni dae ku shiga dasu ciki xanje masallaci nayi sallah yanxu, sae na dawo. Kursum ce ta taya su suka dinga jidar kayan suna sashin inna dasu, shima dan gulma tayi hakan amma ba don saboda da Allah ba, Aliyu suka tarar xaune a palon, inna ta mike cike da doki tace "kar dae har kun dawo?" intisaar tayi mata alamar tayi shiru saboda Aliyu dake xaune, haka ma xainab da ta daura hannunta a baki alamar inna tayi shiru, inna tace "ayyo haka ne pa." Aliyu yace "ina suka je da?" da sauri inna tace "gidan hajiya Maimuna na aikesu." to wannan kayan meye haka? Cikin in ina inna tace "eh eh.. au ita ce ta bada a kawo min mana" nan ya shiga bubbuda ledojin yana kallon kayan baki bude inna tayi maxa tace "maxa kuje can guriin xainabu gani nan xuwa" da sauri kuwa suka juya suka bar wajen, sannan inna ta dinga kwasar kayan tana shiga dasu dakinta Aliyu na binta da kallo "Allahu akbar.. Yanxu har da maltina aka kawo min?? Lah har da madara ni rahma, amma mutanan nan anyi mutanan kirki."Aliyu ya bude baki yana kallonta sae kace warce bata taba shan madara ba ko malt, ita da duk wata abba ke jido mata su dayawa, amma ko sati biyu ba sayi take shanyewa da yara. "kai Allah ya shima wannan yaron Albarka" Aliyu ya dubeta yace "wani yaro?" au na manta ne Allah ya shima maimuna Albarka xance, ko da yake ma duk Daya ne, don dan ta da ya dawo daga waje ne yayo min tsarabar. Aliyu ya tabe baki ya jawo Abincin gabansa xai fara ci akayi sallama faruuq ya shigo palon bayan inna ta amsa da karfinta, Mikewa tayi ta rasa inda xata sa shi sae ca take "sannu da xuwa dan Albarka," ya nemi guri ya xauna ya gaidata ta masa cike da jin dadi, sannan ya ba Aliyu hannu sukayi musabaha, da dan fara'arsa Aliyun ya karba don bai san sa ba. Inna ta Mike ta bude fridge ta jido masa lemo kusan kala hudu da ruwa roba uku, ta dire masa a gabansa Tana tambayensa ya hanya, sannan ta shige ciki ta fito da cin-cin da alkaki bakin nan nata yaki rufuwa. Godiya ya dinga yi mata, don yana jin dadin yanda inna ke nan nan dashi, ko xaka ci abinci ne, bari na kawo maka cokali kuci tare da Aliyu, wannan shine Aliyu jikana da nake baka labari, dariya ma abin ya ba Aliyun, ta dauko cokalin ta saka masa tace suci tare. Aliyun bai yi musu ba ya sauko yana cewa ki dae yi a hankali karki fadi da wannan barin jikin da kike yi. Bata ko tanka masa ba tace "wannan shine faruuq saurayin intisaar ae nasan baka san shi ba, Haisam ne ya san sa," dago kai Aliyu yayi yana kallonsa, nan da nan dan fara'ar dake fuskarsa ya bace, inna tace to kuci abincin mana kar ya huce, ajiye cokalin hannunsa yayi fuskar nan tasa a yatsine yace "ya dae ci, amma ni wannan ba isar mu xai yi ba," faruuq ya dago yana kallonsa, ya gane nufinsa,don hka sae yayi murmushi yace to ni bari naci tunda bako ne ni, da sauri inna tace eh hakan ma yayi sae ya hakura ayi na dare. Hade rai Aliyu yayi yana kallon inna yace "kamar ya na jira na dare? Ban gane nufinki ba?" Inna ta mike ta tabe baki hade dacewa "maida wukar dan nan" sannan ta shige daki sae ga ta ta Fito da garin rogo da suga ta xube masa a gabansa tace "ka debo ruwa a pampo ka jika kasha don ruwan kenan na kwaso wa faruuq. Takaici ya hana Aliyu cewa komai sae bin inna da yake yi da kallo har ta koma ta xauna tana ci gaba da hirarta da faruuq, shi kanshi faruuq din abin ya basa dariya sosae don har sae da ya dan dara, can sae Aliyu ya turawa faruuq din garin yace "shi da ya kwaso yunwa har haka ya shigo sae ya hada ya sha, ni kam am okay" ya fadi a walakance yana duban faruuq din da har yanxu murmushi na fuskarsa, sallamar Haisam ne ya sanya inna bata tanka masa ba, inna ta amsa da murnarta tana cewa "yawwa yaron kirki sannu da xuwa shigo ka taya ni godewa faruuq abin arxikin da yayi min" haisam ya shigo suka gaisa da faruuq da fara'a sannan ya gaida inna da bakinta yaki rufuwa, yace kinga inna bari naci abinci tukun yunwa nake ji, idan yaso in nagama sae na taya ki murnar, faruuq ya dubi haisam yace "bismillah kaxo muci wannan don ni ba wani yunwa nake ji ba," nan da Haisam ya xauna suka fara cin abinci da faruuq din suna hira inna na tsoma masu baki, haisam ya dubi Aliyu da ya kura wa TV ido yace "ya dae bross lafiyanka?, kardai yau ma baka je clinic din ba" Aliyu ya watsa masa harara yace a fusace "spare me malam bana son sa ido plss" daga haisam din har faruuq suka kwashe da dariya inna na tayasu har da kwanciyarta, Aliyun ya kulu matuka amma bai sake cewa komai ba illa gnash din hakora da yayi fuskar nan tasa a tamke. Har dae suka gama cin abinsu sannan inna tace idan basu koshi ba ga gari su jika, faruuq yace a’a ya koshi haka ma, Haisam Nan inna ta fara jawabinta tana washale hakora " kaga haisam daxu su intisaar suka je gaida mamar faruuq suka yi masu sha tara ta arxiki, bari na kwaso maka ka gani, gaskiya gidan mutunci ne wannan gida" nan inna ta dinga jido ma haisam kaya yana ta yabawa da kara taya innar tasa godiya. Ido Aliyu ya xuba mata yana kallonta cike da mamaki, daxunan tace masa kawarta ta bada a kawo mata yanxu kuma tace daga gidansu faruuq, dama gidansu faruuq din sukaje? "kaga har kwalin maltina fa haisam, kai ni dae banda bakin gode maka faruuq, Allah dae yayi maka albarka ya dada budi," ta fadi tana kallon Aliyu baki har kunne, taga yana mata wani kallon rainin wayo yana girgixa kafa, ta juyo tana kallonsa da kyau tace "meye kake kallona haka,? Ka taba kawo koda gwangwanin madara daya ka kawo min gidan nan ne bare maltina? Kuma Don yanxu na samu me min sae ka dinga min bakin ciki? To ahir dinka, Allah ya fika, har gwanda haisam duk sati yana yo min tsaraba amma ban da kai don bakin rowa irin taka," ta juyo tana murmushi taci gaba da shi ma Faruuq da haisam albarka. Ya mike tsam yana kallonta bacin rai karara a fuskarsa yace "ai ke ba uwata bace da xan dauka gwangwanin madara na kawo maki, Idan ma kyautar nake son yi ae uwata na nan da ranta, don haka baki isa nayi maki kyauta ba Hajiya, wa inda suka ga xasu iya sae su maki. Aikin banxa kawae aikin hofi, mutum ya tsufa bae san ya tsufa ba" yana kaiwa nan ya fice Ba tare da ya jira cewarta ba, sashin hajiyarsu ya nufa, yana shiga ciki rae bace ya fara Magana "mumy kina gidan nan xaki bar 'yar ki ta fita raka wata banxa can gidan saurayi? Hajiya ta mike da sauri tana cewa wa kenan? Kursum daka palon tace "xainab mana daxu ta raka intisaar gidan saurayinta suka dawo da kaya niki- niki wallahi," hajiya ta xabga salati tana tafe hannu tace "wallahi ca tayi min inna rahmatu ce xata aiketa gidan kawarta...." bae kara sauraran mahaifiyar tasa ba ya dubi kursum cikin tsawa yace "ina xainab din?" a dan tsorace tace "tana can Palonsu intissaar can inna tace suje ae" maxa jeki ki kiramin ita, ta dan marairaice fuska don ita mugun tsoransa takeyi tace "yaya ko naje ba xuwa xatayi ba da dae kaje da kanka" bae kara bin ta kanta ba yayi sashinsu intisaar din rai bace yana kwadawa kanwartasa kira, yana isowa wajen sae ya daina kiran nata don yasan xata iya gudu idan taji muryarsa, daga dan nisa ya hango ihsaan bakin tap tana dauraye cup din da tasha corn-flakes, tana ganin sa ko ta ruga ciki a guje tace "momy kinga ga uncle nan xuwa," intisaar ta xaro ido tace ya Aliyu? Ihsaan ta gyada kanta, nan suka shige bedroom din momy a guje don tsiyace kadae ke kawo Aliyu sashinsu, yana isa bakin kofar ya bude yana karewa palon kallo, momy na xaune dama ita ma a palon, ya kalle ihsaan yace "xo nan," ta isa gareshi tana kallonsa, yace "me kika gudo kika cewa, kuma idan baki gaya min gaskiya ba xan xaneki yanxu a nan" nan ta marairaice fuska xatayi kuka tace "nace ma Anty xainab da Antyna kana xuwa" shine sae sukayi me? Ya tambayeta yana kallonta, "shine sae suka gudu suka shiga daki," rankwashi ya kai mata har sau uku yace "ki ka sake gani na kika je announcement sae na cire maki wannan katon idon naki, wawiya kawai fice min a gaba. Ta ruga da gudu ta fada jikin momynta da ta tsurawa TV ido tun daxu, tana kuku Ya juya xae bar wajen kenan don yasan ba fitowa xasu yi ba ya ci karo da hajiyarsu itama ta karaso wajen a fusace, Aliyun yace "me kuma kika xo yi nan Hajiya?" bata bi ta kansa ba ta dinga kwada ma xainab kira tana cewa "wallahi ki fito daga gidan nan kar na ci ubanki Munafukar yarinya," ganin momyn intisaar din a xaune A palo ne yasa ta ja ta tsaya, Aliyu yayi dan tsaki yayi gaba abinsa, don baya son uwarsa tana masifa ko neman magana a gidan, ita kuma aikinta kenan. "Zainabu! Ki gya min dalilin sa 'yata bin watsatsiyar yarki gidan saurayi don a bata ta?" hajiya ta fadi fuskarta a tamke, ko kallo bata ishe momy ba da ke ta aikin kallonta tana rungume da 'yar ta, hakan ya kara hassala hajiya don tana matukar bakin cikin sharesu da momyn ke yi a gidan, kenan ma mahaukata kawae ta maidasu don ba dai amata abu ta tanka a gidan ba, cikin daga murya hajiya tace "wae ba da ke nake ba ko kurama ce ke?" nan ma de momy ko kallonta bata yi ba, hava nan hajiya ta dinga gaya mata maganganu marasa dadi masu kuntata xuciya duk don momy ta kulata amma bata ci nassara ba don momy murmushi ma kawae take yi. Hayaniyar hajiyar ne ya fargar da umma ta karaso sashin da saurinta tana cewa "lafiya hajiya me ya faru, rashin kunya ta maki ko me?" ina fa,, yawon iskancin da da ta sa 'yar ta take yi, shi xasu koyawa xainab dita, tunda gashi yau har shiryata tayi suje gidan saurayin 'yar tata. Umma ta xabga salati tana jujjuya kai tace "wallahi kursum taxo ta sameni wae xainab ta bi intisaar gidan saurayi ya cika su da kaya duk na tsamman shirmanta ne shiyasa ban tanka mata ba" hajiya tace "Allah ya isa tsakanina dasu," umma tace "to yanxu ina shegiyar xainab din take" bata jira amsa ba ta afka palonsu intisaar din ta tsaya gaban momy tana cewa "ki fito mana da 'yar mu kar mu aki abinda baki xata ba gidan nan yau," tana magana ne tana nuna momy da dan yatsa, momy tayi murmushi mai sauti, ta kama hannun ihsaan suka shige bedroom ta kulla kofar. Galala umma ta bita da kallo, hajiya ma ta shigo palon tace "idan ba tsoro ba dan uban mutum meyasa bae tsaya ba" nan suka dinga xaxxaga mata rashin mutumci kwando-kwando suna xage-xage, gori kam ta sha shi kala-kala, abinda ya fi bata masu rai bae wuce yanda ta barsu su kadae suna ta haukansu ba, don a da can idan suna mata tayi shiru har dadi sukeji a nasu tunanin tana tsoransu ne,. Ido Aliyu ya xuba masu yana kallonsu, yayi murmushin da xa a iya kiransa da na mugunta sannan ya hade rai yana kallon xainab din yace "ina kuka je jiya?" ta yarfe hannu hawaye na sintiri a fuskarta tace "don Allah kuyi hakuri..." wani irin tsawa ya daka mata yace "it seems kina wasa dani ko?" cikin kuka tace "aa yaya" gud! Gaya min inda kuka je jiya. Ta juya tana kallon intisaar dake kuka wiwi sannan ta kalle abban nasu da ya Aliyun tace "gidansu faruuq muka je gaida mahaifiyarsa" abba yace "waye faruuq din?" saurayin intisaar ne," ta fadi, kanta a sunkuye. Cike da mamaki abba ya tsaya kallonsu, Aliyun yace "amma ina kika ce mun xaku jiya?" "aa Inna ta...." wani irin tsawa ya daka mata yace "rufe min baki kar na taka ki" yayi hakan ne don baya Son Abba yasan da ixinin inna suka je, kawae so yake ya lallasa su barin intisaar. Xainab na ganin hakan tasan yau kam sun banu, nan Aliyu ya dinga tsarawa abba yanda suka yi jiyan da irin karyar da sukayi mashi, xainab ta san inna ce kadai gatansu yanxu don abba yayi fushi matuka, da dubara tashiga yi ma kursum tex da wayan dake hannunta kan cewa ta kira masu inna suna palon abba xa ayi masu duka, duk a rude take, ganin yanda Aliyu ke tayi wa abba tsari yana dada bata masa rai. Ba a jima ba, kursum ta maido mata reply, ta bude da sauri hannunta na karkarwa taga me tace, "NO" abinda ta gani knan boldly wato baxata turo innar ba. Ta kara sautin kukanta tana kallon intisaar da ta kife kanta ita ma tana yi, tun ba yau ba tasan kursum muguwa ce. To wa xata kara yi ma tex yanxu? Don kursum ce kadae hope dinsu, ita ma tace no. Yaya haisam ta tuna, don haka da hanxari ta shiga yi masa tex duk da baya gidan, ya taimaka ya kira masu inna taxo. Kafin tayi sendin Aliyu ya ganta ya fixge wayar da sauri yana cewa "you re vry stupid, wat do yhu fink yhu re doin?" abba ya karba wayan ya ajiye gefensu yana kallonsu. Haisam yyi dariya sosai da yaga tex din, don sbda tsabagen masifa Aliyun yyi sendin bai sani ba. Ai kam yana kiran innar ya gya mata ta taho da gudunta tana salati. Tun daga bakin kofa ta dinga kwada wa abba kira, hkn ba karamin bta wa Aliyu rai yyi ba, don yyi niyar yyi masu laga- laga ne, sai yaji kmr ya hankadata ta koma, nan ta sake masu kuka tana cewa "ynxu Bukar don na tura yaran nan su gaida uwar yaron nan me kirki shine nayi laifi?" Abba ya girgixa kai yace "dama ke kika ce su je?" ta goge hawayen dake idonta tace "eh mana," basu gaya min ke kka ce suje ba ne." ya kallesu yace "ku tashi ku tafi." yyi hkn ne don baya son uwartashi ta daga masa hnkli. Aliyu ya dan bugi kafarsa a kasa yace "shit" inna ta dubi hajiya da umma dake xaune a palon kmr su hadiye xuciya don takaici tace "to munafukai ae sae a tashi a bashi waje kuma ko," tayi tsaki ta wuce tana surutanta, don ana ta tunanin su suka gya masa, duk da su din suka gya masa. . Suna fita Abba ya girgixa kai cikin damuwa yace "ni bn san me ke damun inna ba, tana tsufa ne hnklinta na komawa na yaro," hajiya ta mike ta tabe baki hade dace wa "kawae de ta kare matarka ne, amma ka dae yi bincike da kyau." tana kai wa nan ta fice, umma ma ta bita a baya tana cewa "mu dae Allah ya rufama 'ya yan mu asiri kar a sa su a hnyar da bae dace ba, don wannan lamarin akwae abun dubawa a ciki" momy de bata ce komai ba, amma tasan da ita suke, ta mike itama xata bar palon Abba ya kirata ta dawo, Aliyu ma ya tashi ya bar masu palon cike da jin haushin inna, ko waye yaje ya gya mata ma oho. Suna tsakar gida a tsaye ita da xainab suna ta dariyan abinda ya faru jiya da safe, hajiya da umma sun je barka, inna tana can sashinta, su biyun kadae ne a tsakar gida, shirun da intisaar tayi ne fuskarta ya bayyana alaman tsoro ya sa xainab ta dakata daga surutun da take yi tace "me ya faru," tana waige-waige, da sauri intisaar ta fixgota da gudu suka je bayan wani flower suka buya, xainab na maida numfashi a tsorace tace "wae menene?" ita din ma numfashin take mayar wa tace "ya Aliyu." xainab tace "a ina kika..." tsit tayi ganin Aliyun ya doso ta inda suke, cikin kasaita yake tafiyar tasa, yana sanye da t'shirt fara kal, da 3quatre shima fari tas, intisaar ta bi shi da kallo da idanuwanta kmr xasuyi magana, farar kujerar roba ya dauka ya ajiye ta opposite inda suke ya xauna. Basu da wata fargaba don sun tabbatar idan ba kusa da flowern ya xo ya tsaya ba baxae gansu ba, ya ciro wayrsa daga Aljihu yana dubawa, suka ga yyi murmushi mai kyau har sae da dimple dinsa ya nuna, ya lumshe manyan idanunsa ya sake budesu, ko me ya gani oho. Ashe dae ya Aliyu na murmushi, tambayr da intisaar tayi ma knta knan a xuciyarta, nan dae ta tsaya ta kare masa kallo sosai, don ita kullum kallon tsoro take masa a gidan. A xuciyarta tace "ashe dae yana da kyau har hka," ta tsura ma sajensa da ya kwanta luf- luf a fuskarsa ido, daga sama xuwa kasa ta dinga kallonsa ko kifta ido bata yi, ashe dae shi din kyakkyawa ne sosai, amma duk da hka faruuq dinta ya fisa kyau tasani, xainab ta xungureta tace "ke wannan kallon fa?" a tsorace intisaar din tace "da'alla dubi yanda kika bani tsoro."xainab tace "to naga kina neman cinye min yaya da ido, intisaar ta tabe baki tace "ni kallon mamaki nkeyi masa" to wae taya ma akayi kika san yana xuwa? Xainab ta tambaya tana kallonta, kamshin turarensa, intisaar ta bata amsa ba tare da ta kalleta ba. takun da suka ji yasa suka kara labewa sosai, momy ce taxo ta wuce, bai ce mata ba, bata cemasa ba har ta wuce sa, da alama sashin inna xata, sae da ta wuce shi sannan ya bita da kallo har ta kure masa, yyi murmushin da intisaar ta gaxa gane ko na menene, sannan ya cigaba da danna wayarsa, xainab tace "yau mun shiga uku hka xamu ta tsayawa ni kam na gaji wllh" intisaar bata tanka mata ba ta dan kara satan kallon Aliyun, taga kara hakikincewa yyi ma kan kujerar. Ihsaan ce taxo wuce wa tana kuka, kila ta tashi bata ga momynta ba da yayarta, don bacci take yi, xata wucesa ya fixgo ta yace "cum hia, wa ya dokeki?" bata ce komai ba sae kallonsa da takeyi, ya daura ta kan kafarsa yana cewa "idan kika sake kuka xan maki allura" ba shiri tayi shiru ya dago wayrsa yana ta nunamata ko pix ne ko meye ma oho dae, su dae hka suka dinga lekosu har daga karshe suka ga ya sauke ta ya mata mgna a hnkli ta ruga sashinsa da guda, ba ajima ba ta dawo rike da chocolate, suka ji yace mata "run.. Momy tana wajen inna je ki sameta," da gudu kuwa tayi sashin innar. Idan ba don intisaar da ta dinga rike xainab ba da tuni ta mike ta bar wajen, ita kam tsoran abinda xai yi masu ne yasa ta dinga rike xainab kar ta tona masu asiri. don sun gaji sosai gashi aliyu yaki barin wajen har sunyi kusan awa biyu a durkushe, momy da ihsaan ma tuni suka xo suka wuce. Ba su suka bar bayan flowern ba sae da aka kira la'asar Aliyu ya wuce massallaci. Tana xaune gefen inna da ta dage tana ta kirgan kudi 'yan dubu daddai, da ta kirga sai ta mikowa intisaar ta duba ko dai dai ne, intisaar kam ta xuba mata ido don bata san inda ta samu kudin ba, har dae daga karshe suka gama kirgan kudaden inna ta dubi intisaar din bakinta a wangale tace "nawa knan gaba daya?" intisaar tace "dubu dari biyu da hamsin, ina kika samo su inna?" ba tare da inna ta kalleta ba tana kkrin hada kudaden waje daya tace "fili na na saida." intisaar ta xaro ido hade da bude baki tana kallon inna. Sallamar haisam ya sanyata rufe bakinta, inna ta amsa mashi ba tare da ta lura da halin da intisaar ta shiga ba ya shigo, suka gaisa yace "kina sha'aninki inna, ina kika samo kudi hka?" ya tambayeta yana karewa palon kallo, a xuciyarshi yana cewa kar dae wani abun inna ta kuma saidawa, don saranta knan, in dae bata da kudi to bata ki koh plaxman palonta ta saida ba, hkn kuma na bata wa abba rai sosai ba kadan ba, don duk abinda yke mata bata gani sae ta saida wani abun palonta ko daki, "wllh fili na na saida haisam" haisam yace "mene?" Ba tare da inna ta kallesa ba tace "nace mka fili na na saida. Ko bka ji ne" ya nemi kujera ya xauna yana kallonta cike da mamaki yace "wani filin inna?" don dai shi yasan a ynxu hka inna bata da fili, idan ba dae wanda ake mata gini taje ta saida ba, "wannan din da babanku ya siya min" ta fadi tana mikawa intisaar kudaden ta kai mata daki. Haisam ya yo waje da ido "yace wani filin abba ya baki?" inna ta hade rai tace "na jan bulo mana" haisam ya saki salati yana kallon innar, inna tace "kai ni don Allah ku rabu dani, ina da bukatar kudi kuma baxan saida kaddarana ba?" haisam yace "ya salam! Ynxu inna abba ca yyi maki filin naki ne? Daga ya baki takardu ki ajiye masa sae ki je ki saida fili? Wai ma nawa kika saida filin?" "ni dubu dari biyu da hamsin aka siya," inna ta fadi a marairaice. Haisam ya mike da sauri yana kallonta ya ma kasa cewa komai," filin abban kika saida masa dubu dari biyu da hamsin? Kin san nawa ya sayi filin inna, haisam ya girgixa kai yana kallon innar cike da takaici, ita kam sai wuri-wuri take da ido. Aliyu yyi sallama ya shigo yana cewa "har kin dawo daga yawon inna?" ya kalli haisam da yanayinsa ya sauya xuwa bacin rai yace "me ya faru guy?" Aliyu filin abba taje ta saida dubu dari biyu da hamsin wae" haisam ya fadi cike da jin haushi, Aliyu ya xaro ido yace "wat?" filin da yke cewa xai fara gini cikinsa nxt yr?" dariya Aliyu ya dinga yi har da dafa bango, intisaar kam ido ta xuba masu tana kallonsu ita ma tasan inna bata kyauta ba, tuni inna aka fara hawaye, irin dariyar da Aliyu yake yi ne ya kara kullar da haisam, to meye abun dariya a nan, ta rangada wa abbansu asara, don ko shi bai sayi filin hka ba, cikin karkarwar murya inna tace "to ni ina nasan filinsa ne, da naga bai sake min mgna ba ai nayi xaton ya bani ne, kuma Aliyu ba kai ka bani shawarar ba to?" Aliyu ya xaro ido yace "wa? Aa karki sake saka ni cikin wannan case din Hajiya" inna tace wllh kai ka sani, kana ji ko haisam, jiya ya shigo da daddare nake ce mashi bnda kudi kuma ga bikin jikar aminiyata ya taso bari bukar ya dawo na tambayeshi kudi, sae Aliyu yace min ae Bukar bai da kudi ynxu hka sae dae idan xan saida kujeruna ne na biya bukatata, to naga dae taya xa ayi na saida kujerun palona, palo ya xamo wayam, kuma kwanakin baya ma da na saida fridge dina ma ae sae da bukar yyi min masifa, to yana fita a jiyan sae na tuna ai akwae takardun filin da bukar ya bani......" Aliyu ya daka mata tsawa yana cewa "ke inna rahmatu wllh kar ki saka ni cikin wannan case din na gya maki, idan dae mutum ba hauka ya fara ba ta ya xai kin kima kujerunsa ya saida don an bashi shawarar, ni dama wasa nke maki, kuma magana ce na gya maki." tuni inna aka fara kuka wiwi, Aliyu ya fice yana dariya, Haisam kam kasa cewa komai yyi, tun ba yau ba yasan Aliyu mugu ne, idan ba hka ba taya xa a saida kaddarar mahaifinsa mai muhimmanci yayi ta dariya. Ya juya ya fice kawae ba tare da yace da inna komai ba, to waye ma yyi mata jagora taje tayi wannan aika aikan, Aliyu na fita yaje ya sami hajiyarsa yana ta dariya ya bata lbrin abinda inna tayi, ta hade rai tace "to meye abun dariya a nan Aliyu, gadonku fa ta walakanta kke dariya hka?" ya mike yana kallon umman tashi yace "ni banyi depend a gado ba mum, Allah ya hore min don hka, 4 ol i care," ya fice yana ci gaba da dariyarsa don yasan drama xa ayi a gidan yau idan abba ya dawo. Abba ne tsaye kan inna yana faman bambamin fada kmr xae maketa, inna ba baki sae idanuwa, "kinsan nawa na sayi filin ne xakiyi min hka inna, daga baki ajiya sae ya xama naki, ina aka taba yin hka? Bbu shawara bbu komai xaki je ki walakanta min abun da akalla xan iya saida shi miliyan daya da rabi." hajiya da umma dake palon ji sukayi kmr su shide don murna, Aliyu ya kasa hadiye dariyar dake cinsa ya fasheta, abba ya juyo kansa ya dinga masifa kmr xai maresa, ba shiri ya kame kansa, don ran abba yyi mugun baci ranar. Ganin ba sarki sae Allah yasa inna ta fashe masu da kuka tana cewa "tunda yusufa ya rasu dama nake shan wahala a duniyar nan, daga kai har 'ya yanka bakwa tsinanani da komai, ni ke yi ma kaina duk bukata, Abba ya bude baki yana kallonta ya ma kasa cewa komai, shi din ne baya mata komai? Gnin ta dage sae rera msu kuka take ne yasa ya shiga bata hkri, tce "hka kawae baxan kyautatawa aminiyata ba jikarta xatayi aure, kuma nasan idan na tambayeka ba bani xakayi ba," Abba ya girgixa kai yana mamakin uwartashi, duk juma'ah sae ya bata dubu goma bayan abubuwan da yake siyo mata duk karshen wata sannan ya damka mata dubu ashirin ko tana da bukatar kudi, amma yanxu kiri-kiri tace bbu mai taimaka mata a duniyar nan sae Allahnta, komai ita take ma kanta. Abba yace "to shknan inna, Allah yasa hkn shine mafi alkhairi, kudaden sun isheki de ko? Ta dan fara kame kame tana goge kwalla tace "ni idan san samune akara min dubu hamsin, ko kuma dari ma." takaici yasa abba gyada kae kawae, ya dubi Aliyu yace anjima ka ciro mata dubu hamsin Ali, xan bka, "tab! Ai ni abba accnt dina ko dubu goma bai kai ba ina ga ma." ... Inna ta galla masa harara tace "Allah ya dauwamar dasu a hka," Haisam yace "anjima xan ciro na kawa maki inna." nan ta dinga sa masa albarka, abba yyi mata sallama ya fice daga palon nata cike da jin haushin hali irin nata, Aliyu ya bi bayansa yana cewa "wannan ai sata kiri-kiri ne kawae, daga an baki ajiye sae ki maidashi naki" bai jira me xata ce ba ya fice da sauri yana dariya. Haisam na fitowa daga palon innar umma ta aika a kira mata shi yaje, nan kuwa ta balbalesa da masifa tana cewa" kai dinnan soko ne wllh, Aliyu ya fika wayo nesa ba kusa ba, kana tunanin idan ka dauki kudin naka har dubu hamsin ka bata Alhaji bka xai yi ne? Kai dae bn san wani irin yaro bne Allah ya bani, don meyasa baxakayi koyi da Aliyu ba, duk ka bi ka tare gurinta sae kce ta asirce, wllh idan baka yi gaggawan sauya wannan mugun halin naka ba sae na saba mka" haisam ya girgixa kai cike da takaicin hali irin na uwartasa yace "Allah ya kyauta! Sannan yafice a fusace. Shi kam Aliyu hajiya yaba masa ta dinga yi tana sa masa albrka, shi dae bai tanka mata ba. Da yammacin ranar Haisam ya kaita gidan aminiyartata bayan ta shiga kasuwa tayi kaca-kaca da kudin, a dole ita wae sae ta kyautatawa kawartata tunda bikin jikarta ce. Su hajiya kam sun ji ddin xuwan inna gidan bikin don kwana biyar tace xata yi, ko ba komai xasu dan samu sarari a gidan su sheka tsiyarsu yanda suke so. Intisaar na daki wajajen karfe goma na safe tana duba wani Novel na turawa taji hayaniyarsu hajiya a tsakar gidan, ba shiri ta fito ta tarda su hajiya sun saka momynta a gaba sae maganganu suke gya mata fadila na taya su, "idan banda rainin wayo tun asubar fari take ta facakala da ruwa sae kace ita daya ce a gidan, ynxu idan ruwan ya dauke mu da wanne xamuyi ayyukan mu, mun xo muna mata mgna kuma ta maida mu mahaukata, to dae mai daure maki kugu a gidan bata nan, idan kikayi wasa...." xainab ce ta karaso wajen da sauri ita ma tana cewa hva hajiya meye yyi xafi hka da sassafe xa ku sa momy a gaba kuna..." kyakkyawan mari hajiya ta watsa ma xainab din tana cewa "wuce ki bni waje munafuka kawai, dama tun ba yau ba kike nuna ni ba komai bace a wajenki, idan bnda hka taya xa a maida ni mahaukaciya baki xo kin tsaya min ba xaki gya min mgnar bnxa, baki ga yanda fadila take yi bne don ubanki," intisaar ta kalle momynta da ta tsaya tana kallonsu kawae bata ce komai ba, umma ta hankade xainab tana cewa bace mana da gani mara xuciya kawae warce bata san ciwan kanta ba. Girgixa kai momy tayi kawae taci gaba da wankin da take yi a bakin famfon, hajiya ta fixge bokitin a fusace ta xubar da ruwa da kayan dake ciki sannan tasa kafa tayi ball da sauran bokitan tana cewa "don babanki baxa kiyi wankin nan ba yau wllh, mu ma muna da bukatar ruwa" umma ta kashe famfon tana kwadawa rahma kira ta kawo mata kwado su kulle. Intisaar ta goge hawayen idonta ta dubi momynta da ta tsaya kallonsu kawae ba tare da tace uffan ba, tace "momy ki bari anjima xan je waje na debo makii ruwan wankin, xo mu tafi" ta fara jan hannun momyntata su bar wajen, momy kam kasa barin wajen tayi, ta xubawa fadila dake ta faman xaxxaga mata xagi tana cewa "mutum ya xame mana annoba a gida, kuma idan ana magna ya dinga yi kmr kurma don tsoro, wllh hajiya ni kawae da kun bari watarana na lallasa ta na nuna mata....." ji kke tass! Momy ta xuba mata tagwayen mari masu rai da lfya, hava wa! Nan fadila ta gigice ta fasa ihu don batayi xaton marin ba, cike da mamaki hajiya da umma suka dinga salati suna cewa ita fadilar kika mara? Hajiya ta fixgo fadilar tace "xage ki rama fadila, wllh sae kin rama," umma kam tuni aka shige gida da gudu anje shirin dambe, don tace wllh sae ta rama ma 'yar ta. Fadila ta dage xata mari momyn, intisaar ta fixgota da karfi tana cewa "ke yar karamar 'yar iska, ni xakiyi facing ba momyna ba," nan intisaar ta dage ta dinga xuba mata mari tana tana cakume da kwalar rigarta. Nan fa gida ya hautsine, umma ta fito da gudunta bayan ta canxa kaya, tayo kan momy da gudu tana cewa "ae yau sae dae ni ko ke?" tam nan fa momy ta xage ta kai umma kasa suka dinga cin dambe. Su rahma da kursum suka hadu suka dinga dukan intisaar din da taki sakin fadila har ynxu bayan ta kaita kasa ta haye kan ruwan cikinta tana jibgarta iya karfinta. Hajiya na ganin an kai umma kasa ana ta nakada, ta fice waje da gudu tana kiran jama'ah su xo su ga xainabu xata kashe Shafa. Xainab na shiga daki da kukanta dama abba ta kira amma yaki xuwa, ya Haisam ya tafi kaduna tun jiya, don hka kawae sae ta kira Aliyu tana kuka ta gya masa, sannan ta fito taga irin damben da ake ci, kuka ta dinga yi sosae ta ma rasa abinda xata yi ga muryar Hajiyrsu can a wje tana aibanta momy, mata suka dinga tururuwa cikin gidan duk da wsu gulma ya shigo dasu, ihsan ma kuka ta dinga yi a kusa da xainb tana cewa "Anty kice momyna ta bari. *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** " da kyar matan suka kwace umma a hannunm momy, sannan aka raba su intisaar shi ma da kyar don intisaar komawa tayi kmr mahaukaciya duk tayi ma fadila kaca-kaca hka ma kursum dake.. Xainab ta karasa kusa da intisaar da hanxarinta bayan an rabasu, ta fara janta ixuwa palonsu, fadila kam ihu ta dinga yi tana fixge fixge daga rikon da akayi mata wae a barta sae ta kashe intisaar yau, momy ta ja bokitin ta ta tara a famfon tana cewa "kuma wanki yanxu na fara, bnga uban da ya isa ya hanani ba, kuna tunanin shirun da nake maku tsoro ne, wllh duk wanda yace baxae kame girmansa ba a cikin ku xai ko sha mamaki." rirrike hajiya aka shiga yi wae sae tayi ma momy duka, hka ma umma ko kunya bbu. Wata yar dattijuwa da tashigo gidan ta dube momy tace "to ke 'yar nan tunda gaba suke dake ki bari anjima kiyi wankin mana, ina ce sunce aiki suke son suyi da ruwan su ma" momy tace "ki bari kawae baaba wllh munafukan mutane ne, idan bnda hka famfofin gidan nan sun kai biyar pa, kuma ko wanne na da nasa pampon a bangarensa, nan bangarena ne amma sbda neman mgna suka kwaso jiki suka xo wae baxanyi wanki ba, kuma wllh baaba tank din gidan nan babba ne, ko xan kai washegari ina wanki bbu abinda xae ragu a ruwan amma dayake jirana sukeyi shi yasa nayi laifi, toh bari kuji, wllh tllh daga yau duk shegen da yace xae sake takani a gidan nan sae ya sha mamaki." hajiya tace "mu kke gyawa magana hka xainabu, dama ashe kina mgna hka amma don munafurci idan kinga Alhaji sae ki dinga yi kmr na kirki? Don Allah ku sakeni na gwada mata hnkli." momy tace "ku kyaleta don Allah" umma ta dinga dura mata ashar ta uwa ta uba tana daga inda take, don bata sake gigin matsowa kusa da ita ba, a dai-dai lkcn Aliyu ya shigo gidan, ya girgixa kai cike da takaici ya jingina gefen gate din rungume da hannuwansa yana kallonsu, muryar momy yaji tana cewa "don Allah don Annabi ku kyaleta ta dokeni, wllh tllh Aisha sae kinyi da kin sanin sani na, don laga-laga xan maki kuma ba lallai ne mijin ki ma ya gne ki ba. A fusace Aliyun ya karaso cikin tsakar gidan yana kallonsu daya bayan daya, basu ma san yashigo ba, ya dubi fadila da bata da maraba da hauka gashin nan yyibuya-buya, daga ita sae leggings, intisaar ta dube fadilar dake xaginta ta uwa ta uba tana kiranta da 'yar tsintuwar innarsu, tace " duk da hkn dae ban xage ina karuwanci ba, na fita tun asuba na dawo karfe takwas din dare." fadila ta kara rudewa ta shiga galla wa masu rikonta cixo wae sae sun saketa ta mata duka, sae kace ba ita aka kwata da kyar daga hannun intisaar din ba ynxu, Aliyu ya karaso wajen ya sa kafa ya kwashe fadilar ta xube kasa sannan yashiga ball da ita yana cewa "yau xaku ci ubanku gaba daya, go down on ur kneels, i said go down on ur kneels." ya fadi cikin tsawa sannan yyi kan intisaar din da tuni ta juya a guje xata bar wajen ita ma ya cafkota ya watsa mata mari lafiyayye, momy ta karaso inda yke da sauri tana cewa "kai! Kai! Wllh kar ka kuskura ka taba min 'ya, cika ta, ta fixge hannunsa daga rikon da yyi wa intisaar din, cikin tsawa tace mata shiga ciki, ta ja ihsaan ma suka bar wajen" binta yyi da kallon mamaki, ya juya kan su hajiya dake ta cacan baki amma an rasa wanda xae tunkareta yace "wllh hajiya kina bni mamaki, ynxu meye amfanin irin wannan abun, don me baxa ku kama girmanku ba, dube yanda yar cikin ku tasa ku gaba tana gaggaya maku maganganu, sae faman kumfar baki kuke," kai Aliyu kasan me ya faru ne? Kasan irin abinda tayi ma umma?"hajiya ta fadi tana xaxxaro ido, yyi tsaki yace koma me tayi maku kuka siyar wa kanku. Ya dube su kursum da har ynxu suka ki yin shiru ya daka masu tsawa yana cewa "bna son naga ko wani dabba a tsakar gidan nan ryt now, get out" da sauri duka suka watse suka yi sashinsu, shima yyi nasa bangaren ya bar umma da hajiya a wajen.. Gaba daya mutan gidan sun hallara a falon Abba washegari da safe, Momy na xaune kan 1seater fuskar ta a daure ta xuba ma plasman ake manne jikin bango ido, intisaar na gefenta a kasa a xaune, hajiya da umma na xaune a 2seater suma rai a hade, sauran 'yan matan ma gaba daya sun nemi gu sun xauna a palon, ihsaan kadae ce ke gefen abbanta a xaune, Aliyu ya shigo da sallamarsa a dalilin kiran da abba ya aika ayi masa, ya nemi gefe shima ya xauna. Abba yyi ajiyar xuciya ya dubi intisaar yace "fateemah ki gya min abinda ya faru a gidan nan jiya bayan na fita" nan intisaar ta koro masa duka abinda ya faru a jiyan, ya jinjina kai yace "ikon Allah" hajiya ta yi saurin cewa "kaji munafuka amma ai baki gya masa irin fitsarar da uwartaki ta dinga mana ba" abba ya daka mata tsawa ransa a bace yace "ki shiga hankalinki." ta ja bakinta tayi shiru tana hararar sa. Abba yyi shiru sannan ya nisa ransa a bace yace "xainab ban san ki da irin wannan halin ba, amma gskya jiya kin ban mamaki, a tunanina ko da ace abinda yafi xagi shafa ta maki bata cacanci ki rama ba bare har ki hau ta da dambe ba, kinga kina da laifi a nan tunda dae shafa ba sa'arki bace, don me baxaki jirani na dawo ba ko ki kirani a waya? Har xagi dubi tsabagen idon Aisha baki ji kunyar 'ya yanta ba kice mata karuwa.?" tsam momy ta mike tayi masa wani irin kallo tayi hanyar fita daga palon ba tare da ta ce komai ba, kiranta abba ya shiga yi amma ko waiwayowa bata yi ba har ta fice daga palon. Hajiya tayi murmushin takaici tace "ka gani wa idon ka ko? Wllh jiya na dde ina naxarin anya kuwa xainabu ce wannan, rirrike ta fa aka dinga yi xata min duka bayan an rabata da umma. Umma ta tabe baki tace "uhum ae ni naga abun mamaki jiya, yarinyar da mutum sae ya rantse ya dada rantse wa yace ko kuda baxata iya kashewa ba, amma ashe duk wannan shiru shirun da take yi don taga inna na nan ne, jiya ta nuna mana ko ita wacece." Aliyu kam tunda ya shigo falon yake ta daddanna wayrsa bae ko daga kai ba. Abba ya dube su intisaar din gaba daya yace "daga yau na sake jin abu makamancin hka ya faru a gidan nan wllh tllh sae na karya mutum, kuma bna son naji wata magana ya fita daga nan har yaje kunnan inna, idan na kama mutum da karya wannan dokan sai na saba mashi kwarai da gaske, ku tashi ku ban waje shashashan bnxa kawai" duka suka mike suka bar palon, intisaar kam jikinta yyi sanyi sosae. Hajiya tace tana nuna intisaar "har da 'yar mitsitsiyar 'yar nan, ta dubi tsabagen ido na tace min mayya" sae kuma ta fashe da kuka tana girgixa kai tace amma bbu komai ai tun farko idan muka ce mka ga abinda xainabu tayi bka yarda ynxu kam ai ka gani da idonka, Aliyu ya mike yana kallon abban nasa yace "kayi hkuri abba," sannan ya fice. Nan hajiya da umma suka dinga aibanta momy, hajiya sae matse kwalla take, abba kam tv ya xuba ma ido bai tanka masu ba, umma tace "har ca tayi wae fadila ba 'yar ka bace karuwan....." tsawa abbaya daka masu ya mike yana cewa "ku fitar min a palo don Allah, sannan ya shige bedroom." hajiya ta bude baki hka ma umma, hajiya tace "da yake ran matan so, kuma yar gwal ya bace dole duk ka fice hayyacinka ae. " nan da suka gaba babatunsu su mike suka fice daga palon kowa da takaicinsa. Intisaar na xaune kan darduma bayan ta idar da sllhr isha'i, Abba yyi sallama ya shigo palonnasu, ta ce "sannu da xuwa abba, ina yini" yace "lfya lau fatima ina momyn taku?" tace "tana cikin daki" bai ce komai ba ya shiga dakin da sllma, ba kasafai Abba ke shigowa bangaren matan nasa ba sai da babban dalili, ta mike ta kwashe kwanukan da suka ci abinci ta fita dasu ta wanke don momynta ce tayi girki, sae da tashiga kicin ta kwaso sauran kwanukan wanke- wanken mutan gidan sannan taje bakin famfo tana wankesu don tana tsoran wankesu a kicin kar 'yan gidan su rutsa ta, tun da safe dama momy bata barta ta fito ba, ita tayi duka ayyukanta sae xainab da ta fake idon hajiyarsu ta dan kama mata. Tana gama wanke kwanukan ta kwashesu tayi kicin din don ta ajiye ko wanne a maxauninsa, Aliyu ta gani tsaye yana hada coffee, ta juya da sauri xata bar wajen taji yace "one more step, yhu are in trouble." mutuwar tsaye tayi a wajen xuciyarta na dukan uku- uku, yau ta shiga uka dukanta xai yi tasani " ya karaso inda take ya xagayo ya tsaya gabanta yana mata wani irin kallon, tuni kwalla ya taru a idonta, yyi murmushin mugunta yace "yaushe kuka fara samun liver a gidan nan daga ke har uwarki," amsar ki kadae xata ceceki yau a nan, idan ba hka ba wllh tllh sae na fasa kanki a nan wajen, save my tym ki bani amsata, am ol ears. Ya fadi da tsawa " kuka ta fara yi tace "ni dae don Allah don annabi kayi hkuri ka....." muryar Abba suka ji yana cewa "wat's goin on in there?" ya fadi da xolaya, Aliyun ya kirkiro murmushi ya fara kame-kame, No Abba.. Kawae taimaka mata nke ne... Sae kuma ya karbi kwanukan dake hannunta ya fara kkrin ajiye su inda suke, Abba yace "uhum ok yyi kyau hkn, idan ka gama kaxo ka sameni, we hve an issue 2 discuss" Aliyun yace "yes sir" batare da ya kallesa ba sannan abba ya bar wajen, da gudu intisaar ta juya ta bar wajen bayan Abba yyi gaba, wae juyawar da xai yi sai ganin wajen yyi wayam ba kowa, ya cije lebe cike da takaici sannan ya ajiye kwanukan hannunsa ya juya ya bar kicin din yana tunanin irin abinda xae mata idan ya kamata. Bayan kwana biyu komai ya dawo nml a gidan, da momy ta dauki xafi sosae amma abba na xuwa ya bata hkuri sae ta ajiye fushin da tayi da tace masa komai ae ya wuce, ya ji ddin hkn sosae don idan ba wannan karan ba ma bai taba ganin bacin ranta ba kuma ya gano ita ke da gskya bayan yyi bincike sosae a kan lamarin, su hajiya kuwa ya je yyi masu kashedi mai girma akan su fita harkar matarshi, idan xaman gidan da suka je sukayi na kusan wata hudu bai ishesu ba to xasu koma ne, hkn yasa suka kame kansu don sun san shi sarai. Ranar laraba inna ta dawo gidan da mota shake da kaya, har gida aka kawota aka ajiye, su intisaar da xainab suka dinga shigowa da kaya kowa na murnar dawowan ta, ita kuwa baki har kunne ta dinga fadin irin yanda aka dinga karramata a gidan bikin don inna akwae son girma, bakin kofarta su hajiya suka tsaya sukayi mata sannu da xuwa sama-sama suka yi gaba. Ta ja dogon tsaki tace "munafukan bnxa kawae da alamar ma basu yi farin ciki da dawowa na ba." intisaar dake ta faman bubbude kayan da suka shishshigo da bata tanka wa inna ba. Momy ma taxo tayi mata sannu daxu suka danyi hira sannan ta wuce, falon ya rage daga ita sae jikokinta tana ta faman kullawa kowa tsarabarsa a leda. Intisaar ta kai nasu gida, hka ma xainab da kursum. Fadila ta shigo gaida inna, inna ta saka sallati tana kallon fadilar tace "hatsarin mota kika yi fadila?" ta tambaya ganin yanda bakin fadila ya kumbura da fuskarta, xainab dake cikin bedroom tana gyara ma inna daki, ta toshe bakinta ganin dariya na neman subce mata. Fadila ta harari innar tace "hatsarin jirgi nayi ba ta mota ba." ta juya ta fice fuuuu. Inna ta kwashe da dariya tana cewa "ikon Allah," xainab na gamawa ta fito tana dariya tace "inna ki min alkawari idan na gya maki maganar nan xaki barshi a cikin ki" inna tace "hva Abu, sae kace wata yarinya sae naje ina cewa ga abinda xainab tace min." xainab tace "yauwa inna." nan xainab ta xauna ta xayyane wa inna abinda ya faru kwana hudu da suka wuce a gidan." bata kai karshe ba inna ta mike tana cewa " kut! Ae yau sae sun gya min ko pampopin gidan nan na ubansu ne, sae sun gya min me xainabu ta tsare masu a gidan nan" xainab ta mike a rude tana cewa "nashiga uku inna don Allah ki rufamin asiri abba yace kar wanda ya gya maki, ballani xai yi wllh" shi bukar din yace kar a gya min? to xai dawo ya sameni shima," inna ta fadi a fusace ta fice daga palon." da gudu xainab tayi sashinsu ta shige bathroom ba tare da ta bari hajiya ta ganta ba jikinta na bari. Inna ta karaso tsakar gidan cikin daga murya tane cewa "ina munafukan gidan... To don ubanku ku fito ku gya min ko ubanku ne ya dasa ma da'na famfofi a gidan, ku fito ku gya min ko nairan ku nawa ne a ciki na biya ku. Sbda me xaku sa min 'ya a gaba a cikin gidan nan, uban me ta tsare maku? Ku fito ku gya min me xainabu ta tsare maku nace matsiyata " cikin daga murya inna ke ta xuba masu rashin mutumci. Momy ta dube intisaar fuskarta daure tace "don ubanki sai da kika je kka gyawa inna wannan mgnar bayan abinda....." intisaar ta xaro ido a tsorace tace "wllh momy ban gya ma inna komai ba, tana bani tsarabar mu ae ban sake komawa ba ma." abin ya daure wa momy kai, to waye ya gya ma inna wannan mgnar? Hajiya kuwa kasa xaune tayi sae kaiwa take tana komowa a palonta, ynxu xainabu sae da taje ta gya ma tsohuwar nan wannan mgnar. Hka ma umma dake ta lekar innar ta taga da 'ya yanta, tsinuwa kam sun sha shi ba adadi . Ganin inna taki barin tsakar gidan ne tana ta masifa yasa momy ta fito ta dinga bata hkuri ta koma sashinta, amma kememe inna taki ta dinga xunduma masu ashar tana cewa ae yau sai tasa sun bar gidan nan, momy tayi sumsum ta koma sashinta ganin ba sauraranta inna xatayi ba. Tun a kofar gida haisam da Aliyu suka dinga jin muryar inna kmr speaker, Aliyu ya tabe baki ya koma mota ya ciro apple dinsa da ya manta a ciki, haisam kadae ya karaso gate din ya shiga gidan ransa a bace, wannan wani irin masifa ce hka, kullum sae anji hayaniya a gidansu sae kace makaranta, yana shiga gidan ya ga irin rashin mutuncin da inna ke xubawa a gidan ya juya ya bar gidan kawai. Dariya Aliyu yyi ganin yanda Haisam ya fito daga gidan, ko kallonsa Haisam bai yi ba ya shige motarsa yyi gaba. Aliyu ya shiga gidan ya dauki farar kujerar roba ya xauna gefen wani flower yana ta kallon inna yana cin apple dinsa with much interest. Tana ta masifa har da kukanta, "wllh kwado xan sa wa duka famfofn gidan, duk shegen da xae yi amfni da ruwa yaje waje ," tana kai wa nan ta fice daga gidan tana gunjin kuka. Dariya Aliyu ya dinga yi har da buga kafa, hajiya ta fito jin muryar dan nata, ta rike haba tana cewa "ka ga makirci ko Ali, ynxu bayan duk abinda Alhaji yace sae da wannan tsinanniyar matar ta gya wa wannan mayyar tsohuwar ko?" shi dai bai ce komai ba yana ta cin tufarsa. Umma ta fito ita ma tana cewa " wannan anyi makirar mace....." shigowar inna ce ta sa su yin tsit. Kananan kwadunaye inna ta shigo da har guda biyar, su ka bita da kallon mamaki. " idan akwae shegen da ya isa ya matso kusa da famfofin da na ya gani." hka inna ta dinga dasa wa famfofin kwado tana mita, sashinsu intisaar da nata kadae ne bata je ba, Aliyu binta yke tayi da kallo har ta gama, ta dawo tsakar gidan ta dauki kujera ta xauna tana girgixa kafa. Sumsum su hajiya da umma suka shige gida, Aliyu ya mike yyi hanyar kicin sae gashi ya fito da tabarya, yyi hanyar daya daga cikin taps din, bugu uku yyi ma kwadon ya balle, inna ta taso da gudu tana cewa xan ci ubanka wllh idan ka sake shiga gonata Aliyu.... Tsawa ya daka mata yana cewa "to me kke nufi hajiya, baxan wanke hannuna ba kuma ko meye?" yyi tsaki ya bude tap din yana wanke hannayensa, ranar dae hka Aliyu ya maida inna mahaukaciya a tsakar gidan, tana yi, yana ta kyalkyale dariya, hkn yasa ta dinga rusa kuka wae bukar take jira a tsakar gidan. Abba yyi jigum yana sauraran maganganun uwartasa da bae da ma'ana kuma bai da tushe, ya jira har ta kai aya sannan ya mike yana kallonta rai bace "to wae baaba meye na tada maganar da ya wuce kwana da kwanaki, meyasa kike yin hka ne fisabilillahi, ynxu ca akayi maki xainab din bata hkura bne ko kuma su hajiya basu amsa lafin nasu bne?" inna ta marairaice fuska tace "to ni ina nasani, ca nke ae maganar tana nan ne har ynxu," Abba yyi tsaki yace "wannan wani irin abu ne don Allah, ko ma bai wuce ba ina ruwanki cikin maganar, tsakanina ne da iyalina," inna dae sae wuri-wuri take da ido, su hajiya kmr su yi shewa don murna, ya dube gaba daya 'ya yan nasa dake falon fuskarsa a tamke yace "cikin ku waye ya gya ma baaba wannan maganar? Kuma duk wanda yyi min krya sae na yi mugun saba masa wllh" yasan momy baxata taba gyawa inna wannan mgnr ba duk da su hajiya sun ce masa ita ta gya wa innar amma bai tanka masu ba, don yasan wacece ita. nan xainab ta dinga cunkulin inna alamar ta rufa mata asiri jikinta na bari, hankadata inna tayi tana cewa "ke don ubanki ki rabu dani sae shisshigeni kike yi sae kace yarinya," xainab saura kadan ta saki fitsari don ca take inna tona mata asiri xatayi. Aliyu ya daka ma kanninnasa tsawa yana cewa "ba magana ake maku ba wawaye kawai," inna ta kalle Aliyun kmr me naxari, can sai tace "to ni Aliyu ne ya gya min wannan mgnar ba kowa ba." Aliyu ya firfito da ido yace "ni inna," ta galla masa harara tace "munafuki kawai, shine ya gya min bukar, ko karya nayi mka?" Abba ya juya yana kallon Aliyun ransa ya dada baci, Aliyu xai yi magana abba ya daka masa tsawa yana cewa "karya knan tayi mka," inna tace "Atoh dae, ina xaune yaxo ya sameni ya gya min, intisaar ae tana wajen lkcin, ko krya nayi intisaar?" ta tambaya tana kallon intisaar din. Intisaar tayi narai-narai da ido cikin karkarwar murya tace "don Allah don annabi inna ki rufa min asiri ni wllh ina gidanmu lkcn, bn san kun yi ba" inna tace "au hka ne kuma, daga ni sae shi a palon lkcn." haisam ya kalli Aliyun da ya ma kasa cewa komae sae kada wa da idonsa yyi yana kallon innar ko kifta ido baya yi, sae dariya ta subce masa, abba ya juya yana kallonsa a fusace, ya mike yyi saurin barin palon yana yar dariya, shi dae yasan inna sharri tayi ma Aliyu don Aliyu bai da surutu kawae dae yasan ramuwar irin abinda Aliyu ke yi mata a gidan tayi ne. Ranar kuka ne kawae Aliyu bai yi ba, don wanki babban bargo Abba yyi masa "tashi ka bni waje karka sa na watsa mka mari, abinda yaci ace kanninka ne sukayi sai gashi wae kai da knka kayi" Abba ya fadi cikin bacin rai bayan yyi fadan har ya gaji, Aliyu ya mike kmr xaki ya fice fuu daga palon, inna ta rakasa da cewa "munafuki kawae." hajiya ta mike a fusace ita ma ta fice daga palon, sae bayan ya fita su kursum suka fashe da dariyar da suke hadiyewa tun tuni, inna ma ta taya su dn ta rama iskancin da ya dinga mta a tsakar gida jiya, har xainab sae da tayi dariyar, intisar kadae ce bata yi ta ba ta hade rai. Intisar na tsakar gda tana taya xainb tsifan kanta aka bude gate din gidan gaba daya suka maida hnklinsu wurin gate din su ga wanda xae shigo, Aliyu ne da safeenah su ka shigo gidan, xainab tace "tab, amma wannan yarinyar jaka ce mara xuciya, ynxu sae da ta sake xuwa gidan....." da sauri intisaar ta katse ta da cewa "kinga ni ba ruwana ki bar xancen nan xainab" bangaren hajiya suka wuce bayan intisaar da xainab sun gaisheta tayi masu bnxa, shi ko ya watsa masu harara. Xainab ta fashe da dariya a hankali tana cewa "ina ma Allah ya kawo inna nan mu ci dariya wllh," intisaar tace "ki dae ci dariya amma bnda ni" xainab tayi dariya tace "shegiya matsoraciya, dubi fa kayan da tasa yau har gwanda na ranan nan," intisaar ta mike tace "kinga idan baki son tsifan nan ne na wuce don ni bbu ruwana wllh karki ki jaxa min" xainab ta fixgota tana dariya tace "to yi hkuri nayi shiru xo ki karasa min." suna wajen har bayan kusan awa biyu sannan suka fito, hajiya sae wangale baki take yi tana cewa "Allah yyi maki albarka safeenah, mun gode sosai, ki gaishe min da hajiya kice sae naxo, umma ma tafito tana cewa "Allah dae ya nuna mana wannan abun arxikin" leda kato su hajiya da umma suka cika mata da tsaraba khadija na rike da ledan kmr xata shige jikinsafeenar dake ta murmushi tana gdya, hajiya ta hade rai ganin xainab da intisaar tace "don ubanki kin xo kin gaida antynki ko sae na taka ki a nan," ta galla wa intisaar harara tace "tashi ki ba mutane waje munafuka kawae." da sauri intisaar ta mike ta bar wajen tayi sashinsu, safeena tana yatsine fuska tace "wae hajiya wacece wannan yarinyar?" hajiya ta tabe baki tace "agolar gidan ce" safeenah tace "tabdijam" umma tace to ya muka iya. Aliyu ya fito da makullin mota don maida ta gida xai yi yace "ta yi maki wani abu ne dear?" ta tabe baki tace "muje kawae" har gate hajiya da umma suka rakota suna sa mata albarka, hajiya tace "ki fa ba wa hajiya sakona," tace "xan bata hajiya" sannan suka wuce ita da Aliyun. Umma tace "gskya amintakan ku da hajiya mairo yyi, tunda har ta dauki tilon 'yar ta xata ba danki," hajiya tayi murmushi tace "ae ni bbu abinda xance da mairo, baki ji yanda naji ba ran da ta kirani take gaya min irin rashin mutuncin da tsohuwar nan tayi ma safeenah da bama gidan, wllh naji takaici sosae" umma tace "to ae laifinsa ne, don me yasan bama gidan xai daukota ya kawo ta bayan yasan yan hassada ne a gidan, idan kin bibiya ma xainabu ce ta xuga innar tayi ma safeenar hkan." hajiya tace "ae ba takanas ya dauko ta ya kawo ta gidan ba, hanya ce ta biyo dasu ta nan shine yace bari ta gaida kakarsa, ae tasan bama gidan." muryar inna da suka ji tana kwada wa fadila kira ne yasa suka yi tsit, kursum tace "bata nan" inna ta rike haba tace "ohh ni rahmatu yarinya ta maida kanta gantalalliya kmr akuya anki tsawatar mata, amma ba laifin kowa bne, na bukar ne, ae da ya aurar da ita da duk hka bata faru ba." tayi gaba tana ta mitocinta. Hajiya da umma suka tabe baki, umma tace "randa wannan tsohuwar xata mutu ae sae na xuba ruwa a kasa nasha," hajiya tace "ae ba ke kadai ba shafa." Abba yace "gani inna," bayan yaje kiran da mahaifiyar tasa ke masa. Dama bukar dubu ashirin xaka bani nayi ma yaran Nafisa tsaraba don gobe xanje gidanta, Abba yace "to inna bari haisam yaxo ya ciro maki." tace "yanxu fa nake so ni dae wllh, don bn yarda da wannan wayon naka ba, sau dayawa hka kke min" Abba ya jin jina kai yace "ynxu xai kawo maki baaba." cike da jin haushi yyi maganar ko sati uku ba ayi ba da ta saida masa fili sannan ya kara mata da dubu hamsin amma har tana tambayar wani dubi ashirin din. Haisam tasa ya kaita sukayi shoppin din, ta jida kayan kusan dubu talatin, dole shi ya cika sannan ya maido ta gida. Washegari ta samu Abba wae ya samo wanda xai kaita, haisam baya nan, don hka dole yasa a kira masa Aliyusukayi Aliyu na shigo wa palon Abban nasa ya nemi gu ya xauna ya gaida shi a ladabce sannan yace "gani Abba" Abba ya hade rai yace "ka gaida inna ne yau?" inna ta tabe baki tace "ae ni rabon da Aliyu ya gaida ni tun ran da na ce shi yyi min wannan gulman" Aliyu ya xaro ido yace "kai inna ki dinga jin tsoron Allah mana" inna tayi salati tana kallon dan nata tace "wllh Bukar tun ranar Aliyu ko bangarena baya xuwa, ko ya gan ni sae ya kauda kai." Abba ya dube Aliyun yace "gidan nafisa xaka kai ta anjima," da sauri inna tace "xuwa karfe sha daya dae" Aliyu ya mike yana kallon Abban nasa fuskarsa a tamke yace "gskya Abba ina da urgent meetin da xan wuce ynxu...." Abba yace "ni kke gayawa hka?" ya kauda kansa bai ce komai ba, inna kuwa ta dage da cewa "wllh shi xai kaini, dolensa sae ya kaini, Allah kai xaka kai ni Aliyu" Aliyu ya juya yana mata wani irin kallo kmr ya maketa don haushi. "iyye yaro bashi da mutumci ba shi da kunya sae kace ba jininka ba Bukar, wllh bae yo halinka ba, Haisam kadae da xainab suka yo halinka a gidan nan" abba yyi murmushin takaici ya kalli Aliyun yace "je ka kawai." Aliyu yyi maxa yace "ohk naji xan kai ki ki shirya" inna tace "kaci sa'a wllh" fice wa yyi ba tare da ya bari sun hada ido da abbansa ba. Tare da intisaar da xainab inna xata, amma hajiya na ganin hka sae ta tura xainab gidan wata kawarta wae ta karbo mata sako, duk don kar ta bi innar, don tasa xainab ko ta hanata xuwa ba ji xata yi ba shi yasa ta bullo da hkn. Intisaar bata san Aliyu xai kai su ba da baxata fara bin inna ba, wae sae da suka fito tukunna inna ta fara kwada wa Aliyu kira a tsakar gidan wae ya fito sun shirya. Intisaar ta dafe kirji tace inna shi xai kai mu dama, nayi xaton adai- dai ta sahu xamu hau ae, inna harareta tace "ka ji shirme, gidan dan nawa da motoci xan hau motar haya, inna ta sake kwada wa Aliyu kira sae gashi ya fito fuskarsa daure yana sanye da polo fari da baki, da 3quatre fari kal, shi dae kam yana san 3quatre, intisaar ta fadi a xuciyarta, inna ta xabga salati tana tafe hannu tace "uban wa xaka bi a hka yaron nan?" Aliyu ya hade rai yace "kmr ya wa xan bi a hka?" tace "nashiga uku ni Rahmatu nace uban wa xaka bi da wannan dangalallen wandon?" yyi tsaki ya ce "idan xaki ki wuce na kai ki, don ina da gurin xuwa hajiya, meye ruwanki da abinda nasa" inna ta girgixa kai kmr xatayi kuka tana cewa "la! Wlh baxan je da kai a hka ba kaji min gantalallen yaro." Aliyu ya tabe baki yace "to Allah ya raka taki gona, dama ni bnyi niyar kai ki ba ae," sae ma a lkcn ya kula da intisaar da ta labe a gefen innar, duk wannan abinda akeyi su hajiya na labe a taga suna lekowa, hajiya taji ddin yanda dan nata yyi, inna ta lalubo waya tana kallon intisaar tace "kira min bukar" da sauri intisaar tace "bn iya ba ni xainab ce ta iya."a fusace inna tace "amma kin ji haushi kuwa" nan ta dinga kwadawa fadila kira taki fitowa, sae tayi waje don neman wanda xae ciro mata nmbr dan nata, a dai-dai lkcn Abba ya kirata, ta dauka da sauri tana cewa "Bukar ne?" Abba yace "nine baaba kun tafi ne" tace "ina fa, wandon shaidanu yasa wae xae bini dashi, irin wandon nan dae da ya saba sa wa a gida" Abba ya kashe wayan ya kira a Aliyun, kasa daga wayan yyi ji yake kmr ya makure inna don takaici, can dae ya daga bai ce komai ba har Abba ya gama sannan Abban ya kashe wayan, idonsa yyi jajur, ya juya fuu ya shige ciki, inna tace "Atoh dae." bai jima ba ya fito da dogon wando yyi hanyar motarsa inna ta ja intisaar suka bishi, tana cewa "hka kawae ya janyo mana kallo a gari, yaro sae kace kafiri." shi dae bai tanka mata ba har ta ja intisaar suka shige motar, intisaar dae jikinta bari yake, don bata bari sun hada ido dashi ba, "to uban wa kuka cewa da wannan yarinyar xan kai ku?" ya tambayi innar fuskarsa a murtuke, inna tace "ubanka muka cewa" to bata isa ta xauna baya ba na ja ta don bata kae wannan matsayin ba tun wuri ta dawo gun da ya dace ta xauna, gaban intisaar ya fadi ta kalli inna, to ina xata xauna, ita fa wannan tafiyar ba dole sae ta koma gida, dama don taga tare da inna ne kuma baxai iya yi mata komai ba don inna baxata bari ba shiyasa ma bata ce ta fasa ba, amma da ace da su xainab ne to fasawa xatayi, inna tace "to bbu gun da xata xauna da ya wuce nan, bai sake cewa komai ba don baya son magana, ya ja motar suka wuce. A hanya hka inna ta dinga magana a hnkli a kunnen intisaar, intisaar dae hadiye dariyarta kawae take don bata ma san me inna ke cewa ba ta dage sae mutsu-mutsu take mata a kunne, ita a dole xata ba Aliyu haushi, kallonsu kawae yake ta madubi, intisaar ta lura da hkn sae ta shiga taitayinta, yyi tsaki kawae ya kara volume din wakar dake tashi a motar, a hankli intisar ta matso kusa da inna take nuna mata hanyar gidansu faruuq cikin murya kasa kasa take magana, inna ta bude murya tana cewa "Allah sarki yaron Arxiki" brake Aliyu ya taka da karfi, inna ta saka salati a rude tana cewa "lfya?" ya fito da sauri ya bude bayan motar, da gudu inna ta fito tana cewa "fito intisaar yau mun shiga uku me ya faru?. A rude inna ta dinga tambayrsa me ya sami motar bayan intisaar ta fito, bai ko kalleta ba ya shiga kwaso masu ledojin tsarabarsu da saurinsa, inna ta dada rudewa tana cewa "purse dita na ciki akwae kudade da yawa fito min dashi da sauri wllh har da daham dina a ciki, ya ciro purse din ya ajiye kan ledojin da yake ta dire su a gefen titi, inna ta kin ki me abinta da sauri tana lekar motar a tsorace, "to wae me ya samu motar?" inna ta tambaya tana jan intisaar su matsa daga kusa da motar, bai ko kalleta ba har sae da ya tabbatar ko tsinkesu bai bari a cikin motarsa ba sannan ya rufe motar, ya juyo yana kallonsu fuska daure yace "ku nemi motar haya da xae kai ku inda xaku, don baxan bata lkci na na bar abinda ke gabana na dauko ku a mota ku dinga min iskanci a cikin motar tawa ba." Yana kai wa nan ya shige motarsa ya ja ta ya bar su tsaye a wajen, inna ta xabga salata tana girgixa kai tace "amma wannan yaro na Bukar anyi tantirin dan iska, ynxu xubar damu yyi a dajin Allahn nan ya wuce?" sae kuma ta fashe da kuka tana cewa "wannan masifa da me yyi kama ni Rahmatu" intisaar ta dinga tuntsire dariya tana karewa inda ya ajiyesu kallo ita dae bata ga alamar daji ba a wajen amma inna tace daji ne, sannan ga motoci na ta wuce wa abinsu, har da mutane ma nata harkokin gabansu a wajen. kukan da inna ta dinga rusawa ne ya fara jawo hanklin jama'ah wajen, intisaar tace "kai inna don Allah kixo muje mu hau mota mu wuce, dube yanda kika janyo ana ta kallonmu," cikin kuka wiwi inna tace "wllh baxan hau motar haya ba don ubanki, hka kawae dan nawa na da motoci sae na buge da hawa ta haya" intisaar ta kulu matuka ita kam da ta sani bata bi inna ba, wannan disgrace din har ina? Taruwa mutane suka fara yi a kansu ana tambaya lfya? Nan inna ta dinga surutu ratata akan abinda jikanta yyi mata, intisaar ji tayi kmr ta nutse a wajen don kunya, da sauri tayi gaba ta barta a wajen cike da takaici, ita ba kudi ta fito da ba bare ta hau mota ta koma gida, ta juya daga nesa tana kallon inna da mutane suka gama kewayewa, ko me take gya masu oho. Da kyar mutane suka lallaba inna ta hau adai-daita sahu, tana gunjin kuka ta shiga tana cewa "Allah dae ya isa tsakanina dashi," sae kuma ta fara kwadawa intisaar kira tashigo su wuce, kasa xuwa wajen intisaar tayi sbda mutanan da suka taru a gun, har kusa da ita tricycle din ya tsaya sannan inna tace "maxa shigo intisaar, Allah xai saka mana," fuskarta daure tashiga, mutanen wajen suka bisu dacewa " Allah ya saukeku lfya Hajiya, Allah ya kiyaye, ya ja da ranki" inna ta ding a washale baki tana gdya tare da daga masu hannu, shi kanshi mai tukin dariya yake yi. Sae da suka yi nisa sannan inna ta dube intisaar tace "kinga mutanen arxiki koh, har biya mana sukayi, Allah yyi masu albarka dae" intisaar bata ko kalleta ba bare ta tanka mata. Har bakin gate Napep din ya ajiyesu, inna ta dinga gdya ya fiffito masu da kayansu, intisaar ta dauki wanda xata iya ta shiga cikin gidan inna na biye da ita a baya tana cewa "to ynxu bayan duk wlkcn da yyi mana ba gamu a gidan ba. Nafisa tayi murna da xuwan mhaifiyar ta ta sosai,'ya yanta duk suka xo gaida kakar tasu dayake ranar asabar ce suna gida, sae da inna taci ta sha sannan ta soma xayyano wa Nafisa irin abinda Aliyu yyi masu a kan titi, Nafisa tace "amma wllh Aliyu bai da mutumci ko kadan inna, kinsan kuwa tunda na dawo ko sau daya bai taba xuwa gaida ni ba ko yi min sannu daxuwa, amma haisam xuwansa biyu knan," inna tace "ranar da ya kawosu xainab bai shigo ba?" Nafisa tace "xan masa karya ne inna?" nan inna ta kwadawa intisaar dake dakinsu maryam kira, dayake maryam din sa'arsu ce da xainab, suka shigo tare da maryam din, inna tace "ranar da Aliyu ya kawoku gidan nan dama bai shigo ba?" intisaar tayi jim don dae ba Aliyu bane ya kawosu motar haya suka shiga amma da suka koma gida basu ce kin kai su yyi ba, da sauri tace "eh bai shigo ba" inna ta galla mata harara tace "munafukan bnxa kawae amma ca kuka yi min ya shigo da na tambayeku," intisaar tace "uhm ae xainab ce bni bace" nafisa tace jeki kawae abinki, kika san ko yy masu gargadi akan kar su ce bai shigo ba, bala'i inna ta dinga yi tana cewa "wllh yaron nan mugun shaidani ne, amma xai ci ubansa bari na koma gida dae" intisaar ta fice. The end of book one. INTEESAR BOOK 2 Intisaar ta xaro ido a tsorace tace "nashigauku, wllh bn san...." buga mata baki yyi dakarfi sannan ya tura ta fuskarsa a murtuke yace "wat do yhu fink yhure tryn 2 do? Seducin me or wat?" da sauri ta juya ta bar palon tayi hanyar dakin momy da gudunta, yyi ajiyar xuciya sannan ya buga tsaki ya nemi kujera ya xauna. Maryam ta shigo tace "lah, ya Haidar kai ne a gidan namu yau" yyi murmushi yace "yea kanwata, ykk?" ta xauna gefensa tana dariya tace fyn uncle ya aiki?" yace "alhmdllh, momy fa?" ta yi hanyar bedroom din tana cewa bari na kirata " ko da ta isa dakin momy na rubuce rubucenta ne, tace "momy uncle haidar fa ya xo?" momyn ta watsa mata harara tace to uban me xan masa?" maryam tayi murmushi tace "yana dae palo fa shi daya" momy tace "manta dashi kawae" maryam tace "intisaar fa?" momy tace "ta shiga wanka," maryam ta koma palon tana murmushi tace"uncle gata nan xuwa," yace"yauwa kanwata ya karatu?" tace"muna tayi uncle," sannan tayi hanyar fridge ta dauko masa ruwada lemo ta dire masa a gabansa yana mata gdya." nan ta xauna suka dinga hira amma momy taki fitowa, ya dube maryam din da ita ma bata ji ddin yanda uwartata tayi ba yace "wae halan fushi momy take yi dani ne?" maryam tayi yake tace "ina ga dae wani abun take yi amma tana xuwa," yamike yana murmushi yace "bari dae naje ciki na sameta nasan fushi ake yi dani," har bedroom dinta yyi sallama ya shiga, can ciki ciki ta amsa masa ya yi dariya ya nemi gu ya xauna yana cewa "dama ashe uwa na fushi dadanta," ta galla masa harara tace"kaji dashi dae" yyi dariya yace "toam srry mum," kun shigo Nigeria lfya? Wllh ayyuka ne suka sha gabana," ta tabe baki tace "gskya ne mara mutunci kawae" don tasan ba don Allah yaxo gidan nata ba kila Abba ne yyi masa tatas shine ya kamo hanyar gidanta yau, don inna bakinta ba shiru xai yi ba, dariya kawae yake yi yana bata hkuri har daga karshe ta dan sake, suna hira intisaar ta fito daga bathroom sanye da hijab ta fice daga dakin xata wuce dakin maryam ta kimtsa, momy ta kira ta tace "kin gaida yayan naki ne,? Tayi yake tace hnkli na ne baya wajen, "ina kwana yaya?" ya daga kai yana mata wani irin kallo, sannan yace"lfya," ita kuma ta fice da saurinta.Karfe daya Aliyu ya wuce masallaci xae yi sllh, nafisa tayi tayi dashi yaci abinci amma yaki wae ya koshi, tace "to yyi kyau ae"yyi yar dariya yace "to ku ajiye min idn na fito masallaci xan xo naci sae na wuce gida," tace "um um fa Aliyu," yace "serious anty xan dawo wllh" tace "to sae ka dawo," har gate maryam ta rakasa suna ta hira cikin raha, intisaar kam tunda tashiga dakin maryam dama bata fito ba, tayi mamakin yanda Aliyu kewa maryam dariya, ashe dae yana dariya hka, a bakin gate ya hadu da kannin maryam din sun dawo daga makarnta suka rungumesa suna murnar xuwansa yace su shiga ciki anjima xae dawo idan yyi sllh. Bae shigo gidan ba sae wajajen karfe uku har momy ta fidda rai da xuwan nasa sae gashi, tace "ca nake halin naka kayi min ae" yyi dariya yace "to ina abincin sauri nake yi" nafisa tace au a dole ma xaka ci abincin knan?" yace "hva de wane ni" a dae kawo min abincin, momy ta kira intisaar ta xo ta kawo masa abinci, gabanta na faduwa ta dire masa abincin a gaba, momy ta mata umarni da ta xuba masa a plate, jikinta na bari ta shiga budekulolin, muryarsa taji yana cewa"no ta barshi kawae anty" ta mike da sauri ta bar wajen ba tare da tabari sun hada ido ba. Wajen karfe hudu da rabi yyi ma momy sllma xai wuce bayan ya hada ko wani yaro da dubu biyu a gidan, maryam kuma ya bata dubu goma, momy tace to ita intisaar din fa? Yyi yake yace "ta bari a gida xan bata nata," momy tace"aa wllh ka bata a nan kawae muna gani" ganin momy da gske take ne yasa ya kirgo dubu biyar ya mika ma shaheed ya bata, momy tace "aa ita ma goman xaka bata wllh" anty duk wata fa ina basu, ko sati biyu ba ayi ba ma da na basu a can gida fa" momy tace "to shknan ka wuce dasu tunda gida xaka, su ma gidan xasu wuce yanxu," yace wa? Momy tace intisaar din da maryam mana, ya kirkiro murmushin dole yace "ae ba gida xani ba yanxu," eh ka ajiyesu sae ka wuce inda xaka din," ya rasa yanda xai yi ya ce aa, don hka kawae yace mata to su sameni wajen mota a waje, sannan ya fice bayan ya mata sllma yana kokrin boye bacin ransa. Yana cikin motar suka karaso wajen, intisaar duk jikinta yyi sanyi. . Motar ya bude ya fito yana kallon intisaar din ransa a hade, yyi mata wani irin kallo yace"hope ba wannan motar kike shirinshiga ba?" ta kauda kanta da sauri gabanta na faduwa ta gyadamasa kai sannan ta dau hnyr da xae kai ta babban titi inda xata samu mota ta hau. Maryam tayi sororo tana kallon Aliyu, yace shigo mu wuce kanwata, ta hade rai tace "hva uncle me yasa xakayi hka, ita din ba kanwarka bace?" ya tabe baki yace "idan xaki ki shigo mu wuce kawae" ta juya ranta a bace tace "kaje kawae ni na fasa xuwa" yyi dariya ya shige motarsa ya wuce. Maryam na shiga gidan ta gyawa momynta abinda Aliyu yyi ma intisaar, momyn tace "maxa bita ki kira min ita," maryam ta fice da saurinta, amma bata ga intisaar ba, ta dawo ta gyawa uwartata, kiranta momy tayi a waya, bugu uku ta dauka tace ita tama kusan gida, momy tace to idan kin saukaxan kiraki intisaar kiyi hkuri ki kyaleni da dashi, bake yyi wa ba ni yyi ma, intisaar tayi murmushi tace ba komai momy, amma ae maryam din xata xo ko? Momy tace "aa ita ma ta fasa xuwan saesati mai xuwa," intisaar bata ji ddin hkn ba amma kawae tace "tomomy ngd sae anjima. Intisaar naxaune a bakin kofar palonsu ita da xainab dake fere wa momy doya dan shi xata girka da rana da yake kowa girkinsa yake yi daban da rana har ma da safe, sae dae idan kayi ka kai ma inna, na dare ne kawae akeyi gaba daya, intisaar ta ajiye nail cutter din dke hannunta tana kallon xainab din tace "ki bni na karasa mana, ko ku baxa kuyi girki bane yau?" xainab ta tabe baki tace"ohon masu ni dae doya xanci" intisaar tayi dariya tace "ni dae nasan da biyu kike fere doyar nan" momy ce ta fito daga palo ta karbe kayanta tace "ku tashi ku bni waje ni don Allah, awa nawa xa ayi ana fere doyan nan" takun da suka ji ne yasa gaba daya sukajuya suna kallon wanda ke xuwa, Aliyu ne yana tafe yana danna wayrsa, gaban intisaar ya fadi to me yaxo yi a sashinsu, xainab ma sae da taji tsoro sosae, to me sukayi kuma, momy kuwa cin gaba da aikinta kawae tayi, ya karaso wajen yana kallonsu da daddaya da daddaya, daga xainabdin har intisaar baki na karkarwa suka gaida shi, yau kam suit ne a jikinsa yyi kyau sosai, ko daga inayke oho, bai ko damu da gaisuwarsu ba ya dubi intisaar fuskarsa a tamke yace "wae da jira kke naxo na sameki kafin ki bni kudina ne?" intisaar ta firfito da ido tace "ni?" ya daka mata tsawa yana cewa "yhu re vry stupid, tambayata kike yi ko waye?" a tsorace tace "Allah ni bngne abinda kke nufi ba...." ya gallamata wani mugun harara yace"fito min da dubu biyar dina" ta xaro ido tace "lah ni na mnta wllh kayi hkuri" sannan ta mike da sauri ta shiga ciki, sae gata ta fito dasu, ta mika masa ya fixge ya kirga sannan yyi gaba. Xainab tace "an shiga uku," momy dae bata ko kallesu ba ta dauki doyarta tayi hanyar kicin, intisaar tace "uhmm ni har na manta ma wllh" xainab tace "amma yaya Aliyu bai yi ba a lyf wllh, Allah ma yaso baki taba kudin ba" intisaar tayi dariya tace "me xae kaini dama, ni wllh har ma na mnta da kudin, tun fa ran sunday gashi yautuesday" xainab ta tabe baki tace"Allah ya kyauta toh" yauwa na mnta ban gya maki ba jiya faruuq ya bni dubu biyu wllh, intisaar tace "Allah sarki, ihsaan ma ya bata" ni kuma dubu goma ya bni har ynxu ma yana wajen inna, xainab tace "bawan ALLAH, shine ake neman a maki tijara kan dubu biyar ynxu," suka kwashe da dariya gaba dayansu. Suna sashin inna gaba dayansu yau amma bnda khadija da rahma, intisaar na tsife ma kursum gashi,xainab na kwance suna kallo sukaji hayaniya a tsakar gidan, da sauri suka fiffito har da inna dake binsu a baya da gudu, fadila suka ga ya Aliyu ke duka da belt yana ball da ita, ita kuwa bakinta bai mutu ba yana dukanta tana xaginsa, hajiya da umma na ta masa ihun ya rabu da ita, inna ta karaso da gudu tana yarfe hannu tace "an shiga uku, wae kai Aliyu wani irin shaidani ne, ynxu me tayi mka kke neman kasheta?" cikin xafin nama Aliyu ya kaita kasa ya dinga xuba mata belt din tana ihu, "ae wllh sae ta gya min gidan uban da take xuwa yau, idan ba hka ba na rantse sae na sumar da ita," "ayyo ynxu naji bayani, ae fadila ana kiran sllhn farko take barin gidan nan ba ita xata shigo gidan nan ba sae karfe sha dayan dare," inna ta fadi tana kallon su hajiya da kamar su shake ta, hva, nan inna ta dinga xuga Aliyu ya dinga dukanta kmr xae kasheta, ita kuwa bakin ta yaki mutuwa sae xaginsa take tana ihu, inna ta dauko wani katako da gudu ta kawo masa tana cewa "muka mata wannan Aliyu, wa yasani ma ko karuwanci take fita yi, tsinannun iyayenta sun xuba mata ido," haisam ya shigo gidan, inna ta tsiri yi masa bayani shima yasa kafa ya kwasheta ta xube kasa hka suka dinga dukanta inna na xuga su, kmr xasu kasheta, umma da hajiya ba baki tunda inna na wjen sae matsar kwalla suke, intisaar da su xainab duk jikinsu yyi sanyi ganin yanda akayi ma fadila, xainab tace "ae gwara suyi mata hka kila ta nutsu wllh" . Momynta tashiga kwada ma kira tana bata hkurin ta bude mata kofar tana kuka,ta juya taga ya kusa iso inda take, tasa tafin hannunta ta rufe fuskartata dinga ihu tana bubbuga kafa tana cewa"wayyo kayi hkuri ya Aliyu wllh tllh ni ina xuwa makaranta naje kitso ne yau shi yasabnje ba yau, don Allah ka rufa min asiri kar ka dokeni, ina rokanka," kuka take yi sosae hannunta a fuskarta tana tsalle-tsalle sae kace ihsaan. Shiru bata ji an kamata ana duka ba, ganin shirun yyi yawa ne yasa ta xamehannunta a hnkli daga fuskarta jikinta na rawa, wayam taga wajen ba kowa, ta fara waige-waige tana gwalo ido amma bata ga kowa ba a gun, a hnkli ta dinga kuka tana kallon kofar palon nasu, takai hannu ta bude, taji shi a rufe gam, jikinta a sanyaye tayi bangaren inna tana goge hawayen fuskarta, xaune taga Aliyun kan dakali kusa da wani flower yana ta tuntsira dariya kmr mahaukaci, haisam dake kan kujera yyi tagumi yana ta kallonsa, gabanta yyi mugun faduwa xata juya ta koma da sauri, haisam yace"intisaar wa ya saki kuka?" tsit Aliyu yyi ya sha mur kmr bashi ke dariya ba ynxu, ta girgixa kai tace"ba kowa," sannan ta maxata bar wajen. Xainab na xaune a palonsu intisaar suna kallo intisaar na kwance, wayan xainab yyi kara, ta daga,masifar da take tayi ne yasa intisaar ta mike xaune tana ta kallonta har ta gama ta kashe wayan, intisaar ta tambayeta wanene, cikinfushitace "wannan gantalallen da na ke gya maki ne, tun ranar yake sintirin xuwa gidan nan, nace ya rabu dani bana yi yaki saurarana, wannan wani irin jaraba ce?" intisaar ta tabe baki tace "ae duk hka suke kmr mayu," sannan ta mike ta dauke cup din da kanwarta tasha corn-flakes ta fita dashi tana taya xainab mita. Tana fita tayi hanyar gate, ta ko gansa a tsaye tayi masaiso har wajen inna, tayi sallama inna ta amsa daga can kuryar daki, ta shiga tana cewa "inna bako kikayi," inna tace "hva don Allah, daga ina? Gani nan xuwa" intisaar na 'yar dariya tace "saurayin xainab ne," inna ta sake kabbara daga cikin dakin tana cewa "gani nan xuwa, ya shigo don Allah," intisaar na dariya ta juya xata fita tayi masa iso xuwa palon, suka hada iso da Aliyu dake gefen kujera a xaune yana danna laptop, wani mugun faduwar gaba ya xo mata, ita bata ma gansa ba, wani irin kallo yyi mata yana girgixa kafa, ya hade girar sama da ta kasa,jikinta a sanyaye tace ma bakon ya shigo, ya shigo yana gdya, ya mikawa Aliyu hannu suka gaisa Aliyun ya dan saki fuska,inna ta fito ta dinga wangale baki tana masa sannu daxuwa, kusan duka lemukanfridge dinta ta dire masa a gabansa sannan ta xubo masa cin-cin da alkaki, tana cewa "ci ka koshi yaro nan ma gidanku ne, ae xainab jikata ce, ni na haifi ubanta, kmr an baka ita an gama kaji ko," gdya ya dinga yi shima yana murmushi, intisaar kuwa dama tuni ta nemi lungu ta xauna tana satan kallon Aliyun da shi din ma satar kallon nata yake, suna hada ido ya galla mata harara, ta mike jiki a sanyayexata bar palon, inna dake ta faman xuba da Abdurrahman, tace "aa ina xaki," takirkiro murmushi tace "xainab din xan kira, inna tace "yauwa maxa kije ki kira min ita yar kwal uba, ashe dama tana da santalellan yaro kyakkyawa hka taki gya min, maxa kira min ita," ta fice da sauri tana yake, Aliyu ya mike inna tace "ina xaka malam bayan kaga munyi bako," ya kirkiro murmushi yana kallon Abdul din yace "ina xuwa ynxun nan ae xan dawo," sannan ya juya da saurinsa ya fice, shit, ya fadi da karfi ganin har tayi kwana, bae san ta fisa wayo ba, dama tasan sae ya biyo ta don hka da gudun ta tayi sashinsu, tana shiga palon nasu, xainab tace "ina kika je ina kiranki tun daxu kixo ki ga abu," intisaar ta tabe baki tace "kicin na tafi, inna tana kiranki fa." xainab ta kalleta tace "a ina kikaga inna?" tsakar gida tana neman ki, intisaar ta fadi ba tare da ta kalle xainab din ba, xainab ta mike tayi sashin innar, intisaar ta dinga dariya bayan ta wuce, ita ma ta rama abinda xainab din ta mata ranar da faruuq ya fara xuwa gidan. A hanya taga ya Aliyu ya watsa mata harara ta kauda kai tare da xumburo baki tayi gaba da sauri, yyi kwafa tare dacewa "xakuci ubanku gaba daya ae, ke mai saurayin da me kawo shi cikin gidan dukxan kama ku, yara basu kai ko ina ba amma sun san su ajiye samari," shi daya ke maganarsa don tuni xainab ta ma kusa sashin inna. Da daddare intisaar taje siyo masu table water momy ta aiketa, tana ganin xainab tasaka gudu ta fice daga gate din tana dariya, xainab bata ko kalleta ba tayi sashinsu, ta dawo rike da ruwan a hannunta ta shiga cikin gidan tana adduar Allah yasa xainab bata nan, mutum taci karo da a bakin gate din ta koma baya da sauri ta ga ko waye, taji an riketa gam, gashi wajen bbu wuta kuma bata fito da torch ba, tana jin kamshin turaren ba sae an gya mata ko waye ba, kankamesa tayi jikinta na bari tana cewa "wayyo momyna, me nayi kuma" tura ya shiga yi amma taki sakinsa ta dada rungumesa gam tanai masa magiyan yyi hkuri..... . Cikin murya kasa-kasa take rokansa ya rufa mata asiri kar ya doketa, bae ko saurareta ba cikin xafin nama ya fara kkrin banbareta daga jikinsa amma hkn yaki yiwuwa sbda irin rikon da tayi masa, jikinsa yyi sanyi kafarsa ya kasa daukarsa, murya can kasa- kasa yace "get off me, ko kuma na baki mamaki," wayyo dukana xaka.... Ji tayi ya daga hijab dinta ya shige ciki, cikin muryar da ba tata ba tace"nashiga uku...." da sauri ta sake shi daga rungumar da tayi masa tana neman guduwa, ya fixgota hade da kankameta ya mannata da bango,kuka ta saki a rude ta fara kkrin turasa, ya matse ta da karfinsa fuskarsa wuyarta tana jin numfashinsa, tayi kicin-kicin ta galla masa cixo a kirjinsa, ya dada kankamta kmr xasu dawo daya yana magana a hnkli yace "dnt utry dat again...." murmushin mugunta yke yi, hkn ya kara tsureta jikinta ya shiga bari tana cewa "don Allah don annabi ka rufa min asiri kayi hkuri," buga bakinta yyi da karfi yana cewa "kar ki sake hada ni da Allah" gyaran murya suka ji an yi daga dan nesa dasu, ya saketa da sauri tare da juyawa, haisam ya gani xaune kan plastic chair ya kauda kansa yana kallon taurarin dake sama, jikin intisaar yyi sanyi, ta gyara hijab dinta, ta durkusa ta dauki ruwan da ta ajiye a gurin tana satan kallon haisam din da har yanxu bai juyo ya kallesu ba, ta bar wajen da saurinta tayi sashinsu, Aliyu ya karasa kusa da haisam din yana cewa"yane?" ba tare da haisam ya kallesa ba yace "nothin" sannan ya mike ya bar wajen, ashe tun daxu yke wajen a xaune yana kallon duk abinda sukeyi, duk da dae ba jin abinda suke cewa yyi ba, haisam yyi murmushi bayan ya bar wajen yace"Intisaarr"Aliyu kam binsa yyi da kallo har ya bace masa, yyi tsaki mai sauti ya bar wajen yana tunanin irin abinda xae yi wa yarinyar nan idan ya kamata, tun ba yau batake seduce dinsa dama, gashi yau har sae da taci galaba a kansa, to wae ma garin yaya hkn ta faru. Intisaar kam har washegari jikinta a sanyaye yake, ko abba kasa xuwa gaida shi tayi don bata sonhaduwa da haisam, har taje islamiyya ta dawo bata je gun inna ba, sae da yamma ihsaan taxo tace mata inna na kiranta, ta dae daure tayi sashin innar tana adduar Allah yasa baxata hadu da haisam ba, don ko tunanin Aliyun ma bata yi ita kmr haisam, tana shiga palon inna ta ko tar dashi a xaune, kunya ya kamata taji kmr ta nutse a inda take, "ina yini ya haisam" ta gaidashi ba tare da ta kallesa ba, ya amsayana cewa "sae ynxu kika fito knan" ta kirkiro murmushi kawae tace"uhum" gyaran daki tayi ma inna sannan ta ce mata tana xuwa xata dauko abu ta dawo, hnyr gudu dama take nema, tana fita kuwaya bita,ta rasa yanda xatayi har ya karaso kusa da ita, "me ya hanaki fitowa yau?" ya tambayeta suna tafiya tare, ta kirkiro murmushi tace"bakomai" yace "hmm, Aliyu fa?" ta xaro ido tace "nima ban sani ba" ta marairaice fuska da sauri ta fara magana ganin inda ya dosa tace"kaga ya haisam wllh jiya aikena akayi shine ya tsareni a gate wae xae dokeni" murmushi haisam yyi bai ce komai ba, hkn ya kara daga matahankali tace "Allah da gaske nke ya haisam" yace "uhum shine kika rungumesa knan" ta xaro ido tace "aa rikesa nayi kar ya dokeni" suna shan kwana suka ga Aliyun a xaune yana waya, yana ganinsu ya kashe wayan, gabanta ya fadi muryarta na karkarwa tace "ya haisam don Allah rakani kar ka barni a nan," ganin a nan xasu rabu ne yasa tace masa hka, yyi dariya yace "aa Aliyu dae xae rakaki ni ba ruwana,"hannunsa ta kama tana rokansa, aliyu ya bisu da kallo har suka wuce,haisam na dariya, ya mike yyi tsaki yace "ikon Allah kadae ne xae sa baxaki suma a hannuna ba idan na kamaki " dagaita har haisam bbu wanda ya kallesa bare ya amsa masa. . Yau juma'ah tana xaune palonsu ita da xainab, suna hira bayan sun dawo dagadubiyar wata yar ajinsu farida da bata da lfya, kusan karfe biyar ce ta yamma, daga intisaar din har xainab material iri daya suka sa purple nd pink sunyi kyau kwarai, kursum ma tana palon nasu tana cin abincin intisaar da momy ta ajiye wae ba aajiye mata abinci ba, intisaar tace taci natadon a koshe take ita, kirar wayar faruuq ne ya shigo wayrta, ta daga suka gaisa sannan yace mata gashi a wajen inna, ta shiga daki ta nemi ixini gun momynta, sannan ta fito tace ma xainab ta rakata, xainab ta galla mata harara sannan tace"anki!" intisaar tayi 'yar dariya sannan tace"karki raka ni din ma to sae me" xomuje kursum," ta fadi tana kallon kursum din, kursum ta tura kwanun abincin tace"muje," suka fice tare intisaar nai ma xainab dariya. Suna shan kwana fadila ta kwada ma kanwartata kira, kursum ta haderae tace "meye" umma ta leko tana cewa"don ubanki kanwar uwarki ce kota ubanki wannan shegiyar?" kursum ta xumburo baki, uwar ta daka mata tsawa cin bacin rai tace taxo ta wuce, dole intisaar ta kama hanyr sashin inna ita daya. Tana isa tayi sllma murya can ciki inna ta amsa da karfinta tashiga palon tana addu'ar Allah yasa ba surutunta na bnxa takewa faruuq ba, tana shiga palon suka yi ido hudu da Aliyu, gabanta yyi mugun faduwa har ta mnta lst tym din da ta gnsa ita kam,sanye yake da shadda fara kal, ashe dae su Aliyu ana sa manyan kaya, ta kalli haisam ma dake xaune a palon shi din ma shaddar ce fara, hka ma faruq dinta, gaba daya dae anko sukayi, ta nemi gefen inna ta xauna, bata bari sun hada ido da faruuq din dake ta kallonta ba, inna tace "sae ynxu ku ka dawo?" tace "eh" a takaice kawae, sannan ta gaida haisam da har lkcn kallonta yke yi,yyi murmushi yace"lfya kanwata kinga yanda kika yi kyau kuwa yau" ta sunkuyar da kai tana murmushi tace "kai yayana kullum sae ka xolayeni wllh" sannan ta sata kallon Aliyu, kallonta ykeyi amma fuskarsa a hade, ta dauke idonta da sauri ta dube faruuq dake ta faman kallonta kmr xae cinyeta, ta galla masa harara da wasa tace "wannan kallon fa" dariya yyi ya kashe mata ido yace "naga kin kara kyau ne yau bby," ta xaro ido tana kallon inna data bude baki tana kallonsu, dariya suka yi gaba dayansu har da haisam, innar ma ta taya su, Aliyu dae ya maida dubansa ga plasma, lallai yarinyar nan ta rika, ko gaishesa ma bata yi ba, faruuq ya dubi haisam yace "big bro, plss tel her nt 2 let me down, coz i'm blindly in love" haisam yyi dariya sosae, ya kalli intisaar dake ma faruuq din wani irin kallo ya dawo gefenta ya xauna yace "hope u heard wat he said cweet sis, i wont love 2 c anythin bad goes wrong wit my frnd" tayi 'yar dariya ta daura kanta a kafadar haisam din tace"ok cweet bro, help me let him knw dat...... Am his nd his alone,nd i promise nt 2 let him down," ta karasa mgnrta tana satan kallon faruuqdin, dariya sukayi gaba daya, haisam yace yana kallon faruuq "hope dat's clear besty" inna da tuni ta hangame baki tana kallonsu ta mike tayi narai-narai da ido tana cewa "yau de xagina ake tayi, tunda gashi Aliyu bae ce komai ba, bari kawae na bar maku palon" dariya intisaar tayi ta riketa tana cewa "kaji mana wannan tsohuwar mu soyayyar mumuke yi don Allah ki xauna ," *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** inna tace "lah" bari de nashiga ciki idan kun gama xan dawo, faruuq yyi dariya yace "inna ta tsargu," ya dawo gefen intisaar ya xauna yana mata wani irin kallo kmr maye, cake ya dauka ya kai mata baki yace "bude bakin na baki kanwata" ta hararesa tace "bna ci," haisamyyi dariya ya mike ya koma kan kujera yace"kila don dae ina gefenku ne amma na tashi karbi kayanki ke dae"dole sae da faruuq ya tilasta mata yasa mata cake din a baki, ta kauda kanta a kunyace, kawae suka hada ido da Aliyu da ya xuba mata ido yana kallo, gabanta yace dam, taga ya kauda kansa yyi murmushi, mikewa tayi dasauri tana kallon faruuq din tace " lah! ina xuwa ya faruuq minti biyar na daura abu a kitchen," ta mike da sauri ta fice, ta kinkimitakalminta ta ruga a guje, tana fita kuwa Aliyu ya mike shima ya fice. Shit! ya fadi dakarfi yana huci, ya girgixa kansa yabar wajen kawae. Ita kuwa tana isa sashinsu ta shige palo gabanta nafaduwa, ta shiga wanka kawae, ko da ta fito xainab ta tafi, tayi sallah, sannan ta saka kayan barcinta ta jawo abincinta taci, ta koya ma ihsaan assignment dinta wajen karfe takwas knan, ta idar da sallahn isha'i knan faruuq ya kirata kunya yasa ta kasa daga wayan don tasan bata kyauta ba, daga karshe dae ta daga, yace "uhun to ai kya xo muyi sllma ko kanwata" tace "lah bka tafi ba dama yaya" yace "yea mun danyi wani abuda haisam ne a laptop, ynxu xan tafi ki fito ina ma bakin gate, daxu dae nasan babanki yasa ki barin falon" ya fadi cikin xolaya, taji kunya sosae, tace "hm to ka shigo ka gaida momy mana idan yaso sae na raka ka gaba daya kaga ni kunya nke ji baxan iya ce mata xan fita ba kuma" yace"ohk gani nan xuwa kanwata. . ... Har parlor faruuqya shigo ya gaida momy, ta amsa masa da fara'arta tana tambayrsa mutanen gidan yace duk lfya momy, sun danyi hira kadan sannan ya mike yace "ni xan koma momy, dare yyi," tace "to ka gaida mutanan gidan mun gode kwarai," ya ciro kudi mai yawa ya mikawa ihsaan da ya xaunar a gefensa momy tace "hva don Allah kar ayi hka umar," yace "aa momy xata siya chocolateko ihsaan?" ya fadi yana kallon ihsaan da tayi dariya ta gyada masa ka, ihsaan momy ta aika ta kira intisaar a daki, ta fito sanye da hijab dinta har kasa, sannan ta fita rakasa, suna isa bakin gate ya dauko kujeru biyu ya ajiye yace "hira xamuyi kanwata, don daxun wayo kika min kika gudu" ta dan xaro ido tace "ya faruuq abbafa ya kusan dawowa," ya bata rai yace "to shknansae da safe," ya mike xae bar wajen ta riko hannunsa tace "wayyo yi hkuri yayana, xamuyi hirar amma ba da yawa ba" yyi murmushi ya koma ya xauna yace "to na yrda kanwata, xo ki xauna," ta xauna kan kujerar kanta a sunkuye, ya tsura mata ido yana kallonta, a hnkli yace"i love yhu intisaar," ta rufe fuskarta da tafin hannunta bata ce komai ba, ya sa hannu ya cire hannayen nata daga fuskarta yana kallonta, duk da wajen ba wani hasken kirki bne dashi, kunya ya kamata sosai tace a hnkli "kaga nafara jin bacci yayana," yyi shiru bai ce komai ba sae kallonta da yake yi, can dae ya mike tsaye yana cewa"to shknan kanwata sae munyi waya knan," kudi ya ciro ya mika mata taki karba ya bata rai yace "kin raina knan ko" ta wara ido tace "hva deyayana wllh kawae de ngd ne" yyi fuska ya ajiye mata kudin kan cinyarta yace "ki watsar dasu to," tayi shiru takasa cewa komai, yace"ina xuwa bni 2 mint," ya fita waje saegashi yashigo da leda a hannunsa ya mikamata yace "ummi tace a kawo maki," tace"kai hva de yayana, ni wllh da baka karbo ba....." ya ajye mata shima a gefenta yace"to shi din ma ki jefar" sannan yace mata sae da safe, ya fice daga gidan, ta bisa da kallo har taji tashin motarsa sannan tayi ajiyar xuciya, Allah dae ya gani tana son faruuq fiye da yanda take tunani, jiki ba kwari ta mike ta dauki ledar ta maida kujerun gun da suke sannan ta juya xata yisashinsu taji taci karo da mutum, tashiga uku talalace, ta saki ledar hannunta ta juya da sauri xatayi hanyar gate don nan kadae ne xata tsira idan tabi, ya fixgota, xata fasa ihu yasa hannua bakinta sannanya juyar da ita, "ya Aliyu ka taimakeni, ni bnmka komai ba wllh" cikin kuka da rawar murya take maganan, ya kai mata tagwayen mari masu lfya, sannan ya buga ta a bango da karfinsa, fuskar nan tasa bbu alamr rahma, kuka mai tsuma xuciya ta saki tace"don darajan iyayenka kayi hkuri plsss" buga mata baki yyi da karfi harsae da bakinta ya fashe, yasa kafa ya kwasheta, ta mike da sauri agigice tana cewa "nashiga uku, don Allah....." wani mugun naushi ya kai ma cikinta ta firfito da ido tare da saki wani irin axababben kara damuryar da ba tata ba, ya kai mata wani marin tare da daura yatsunsa a bakinsa alamr tayi shiru, ta sa hannu ta toshe bakinta tana karkarwa ta girgixa kanta hawaye mae xafi na xuba a idonta. Aliyu bae kyaleta ba sae da yaga ta kasa tsayawa sannan ya fixge kudin dake hannunta yasa a aljihu, a karo na farko ya bude baki yyi magana"kadan knan kika gani, Wllh tllh ni Ali sae na sumar dake watarana a gidan nan idan baki fita hanyata ba" ya juya ya barta nan a durkushe kanta a kasa, da kyar ta iya mikewa ta bar wajen tana ganin double koledar da faruuq ya bata ma bata dauka ba don ji take kmr xata suma awajen, tayi bangarensu tana daddafe bango don wani irin jiri dake kwasarta. Ko da tashiga palonsu ma momy shafa'i da wutr take ta shige bedroom kawae ta fada kan gado tana juye juye kmr xata mutu, wani irin ciwo cikinta ke mata ta dalilin naushin da ya kai mata, hka ma kanta da ya buga da bango, cikin ikon Allah bacci ya dauketa amma can cikin dare ta farka da matsanancin ciwon kai ga mugun xaxxabin da ya rufeta, juye-juyen da takeyine ya tada momynta, ta mike xaune ta kunna wutan dakin tana kallonta tace"lfyarki kuwa intisaar," kasa magana tayi momy ta kai hannunta jikinta taji kmr wuta,"me ya sameki hka" ita dae ba baki sae kuka da ta fashe da, paracetamol momy takawo mata ta bata ta karba da kyar tasha, sannan ta kashe ac dake dakin ta lulube tadalilin rawar sanyin da takeyi, ranar dae daga ita har momy basuyi bacci ba, momy ta rasa abinda ke damun 'yar tata, duk ita ma hnklinta ya tashi. Gari na wayewa momy taje ta sami abba ganin yanda jikin nata yyi tsanani, gashi sae aikin kuka take, duk ita ma tabi ta daga hnklinta don akwae soyayya da shakuwa mai karfi tsakaninta da 'yar tata don ita kadae take gani taji ddi idan ta tuna mijinta na farko umar, har daki abba ya shigo duba intisaar din, "me ya sameki fatima, ina ke maki ciwo?" ya tambayeta dadamuwa yana yaye bargon da momy ta lullubeta dashi, ita dae ba baki sae kuka, abba yashiga lallashinta yana cewa"damabaki da lfya ne fatima, kuma bakiyi maganaba tun jiyan?" ta girgixa masa kai kawae, xainab tashigo dakin hankalinta a tashe bayan ta tambayi ihsaan ina intisaar don ita har tayi shirin islamiyya da yake tare suke wuce, ihsaan tace mata "my aunty is sick," hkn yasatayo bangaren nasu da saurinta, abba ya dubi xainab da tashigo yace"je ki ki kiramin Ali xainab," tace to sannan ta fice da sauri, a hanya suka haduda kursum take tambayrta ko intisaar ta shirya don ita ma shirin islamiyyar tayi, tunda Aliyu yyi masu mugun duka ranannan suka fara xuwa makaranta gaba dayansu dama, xainab tace "bata da lfya baxa taje ba," kursum tace "hva de me ya sameta," xainab ta yarfehannu tace nima bn sani ba ynxu ma ya Aliyu xan kira abba ma yana can, kursum tayi sashin nasu da sauri xainab kuma ta tafi kiran Aliyu, tana isa tayi sllma ta shiga palon, baya nan, tayita kwada sllma ko yana cikin daki amma shiru, sanin halin yayan nata ne ya sanyata karasawa cikin bedroom din nasa yana ko xaune laptop a gabansa yasa earpiece kunne daya yana danna laptop, ya daka mata tsawa a fusace yana cewa"baki da hnkli ne don ubanki ko ke jahila ce,baki san idan kika yi sllma a waje kika ji shiru gaba xakiyi ba, xaki afko min cikin daki, ban hanaki wannan habit din ba," au ashe ma yana jinta, ta tabe baki cikin rashin damuwa tace "dama abba ne ke kiranka" ta juyafuu xata wuce ya mike da sauri yana cewa "xainab, xainab," amma bata tanka masa ba, ya fito palon da sauri har ta fice ya bita da sauri yana kiranta, ta dawo tana kallonsa fuskarta a hade tace"gani," me yasa abba ke kirana, ya tambayeta yana kallonta don dae yasan sae da dalili ake kiransa, don kan abba ya kirasa sau daya ya kira haisam sau goma,"nima ban sani ba, intisaar dae ce bata da lfya shine yace naje na kiraka" ta fadi tana kallonsa, gabansa ya fadi yace "to menayi ake kirana" tace "ni kuma ina xan sani" hnklinsa ya tashi yace "me tace wa abban?" tace "oho, ni ina shigowa abba yace nayi maxa naje na kiraka" don ta gaji da tambayoyin nasa, bai damu da ohon datace masa ba ya kara tambayrta "ya mood din abba yake" tace a kage "kai yaya ni ma ban sani ba abba nacan yana jiranka," ta juya ta yi gaba ta barshi nan a tsaye. Ya bita da sauri kuma yana kiranta, ta juya rai bace tana kallonsa yace "ina abban?" tace"yana can dakin momy" ya xaro ido yace"yana me?" tace "oho! tayi gaba abinta" ta fara suspect dinsa ita kam. Tana komawa sashinsu intisaar abba ya tambayeta meya tsayar da ita kuma ina Aliyun, tace"nemansa nke a gidan abba amma gashi nan xuwa" ya dubi momy da ta xauna tayi jigum yace "ki hado mata tea xainab," ta mike tace to sannan ta fita, tana fita sae ga inna, tun daga waje suka dinga jin muryarta kmr speaker tana cewa"me ya samu intisaar din, ni rahmatu," abba ya juya rai bace yana kallonxainab yace "donuwarki ca nayi ki ji ki gaya wa inna taxo ta daga mana hnkli a nan ynxu?" xainab ta mike da sauri ido a waje tace "wllh tllh abba ban je wajen inna yau ba ni," abba bae sake cewa komai ba har inna ta shigo dakin, "bukar me ya sameta wae" abba ya dubeta yace "shine ae xa a dubata don bbu wanda yasani," inna tasaki salati tana girgixa kai tace "Allah ubangiji dae ya bata lfya wllh duk hankalina ya tashi da aka je aka gya min," abba bae sake tanka mata ba tana ta surutanta, illa Aliyun da yake jira, murya can ciki Aliyu yyi sllma, duk jikinsa yyi sanyi, ynxu yarinyar nan sae ta iya bude baki tace yyi mata wani abu dama, inna ce ta amsa masa da karfinta tana cewa "maxa shigo," hankalinsa ya kara tashi ya shigo palon ya tsaya yana waige-waige kmr munafuki, abba yace"karaso mana" da kyar yyinamijin kkri ya shiga dakin, ya rusuna ya gaida abba don duk yau bai je gaisheshi ba gashi har karfetara, ya juya ya gaida inna ma sannan yace"abba gani," . Dama fatima ce bata da lfya, shine nace a kiraka ka dubata, abba ya fadi yana kallonsa, Aliyu ya saki ajiyar xuciya, sannan ya maida dubansa ga kangadon yana kallonta, idonta a lumshe yake, duk da dae ba bacci take ba, ya karaso kusa daita yace "meke damunki?" tayi shiru kmr mae bacci, hkn ya bata masa rai don yasan idonta biyu, a dan fusace yace"kinajina xakiyi min banxa?" inna cikin tsawa tace "kai mahaukacin wani gari ne, baka ga bacci take ba yarinya tana fama da kanta xaka dinga mata ihu," xainab ta karasa kusa da ita tana bubbuga kafarta a hankli tana kiran sunanta, ta bude ido tana kalln xainab din, Aliyu ya juya yana kallon abban nasa yace "ko dae a wuce da ita clinic kawae abba" inna tayi karaf tace"wllh bbu inda xa a kaita, gamu da likita a gida kace xa a wuce da ita wani wajen, meye amfanin ka" Aliyun ya dubeta rai bace yace "to ni din Allahn musuru ne da xan san abinda yke damunta," cikin tsawa inna tace "shiyasa naga an kai fadila asibitida bata da lfya, don ubanka ba kai ka dubata ba ka bata magunguna da allurori ba kuma gashi nan ta warke," Aliyu ya dubeta a walakance ya kauda kai kawae, abba yace "shknan bari a kaita asibitin ka iya tafiya" da sauri yace "aa abba bance baxan dubata ba ae, guri nake jira su ban na dubata," ya fadi yana kallnsuinna, haisam ya shigo dakin da sllmrsa ya karasa kusa da intisaar din ya xauna cike da damuwa yana kallonta yace "intisaar me ya sameki, dama jiya baki dalfya baki yi magana ba," ta sunkuyar da kanta kawae sae hawaye, nanya shiga lallashinta, ya dube abba yace "asibiti xamu wuce abba?" inna tace "asibitin lfya ga likita a gida, ynxu xae dubata ae" sllmrsu hajiya da umma ne yasa kowa yyi tsit a dakin, momy ce kadae ta amsa masusuka shigo suna cewa ashe abinda ya faruknan, momy ta basu waje suka xauna sannan suka gaisa, suka tambayeta mae jiki tace masu da sauki, hajiya tace Allah sarki duk ta rame sae kace warce tayi sati tana jinya, umma tace wllh kuwa baiwar Allah, inna ta tabe baki tace "ikon Allah" xainab ta girgixa kai cike da takaici, ynxu har anje an barbada masu shine suka kwaso jiki suka xo gulma, kumatasan baxae wuce kursum ba ko rahma, abba ya dubi gaba dayansu yace "to ae kwa bashi waje yyi aikinsa de ko" hajiya ta mike tana cewa"me xae hana, Allah dae ya bata lfya yasa xakkan jikine," suka mike gaba dayansu har da yaran xasu bar dakin, Aliyuyace "to..to abba ya xa ayi treatin din nata?" abba da har ya kai bakin kofa xae fita ya juya yana kallonsa cikin rashin fahimta yace "kmr ya fa?" yace"aa...dama...emm, to to ae naga sae da magunguna da allurori xa ayi treatn din nata, kuma ni...." sae kuma yyi shiru yana kallon tagan dakin, abba yyimurmushin takaici ya girgixa kai yace "to nawa xa a baka?" inna ta mike ta saki salati tana girgixa kai tace "ita intisaar din sae....." da sauri abba ya katse ta yace "aa baaba ae hakkinsa ne bari a basa" nawa ne kudin treatment din gaba daya? Abba ya tambaya yana kallonsa, cikin bacin rai haisam yace "abba ka bari na wuce da ita asibiti kawai," abba yyi saurin cewa "aa haisam ka bari xae dubata," abba ya sake tambayrsa nawa xae basa, yyi shiru kmr me lissafi sannan yace ba tare da ya kalli abban nasa ba "dubu takwas da dari biyar gaba daya," abba yyi murmushi, haisam cike da takaici yace "to yyi kyau, ka dubatani xan baka," da sauri ya juya yana kallon haisam din rai bace yace "to da baki na xan siyo kayan ne koya? Ko kuma ina da kudin xan tsaya cewa abba ya bani," inna cikin ihu tace "Allah ya babbake mae krya sannan ya tsinemasa," Aliyun ya juya ya galla mata harara sannan ya dauke kansa, haisam ya ciro dubu biyar daga aljihunsa ya mike xae fita abba yace ina xaka, yace xan dauko kudi ne,abba yace nawa ne a wajen ka ynxu, yace dubu biyar, abba ya ciki dubu hudun haisam ya mikawa Aliyun ya karbe yana kirgawa, duk wannan abinda akeyi a kan idonsu hajiya ne, hajiya taji kmr ta maida dan nata ciki don murna, sae murmushi take yi, umma kuma ji tayi kmr ta tsine ma haisam da bai yo hali irin ta Aliyu ba, shekaranjiya tace ya bata dubu goma yace bai da, amma sae gashi ynxu ya kirgo har dubu biyar ya bada don a duba wata bnxa ita kam bata san irin dan da Allah ya bata ba, momy kam sunkuyar da kanta tayi tana jin duk abinda sukeyi cike da takaici, intisaar kuwa idonta ta rufesbda axabar da take ji ko ina na jikinta ciwo yke mata barin ma kanta sannan kuma ga ciwon mara shima ya kunno kai, abba kam tuni ya fice su hajiya suka bi shi a baya a xuciyarsu suna fatan Allah yasa cikita yo, don rahma ca tayi masu amai take ta kwararawa, Aliyu ya dube inna yace"a bata tea kafin na dawo, xan je siyo abinda ya kamata," ya fice haisam ya bisa a baya da sauri, sai da suka kai tsakar gidan sannan yace "canjin nawa xaka dawo da knan?" Aliyu yace kmr ya, haisam yace eh ae dubu tara aka baka, kuma dubu takwas da dari biyar kace, Aliyu yyi masa wani irin kallo sannan yace "to da kafa xanje siyo magungunan?" sannan yyi tsakiya wuce yana cewa "dn ma kun samu xan bata lkcn" . . Su Aliyu na fita inna ta mike tana tambayr intisaar din me xata ci, ta girgixa kai alamar ba komai, xainab tace"to ki daure kisha tea din" inna ta dauki kofin ruwan shayin ta isa kusa da ita tana cewa "tashi ki sha kafin ya dawo to" intisaar ta girgixa kai murya can kasa-kasa tace "wanka xan fara yi," momy ta shiga bathroom ta hada mata ruwan wankan sannan ta mike da kyar jiri na kwasarta ta shige bayin, ko da ta fito rawan sanyi ta dinga yi, inna ta lullubetatana cewa "ikon Allah, ciwan lkci daya ya kwantar da ita," ya haisam ya shigo dakin yana tambayr ko Aliyun ya dawo,inna tace "ina fa! yana can yana sokwanci" haisam ya girgixa kai yace "ni dae wllh inna nafi son a kaita asibiti," inna tace "wae ni kuna bani mamaki wllh, ga likita a gida kuyi ta kiran asibiti," haisam yace "to shknan, ni xan wuce kd ne ynxu ina da wani aiki a can amma yau xan dawo in'sha Allah," inna tace "to Allah ya kiyaye" yace "ameen" sannan ya karasa kusa da intisaar yana kallnta yace "Allah ya sauwake kanwata kinji" tayi murmushi, a hnkli tace "ngdyayana" yyi ma momy ma sllma sannan ya fita. Da kyar inna ta lallabata tasha kunun da ta dama mata, xainab sae fama kallon agogo take yi dn har sha daya ya wuce, tun kusan karfe goma da Aliyu yaje siyo magunguna har ynxu bai dawo ba, tuni bacci ya dauke intisaar din bayan inna ta bata paracetamol kafin Aliyun ya dawo, amma har karfe sha biyu bbu Aliyu bbu lbrinsa, "kai jama'a ko dae wannan yaron bata yyi ne" inna ta fadi tana kallon momy da xainab dake dakin bakinta a bude, momy dae bata ce komai ba, xainab ta tabe baki ita ma bata ce komai ba, wasa-wasa har karfe biyu bbu Aliyu, inna na idar da sllh tana xaune kandarduma cikin ihu tace "amma wannan anyi tsinannan yaro," daga momy har xainab sae da suka raxana sbda irin bude muryar da inna tayi, momy tace "kai inna, kika san uxurin da ya tsayar dashi," a fusace inna tace "yaci ubansa shi da uxurin," ku bni waya na kira bukar, momy tayi ma xainab ido alamar kar ta kira mata abban, inna ta mikawa xainab din wayar tana cewa "maxa kira min uban nasa" xainab ba don ranta yaso ba tace ma inna baya xuwa bayan ta kara wayr a kunne kmr me kira, don ita da momy ta barta kiran abban xatayi, ita kam bata san irin yayan nata ba, basu san tuni abba ya kira momyn yana tambayrtajikin intisaar din ba tace masa da sauki sosae, yace Aliyun ya bata duka magungunan tace masa eh sannan sukayi sllma, xagi kam Aliyu ya sha shi a wajen inna ba adadi, har da dan hawayenta, "ni da nasan abinda tambadadden yaron nan xae yi knan da asibiti kawae na bari muka wuce, gashi ynxu yrnya na ta shan axaban ciwo ba magani, shi kuma bukar na rasa uban me xae sa ya dinga kashe wayarsa ni kam, ynxu wa xae kai mu asibitin gashi haisam ba ya nan," daga momy har xainab bbu wanda ya tanka mainna, intisaar kam jikinta yyi xafi sosae kmr wuta, hka inna ta ishesu da mita tana hawaye, wajen karfe uku da rabi wayan intisaar yyi kara xainab ta dauka tana kallon me kiran, faruuq ne, da har xata ajiye don bacci intisaar din take yi sae kuma ta fasa ta daga, suka gaisa ya tambayeta intisaar din fa, tace "bacci takeyi wllh, bata da lfya," cike da damuwa yace "subhanallahi, me ya sameta" xainab ta yarfe hannu tace "wllh bamu sani ba, tace dae ciki da kantake mata ciwo," yace "tun yaushe?" tun jiya da daddare wae,yace "ya salam! kunje clinic ne?" tayi shiru ta rasa me xata ce, yyi saurin cewa "ohk... Gani nan xuwa," ya kashe wayr, inna tace "faruqu ne?" xainab ta gyada mata kai kawai, cikin minti goma sha biyar faruuq ya iso gidan, hanklinsa ya tashi sosae, momy da ta bar masu dakin ya rage inna daxainab kawae, ta tashi xaune tana kallon faruuq din da ya sata gaba yana tambayrta inda ke mata ciwo, cikinta t.a nuna masa da kai, yasa hannu ya danna cikin nata ta xaro ido tace "waii! ciwo yake min" me ya buge ki a nan ya tambayeta yana taba goshinta da yaji xafi sosae, ta girgixa masa kai kawae sae hawaye, duk ya rude ya shiga lallashinta yace "dama kina ciwon kai ne," ta girgixa masa kai kawae, ya mike yana kalln inna yace "bari ina xuwa yanxun nan inna," inna tace "to dan albarka, wannan shaidanin yaron aka ba kudi ya siyo mata magunguna bamu sake ganinsa ba " bai tanka wa inna ba ya fice da sauri, ko minti talatin bae cika ba ya dawo dauke da kayan magunguna da allurori sae ledar ruwa dan karami da xae sa mata, ya ce wa xainab ta hado mata tea mai kauri ta kawo mata, shi da kanshi ya shiga bata, amma ta karba tace xata iya sha, yana ta hada allurorin da ruwa har ta sha rabi ta ajiye tace "ta koshi," yace "ae baki ma ci komai ba tukunna, tuwo xa a kawo maki kici ynxun," inna ta mike tana cewa "gskya ne, bari naje da kaina ma xan mata ynxun nan," da kyar ta yrda yyi inject din ta sannan ya sakamata ruwan ya bata wasu daga cikin medicines din tasha ta kwanta, ya xauna ya xuba mata ido yana kallonta cike datausayi, xainab dama tuni.. Faruuq na xaune har ruwan da yasa mata ya kare da yake karamin leda ce, ya cire mata don bacci ma takeyi, yana gama cire mata ta bude ido tana kallnsa, yyi mata murmushi yace "ya jikin kanwata," ta tashi xaune tace "da sauki," ba tare da ta kallesa ba, ganin tana kkrin mikewa tsaye ne yasa yace "ina xaki kuma kanwata," murya can ciki tace masa "2 ease my self," ba tare da ta kallesa ba, ya taimaka mata ta tashi tsaye dn jikinta ba kwari dukda taji ta garau ynxu, tuwon da inna ta kawo mata ya shiga xuba mata, ta fito ta nemi gefe ta xaunatana kallonsa kmr xatayi kuka, ya dago kai yana kallnta yace "kici abinci ki sha sauran medicine dinki kanwata, kusa da ita ya durkusa yana kallonta yace "ya dae kanwata, cikin na maki ciwo har ynxu ne, naga yhu re restless" ta girgixa masa kai kawae bata cekomai ba "say somethin mana kanwata, ina ke maki ciwo kuma?"ya tambayeta cike da damuwa, itakam kunya take ji tace masa mararta ke mata ciwo, don hka tace "ni bbu inda ke min ciwo," sae kuma ga hawaye, nan da nan ya rude ya shiga lallashinta yana cewa "plss kanwata ki gya min mene mana, kan bai daina bane?,"ganin yanda duk ya bi ya daga hanklinsa ne yasa tace "cikina ke ciwo," ba tare da ta kallesa ba, yace "ciki kuma, ba kin ce ya daina ba, to wae me ya buge ki a cikin ne" a hankli tace ba shi bne, yyi shiru kmr me naxari sannan yace "on yhur Period?" yana kallonta, tayi shiru bata ce komai ba kanta a sunkuye, yace "ohk ina xuwa kanwata," ya mike ya fice. Ko da ya dawo tana xaune a falo ita da momy da inna sae kursum, tasa tuwo a gaba amma taki ci, ynxu kam jkinta yyi mata sauki sosae, da sllmrsa ya shigo falon rike da ledan magani karfe biyar da minti goma na yamma, ya gaida momy don tun xuwansa na farko bai sake ganinta ba sae ynxun, ta amsa tanai masa sannu da xuwa sannan ta mike ta bar falon, xainab ta shigo ta xauna gefen intisaar din tana mata ya jiki, tayi murmushi tace "da sauki"maganin da ya xo da shi kala uku ya dauki daya ya buda ya bata, ta karba a kunyace xata ajiye yace tasha ynxun, inna tace "ae hka nan take yarinyar nan bata san magani, nayi mamakin ma da tasha wa inda ka bata daxu," faruuq yyi murmushi kawae yana kallnta har ta kora maganin da ruwa sannan ya sa ta cin tuwon dake gabanta, bude kofar da sukaji anyi irin ta mahaukata ne yasanya su juyawa gaba daya, Aliyu ne ya shigo dakin sanye da t-shirt fara kal da wando three qtrshima farin, yyi kyau sosae, hannunsa rike da leda da basu san ko meye a ciki ba, intisaar ta sunkuyar da kanta da sauri, faruuq kuwa kallo daya yyi masa ya kauda kansa, kallonsu ya shigayi daddaya da daddaya, inna tana sakace hkori ta tabe baki tace "ae sae ka je ka tsis-tsira ma kanka allurorin ka shanye magungunan don jikata kam ta warke, dan arxiki wanda aka haifa tsiya na bacci ya xo ya duba mana ita" Aliyu ya yo waje da dara-daran idanunsa yana kallon innar, wato shi aka haifa tsiya ido biyu, ya juya yana kallon faruuq din da intisaar, xainab ta labe bayan intisaar sbda wani irin dariya dake cinta, hka ma kursum da ta rufe fuskarta a jikin inna, Aliyun yatsura wa faruuq din ido kmr xae shake shi, faruuq bai ma san yanayi ba, ya dube intisaar yace"kanwata kin ki cin tuwon ko na taya ki ne?" ta kirkiro murmushi bata ce komai ba, yace "au kar na taya ki?" a hnkli tace "kaci mana" yyi murmushi yace ok, sannan ya mike ya dauki ruwan goran dake gabanta ya bi gefen Aliyun ya fita, Aliyu ya bishi da kallo har ya dawo ciki sannan ya xauna gabanta yace "to muci," a kunyace tasa hannu cikin tuwon sannan shi ma ya saka, inna tace "yauwa faruqu kila ma xata fi ci idan taga kana ci," faruuq yyi 'yar dariya ya dubi xainab yace "xo muci xee" xainab tayi dariya tace aa ni naci nawa ae, inna ta dubi Aliyu tace "to ka tsaya mana kerere a ka kmr wani tsohon soja, da'alla fice ka ba mutane waje su ga haske,gantalalle kawae dogon bnxa, knka ka cuta ba mu ba " Aliyu yyi huci mae xafi yana kallonintisaar din dake cin tuwonta a hnkli ita da faruuq," juyawa yyi ya fuce fuuu, inna ta kyalkyale da dariya ya dawo da sauri idon nan nasa ya kada yace "kika ce me?" bata tanka masa ba sae dariyar da take ta yi kawae, ya juya yyi gaba yana cije lebensa. Kursum da xainab suka dinga kyalkyale dariya inna na taya su, faruuq kam murmushi kawae yke yi, intisaar kam jingina kanta tayi jikin kujera tana kallonsu. . Gajiya tayi da tsayuwa taga ba sarki sae Allah, tayi shahada, ta kusa kai cikin gate din tana karanto duk addu'ar da taxo mata don duk a rude take, a dai-dai lkcn shi kuma ya mike tsaye xae bar gidan ya wuce masallaci don maghrib ya kunno kai, duk gidan yyi masa xafi, wata raxanan nan kara ta saki ganin ya mike tsaye a dai-dae lkcn da ta shigo gidan, don a nata tunanin dama can ita yake jira yana ganintakuma ya mike, shi kanshi sae da ya firgita da irin karar da tayi, ta kuma juya a guje kmr mahaukaciya xata bar gidan, yyi saurin fixgota da karfinsa ransa a bace, bae an kara ba sae ganin yarinya ta sulale kasa yyi, yyi hanxarin rikota ta xube jikinsa sumammiya, ya durkushe wajen yana kallonta cike da mamaki, yasan suma tayi, jijjigata ya shiga yi a hnkli ya ma rasa abinda xae yi ya fara waige-waige gashi bbu kowa a tsakar gidan dan gari ya fara duhu, ruwan goran da ya fitoda yasha ya rage, ya dauko ya bude ya shiga yayyafa mata ruwan, a hnkli ta bude idanuwanta ta daura kan nasa idon da ya tsura mata a fuskarta, kuka ta saki tana kkrin tashi daga jikinsa tana cewa "don Allah don annabi ya Aliyu ka daina dukana, ni bn maka komai ba....." buga mata baki yyi yace "keep mute!" ba shiri tayi shiru, ya turata daga jikinsa fuska a hade yace "don ki kara ja min bakin jini wajen abbana shiyasa xaki tsiri suma da kin ganni ko" girgixa kai tayi hawaye na sintiri a fuskarta, ya daka mata tsawa "tashi a kaina kar nayi ball dake munafuka kawae," ta mike da sauri jikinta na rawa, shima ya mike tsaye, tayi baya xata fadi, yyi saurin tallabota, ta fada jikinsa ya turata da sauri sannan yyi maxa ya riko hannunta dn faduwa xatayi, ya fara fixgarta kmr wata dabba tana binsa jikinta ba kwari sae jiri dake kwasarta amma bae bari ta fadi ba, yyi sashinsu daita, har bakin kofarsu ya kaita ya bude kofar yana kallonta, duk a tsorace take, ya tura ta ciki har tana faduwa yyi gaba, momy ta taso da sauri ganin yanda 'yar tata ta fado falon tana cewa "lfya intisaar," . Karfe tara abba ya shigo duba intisaar, har lkcn inna na falonsu bata tafi ba, abba ya shigo mata da fruits da tsire a leda ya ajiye mata yana tambayarta ya jikin, tace "da sauki abbana" sannan ta mike ta shige bedroom ta bar masu falon, abba ya dubi inna yace "nan xaki kwana knan yau?" tace "aa dama kai nake jira, kasan iskancin da wannan dan naka yyi mana yau" abba yyi shiru yana kallonta, ta tabe baki tace "wllh bkayi sa'an da ba bukar, shanya mu yyi a nan ya gudu da dubu taran da kuka bashi, sae wannan yaron faruuq yaxo ya dubata kmr xata mutu" abba ya tsura mata ido yana kallonta ya kasa cewa komai, "wllh ko minti goma ba ayi da fitan yaron ba ka shigo, tun safe yaki barin gidan nan yana kanta, gashi ynxu jiki alhmdllh, yaron mutunci ne wllh" abba ya jinjina kai cike da takaici yace "to shknan yyi masa kyau, hkn yaga yafimasa alkhairi," inna ta mike ta tabe baki tana cewa "ka rakani bangarena" yace "to sannan yyi sallama da momy, ta rakosu har bakin kofa tana ma inna sae da safe. Karfe goma haisam ya shigo duba intisaar, momy tace "kar dae ynxu ka dawo haisam" yace "wllh kuwa momy," bae bar sashin nasu ba sae kusan karfe sha daya, suna ta hira da momy da intisaar da ynxu bata jin ciwo a ko ina na jikinta. Da safe ita da ihsaan suka je gaida abba, kmr ba ita tayi ciwo jiya ba, Aliyu na xaune a falon kansa sunkuye bayan abban nasa yyi masa tatas, intisaar ta nemi gefe ta xauna ganin Aliyu duk sae jikinta ya mutu, ta gaida abba ya amsa da fara'arsa yana tambayarta jiki, tayi murmushi tace abba da sauki, ta kalli Aliyun da har ynxu kansa a kasayake tace "ina kwana yaya," ya dago yana kallonta idonsa yyi jajir ya kauda kai murya can ciki yace "lfya lau," ta mike tana kallon abba tace"abba sae anjima," yace "yauwa intisaar, kin dae sha magungunanki dae ko," tace "eh abba nasha" yace "to yyi kyau" sannan suka fice, Aliyu ma ya mike yana kallon abban nasa yace "Allah ya huci xuciyarka abba," abba ya dauki kudin da Aliyun ya ajiye masa ya watsar masa dasu yace "nace kaje da su bama bukata," Aliyu yyi jim sannan yace "kayi hkuri abba, ita ma kanwata ce bbu yanda xa ayi na karbi kudi wae don xan yi treatn dinta, na gya mka dalilae na nayin hkn, kuma bayan hka ma ni bn samu na yi treatn dinta ba " abba ya galla masa harara yace "dalilanka na bnxa, ina ruwanka da uwartaka da har xakayi hkn wae sbda taji ddi, wae kae me uwa, ka burge uwarka amma kuma ka xubda kimarka a idanun mu, kai ko kunya ma bka ji ba, wawa kawae, da'alla get out malam" Aliyu ya juya jiki ba kwari ya bar falon. Da yammar ranar ummi kanwar faruuq taxo duba intisaar, yayan nata ya ajiye ta sannan ya wuce, sun jima suna hira da intisaar da xainab kmr da can sun saba sannan suka kaita gun inna, inna ta rasa inda xata sata don farin ciki, tsaraba ta hada mata lkcn da faruuq din ya kirata wae yana waje don baxae shigo ba wae, momyma ta hada mata nata abun arxikin sannan intisaar ta rakota don xainab tuni hajiya ta aika khadija ta kira mata ita, a bakin gate suka gaAliyun a xaune fuskar nan tasa bbu alamar rahama, ummi ta gaisheshi, ya dago kai yana kallonta fuska daure yace "lfya," intisaar ma ta gaidashi gabanta na faduwa yyi bnxa da ita har suka fice, ummita juya tana kallonta tace "waye wannan kuma," intisaar ta kirkiro murmushi tace "babban yayanmu ne" don ita ynxu tunanin yanda xatashiga gidan yana bakin gate din take, har bakin motar faruuq din intisaar ta rakata suka yi sllma faruuq ya kashe mata ido yace "sae nakiraki bbyna," ta kauda kanta da sauri tana murmushi ta bar wajen, ya ja motar suka wuce, ta kasa shiga gate din ta tsaya a waje, har wani bari jikinta yake yi don tsoro. Dago ta momy tayi tana kallon ta tace "jikin ne intisaar?" ta girgixa kai ta mike da kyartace "aa faduwa nayi," bedroom ta shige momy ta bita da kallo ta kasacewa komai tausayin yar tata ya cika ta, ita ta rasa abinda ke damunta. Washegari da ciwan kan ta tashi amma bata bari momy ta gane ba don bata son tana daga wa uwarta ta hnkli, faruuq ya kirata da safen yana tambayr jikinta tace yyi sauki sosae, tare abba ya shigoda Aliyu falon nasu wajen karfe tara, lkcn innana nan a xaune don tun karfe bakwae ta iso sashin nasu da kunun ta da kosae ta kawo ma intisaar, ihsaan ta rungume abban nata ya daga ta sama yana cewa"how re yhu momyna" tace fyn sir, ya dubi intisaar yana murmushi yace "ya jikin fatima? Tayi murmushi tace "da sauki abbana," to Allah ya kara sauki, kina shan magani dae ko? Tace "eh abba ina sha," Aliyu ya nemi guri ya xauna yana satan kallon momy dake xaune tana linke kayan ihsaan, ba tare da ya kalleta ba murya can ciki-ciki yace "ina kwana," tayi kmr bata ji sa ba, ya tabe baki ya gaida inna ita ma tayi masa bnxan, ya dake yana duban intisaar din yace "ya jiki," ta sunkuyar da kanta tace "da sauki," sannan tace masa"ina kwana" ba tare da ya kalleta ba yace"lfya lau," ya sata kallonabbansa da ke kallon Tv, yace ba tare da ya kalleta ba"kwaso min medicines din da kike sha nagani," ta mike jiki ba kwari ta shiga bedroom ta kwaso masa magungunan da faruuq ya bata ta durkushe gabansa ta xubesu tana kallonsa, inna ta tabe baki tace "ko uban me xae yi dasu idan ba gulma ba," bae tanka mata ba ya shiga dudduba magungunan ya cire guda biyu a ciki yace "ki ajiye wa innan kar ki sha," to kadae tace, inna tayi karaf tace "akan wani dalilin, kafi sa sanin aikin nasa ne malam," da'alla kwashe magungunanki ki maida kirabu da wannan gantalallen, dariya ma abun yaba Aliyun, abba ya dubesa yace"sbda me xata ajiye su," ya shafa kanshi yace "sbda aikinsu kusan iri daya ne gaba daya, dama xan karo mata wasu ne shiyasa nace ta ajiyesu," abba yace "no ka bari ta gama da su tukunna sae ka bata wanda xaka batan, shima yasan abinda ykeyi ae yaron," Aliyun yyi shiru bai ce komai ba, inna ta galla masa harara tace"munafukin bnx kawae, idan yaga ubansa ya dinga yi kmr na Allah," Aliyun ya mike yana kallon abban nasa yace "abba xan wuce clinic sai na dawo," inna tace "kaji makaryacin bnxa, ca xakayi xaka je gantali,kai din aiki kke xuwa," ya tabe baki bae tanka mata ba, ya dan kalli intisaar din ya watsa mata hararar tsana yace "Allah ya sauwake," ya juya ya fice. Suna tsakar gidagaba dayansu intisaar na sa ma rahma rani a hannu da yamma, su hajiya da umma anje gidan suna, momy na can bangaren inna, haisam da abokinsa sadeeq suka shigo gidan, dukansu suka gaida su, sadeeq ya dubi xainab yace"xainabu ya garin," ta galla masa harara tace " kaji dashi malam," yyi dariya suka wuce ciki da haisam yana satan kallon intisaar da tun da ta gaida su bata sake daga kanta ba, sadeeq din ya dubi haisam bayan sun shiga ciki yace "wacece wannan yarinyar dan Allah," haisam ya hararesa yace ita intisaar din ce bka sani ba, sadeeq yace wllh bn ma taba ganinta ba ni, haisam yyi murmushi yace "kanwatace,'yar wajen momyn ihsaan ce," sadeeq yace "waww amma yarinyar tayi sosai," haisam yyi 'yar dariya bai dae ce masa komai ba, sadeeq yace "uhm naga baka son maganar, ko dae kana ciki ne?" haisam ya hararesa yace "kanwar tawa? Sadeeq yace "so, sae akayi yaya? Bbu auretsakaninku ne ko me kke nufi" haisam yyi murmushi, sadeeq yace"yess?" Allah idandae bbu komai tsakaninku ni kam ina ciki, yarinyar tayi ne wllh, haisam yace "kunyar ta nake ji ne sadeeq, amma baxan boye mka ba, sonta ya wahal dani fiye da yanda kke tunani, but bbu yanda xanyi, ni kam nahkura, na kuma dauketa a matsayin kanwata ne," sadeeq ya galla masa harara yace "amma kai wani bnxa ne wllh, wannan ae xancen bnxa ne kke min," haisam yace "to ya xanyi?" sadeeq yace"tun kararta xakayi kace kana sonta, kaga sae ayi tuwonamai na, sincerly sayin kar ka bari yarinyar nan ta wuce ka, xakayi babban asara," haisam yyi murmushin takaici yace "to ae its too late, ni nan na bata go ahead na kula samari kuma ynxu hka akwae wanda xae aureta, kuma frndship ma muke yi dashi, abokina ne ynxu hka," sadeeq yyi tsaki yace"nonsense ni kuwa xan shigar da kaina nace ina sonta, watch nd c" haisam yace no kar kace hka plss baxan iya yi wa faruuq hka ba, sadeeq dae bai kara tanka masa ba, har suka gama abinda ya kawosu, suka je masallaci sukayi sllhr maghrib, sannan sukayi sashin inna, har lkcn jikin haisam a sanyayye yake, basu bar wajen inna ba sae kusan karfe takwas da rabi, sadeeq ya shiga ya gaida hajiya daumma sannan ya baro haisam a falon hajiya yace yana xuwa, xainab sadeeq ya kira yace taje tace da intisaar haisam na kiranta don kar ace shine taki fitowa, tace haisam ae yana falon mu, Yace do as i saymana kanwata, ta kuwa j . . Suna fitowa tsakar gidan intisaar tafara tambayr xainab ina ya haisam din, xainab ta nuna mata can kusa da wata flwer inda sadeeq yake a xaune, ta karasa wajen, "gani ya haisam," ta fadi tana kkrin xaunawa kan wani dakali, suna hada ido da sadeeq tayi saurin mikewa tana kallnsa,ta juya a fusace gun xainab amma tuni xainab tayi gaba tana dariya, donta gano sadeeq din, intisaar ta juya xata bar wajen,yyi saurin shan gabanta yana cewa "hva kanwarmu, ni ba yayanki bne da har...." tayi tsaki tace "ka bni waje malam ina da abin yi," ta katse shi, yyi murmushi yace"to naji baxan bata maki lkci ba, amma sae kin xauna sae muyi magana," tayi masa wani irin kallo tace "dan Allah ka bni waje na wuce, ni mamata bata san na fito ba" yyi shiru yana kallonta sannan yace "uhum faruuq ya riga ni ko?" directly tace masa"yeah!" yyi murmushi mae sauti yace "to kika san ikon Allah" ta watsa masa harara tace "kayi hkuri ka bani guri na wuce," "to idan Allah yyi nine mijinki fa?" xatayi magana taji an fixgota ta baya an juyo da ita, a tsorace tace "ya..ya Ali...." marin da ya kai mata ne ya sanya ta kasa karasawa, ransa a bace ya fara mgna "ke don uwarki baki da aikin yi sae tara mana samari a gida, wannan gajan ya shigo wancan gajan ya shigo kin maida mana gida kmr hotel, cikin gidan nan uban wa kikaga yana shigowa da samari, sae ke tatatcciya,marakunya ko?, to daga yau na sake ganin ki da wani shege a tsaye a gidan nan sae na...." turasa tayi da karfinta har sae da yyi ba, dan unexpectedly hkn ya xo masa, ta koma baya tana kallonsa hawaye na sintiri a fuskarta, ta yarfe hannu cike da takaici tana magana "ni me na tsare mka agidan nan ka gya min don Allah, kullum sae ka cuceni ba tare da dalili ba, to kasani wllh sae Allah ya saka min,kace ba ruwanka da harka na ba ruwanka da lamarina, to ina ruwanka da samarin da naketarawa, ka fita rayuwata don Allah don annabi ka rabu dani, ka kyalenini ban tsare ma komai ba gidan nan, just let me leave my lyf am beggin yhu " ta kara fashe wa da kuka ta juya da gudu ta bar wajen, sororo Aliyu ya tsaya kalln intisaar ransa a jagule, kansa ya dinga juyamasa, ya firfito da ido cike da mamaki, kansa na tsara masa ya dafe maganganunta na dawo masa a ka, sadeeq dake tsaye cike da mamaki yana kallonsu yyi masa duban wlkcn sannan yace "to kaji dae malam," Aliyu ya juya cikin bacin rae ya cakumeshi da karfi yana cewa "kace me??? " haisam ne ya karaso da sauri don dama yana tsaye yana kallon duk abinda ke faruwa, yafixge yayan nasa daga rikon da yyi wa sadeeq dake ta tuntsira dariya kmr wani xautatce, Aliyun ya tsaya yana huci yana kallonsa kmr kirjinsa xae yi magana, sadeeq ya kalli haisam yana dariya sosae yace "wannan dan uwan naka yana bukatan xuwa psychiatry a duba kwakwalwarsa urgently" da haisam bae ja sadeeq sun fice daga gidan nan ba da ba karamin tashin hnkli xasuyi da Aliyu ba, barin ma Aliyun najin haushin sadeeq din tun da ddewa. Sashinsu intisaar din yyi kmr wani xaki ya kasa daina tunano kalamanta, yana isa ya tura kofar da karfi har sae da momy dake ba ihsaan abinci ta raxana, intisaar tana shigowa ta shigedakidama, da ace ya ganta a falo a wannan lkcn da bbu abinda xae sabaxae sumar daita ba gaban uwarta, shi ta gaggaya ma maganganu hka? Juyawa yyi ya bar sashinnasu ba tare da yace ma uwartata komai ba. Falon hajiyarsu ya shiga, tana ganinsa ta mike da sauri tana cewa "me ya faru Ali, wa ya bata maka rae hka" yyi huci me xafi ya dafe kai yace "wae momy ni yarinyar nan tasa gaba ta gaggayawa magana yau, ya salam!," hajiya ta rude tace "wace yarinyar Aliyu," ya mike tsaye ya kifa kai dabango yace "yarinyar gidan nan," hajiya ta hade rae tace "wae tsinanniyar yarinyar nan intisaar?" kasa cewa komai yyi sae idoda ya tsurawa bangon dakin, wae shi yau intisaar ta bude baki take ce ma Allah xae saka mata, "goshh!" ya fadi da karfi, towaema garin yaya ya tsaya kallonta kmr soko ya kasa mata komai har ta bar wajen? To wae ma waye ya bata bakin magana a gida? Budewar kofar da yaji hajiyarsu tayi ne ya sa shi juyowa da sauri yanakallonta,ashe tayi surutun ta ta gaji ba tare da yasan me take cewa ba,ina xaki hajiya, ya tambayeta yana kallonta, ranta a bace tacesamun su xanje nayi, nasan shegiyar uwarta ce xata sata tayi hkn, duk abinda xae faru sae dae ya faru a gidan nan don bbu mai taba min kai ya xauna lafya,"yyi huci me xafi yace "ki barsu kawae momy, amma koma me nayi mata a gidan nan baxanyi nadama ba ko dana sani saedae duk abinda xa ayi min a min, amma sae nahallaka ta. Hajiya tayi ajiyar xuciya tace"shknan son, na baka go ahead kayi mata duk abinda yaxo knka." ya juya ya fice ba tare da ya sake cewa komai ba, yana tunanin irin abinda xae yi mata idan ya kamata, sadeeq kuma har gidan ubansa xae je ya samesa. . . Yau tun da gari ya waye intisaar batafita ba, duk ta rasa abinda ke mata ddi a gidan ga yawan faduwar gaba da take yi duk ta rasa sukuni, ko islamiyya ma taki xuwa da yake ranar lahadice, tun bayan abinda tayi ma ya Aliyu jiya da daddare ta kasa samun nutsuwa har ynxu, tayi da ta sanin abinda tayi masa yafi a kirga, tasan baxa ta ji da ddi ba idan tashiga hannunsa,to ma wae me ya kai ta, kai xuciya ma dae ba a iya masa, jiya ce rana ta farko da tayi ma ya Aliyu hk, momy tai tayi da ita ta gyamata me ke damunta taki fadi, sae dae tace ita bbu abinda ke damunta, ta mike daga kwance da take tana kallon agogo karfe goma da minti goma na safe, hijab din ta ta dauka ta leka bedroom tace ma momy ta tafi wajen inna, momy ta dan ji ddin hka don ta rasa kan 'yar tata, tace "to ki gaida min ita," tace "to" sannan ta fice gabanta na mugun faduwa, gudu-gudu sauri-sauri take tafiyar, gidan tsit don duk 'yan matan gidan sun tafi islamiyya, sllma tayi kofar falon abba jikintana rawa, abba ya amsa ta shiga ta nemi gefe ta xauna tana gaida abban, abba ya amsa da fara'arsa yace ta tashi ta xauna kan kujera,takoma kan kujerar, abba yace "me ya hanaki xuwa makarntar yau?" ta kirkiro murmushi ta lafta masa karya, "wanki nayi abba," yace "to yyi kyau" bbu matsala ko? Ta dan fara kame-kame, tace"aa...dama...abba.." wayr abba tayi ring ya dauko yana duba mae kiran nasa, ya daga.Shiru intisaar tayi ta jingina kanta jikin kujerar tana tunanin me xata ce da abba, sllmr da taji da muryar mae sllamar yasa xuciyarta ya kusa shigewa cikinta don tsoro, da kyar ta iya amsa masa tayi saurindauke kanta, Aliyu ya shigo palon sanye da bakar jallabiya, kallo daya yyi mata ya dauke kansa ya nemi gefe ya xauna ya tsura ma A.cn dake ta aiki a falon ido, ta mike jiki a sabule xata bar falon don har ynxu abba waya yake, abba yyi mata alama da hannu ta koma ta xauna, ta koma cikin rashin kuxari ta xauna tana wasa da long fingers dinta, ta saci kallon Aliyun taga kallonta yake yi, da sauri ta dauke kanta xuciyarta na bugawa, abba yagama wayan ya juya yana kalln Aliyun yace "sae ynxu garin ka ya waye knan malam," ya shafa kansa ya danyi murmushi yace "kayi hkuri abba, yau na tashi da ciwon kai ne," abba baice masa komai ba illa Allah ya sauwake, yace"ameen" sannan yace "ina kwana abba," lfya lau, ka tashi lfya?" abba ya amsa yana kallon intisaar da har ynxu kanta a sunkuye yake, kun gaisa da yayannaki ne? Ta dago kai da sauri tace "ina kwana yaya?" Aliyun yace "lfya lau, da kina jiran na gaida ke ne halan" ya fadiyana kirkiran murmushi ganin yanda abban nasa ya kafa masa ido, ita din ma murmushin ta kirkiro tace cikin muryar da ba tata ba"kayihkuri na sha'afa ne" abba ya dubi intisaar din yace "yauwa ina jinki fatima," ta gwalo dara-daran idonta ta rasa me ma xata ce da abban, sae kawae ta samu kanta da cewa "aa dama abba gidan momy nke sonnaje ne yau," abba yace "wace momyn knan?" da sauri tace "momynsu maryam" yace "ohhk gidan nafisa xaki" tace "uhm," abba yace yaushe xaki dawo idan kinje? Da yamma xan dawo abba, ta fadi da sauri tana kallonsa, duk da tasan idan taje ba lallai bne ta dawo kuma, kila can xae fiye mata xaman lfya. "wa xae kai ki knan?" tayishiru sannan tace "xan hau tricycle abba" abba yace "aa Aliyu dae ya kai ki, tunda yana gida. Intisaar ta dago kaida sauri tana kallon Aliyu, taga yyi wani murmushi irin tamugunta, ta girgixa kai gabanta na faduwacikin tausasa murya tace "abba ya haisam yace xae kai ni kuma..," Aliyu ya kalleta yana murmushi yyi saurin cewa "ni cinyekixanyi a hanya knan?" ita din ma kirkiran murmushin tayi tace "aa ba hka bne, kaga na riga da na fara gya masa, da bn gaya masa bne sae ka kaini," to ai ni da haisam daya ne, meye a ciki idan ni na kai ki din? Ya tambayeta yana kallon tsakiyar idonta, Ta xaro ido xuciyarta na bugawa tace"gskya ne," abba yace "toma wae a ina kika ga haisam din?" ta fara kame-kame tama rasa abinda xata ce masa, abba yace"tun asuba ya shigo yace min xae tafi jigawa, ko ya fasa ne?" ta dan sata kallon Aliyun da ya kafa mata ido yana murmushin da ta san na mugunta ne, ta rumtse idonta cike da tsoro tace "na manta ne, hka ne abba," Aliyu yyi 'yar dariya yace "to yanxu kin yrda na kai ki?," tace "uhm" yace "aa kiyi magana mana, ta mike tana cewa "bari naje na shirya," abba ya kirata ya dauko dubu biyar ya bata, yace"ki gaida min dasu shaheed," ta durkusa har kasa tayi masa gdya sannan ta fice da sauri kafarta na hardewa, abba yyi murmushi, yana jin ddin alakar 'ya yan nasa, don a nasa tunanin, Aliyun son intisaar din yake, ganin actions dinsa. Intisaar na fita da gudu tayi sashinsu don tana tsoron kar ya biyota, momy ta kalleta tace "har kin dawo?" tace "uhm, momy manta da innar nan, gyangyadi take ta minna gudo," bedroom ta shige da sauri ta fada kan gado, ae xuwa gidan anty nafisa kam ya sha ruwa ysu don ko hauka take ita kam baxata bi Aliyu ba. Aliyu kam yana barin falon abba ya shige bedrom dinsa cike da jin ddi ya shirya, irin abinda xae mata ya dinga kitsimawa a ransa, rannasa na dada baci, ya gama shirinsa tsaf ya fito,hajiya na tambayrsa inda xa shi amma baetanka mata ba, kujera ya ja a tsakar gidan ya xauna jiranta, amma har kusan karfe sha daya da rabi bata fito ba, ya gaji da jiragashi bbu kowa a gidan bare ya aika kiranta, shi kam yau idan bae ma yarinyar nan abinda ke cikin ransa ba ciwon xuciya xae iya kamasa, yyi huci me xafi ya mike tsaye yana waige- waige, kasa daure wa yyi yaje sashin nasu, yana isa ya bude kofar falon momy na xaune tana duba wani littafi, intisaar ma lkcn ta fito falon tana kwance tana kallon Mbc2, ya kalli intisaar din ya dake yace "kin shanya ni ina ta jiranki?" ta mike tana kallonsa tace"tafiyar nan fa ina ga na fasa kayi wuce war ka kawae," ta juya ta shige bedroom xuciyarta na bugawa, don taga kkrinta na fada masa hkn, tsaye yyi bakin kofar kmr ruwa ya cinyeshi, ya juya ya bar wajen xuciyarsa na harbawa, lallai yarinyar nan tadauko hnyr raina shi ne kuma xae yi maganinta, ransa a bace ya bar gidan yanatunanin me xae ma intisaar yaji ddi idan ta shiga hannunsa?" kiranta momy tayi bayan ya fice fuskarta daure tace "meya hada ki dashi, kuma ina xakuda?" nan ta koro ma momy yanda sukayi momyn ta hade rae tace "karki kuskura, ko da wasa kuma." yau kusan sati biyu knan suna wasar 'yar buya da Aliyu duk inda tasan xasu hadu bata xuwa, bangaren inna ma ba kasafai take xuwa ba kullum dae tana kunshe a daki kmr sabuwar amarya, shi kam kullum cikin addu'ar ta shigo hannunsa yake, ya rasa kwanciyar hankli har sae ya mata abinda ke ransa har gobe idan ya tuno kalamanta sae ransa yyi mugun baci, ya ma daina ganinta kwata-kwata a cikin gidan, har yyi tafiya xuwa lagos basu hadu ba. faruuq kam kullum suna manne da juna, idan bae xo ba to xai kirata, shakuwarsu ya wuce misali, shi kullum matsalarsa ta xamomatarsa, dn yaxo ya sami inna tace ya bata wata guda suna shawara ne da abba, to gashi har anyi wata biyu shiru, intisaar a ko da yaushe cikin kwantar masa da hnkli take, takan ce masa ae babba baya magana biyu, tunda inna tace ya kwantar da hnklinsa an bashi, kawaeya daina tada hnkalinsa ita din tasa ce. yau kam wajen innarta ta shirya xata je suyi hira don ita bata cika hira da momy ba, falon abba ta fara shiga da sllamrta tana tunanin ko dae ta jaraba abinda maryam tace mata a kan karatunsu, "ya dae fatima ba matsala ko?" abba ya tambayeta bayan sun gaisa, tayi murmushi tace "dama abba ca nayi don Allah ka bar mu muci gaba da karatunmu," abba yyi murmushi yana kallonta yace "karku damu fatima, xakuyi karatu sosai ammaa gidan maxajenku, don hka tsarin inna yake, kinga nafisada kike ganinta ita ma a gidan mijinta ta karashe karatun ta kuma kinga ynxu tana aikinta," tayi shiru kanta a kasa, duk da bata so hkn ba, kawae tace masa "to abba ngd" Abba yyi murmushi yace "dama ina san magana dake intisaar, wannan yaron da yake xuwa wajenki faruuq kin tabbatar kina sonsa?" tayi shiru ta kasa cewa komai ga kunya da ya lullubeta, abba ya cigaba dacewa"manyansa sun xo sun sameni ne, amma nace su dakata don akwae wata shawara da mukeyi da inna, duk me ake ciki nace xan sanar da su," ke kina sonsa?Ta sunkuyar da kai bata ce komai ba sae wasa . ... Salon ku batawa dana suna daga ke har gantalalliyar yar taki, to ahir dinku, aure kuma kmr anyi an gama ne indaiina raye, ina nan ina lissafi yau shekara daya knan da ta kaso aurenta ta dawo mana gidan nan take ta tsula tsiyarta kun sa mata ido, umma a fusace ta mike tana rike da kugu tace "to a kanki take xaune a gidan ko kuma ciyar da ita kke ko....." tsawa abba ya daka mata ya mike yana kallnta a fusace "fice min daga falo," inna da tuni ta fara matsar kwalla tace "wllh ka korata idan ba hka ba ni xan bar maku falon," umma tace "ko bka fada ba dama, amma wllh tllh baku isa kuma 'yata dole ba" ta juya fuu ta fice, fadila ta mike ita ma tana kuka xata fice Aliyu ya daka matatsawa "gidan ubanwa xaki, c'mon get back kar na ballaki" ta koma tana goge hawaye ta xauna, abba ya dubeta fuskarsa a hade yace "ki sa a ranki cewa nan da wata biyu ne bikinki, kuma daga yau bna sn ko kusa da gate ki je," inna ta cafke "ae wajena ma xata dawo har ranar bikin, kinakomawa ki tattaro kayanki ki dawo bangarena" abba yace kin dai ji, kuma bna son a tunasar dake a kan hkn, hajiya ta rike haba cike da jimami tace "abu dae bae yi ddi ba, kuma nasan wannan xugi ne akayi, amma Allah ya fi koma wa yyi," ta fadi hkn ne tana satan kalln momy da tayi jigum tana sauraransu, abba yyi tsaki yana kallon hajiyar amma bae ce kmai ba, ita kuwa sae girgixa kafa take bakinta a tabe, haisam kam tv ya kafa ma ido, abba ya dubi haisam din yace "ya maganr da mukayi da kai haisam," haisam ya danyii murmushi yace "abba ni na amince ae xabinku shinenawa," abba yace "to Allah yyi maka albarka," yace "ameen abba," abba ya dubi maryam din Anty nafisa yace"daughter kema dae kin amince ko?" ta rufe fuskarta bata ce komai ba, abba yyi murmushi yace "to Allah yyi maku albarka, yasa hkn shi yafi alkhairi," gaba daya falon suka ceameen, inna baki har kunne sae sa masu albarka take, Aliyu yyi dubara ya koma gefen haisam murya can kasa-kasa yace "wae da maryam abba xae hadaka kace ka amince?" haisam ba tare da ya kallesa ba yace "um" Aliyu ya wara ido da mamaki yace "gosh, amma an cuceka, kai din yaro ne da xa a xaba mka mata, me xakayi da wannan kwailar da bata wuce 18 ba battun ga big babes a gari? Kaiian cuceka wllh, ae abba yasan baxanyi toleratn hkn ba shiyasa bai dosheni da wannan wawan xancen ba," in kagayanda ran Aliyu ya baci sae ka rantsa kace shi aka xaba mamata a lkcn, amma haisam ko a jikinsa don bai da wata mafita tunda abba ya dde yana masa mgnr ya fito da mata,kuma abba sae da ya nemi shawarsa kafin ya hadasa da maryam, kuma dae maryam kanwarsa ce, bayan hka ma maryam kyakkyawa ce ga ilimi both, sannan ga hnkli da nutsuwa shi kam bae ga aibunta ba shiyasa bae ma yiwa abbansa musu ba don yasan warce ya so a rayuwarsa baxae taba samunta ba, wato intisaar. Hajiya kanta sae faman hararar haisam din take kmr ta makuresa amma yaki dago kan, yau dae xafi Alhaji da uwarsa sukayi niyyar tarawa umma, tunda gashi 'ya yanta biyu gaba daya auren hadi xa a yi masu, tab ae ita kam baxata yi tolerate din wannan ba. Intisaar sae tsunkulin maryam take yi tana 'yar dariya tana cewa "amaryar yayanmu," xainab ma hka ta dan dinga tsokanrta murya can kasa, ita dae bata ko daga kai ta kallesu ba, Abba ya kira Aliyu dake ta hararar inna da 'yar ta nafisa don yasan sune kan gaba akan wannan abun,ya dago kai fuskarsa a dan daure yace "na'am" abba yace"ya maganar aure fa?" ya dan yatsine fuska yace "ban shirya ba abba" abba ya tsura masa ido yana kallonsa kanayace "matarce bbu ko kudi?" ya tabe baki yace "duka" don bae ga dalilin wannan tambayr da abba yake masa gaban yan sa idon nan ba, har da inna yake nufi da momy, dama shi daya abba ya kira ya tambaya da xae ce masa yana da safeenah, amma ba gaban wannan group din da ya tara ba. Hajiya taji ddin yanda dan nata yaba uban nasa amsa har ta kasa boye hkn sae murmushi take, abba yyi murmushi yace "to yyi kyau," sannan ya juya yana kallon intisaar yace "ke inna tace akwae me nemanki ko?" gabanta yyi mugun faduwa ta sunkuyar da kai bata ce komai ba, abba ya nisa yace "baxan iya bashi ke ba fatima, ke din tamu ce baxan bari ki fita daga gidan nan ba sae daeyyi hkuri, amma idan har yaga akwae wanda yake so a gidan nan xan iya bashi, don naga inna ta yaba da hnklinsasosae," kmr saukar aradu mgnr ta dinga xuwa ma intisaar ta kasa dago kanta sae jirin da take gani daga xaune, falon yyi tsit kowa na kallon abba, ita kanta xainab sae da tayi mutuwar xaune don maganar ta girgixa ta sosae, abba yyi shiru sannan yaci gaba da magana kmr hka, "ynxu abinda nke son kowa ya sani a nan shine, Ni da mahaifiyata munyishawara daga karshe muka kawo conclusion a kan cewa, na hada auren 'ya ta fateema da Aliyu, kuma ni din xan masa komai na auren tunda yace bae da kudi," final decision din da na ynke knan, don hka bna son wata magana kuma indae a kan wannan ne daga bakin kowa, ya fadi yana kallon su gaba daya. . .....Har daren ranar Intisaar bata daina kuka ba,ita kam tunda take bata taba shiga tashin hnkli irin na wnn rana ba, momy tayi lallashin har ta gaji ta kyaleta ganin kamar kara tunxurata take, ita gani take kmr momy ba sonta take ba tunda har taki cewa komae a falon, Zainab da maryam ma sun gaji da lallashin sun kyaleta, hka ma Anty Nafisa da ta hau ta da fada ganin lallashin nata da ake kmr xuga ta ake tayi ta kuka,ita kam ta rasa abinda ke mata ddi a duniya. Karfe tara da minti biyar na dare Haisam ya shigo falon nasu, momy na xaune ita da ihsaan suna cin abinci, ita ko tana kasan tiles a xaune ta kife kanta da kujera tun safe take a hkn, sllh kadae ke mikar da ita kuma da tayi xata dawo ta xauna taci gaba da aikin kukanta, dama tuni momy ta fita harkarta, don abincin ranar da ta xubo mata ma kin ci tayi, hkn ma yasa bata xubo mata na daren ba tunda abun nata kmr iskanci ne. Haisam ya gaida momy taamsa da fara'arta ta bar masu falon, ya dawo gaban intisaar ya durkusa yana kallonta kmr shima ya taya ta kukan, wani sabon kukan ta fashe da tana kallonsa gwaninban tausayi, ya xauna gaban nata hade da dago kanta cike da damuwa yace "haba intisaar, so kike ki janyo ma kanki wani ciwon ko," xubewa jikinsa tayi cikin kuka tace "ka taimakeni ya Haisam, ka ba ma Abba hkuri wllh bna son ya Aliyu, kasheni xae yi idan....." ya rufe mata baki hade da rungumota yace "ya isa hka kanwata, bbu abinda ya isa ya maki wanda Allah bai maki ba," a hankli ta fara kkrin hadiyekukan nata sae ajiyar xuciya da take yi, har lkcin yana rungume da ita, murya can kasa tace "ya Haisam," shima murya can kasa yace "kanwata" ta girgixa kai a hnkli tace"da ma kai ne" ya dagota yana kallonta yace "ni ne me?" wasu sababbin hawaye suka gangaro bisa kuncinta, ta maida kanta ga kafadarsa cikin rawar murya tace "dama kai ne Abba ya bani, Bayan sati biyu da faruwar lamarin, tana xaune ita dazainab da kursum a tsakar gida, su suna cin gyada suna hirar irin abubuwan da xasuyi a bikin fadila da ya rage saura sati biyu don abba ya maido dashi kusa a dalilin fitsarar da taje tayi ma inna wae sae tace ma abba ya janyemaganar aurenta da mai 'ya ya har uku tunda ita ce ta xugasa ya hadasu dama, kowa dai yasan umma ce ta sa taxuwa tayi ma innar hka, inna ko ta kwashe abinda ya faru da wanda ma bai faru ba duk ta tsara mar abba tana matsarkwalla, har da ce masa da bulalarta taxo wae xata mata duka, kuma daga Aisha har shafa bbu wanda ya hanata suna kallonta, abba yasa Haisam ya xane ta snn ya maida bikin kusa. intisaar tayi xurfi cikin tunanin da tke yi, xainab ta kwashi bawon gyadar da suka gama ci ta watsa mata su, ba shirita dawo daga duniyar tunanin da ta shiga, ta hade rae tace "meye hka xainab," xainabta dawo gefenta taxauna tana kallonta tace "haba intisaar ke baki da aiki ynxusae tunane tunane, dubi fa yanda duk kika bi kika lalace," intisaar tayi narai-narai da ido kmr xata yi kuka amma ta kasa cewa komai, xainab tace "ynxu tsakaninki da Allah meye matsalarki ki gya min," nan da nan ta fara hawaye tana kallon Zainab din tace "ya faruuq," xainab tayi tsaki tace "yyi pick din cal din naki ne," ta girgixa mata kai a hnklitace "A'a, he ix nt still respondn," xainab ta tabe baki "to tunda ke kuma shashasha ce 'yar wahala ae sae ki ta kiransa, nan a gabanki ya haisam yyi ta kiransa ranar kinga ya daga, mutumin da har office ma ya bi sa, sae dae ace masa baya nn, alhalin kuma yana nn din, kwanakin baya kusan kullum sae inna ta kirasa kinga yana daga wayar, mutumin daya gujeki lokaci daya idan ba ma wauta ba meye na damuwa dashi," cikin kuka intisaar tace "haba xainab ba dole ya guje ni ba, ai tunani xae yi na yaudaresa ne, kuma ko..." xainab ta buga tsaki tace"gskya ne, sae ki tayi ai," snn ta bar ta wajen tayi gaba, kursum ma ta mike tace"duk kin bi kin daga ma mutane hankali akan wanda bai ma damu da ke ba, idan har sonki yake da gskya, ai baxae guje ki lkci daya ba, kuma idan shi dan mutunci ne bai ci ace ya ma ya Haisam abinda yyi masa ba" ita ma tana kai wa nn tayi gaba, ta kife kanta kan gwiwowinta, kuka take kamar ranta xae fita, ita kam ta ga rayuwa, ynxu bbu wanda xae fahimce abinda take ji a ranta, momy damatuni ta dawo daga rakiyarta, ga wani irin sabon tsana da hajiya ke mata a gidan don ji take kmr ta kasheta ta huta, hkn yasa bata da ikon ko lekowa compound, ynxu ma bata gidan shine dalilin fitowar ta tsakar gidan dasu xainab. Budewar gate din da taji ne yasa tadago kanta a tsorace don tayi tunanin su hajiya ne suka dawo, wani irin muguwar faduwar gaba yaxo mata ta dalilin hada idoda suka yii da ya Aliyu, tuni jikinta ya fara bari tayi saurin mikewa tsaye, tana kakkabe jikinta duk na karfin hali. Sae da taga ya wuce ta snn murya na rawa tace"ina yini," shima don gudun kar yace bata gaishesa bane, ta ga ya juyo yana dawowata inda take kuma, salati ta shiga yi a xuciyarta gabanta na ci gaba da bugu, shi knn ta ja ma kanta, da ta sani da bata gaishesa ba ma, gab da ita ya tsaya yana kallonta, ta kasa dago kai ta kallesa don tsoro,"kika ce me?" ya tambayeta cikin daga murya, ta fara kame-kame. "aa.. Dama ni em gaisheka nayi dama," ya fixgota hade da dago kanta yana kallonta, ta tsura masa ido ganin yanda ya rame sae idanuwa, lips din nn nasa yyi wani irin pink sae sheki suke. Wasu sababbin hawaye sukagangaro bisa kuncin ta. . Abba na barin wajen, Aliyu ya fito yyi hanyar gate yana hararan inna da har ynxu ke tsaye tsakar gidan tana kuka, inna ta bisa da gudu ta datse gate din tana cewa gidan uban wa xaka? Sae kuma ta shiga kwada ma Abba kira"Bukar maxa ka fito gashi nn xae gudu wllh," Abun dariya abun takaici, su fadila da kursum dake leke ta taga suka dinga dariya har da faduwa, nn da nn Aliyu ya saita murya ya marairaice mata yana rokan ta ta bude gate ya fita ynxu xae dawo, inna taki sae faman kwala ma Abba kira take tana cewa xae gudu, Haisam ya fito yyi bangarensu intisaar, ba a dau lkci ba suka fito tare da momy suka shigafalon Abba, duk wnn abun da ake akan idonsu hajiya dake leke ta taga ne, wayar Aliyun yyi ring ya duba ya ga Abba ne, ya maida aljihu, yace "don Allah inna ki bani waje na wuce, kati xan je siya," inna ta galla masa harara tace "ae wllh bbu inda xaka sae bukar ya ci min ubanka yau," dariya ta kubce masa, ya ko dinga yi har da buga kafa, karar da wayarsa ta sake yi ne yasa yyi saurin juyawa yyi bangaren innar, inna tace "gidan uban wa xaka, kar ka kuskura ka dosa falona," ko kallonta bai yi ba yyi saurin shan kwana, sae ga Abba ya fito fuskar nn tasa bbu alamar wasa xae yi bangarensu Aliyun inna tace "yyi bangarena maxa ka bisa" bai kara bin ta kanta ba yyi sashin nata, Aliyu kam bae tsaya sashin inna ba don yasan biyosa abba xae yi, yyi nisa da bangaren inna ya tsaya kare ma fence din gidan kallo duk electric wire ne, baxae yiwu ya dira ba, yayi jim kmr mai naxarin yanda xae yi sae kuma ya xaga kawae har bangarensu intisaar, ta gama dauraye kwanukan da suka ci abinci knn a bakin famfo ta juya xata shiga falonsu ta gansa, ta tsorata ainun, ta yo waje da ido cikin tashin hnkli,shiknn ta shiga uku gashi Abba ya kira momy ta tafi, ita kadae ce wajen don ko ihsaan ma na bacci a sashin inna, ihu ta bude baki xata kwada jikinta na bari yyi saurin fixgota hade da rufe mata baki ta fado kansa ya ja ta suka shige falon nasu ya kullo kofar. . 69..... Suna shiga falon ya turata yyi xamansa kan kujera, sai kuma ya mike ya bude fridge ya dauko ruwan gora ya dawo ya xauna yana sha, ita ko jingina tayi jikin bango xuciyarta na harbawa tana kallonsa,ya xabga mata harara"da'alla get out malama ki bar kallona idan ba hka ba na fasa maki ido," da sauri ta dauke kanta tayihanyar bedroom, ya daka mata tsawa,"cum back hia dabba gidan uban wa xaki, ba aiki kike ba" ta tsorata da yanda yake mata maganar ta dawo da sauri kuma ta bude kofar falon ta fita ta dauki broom ta fara sharan dole, to me ya kawo sasashinsu, Abba ta hango yana tahowa inna na biye da shi a baya "Bukar wllh yana cikin gidan nn baxae yu ace ya fita badon na datse gate din, bari dae mu duba ko nn ya yo," itakadae ke xubar ta don Abba ba sauraranta yake ba ma, intisaar taajiye broom din hannunta ta shige falonsu da sauri ganin basu ganta ba, kwance ta gansa kan kujera yana kallon tashar Mbc2,shi ynxu ko shakkar momy ta xo ma ta sameshi bayan abinda yyi mata yau baya yi, ya galla mata harara yace "ke fice ki banwaje kar na taka ki a nn, kar ki sake shigowa falon nn sae na fita," ta girgixa kaitace"A'a Abba ne naga yana xuwa nn....." ya mike xaune da sauri yace "nan yake xuwa?" ta gyada masa kai, yyi shiru sai kuma ya tabe baki yace "Allah ya kawosa lfy, get out ke kuma," ta juya xata bar falon sae kuma ta sake waigowa tace "har da inna fa," ya xaro ido yace "wat? inna" kawae sae ya mike yyi bayan kofa da sauri jin muryar innar, don yasan inna akwae xugi, xatai ta xuga abba ne shi kuma ya dauka yai ta xauna wa a ka, yasan hkn kuma baxae sa yaji da ddi wajen abban nasa ba in dae hajiya inna na gun. "ae yau kam mai raba mu dashi sae Allah ko Bukar?" Abba dae bai ce komai ba ya budekofar falon suka shiga, intisaar dama tuni tayi hanyar bedroom tun kan su shigo, inna ta kwado mata kira ta fito da sauri tace "abba sannu da xuwa," inna tace"Aliyu ya yo nan hka?" intisaar ta girgixa kaida sauri tace "aa ban gansa ba," inna kamrtayi kuka ta dage ita fa Aliyu na cikin gidannn bai fita ba, Abba ya sake dialin nmbrsa xae kira, intisaar dama na ganin yana danna waya tasan kiransa xae yi, duk ta rikice ta fara kame- kame"aa,.. Ab.. Abba aibai taho nan ba, emm kila de yana falon Hajiya ne, amma baya nn wajajen," kmr ance ta juya taga wayoyinsa har uku kan kujerar da ya xauna, ta xaro ido a tsorace ga abba ya dage sai neman kiran wayar tasa yake, cikin dubara tayi ta wajen kujerar da wayoyin nasa suke ta xare dankwalin kanta ta jefa kan wayoyin, sae kuma ta xube kan kujerar da karfi, gaba daya suka juya suna kallonta har suna hada baki "lafiya, me ya faru?" ta dafe kanta murya can kasa tace " kai na ke mani ciwo, jiri nake gani," Abba yace"subhanallahi, tun yaushe," ta sake marairaicewa tace "tun daxu," inna tace"bari ina da maganin ibba ki sha nasan shi ne," Abba ya bata dubu biyuta siyo magungunan da take sha ya juya ya fice, inna ta bi sa a baya tana cewa "wae to yanxu ina Aliyu ya shiga jama'ah, Allah yasa dae ba tserewa yyi ba," suna fita tayi ajiyar xuciya ta mike tsaye ta dauki dan kwalinta ta daura tayi hanyar kofar da saurixata rufe, ta kusan cin karo da momy, ta xaro ido cikin tashin hankali tace "mo momy kin dawo," Kallon mamaki Aliyu ya tsaya yi ma Haisam, "ka mareni?" Haisam ya matso gabansa yana kallonsa da kyauyace "an mareka din," inna tuni ta ja intisaar suka shige daki da sauri suna rusan kuka, cikin sanyin murya Aliyu yace masa "xaka gane kuranka," snn ya fice daga falon, hajiya da umma na labe bakin kofa tun bayan ihun inna na farko da ya fargar dasu suna lekan duk abinda ke faruwa, Haisam na fitowa umma ta bi sa da masifa kmr ta rufe sa da duka, "wawa kawae ko ina ruwanka oho," ko kallonta baiyi ba yyi gaba abinsa. Karfe shidda na yamma abba ya dawo gida bayan inna tasa su fadila su kira mata shi ya maxa ya dawo gida ynxun nn, abba ya dafe kansa bayan yagama sauraren surutan inna, gashi sai wani irin ihu take masu a falon , dama da belt din ta shigo falon dan abba ya gani da kyau, "kalle jikina" ta fadi tana nuna ma abba hannayenta da kafafuwanta, sai kuma ta sake fashewa da kuka har da kwantawa inda take tana cewa "wllh yau idan baka dau mataki kan wnn shegen hatsabibin yaro naka ba bar min gidan nn xakuyi daga kai har shi ba mae kwana gidan nn" su xainab sae boye fuska suke suna dariya, intisaar kanta ma dariyar take yi, su hajiya sai faman tabe baki suke suna hararta, momy kam kallon tv kawae take yi a falon, Haisam kuwa na gefen abbansa a xaune, Abba ya jinjina kai cike da takaici ya sake kiran Aliyun da ya kira yafisau goma sae dae yace masa yana xuwa, har ya gama ringin dis tym around ma bai daga ba, abba ya sauke ajiyar xuciya yana kallon innar da ta hade rai, ita kawae jira take taga hukuncin da xai dauka kan dan nasa, ya dubi haisam yace "je ka kace masa ko na xo na samesa ne," haisam ya mike knn xae fita sae ga Aliyun ya shigo da sllmarsa wanda idan ba kunne kasa ba ma baxa ka ji ba, ya nemi gefen khadija ya xauna, yana kallon abbansa fuska a daureyace "gani nn abba," inna tace "to uban waye bai ganka ba, mugu kawae munafuki algungumi, shaidanin mutum kawae, ma dae kam Allah ya isa bamu yafe mka ba" sae kuma ta fashe da kuka ta kwanta kan intisaar tana rerawa, har Haisam sae da ya dan dara a falon, su fadila ma sae yi suke yi, intisaar kadae ce ta hade rai kanta sunkuye, Aliyu yyi ma innar wani irin kallon bnxa ya tabe baki ya maida hnklinsa wajen TV, Abba yyi nisa yana kallonsa rai a bace yace "me intisaar tayi mka ka doketa da belt daxu?" inna ta mike da sauri tana xaro ido tace "kaji wani shirme irin na Bukar, intisaar kadae? Ae ca xakayi me intisaar da inna suka yi maka xaka xanesu da belet daxu, kai jama'ah ni saenaga ma kamr tsoron dan iskan dan nan naka kke yi wllh, idan ba hka ba kai ba ka tashi ka rama min Bukar, dukanmufa ya dinga yi yana kwallo damu kamr wasu 'yan cikinsa, yana xaginmu wae yau sae ya hallaka mu, da kyar Haisam ya kwacemu a hannunsa, duba jikina duk shatan belet ne, hka ma na yarinyar nn" ta gama magana tana huci, abba yyi murmushi yana gyada kai yace, "to miko min belt din baaba," ta mika masa da sauri har tana tuntube, ya mike tsaye ya mika mata belt din kuma yace "gashi nn baaba ki rama bugun da yyi maki, snn ki mika ma fateemah ma ta rama wanda yyi mata," abba ya koma ya xauna, inna tuni hakoranta suko yo waje, intisaar ta rike hannunta murya can kasa tace "inna kawae ki kyalesa don Allah, ki daina biye masa, kawae mu barsa da....." inna ta tureta da sauri rai bace tace " kaji min muguwar yarinya, a kan wani daliin xan kyalesa don uwarki, amma yarinyar nn muguwa ce wllh, ke idan baxa ki iya dukansa ba ma ni xan taya ki wllh" ta mike tsaye tayi wajen Aliyun tana huci, kowa sae hadiya dariyarsa yake a falon yana kallon inna, ita kuwa tsakani daAllah take abunta. "Bukar kace masa ya cire wnn katuwar rigar jikin tasa" abba yace "aa baaba ki rama a hka, shirt ce ai " inna tace "tam," Nan fa inna ta dage da dukka karfinta ta dinga xuba masa belt din tana huci, "mugu... mugu... Axalumi axalumi, mugu axalumi," abunda ta dinga fadi knn tana lafta masa belt din, dariya kam har da na hauka a wajensu fadila da xainab, abba kam murmushi kawae yake, haisam ma kansa dariya yake, hajiya kuwa mikewa tayi ta fice daga falon fuu, umma ma ta bita a baya. Aliyu kam ko gezau, sae dae tuni kamaninsa suka canxa idon nan yayi jajur kamr gauta, sae huci yake yana kallon innar, sae da inna ta gaji snn ta juyo tana huci ta mikawa intisaar belt din "tashi ki rama ke ma," intisaar da tuni ta marairaice fuska tace "ni dae na yafe masa," inna ta xuba mata belt din a kafa tace "to don uwarki ni xan rama maki," ta koma taci gaba da xuba masa belt din tana xaginsa, ta gaji don kanta ta ajiye belt din tana huci kmr warce tayi tseran gudu, Aliyu ya mike yana kallon dukkansu dake falon a xaune ya juya xae fice abban ya daka masa tsawa yace"kuma na bka sati uku ka miko min sadakin 'ya ta." . . Intisaar ta dago kai tana kallonsa ya gallamata harara yace "ba dae ice-cream xaki sha ba,ki shanye su tas ki bani rubbers din ynxun nn," tamarairaice fuska kmr xatayi kuka tace "Allahyaya karya take min ni ban ce...." ya batarankwashi mai xafi cikin tsawa yace "i did nt ask4 ur opinion, i only ask yhu to finish ol nd giveme d bowls," ta jawo roban ice-cream din a hnklita bude ta dauki spoon ta fara sha, ya mike yakoma kujera ya xauna yana kallonta, xainab tunita labe bakin kofa tana lekosu, inna da kursumdae sae kallon intisaar suke tana ta tura ice-cream, ita ga ta ba gwanar son ice- cream ba dontana shan rabi yake gundurarta, ta dago kai dakyar xuciyarta na tashi tace "wllh yaya na koshi,"ya galla mata wani mugun harara yace "xan kofasa maki kai idan baki shanyesu dukka ba," tunihawaye ya cika idonta tana kallon ice- cream din,inna ta fashe da dariya tace "oho dae can tamatse maku, ni ai ba ruwana da lamarinku, kujekuna kunyata ni gaban Bukar," kursum ma dariyatake hka ma xainab shi ko ya hade rai yanakallonta, yunkurin amae ta fara yyi saurinmikewa ya janye ice-creams din a gabanta, ya sakafa yyi ball da ita "don uwarki ciki xakiyi amanda" ta girgixa kai a tsorace tana kallon inna, yadauki rabin da ta rage ya kifa mata a ka, duksuka sauka jikinta, tasa kara don axabar sanyi ,shi ko ya kwashi sauran xae fita inna ta mike dasauri ta jawo robar furar da ke gabanta, yanaganin hka ya fice da sauri ta ko bishi da guduhar tana neman faduwa har waje ta bisa dashi takwara masa amma tuni ya bar wajen don bai mataba shi ba, "gantalallen bnxa kawae mugu," tafadi tana huci ta dawo da robar furarta, kwancetaga xainab da kursum suna dariya kmr wasumahaukata, har ita kanta intisaar din ma dariyartake, xainab tace "ko ba komai dae kinsha ice-cream yarinya, ina ma ni na sami hka," inna nashigowa ta hade rai tana kallonsu tace "kai dukku tashi ku bar mun falona wahalallun bnxakawai tababbun hofi," kursum ta mike tana dariyatace "ni ba sae kin xageni ba ma hajiya inna saeda safe" ta fice, intisaar ta mike da sauri ice-cream na xuba jikinta tayi bathroom din inna donma kar ta koreta don bata san inda xata ba. . ... Tura sa ta shiga yi a tsorace tana nemankwacewa daga rikon da yyi mata amma ta kasa,Aliyu kam bai ma san tana yi ba don idonsa yarufe yyi nisa a abinda yake yi, ganin Aliyu dagaske yake don har ya fara canxa salon abindayake yasa ta shiga dukansa a kirji tana kkrinkwace kanta da duk karfinta "don Allah ka rufamin asiri ya Aliyu kar ka min hka ina rokankaplss" a rude take masa magiyar tana kuka gninabinda yake shirin yi, bata xata ba kawae taji yawanke ta da mari ya shaketa yana numfashi dasauri da sauri, tuni yanayinsa suka canxa,hawaye kawae take hannnunta a baki tanagirgixa masa kai, sun kai minti biyar a tsaye ahkn, har lkcin bae cire hannunsa daga wuyartaba, amma numfashinsa ya dawo nml, ita daesunan Allah kawae take ambato a xuciyarta tanaduk adduar da ya xo bakinta ga wani mugunbugu da xuciyarta ke yi, fixgota yyi ya budebayan motar ya jefata ciki, ya shiga driver sit yaja motar suka bar wajen, wnn karon duk iriingudun da ya dinga yi bata sake gigin cewa komaiba, sae adduar da ta dinga yi kala-kala axuciyarta gabanta naci gaba da buga wa, dae-dae wani katon gida taga yyi park, tsoranta yalinku a kan nada ta toshe bakinta gudun kar tafasa ihu don hkn ba karamin aikinta bne, hawayesosai take yi tana kallon Aliyun, ya bude motarya fita ya kulle, ta bisa da kallon tsoro ganinyanda idonsa ya kada yyi jajur don duk wajenakwae wuta, taga yyi hanyar gate din yana wayaduk da ba jin abinda yake cewa take ba "nashigauku ni fateemah," abinda ta fadi knn a fili tanakuka, taga ko minti biyar ba a yi ba aka budegate din ya shiga. Kuka ta fashe da sosae tanarokan Allah ya kareta daga sharrin Aliyu, a hkabacci yyi gaba da ita cikin motar duk da ba nakwanciyar hankali bne. Karfe biyu saura Aliyu yafito daga gidan, ya bude motar ya shiga, kallodaya yyi mata ya dauke kansa, ya tada motar yashiga driving a hankali, ita ko har lkcn baccitake. Anty nafisa dae kasa daurewa tayi ta kiraxainab don ta san tana da hankali, ringin hudu tadaga cikin muryar bacci tace "Anty Nafisa," antynafisa tace "xainab kiyi hkuri nasan kinyi bacci,kina ina ne," cike da mamaki xainab tace "inafalon inna a kwance, me ya faru anty?" antynafisa tace "intisaar fa?" xainab tace "intisaarkuma, ae ca nake tana gidanki" "nashiga uku niNafisa, xainab don Allah bata dawo ba," tatambayeta a tsorace, xainab ta rude ta mikexaune tace "ta dawo ina?" anty nafisa tace"xainab tun wajen sha biyu saura na hadata daAliyu su taho....." xainab tace "innalillahi antymeyasa baki bar ta ta kwana wajenki ba, kinkirata yanxu?" nafisa a rikice tace "ina fa xainabduk wayoyinsu a kashe yake," xainab ta girgixakai tace "anty wllh ya Aliyu mugu ne, ynxu inaxae kai 'yar mutane cikin daren nn" anty nafisatace "innalillahi wa inna ilaihi raji un, ni kam nagata kaina, ki rufa min asiri xainab kar ki sanar dainna" sae kuma ta kashe wayar, baccin da xainabbata sake komawa ba knn, ita ma duk hankalintaya tashi ta shiga kiran nmbr intisaar din da Aliyuduk switch off, tasan yayanta bai da imani kokadan, to ynxu meye abun yi. To fa, ko ina ogaAliyu xae kara lulawa da matarsa oho.... Tam mudae 'yan look ne. .....A hankali Aliyu yyi parkin dae-dae bakin gate, ya juya for d first tym tunda ya fara drivin yana kallonta, har ynxu bacci take, ya kalle wrist watch dinsa ya ga karfe uku da minti biyar, ya shiga tunanin yanda xae yi, Haisam ya fado masa, sae kuma yyi saurin kauda tunanin, a dalilin tunawa da yyi ae har yau ba sa shiri, ya dae gama tunane tunanen mafita daga karshe ya yanke conclusion kawae ya kira Haisam, ringin biyu ya daga, Aliyu yace "xo ka bude min gate," snn ya katse kiran, bayan kmr minti biyar Haisam ya bude gate din, yyi drivin motar cikin compound din yyi park, ya fito ya kulle motar, haisam yace "daga ina hka" ko kallonsa bae yi ba yace "inda ka aikeni," Haisam ya ja guntun tsaki ya juya xae shiga ciki sae ga Abba ya fito, ya tsaya kallon Aliyun yace "daga ina hka Ali," ya dan shafa kanshi yace "No wani abokina ne ya kirani bai da lfya shine naje," abba yace"ok, ya hanya," yae "lfya" ba tare da ya kallesa ba ya bi bayan haisam da sauri, abba ma ya koma ciki... Haisam yace "wa yasani ma ko wajen shaye shayenka kaje," don bae ga alamar gskya a tare dashi batunda yaki tsayawa abba na masa mgna, Aliyu ya shige gabansa da sauri yana masa wani irin kallo yace "kace me?" Haisam yace abinda kaji snn ya shige bedroom ya kwanta. . Sae kusan asuba intisaar ta farka cikin motar, a hankali ta shiga bn motar da kallo da mmaki tana kokarin tuna abnda ya faru, nn da nn ta tuna, ta jawo wayrta da sauri ta kunna don ta ga karfe nawa, hudu da kusan rabi ta gani, hankalnta ya tashi, to ina Aliyu yaxo yyi parkin dinta ya wuce, ta matso kusa da glass din motar tana leken waje, mamaki ya kamata sosae ganin a cikin gida ne, nn da nn taji ta samu nutsuwa ta shiga hamdala a xuciyarta, wayarta yyi ring ta duba da sauri taga Anty ce, ta daga kan tace komai anty tace "intisaar kina ina ne," a rikice take maganar, intisaar tace "ina cikin motar ya Aliyu..." anty tace "mene? Kina me?" tace "nima ban sani ba anty," anty ta dakamata tsawa tace "don uwarki baxa ki gya min inda ya kai ki ba," ta marairaice kmr xata yi kuka tace "wllh wllh anty kawae yaje yyi parkin dina a wani gida ne, ya shiga ciki ya bar ni cikin motar ban kara ganinsa ba har nayi bacci, ynxun nn na tashi na ganni cikin motar amma a nn gida," anty tace "kin tabbata intisaar, ki gya min gskya donAllah," tace "Allah anty gskya na gya maki" anty nafisa tace "shiknn sae na shigo anjima," snn ta kashe wayar. Karfe biyar saura abba ya fito ya wuce masallaci, Haisam ma ya fito tare da Aliyu suka wuce masallacin, ta bi su da kallo, Aliyu ko kalln motar bae yi ba kmr bae san da mutum a ciki ba yyi gaba, tana nn a hka har su ka dawo daga masallaci har da abba, intisaar taji kmr ta fashe da kuka ganin inda kokallon motar Aliyu baya yi, ta bisu da kallo har suka yi bangarensu da haisam, sae kusan bakwae saura Aliyu ya fito yyi kusa da motar ya bude, abun dariya Aliyu bae bari sun hada ido da intisaar ba ya fixgotaya wurgar waje ya rufe motarsa ya wuce ciki, tayi bangarensu da sauri a tsorace, ta tarda momy na shara ta gaisheta duk da tasan batayi sllh ba don tasan momy xata yi tunanin bangaren inna ta kwana, momy ta amsa ba tare da ta kalleta ba taci gaba da abinda take yi, ta shige bedroom da sauri don ta samu tayi sllh kafin momy ta shigo. . .Karfe takwas anty Nafisa ta shigo gidan yayanta tayi bangaren su Aliyun xuciyarta na tafasa, don tun asuba take kiransa yaki daga wayar, ta kira Haisam tace ya basa yaki karba wai yana busy, direct bedroom dinsa ta shiga yana xaune yana danna laptop Haisam na rubutu a file, cikin bacin rai take magana tana kallonsa "Aliyu nagode da abunda ka min jiya ka kyauta, ni ai ban san kai mahaukaci bne mara tunani sae jiya, wllh kaci sa'ar abu daya yau da sae ka sha mamaki," ita daya ke ta kumfar bakinta, don Aliyu ko dago kai bai yi ba idonsa na kan abinda yake yi a laptop, hkn ya dada tunxurata ta fixge laptop din a fusace ta jefar kan gado tana cewa "don uwarka ba magana nake maka ba xaka maida ni mahaukaciya," ya mike a fusace yana kallonta yace "wllh kika bata min laptop sae kin siya min sabo," anty nafisa ta cakumosa rai bace " iyye! ni ka ke gya ma hka don uwrka, ai Aliyu da mari na kawae kayi ka nuna min kai tatattcan dan iska ne," haisam dae na xaune yana kallonsu bai ce komai ba, nananty nafisa ta dinga masa tijara tana xaxxaga masa rashin mutunci kala kala kmr xata maresa, shi dai ido kawai ya xuba mata yana kallonta sae dae ya tabe baki, sae da ta yi mai isarta bayan tayi ma haisam bayanin abinda ya faru ta fice tana cewa "jahilin bnxa kawae, a hkn xa a dauketa ma a baka idan ba jaraba irin na yaya ba, don inna tuni ta gama sarewa da kai," tana fita Aliyu ya mike ya ja dogon tsaki yce "kawae taxo da sassafe ta cika ma mutane kunne kmr wata sabuwar kamu," Haisam ya girgixa kai yace "kadae bi duniya a hankaliAliyu, indae mutum yyi da kyau...." Aliyu ya shakesa idon nn nasa ya kada yyi jajur yace "kace me dn babanka?" haisam yyi murmushi yanakallonsa kawae bae ce komai ba, hkn yasa ya turasa da karfi yace"don uwarka da ca nayi mka da gudu na bi duniyar," haisam dae bai ce komai ba ya fice ya bar masa dakin, ganin ransa ya bace sosae, don ahka suka taso in dae ran daya ya bace cikinsu daya na kkrin ganin ya fita harkar daya no matter abinda xae masa. Ganin inna da gaske take yasa Anty Nafisa ta fita ta kira abba ta sanar dashi abinda ke faruwa, abba ya rasa ma me xae ce mata don takaici, shi dae har ga Allah uwar nn tasa tana basa matsala tare da daga masa hankali a gidansa, yace ma Nafisar xae kirata snn ya kashe wayar, yana kashewa kuwa kiran inna ya shigo bai daga ba ya kashe wayar ma gaba daya.Ya kira Aliyu ta wayan Alhaji mukhtar yace masa yaje gida yanxun nn ya duba Fateemah bata da lfya, Aliyu ya danyi jim, har sae da Abba yace "kana jina," yace "eh ynxu xan tafi gidan," snn ya kashe wayar. Abba ya tura Alhaji mukhtar yaje gurin inna, bayan yyi masa bayanin da Nafisa tayi masa, Alhaji mukhtar yyi dariya yace "tsufa ne ba wani abu ba ke damun inna," ko rufe baki bai yi ba sae ga kiran innar ya shigo wayarsa, abba yace ya daga, yana daga wa kuwa muryarta kmr speaker cikin tsawa take mgnr "Mukhtar Mukhtar, ina Bukar, kace masa wllh tun kan nasa a kawoni inda yake yaxo ya raba wnn gantalallen auren da ya hada, don wllh baxaku kashe min jika a bnxa ba,kuma bbu shegen da ya isa yyi mata dole " alhaji Muktar ya dinga bata hkuri ya samu ya lallabata yace "gashi nn xuwa," yana kashe wayar yace ma Abba suje can gida abba yace aa shi dae yaje, a hka suka rabu Alhaji mukhtar ya kama hanyar gidan shi daya. Aliyu yyi parkin motarsa a kofar gida amma ya kasa shiga gidan sbda jama'ar da suka cika gidan ta ko ina, ya ciro wayarsa ya kira haisam yarakasa su shiga gidan tare Haisam yace masa yana ciki shimabae dde da shiga ba Anty Nafisa ce ta kirasa, da kyar ya fito daga motar ya shiga gidan yyi bangaren inna ba tare da ya kalli kowa ba duk da tsokanarsa da aka dinga yi, bbu kowa falon inna duk ta koresu ta kunna TV tana kallo fuskar nn tata a tsuke, da yake sun san halin innar kuma da sha'anin tsufa bbu wanda ya kawo komae a ransa sae dariya ma da suka dinga yi suka bar mata falonta, basu san inna da gske take ba, bakin kofa Aliyu yaci karo da Haisam ya fito daga falon ransa abace, Aliyu ya tambayesa me ya faru, yyi tsaki yace ka shiga ka gani, snn yyi gaba, . ya shiga falon yana kare ma ko ina kallo, inna na ganinsa ta dada tsuke fuska tana xare masa ido tace"inji dae da takardar jikata ka shigo" yyi mata wani irin kallo na rashin fahimta, da kmr xae yi magana sae kuma ya fasa yyi hanyar bedroom dinta, ta bi sa da gudu ta shige gabansa tana huci tace "wllh wllh ka ba jikata takardarta kar na tara maka jama'ar kano yau gaba daya,Abin ma dariya ya ba Aliyu, ya tsaya kallon innar yana gyada kai, yace "kan wani dalili xan bata takardar," inna ta gyara tsayuwa tace "sbda saura kiris ta amaye hanjin cikinta yau" dariya Aliyu ya dinga yi har da buga kafa yana kallon innar, inna ta bude baki tana binsa da kallo daga sama xuwa kasa a fusace tace, "ka maida uwarka Aisha mahaukaciya ba ni ba," nan da nn ya hade rai yace"kika ce me?" tace "abinda kunnenka ya jiye mka," bae sake ce mata komae ba ya bi ta gefenta xae shiga dakin ta tare hanyar da sauri tana huci, "nace takardarta kawae xaka bata," wani irin tsawa da ya raxanata ya daka mata, "da'alla ki fice ki ban waje hajiya, naki bada takardar," inna ta fasa ihu mai kara tana kiran jama'ah su xo su taimaketa duniya taxo karshe Aliyu ya bangajeta gefe, abun dariya abun takaici, Anty nafisa dama tuni ta yafa gyalentata bar gidan, momy kuwa can uwar dakanta ta shige, su hajiya da umma kmr suce wayyo Allah don ddi, ga gida cike dam da mutane . Hka inna ta dinga gabxawa da Aliyu kan sae ya ba intisaar takardarta kuma taki barinsa ya fita, dariya kam wasu har da hawaye, intisaar dae duk wnn abun da ake bata sani ba, bacci mai nauyi yyi gaba da ita. Aliyu kam ya kasa ce da inna komai sbda mutanen da ke wajen sae binta yake da ido tana ta xuba masa rashin mutunci, can dae ganin abun nata gaba yake ba baya ba yace "ke wllh baki da maraba da tsofaffin yarbawan lagos, dama can cikinsu kika je kika xauna da yafi maki alkhairi, haba mutum bashi da aiki sae masifa da fadan rashin gskya, wnn wllh duk halin tsofaffin yarbawa ne," nn fa Aliyuya sama ma kansa lfya, don xube wa inna tayi gun ta dinga rusa ihu wae jikanta ya hadata da kafurai yace mata tsohuwar bayerabiya, hehehe gidan Bukar dae ya tashi daga gidan biki ya koma gidan comedy, hmm bari kawae mu tsallake nn wajajen sisters. Karfe takwas aka gama walimar da Anty Nafisa da kawayenta suka shirya don kmr yanda Aliyu yace baya son ko wani irin party, Abba bae bari anyi komai ba duk da Anty Nafisa ta so ko dinner ne ayi, ynxu kam intisaar ta daina kukan da take yi sae dae ta xama kmr wata gunki ga muguwar ramar da tayi duk tayi wani irin sanyi tun bayan nasihar da Alhaji mukhtar yyi mata daxu da wani abokin abba, karfe tara aka fara shirye shiryenwucewa da amarya don abba yace ranar xa a kaita, inna ta shigo dakin rike da kofi tana wangale baki tace "maxa ki shanye wnn jikalleta, shine na karshe," sae ka rantse kace ba innar daxu bace.Anty Nafisa ta dago intisaar tana kallonta tana murmushi bayan matar da ta kawo musamman dongyaranta ta gama tsantsara mata kwalliya na fitan hankali bayan ta gama mata gyaran karshe, lace ne mai laushi da shegen kyau, shi ba milk colour ba, kuma ba light brown ba, da ratsin orange colour a jiki sae daukar ido yake, fuskar nn tata tasha cool make up, ga design din lallenta da yyi ma fara fatar ta kyau sae sheki yake, Anty nafisa ta dago fuskartatana kallon idonta, ta girgixa mata kai hade da bata rai ganin hawaye makale a idonta suna neman xubowa, ta dauki hankerchief ta goge mata hawayen, snn ta dauki babban mayafinta fari ta yafa mata a ka, . ta dauko mata takalminta shi ma farin ta saka, snn ta ja ta tayi bangaren Abba da ita yan rakiyarsu na biye dasu a baya, Nasihar karshe abba xae mata, fuskarta a rufe yake Anty Nafisa tayimata jagora har cikin falon Abba, ta xaunar da ita har lkcn fuskarta a rufe yake tana hawaye duk da Nafisa bata san kuka ma take ba, kamshin turaren Aliyu ta dinga ji a gefenta hkn yasa gabanta ya shiga faduwa, ta juya da kyar ta kalli gefenta taga Aliyu xaune shima kansa a kasa, yana sanye da shadda ruwan kasa yyi masa kyau sosai, cikin dubara ta dan matsa ganin kusa kusa suke,"fateemah" taji abba ya kirata cikin nutsuwa, ta amsa da dashashiyar murya tace "Na'am Abba," abba yyi murmushi yace "kin san abinda nake so dake," ta girgixa kanta ba tare da ta dago ba, nn daeabba ya dinga mata nasiha tun tana daure wa har ta kasa ta fashe da kuka sosai, hkn yasa Abba ya kyaleta ya juyo kan Aliyu, shi ma dae har Abba ya gama bae dago kai ba, sae maganar abba ta karshegareshi ne yasa sa dago kai yana kallon abban,"kuma Ali idan ka cutar min da fateemah bana tunanin xan iya yafe mka," *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Aliyu yyi wani kasaitattcen murmushi tare da maida kansa kasa, Abba ya sa masu albarka snn yace su tashi suje Allah ya basu xaman lfya, intisaar na gaba yana binta a baya mutanen da suka rakota falon suka rufa masu baya, anty nafisa kuwa ta tsaya don tana son magana da yayan nata kafin ta fita, sae ga inna ta shigo tana murmushi tace "Bukar Bukar, wae da ca nayi don Allah ko xan iya binsu na koma can da xama, don gskya gidan nn naka duk ya fitar min a rae barin da xasu barni ni kadae, dama ga matanka ba gani na da gashi suke ba gaba dayansu, can ko kaga muna tare gaba daya snn suna gani na da mutunci, idan ya so duk bayan wata biyu sae na dinga kawo maka xiyara nn ko ya ku ka gani....." abba ya juya cike da takaici yana kallon Nafisa da ta kauda kanta, ya mike tsaye rae bace yace "ae saeki bi su to" snn ya shige bedroom dinsa, Nafisa ta mike ba tare da ta kalli uwartata dake nn tsaye kmr gunki baki bude ba ta fice. Momy ta kasa ce da intisaar dake durkushe gabanta tana jiran tata wordof advice din kan xamantakewar aure komai, Nafisa dake kan su a tsaye tace "kiyi magana mana maman ihsaan lkci fa na wuce wa," momy tayi murmushi tace "Allah ya basu xaman lfya, kuma ya albarkaci aurensu, shi knn abinda xan iya cewa knn," anty Nafisa tayi murmushi ta dago intisaar dindake kuka sosae tace "mamanki ta maki addu'a fateemah, kice ameen," . intisaar ta xube jikin uwartata tana kuka sosai tace "momy ni bna son nabarki baxan iya ba, don Allah kice su bar ni, bana son naje ko ina," da kyar Anty nafisa da kawar momy suka fitar da ita daga falon don haukace masu tayi, momy duk iya dauriyarta sae da ta xubdama 'yar tata hawaye don taji tausayinta sosae, kuma sae gashi Allah bae sa tayi dacen miji ba, da har su Anty nafisa xasu kai ta wajen inna tayi mata tata nasihar aka ce masu ae fa inna na can tana ta rusa ihu, ba shiri suka saka intisaar a motar ita da kawayen nata, wato su zainab, Anty nafisa ma ta shiga motar suka kama hanyar gidan Aliyu dake can Hotoro, su Hajiya da umma dama tun da rana suka kulle kofofinsu kmr bbu kowa a ciki, don cikin lodin jama'ar da suka xo bikin bbu dangin hajiya ko daya bare kawayenta hka ma umma.karfe goma da kusan rabi motar da ta taho dasu tayi parkin cikin gidan Aliyu bayan mai gadi yabude gate din, abokinsa ne Mujaheed yyi drivin din, gida ne babba mai kyan gaske ya kawatu da shuke shuke ta ko ina masu daukar hankali, ginin tsarin duplex ne, dakuna uku da bathrooms a ciki each, sae babban falo da bathroom da toilet a ciki daga downstairs don sae ka hau stairs xaka tafi dakunan,kitchen din babba ne sosai sai kuma store dake cikin kitchen din, stairs uku xae yi lead dinka xuwa dinning din da aka xagaye da labule snn akwae kawatattcen garden dake ta bayan gidan, Anty nafisa ta fito da intisaar daga motar fuskarta a lullube suka hau stairs na balconyn, Anty Nafisa ta fadi mata adduar da xata karanta a kunne kafin ta shiga gidan kuma ta tabbatar da kafar damanta ta shiga gidan, sun tar da mutane da dama cikin gidanmasu jiran kawo amarya, har bedroom Anty nafisa da yan rakiyar suka yi ma intisaar jagaro suna guda, ita dae intisaar ji take kamr ba ita ba binsu kawae take kmr wata gunki, Aminiyar inna ta xaunar da ita gefen gadon tana ce ma mutanen da suka shigo suka cika dakin su fita su bata waje xatama intisaar magana, duk sae da ta koresu dakin ya rage daga ita sae Anty nafisa da xainab, maganganun da intisaar bata yi xato ba masu nauyita dinga gaya mata ga anty Nafisa tsaye, xainab dama tsum tsum tayi ta fice daga dakin, ita dae fuskarta a rufe yake, daga karshe ta dada mata nasiha sosai, Anty nafisa na tayata, kuka sosae intisaar ke yi tana tausayin rayuwarta don tana da tabbacin kila farin cikinta ya gama karewa a duniya, . karfe sha daya bakin suka watse gida ya rage daga Anty nafisa sae xainab don har ta kawayen amarya ma sun tafi, su ma suna ta shirin wucewa ne, dama Anty nafisa ta ajiye mata kayan baccin da xa ta saka snn ta nuna mata turarrukan da xata shafa kafin ta kwanta, ta tambayeta tana jin yunwa ne, tace A'a, ta fita kitchen ta hada mata wani tsumi ta bata ta shanye gabanta, lkcin da xasu tafi kuwa intisaar rungume anty nafisa tayi tana kuka sosai wae kar su tafi su barta don Allah tsoro take ji, sae da xainab tayi kuka don tausayin intisaar don gigicemasu tayi, da kyar Anty Nafisa ta lallabata bayan tayi assure dinta cewar yanxu su Aliyu xasu shigo don ta kirasa yace suna hanya da frndx dinsa kuma gobe in'sha Allah xata xo da safe snn ta samu suka bar gidan don mijinta na busstop yana jiranta, gidan ya rage daga intisaar sae halinta, kuka take sosae kamr ranta xae fita, ta kasa xaune ta kasa tsaye don tashin hankali, yau ga ta ga babban makiyinta xasu kwana gida daya, duk tabi ta takure kanta waje daya tana rawan sanyi tsoro. Karfe kusan sha biyu taji shigowar motar Aliyu, xumbur tamike a tsorace ta daura hannu a ka tace "nashiga uku ni fateemah," ta koma ta gefen madubinta ta tsaya jikinta na bari tana hawaye sosae, tana ji ya shigo gidan ya rufe kofofin, tun kan ma ya hayo sama ta dinga jin kamshin turarensa da ya shiga tada mata xuciyarta don tsabar tsoro. A hankali taji yana taka matakalan benen yana hayowa sama, xuciyarta ya tsananta buga wa, ta rumtse ido cike da tashin hankali tana yarfe hannu hade da shesshekar kuka, can kuma sae taji tsit kmr ba mutum a wajen, ta bude idonta a hankli tanakallon kofar dakin a tsorace, taji an bude kofa, saurakiris ta saki ihu jikinta ya dau rawa, kafanta suka kasa daukarta ta durkushe wajen tana maida numfashi kmr warce tayi gudu, a hankali taji an rufekofar da aka bude. ba dakinta ya shigo ba ta fadi a xuciyarta tana kkrin maida hawayen dake neman saukowa a idonta, ta xaune kan tiles din dake shimfide a dakin ta jingina jikin gadonta kanta a kangadon, kmr xata fara sabon kuka kuka, to ta tabbatar baxae shigo din ba, tayi jigum ta xuba ma kofar ido tana tunanin irin abinda Aliyu xae mata indae har ya shigo dakin nn, kila ma jefar da ita xae yi ta tagan dakin gaba daya, tunda wanda ya iya bude mota ya wurgota waje ae komai ma xae iya yi. A hankali intisaar ta bude idonta jin haske da ya addabi fuskarta, ta fara waige waige a tsorace tana kallon inda take, har lkcn tana jingine jikin gadon nea xaune, sun ray ne ya shigo dakin ya sauka kan fuskarta, ta mike da sauri tana kallon agogon dake manne a dakinta taga karfe bakwae, ta xaro ido hade da dafe kirji don ko sllh bata yi ba,ita bata ma san yaushe baccin ya dauketa da har gari ya waye ba, budewar gate din da taji ne ya sa ta xuwa kusa da window ta bude curtain dinta a hnkli tana lekan ma xa ayi, Aliyu ta gani cikin motarsa yana gaisawada mai gadi snn ya ja motar ya fice daga gidan mai gadi ya kulle gate, intisaar ta sauke ajiyar xuciya ta jingina jikin wall din dakinta tana tausayin kanta, ganin hkn ba shine gabanta ba yasa ta shige bayi tawanke bakinta tayi alwala ta fito, tana idar da sllh tashiga gyara bedroom dinta ta tabbatar komai yyi mata yanda take so ta feshe dakin da turaren da anty nafisa ta nuna mata xata dinga sawa a daki ta hada da room freshner snn ta shiga wanka tana gama wankan ta wanke bathroom dinta tsaf ta feshe ko ina da freshner snn ta fito dakin, tana cikin fito da kayan da xata saka taji an bude kofar, ta juyaa tsorace tare da sakin abinda ke hannunta a gigiceta fasa wani raxanannen ihu tace "wayyoo Abbana nashiga uku," Zainab ta tsaya baki bude da mamaki tana kallon intisaar, a hankali intisaar ta sulale kasa ta xauna tare da dafe kirjinta da ya kasa daina bugu da sauri,ta galla ma zainab din harara duk da taji dadin ganinta tace " dubeta don Allah, baki iya sallama bne malama xaki tsorata mutane," zainab tayi dariya tace "xa ma ki fadi gskya ne, wae ta tsamman angonta ne, shine xata wani wayance ma mutane" intisaar ta galla mata harara da wasa tace" angon bnxa, meye hadina dashi, " zainab ta tabe baki tace " kya ji dashi dae," snn ta karasa cikin dakin ta ajiye basket din dake hannunta da leda ta shiga fiffito da kulolin dake cikin basket din da flask,intisaar ta xauna gaban madubinta tana shafa mai zainab ta dago tana kallonta tace "kin tashi lfya amaryarmu," tayi kmr bata ji ta ba, zainab tayi dariyar tsokana tace "kice sae ynxu ma xakiyi sllhn, ina yayana, nasan kin sa shi makara yau da gani," intisaar dae bata kara kallon inda zainab take ba ta gama shafa mai ta shiga sa kayanta wani material mai kyau orange n milk colour, . Zainab ta sauka kicin ta dauko plates da cups ta dawo dakin tana kallon intisaar dake gyara fuskarta gaban madubi tace " wae yaya fa?" intisaar ta baxa mata hannu alamar ita ma bata sani ba, xainab tace "joke apart intisaar da gske baya nn," intisaar tace " Allah ni ban gansa ba ma tun jiya, daxu dae naji fitar motarsa" zainab ta tabe baki tace "to Allah ya kyauta, kice jiya ma baki ci 'yar kazar nn da madara ba" intisaar ta sauko kasa ta xauna kusa da xainab kmr xata yi kuka tace "inna fa?" xainab tayi dariya tace "ke dae bari, ai yau karfe 5 duk muka tashi a gidan nn wae xa tayi maku waina kuma a murhu xatayi, snn xata dama kunun gyada ta dafa muku ruwan lipton hadadde, ae mun aikatu yau, har da su farfesun kaxa da kayan ciki, duk ga su nn" intisaar tayi dariya sosai tace "Allah sarki innata, amma de ba yanxu xaki tafi ba ko xainab?" xainab ta galla mata harara tace "to uban me xan maki, ni de daukokuloli ki juye abincin nn don dasu xan wuce gida , kuma islamiyya xan wuce," intisaar ta kamo hannunxainab din hawaye ya cika idonta tace "Zainab ni kadae ce a nn tsoro nke ji wllh," zainab tayi dariya tace "xaki saba ne ai, kuma naga ai yaya na dawowa da yamma," intisaar ta goge hawayen idonta tace " aa ni dae ki bari anjima ki tafi don Allah," xainab tace to naji je ki dauko abu na juye maki abubuwan nn, intisaar tace "ni ban san ina ne kitchen din ba ai," xainab tayi dariya tace "yaya bai xaga dake gidan ba knn," intisaar ta harareta tace"wnn yayan naki mutum ne," xainab ta dinga dariya ta ja ta suka sauka falo suka xaga ko ina na gidan, intisaar dae bbu abinda ya burgeta game da gidan hasali ma ita tsanar gidan tayi, dakinsa kadae taki shiga duk da irin tilasta mata da xainab ta dinga yi tace baxata shiga ba, xainab din dae ta shiga ta fito.sae kusan karfe goma suka karya da xainab, ta dinga ji kmr xainab ta dawo gidan da xama kwata kwata. Karfe sha daya xainab ta tattara ina ta ina taxata tafi gida intisaar ta dinga kuka wae don Allah kar ta tafi, xainab tayi ta kwantar mata da hankali tare da assure dinta ae xata kawo mata abinci da yamma. . Da yammar kuwa Zainab ta kawo mata tuwan shinkafa da cous-cous sae dan fankasau da miya kusan kala uku, sae farfesun naman rago, intisaar tace " xainab na safen da kika kawo fa na nn har ynxu, ya xanyi da wa innan kuma" xainab ta harareta tace "to shi kuma yayan fa, ai ba ke daya inna ke yi ma ba, ke dashi ne," intisaar ta tabe baki tace "to ai sae ki jira randa ya dawo sae ki kai masa," xainab ta girgixa kai tace "intisaar knn, baki san ke mace bace kece xaki jawo hankalin mijin ki gare ki, duk wani tsoro da fargaba ki ajiye sa gefe ki daure....." intisaar ta dakatar da ita a fusace "kinga idan baxa ki min maganar arxiki ba kiyi shiru, ni fa ban dauke ya Aliyu matsayin mijina ba fa, yanda aka tilasta masa aurena nima tilasta min akayi, wllhwllh bana sonsa," xainab ta mike tace "to ai yyi kyausae kuyi ta xaune a hkan, kinga tafiya ta sae da safe." intisaar bata ce mata komai ba duk da bata ji ddin tafiyartata ba har ta fita daga dakin, karfe goma tana kwance kan gadonta rike da littafin hisnul muslim tana dubawa taji shigowar motar Aliyu, gabanta ya fadi ta mike xaune ta kashe wutandakin gaba daya, ta takure gefe daya xuciyarta na mugun bugu, har taji ya hayo sama ya bude dakinsaya shiga ya rufe. Ta sauke ajiyar xuciya ta koma kangadon tayi kwanciyarta ta lullube da blanket. Washegari tana kan darduma tana tilawa bayan ta idar da slln asuba taji fitan Aliyu da motarsa daga gidan, a xuciyarta tace ae indae irin xaman da xasuyi knn baxae dinga cin ubanta ba Alhamdulillah.Yau kwanan intisaar hudu a gidan Aliyu, amma ko sau daya basu taba haduwa dashi ba, in ya fita tun bakwae na safe baya sake waiwayo gidan sae karfegoma wani lkcn ma har sha daya na dare, ko kadan hkn bae taba damunta ba don ita gaba ma ya kai ta, ita kam bata taba tunanin Aliyu xae bar ta ta kai har wnn lkcn a gidansa ba tare da ya cuceta ba, sae daefa bai san cin ta da shan ta ba. Yanxu kam ta fara kwantar da hankalinta a gidan ta fara sabawa da xaman kadaici, dama yana fita xata fito ta gyara ko ina na gidan ta share ta goge snn tayi moppin, ta fito da kwanukan da taci abinci a daki ta wanke a kitchen ta gyara kitchin din ta tsaftace ko ina, ta kanyi mamakin inda Aliyu ke cin abinci safe da ranadon tasan shi ba gwanin cin abinci a waje bane da daddare kuma yafi shan tea ko coffee, indae ta shigo kitchen da safe ta kan ga mug din da yasha coffee da daddare sae ta wanke ta maida inda yake. Duk safe da yamma inna na ba xainab abinci ta kawo mata wani lkcin zainab ta dan tsaya taya ta hira wani lkcin kuma tace sauri take duk da tafi tsayawa ma da yamma, don da safe tana xuwa islamiyya, intisaar ta sa zainab ta kawo mata novels na turanci dayawa don ita bata fiye karanta littafin Hausa ba kuma kallo ishenta yake don wani lkcin sae ta yini bata kunna tvn dakinta ba, karatun da take yi yana matukar taimakonta don yana debe mata kewa sosai, wani lkcin idan ta gaji da karatun ta kan tafi garden tayi xamanta tana kallon tsuntsaye, yau ma kmr kullum intisaar na falo tana goge gogenta da ta saba, wajen karfe karfe sha daya na safe ne don Zainab duk ta bata mata lkci ta cika ta da surutu da ta kawo mata abinci da safe bata barta tayi aikinta ba don bata fi minti goma da barin gidan ba intisaar ta fara gyare gyaren gidan har lkcin kuma kayan barci ne jikinta, muryar Aliyu taji bakin kofa yana waya duk da bae shigo falon ba amma ya bude kofar, gabanta yyi mugun faduwa ta mike a tsorace tayi bayan kujera da gudu ta durkushe a wajen tana xare ido, taji ya karaso cikin falon tare da rufe kofar, bata kara jin takunsa ba ko ina yyi tsit, ta rasa inda ya shiga, a hankali xuciyarta na bugawa ta dan leko daga bayan kujeran da take ta gansa tsaye kmr mai naxari yanabin ko ina na falon da kallo, ta maida kanta da sauri tare da toshe bakinta gudun kar ta fasa ihu jikinta ya dau rawa, can dai taji yana hawa stairs har taji ya bude kofar dakinsa ya shige, ta mike tsaye da sauri jikinta na rawa tayi hanyar stairs da gudu bata lura da ruwan dake cikin bucket da take mopping ba tayi ball dashi ya kife a wajen tsantsi ya kwasheta tun kan ta kai ga fadawa kan centre table din dake gabanta don kansa ta ga take shirin fadawa ta fasa wani ihu, cikin ikon Allah bata wani buge ba, amma taci wahala ledar da Aliyu ya ajiye kan table dinma sae da ya fadi kasa, duk kayan dake ciki su ka xube cikin ruwan da ya malale ta ko ina a falon, intisaar duk ta rude ta mike da sauri tana rike da cikinta ta haye sama har tana tuntube ta bude dakinta ta shige.Tana shiga daki taji ya bude kofar dakinsa ya fito, takoma gefen gadonta da sauri gabanta na faduwa ta rakube ta dinga yarfe hannayenta tana hawaye, xuciyarta kmr xae shige cikinta don tsoro, yau kam tasan tata ta kare in ta shiga hannun Aliyu, tayi kusan minti goma a hka amma bata ga Aliyu ya banko kofar dakinta ba don ita jiransa kawae take ya xo yaci ubanta kafin hankalinta ya kwanta, ta mike tsaye da kyar jikinta na rawa, taji an bude kofa downstairs snn aka rufe, tayi kusa da window dinta da sauri ta dan bude curtain din tana lekan compound din, . tafiyar nn tasa yake ta kasaita yana sanye da shadda fara yyi mugun masa kyau, har ya isa kusa da motarsa dake ajiye a garage don bae fiye fita da ita ba kuma da alamar shigowarsa gidanaka wanke motar, taga wani mutumi ya mika masa makullin motar a ladabe snn ya juya ya bar gidan, ya bude motar ya shiga ya tada ta maigadi ya bude masa gate ya fice ta bi motar da kallo cike da mamaki anya kuwa Aliyu ne wnn, sae a lkcn ta tuna ashe ma ranar jumma'ah ce, don da safe kananan kaya ta ga a jikinsa da ta leko ta window don indae taji fitansa daga gidan to sae ta lekosa ta taga tun kan ya shiga mota, jikinta a sanyaye ta sauko downstairs, barnar da tayi yana nn yanda yake sae dae ya kwashe ledan magunguna da allurorinsa da suka xube cikin ruwan, ta dauki mop ta fara share ruwan da ya malale ko ina na falon, ba karamin gajiya tayi ba da aikin falon don sae kusan karfe uku komai na falon ya dawo dae dae, ta dauko turare ta feshe a falon snn taje tayi wanka a sama. Karfe biyar xainab ta kawo mata abinci tace ba dde wa xatayi ba don sauri take amma bari ta bata waya su gaisa da inna don kullum cikin mita take an hanata xuwa wajen jikokinta kuma an ki barin ta ta kirasu su gaisa, intisaar ta karbi wayan da murnarta suka gaisa da inna kmr xatayi kuka wae kullum ta kira Aliyu ya bata sae yace tana bacci, intisaar tayi yake tace eh hka ne inna, sun dde suna hira da inna daga bisani xainab ta kwace wayarta ganin suna nema su cinye mata kati tace "ke ma ai sae ki ce da mijinki ya siyo maki waya tunda baki taho da taki na da ba," intisaar dae bata tanka mataba sae murna take yau taji muryar innarta, xainab tace "daxu fa ya Aliyu ya xo gida," intisaar bata ce mata komai ba hkn yasa ta mike tace kinga sae da safe, intisaar tace Allah ya kai mu, gobe kice ma inna dan wake xata min, xainab tayi mata bnxa ta fice abinta . Ranar dae har tayi bacci bata ji shigowar Aliyu ba, washegari asabar ma bata ji fitarsa ba hkn yasa ta gane bae kwana gidan ba knn, karfe biyar da rabi zainab ta kawo mata abincindare, tuwon shinkafa ce da miyar ganye sae farfesun kifi, intisaar ta tabe baki tace "to ynxu ni canayi ma inna ina cin kifi," xainab tace " iyye samun waje, ba laifinki bne, kuma ni da kaina xan xuga inna nace tunda kinyi sati kawae ki fara girki," intisaar tayi dariya tace "ke kin isa ki shiga tsakanina da innata, ae ta dinga kawo min girki knn har sae nayi shekara," xainab tace gskya ne matar yayanmu, snn ta hada mata wani tsumi da inna ta bata ta kawo mata tace "gashi nn inna tace ki sha wnn," intisaar ta yatsine fuska tace "na meye," xainab tace "yana sa mutum yyi fresh, yyi kyau," ganin yanda xainab tayi serious kuma taga har da madara ta xuba ciki yasa intisaar ta yarda ta jawo ta fara sha, xainab ta danyi murmushin intisaar wawiya ce, snn ta bata turarrukan da inna ta bata takawo mata kusan kala uku, tayi mata sllama tayi gaba abinta. Karfe takwas intisaar ta gama kallon tasharta ta Mbc bollywood ta kashe kayan kallon snn ta kwashi kwanukan da ta ci abinci tayi kitchen dasu xata wanke, ta gama wanke wanken tana dan goge kitchen din da ruwa taji shigowar motar Aliyu, gabanta yyi mugun faduwa ta kife kwanukan da ta wanke da sauri har tana xubar da ruwa kitchen din don har wani bari jikinta yake don tsoro, ta kashe tap ta fito ta rufe kofar kitchen din ta haye sama da gudunta ta shige daki ko me ya dawo da shi da wuriyau don tasan ba lkcn dawowarsa bne ynxu. Tana jiya bude dakinsa ya shiga, ta kashe wutan dakinta snn ta shiga bathroom tayi wanka ta fito ta fara shafe shafenta gaban madubi, ta dauki turaren da xainab ta kawo mata ta shafa kamshin turaren yyi mugun tafiya da imaninta, dama ga ta gwanar son kamshi, ta lumshe idonta ta bude cike da jin ddi, ta tsura ma kanta ido a madubi tana kallo, ta yi murmushinta mai kyau snn ta mike ta dauki wani kayan barcin ta pink colour mai hannun singlet tsayin iya cinyarta sae wando da shima da kadan ya wuce cinyar ta saka, tana ji Aliyu ya bude kofar dakinsa ya fito ya sauka downstairs, ta san coffee kila xai je hadawa a kitchen, shi ko yana shiga kitchen tsantsin ruwan da ta xubar kan tiles ya kusan kwashe sa kasa, yace "subhanallahi,"yyi stilla wajen baki bude yana kare ma kitchen din kallo ransa yyi mugun bacewa ya juya a fusace ya bar kitchen din ya haye sama kmr wani zaki yyi hanyar dakinta.Yana hawa sama yyi hanyar dakinta a fusace ya sa kafa ya buga kofar dakin da karfi, tun da aka kawo ta gidan ranar ce rana ta farko da Aliyu ya shigo dakinta, tana xaune gaban madubi tana kokarin saka gashinta cikin net snn ta kwanta, ta mike a raxane ta yo waje da ido tare da dafe kirji muryarta na rawa tace " na nashiga uku ya ya Aliyu," bai ko damu da halin da ta shiga ba yyi kusa da ita yana huci cikin tsawa yace "don uwarki karya ni kike son yi a gidan nawa duk da fita harkarki da nayi da xaki xubar min ruwa a kitchen kiyi gaba," jikinta ya dau bari tana kallonsa, daga shi sae three quatre ko singlet bbu, ta fasa ihu ta haye kan gado a rude ta koma ta daya side din har tana faduwa cikin kuka tadinga cewa "wllh wllh wanke wanke nayi ya Aliyu kayi hkuri don Allah," ko sauraranta bai yi ba ya xaga yana kkrn cafketa, tana ganin hka ta sake fasawani ihun " wayyo nashiga uku xae kasheni, ya Aliyu don darajar iyayenka kar ka dokeni wllh baxansake ba," idan akwae abinda ya fahimta game da intisaar bae wuce na rashin son a taba lafiyarta ba, tana da tsoran duka sosai tun tana karamarta, ganin bbu inda xata bi ta gudu ne yasa ta dinga tsalle tana ihun kar ya doketa don Allah, hkn ya dada tunxurasa sosai ya karasa gabanta ya fincikota da karfi fuskar nn tasa bbu alamar rahamaya take mata kafa da tasa kafar, wani raxanannen ihu ta saki tare da kankamesa ta saka kanta kan yalwataccen kirjinsa jikinta na rawa "kayi hkuri ya Aliyu nace maka baxan sake shigar maka kitchen ba daga yau" cak ya tsaya, yaji wani yarr tun daga kansa har yatsan kafarsa, mutsu- mutsu ta dinga yi a kirjin nasa tana kuka hade da rokan kar ya doketa don Allah, ji yyi kafarsa ta kasa daukarsa, ya shiga turata daga jikinsa amma sae dada kankamesa take da karfi, . jikinsa duk ya mace, cikin muryar da ba tasa ba ya samu kansa da cemata "cikani," cikin kuka tace "Aa wllh dukana xakayi, kayi min rai ya Aliyu wllh baxan sake shigar maka kitchen ba nace"numfashinsa ya dinga fita da kyar snn ga wani mayen kamshi dake neman xautar dashi ba gashinta ba ba jikinta ba, bae san lkcn da ya saka fuskarshi cikin gashin nata ba shima ya kankameta da karfi har sae da tayi yar kara, to fa, nn ya Aliyu yashiga sumbatarta ta ko ina kamr xae cinyeta, a tsorace ta fara kkrin kwace kanta ganin hkn tana cewa "meye hka ya Aliyu, na shiga uku don Allah ka bari," cikin kuka sosai kuma a gigice take masa magiyan, maimakon Aliyu ya sake ta taga sai gaba abin nasa yake dada yi, kokuwa ta shiga yi dashi da karfinta tana cewa "wllh xan cije ka idan baka sakeni ba, wayyoo momyna na shiga uku, ka rufa min asiri ya Aliyu, wllh xan maka ihu," bata ankara ba taji ya ja ta sun xube kan gado, duk ya gama fita hayyacinsa, duka ta shiga kai masa da cizo da sauran karfinta don duk jikinta ya mace itama, wani gigitattcen mari ya kai mata hade da danneta da karfi snn ya soma rabata da kayan jikinta, ganin da gske yake yasa ta dinga ihu tana kiran duk sunan da yaxo bakinta tana kokuwa dashi, amma duk a bnxa dn karfinsu ba daya ba, . wannan dare kam intisaar baxa ta taba mance shi a rayuwarta ba don kaca-kaca Aliyu yyi mata tana ji tana gani, tun dagakan gado har suka sauko kasa, tai ihun tai ihun har ya kai ga muryarta ya daina fita, tai kuka tai kuka har ya kai ga bata iya kukan, tayi rokan har ta rasa wani iri kuma xata yi, Aliyu bai bar ta ba sai da yagata daina motsi, ya jima gefenta a kwance snn ya mike da kyar don shima ta bashi wahala sosai, wajen karfe biyu ya bar dakin ba tare da ya bi ta kanta ba duk da yasan suma tayi, yana komawa dakinsa ya shige bathroom yyi wanka duk jikinsa bakwari snn ya kwanta ya ja bargo duk da yasan ba barcin xa yi ba. . Sanyin tiles hade da na A.C snn da sanyin ruwan da aka tsula daren ranar suka taru suka farfado da Intisaar, tayi kkrin jawo rigarta ta rufe jikinta amma ta kasa daga hannun, bata sake yunkurin yin komai ba sae hawaye mai xafi da ya dinga saukowa bisa kuncinta, Aliyu ya cuceta, ya walakanta ta, yyi raping dinta, wayyo Allahnta, kuka ta dinga yi sosae da dashashen muryarta da ko fita baya yyi, sbda cikin sanyin da ta kwana, tana ji aka yi sllhn Asuba amma ta kasa ko motsi daga inda take, duk jikinta yyi tsami sosai snn ya mata nauyi, ta kara yunkurin tashi amma ta kasa, ga wani rawan sanyi da take yi, kuka sosae ta saki tana kiran Allah a xuciyarta, kofar dakinta taji an tura a hankali, gabanta yyi mugun faduwa, ya karaso kusa da ita ya durkusa, karkarwa ta shiga yi cikin dashashiyar muryarta take rokansa "ka rufamin asiri ya Aliyu, kasheni xakayi, don Allah don annabi don....." ganin ya dago ta ne yasa ta kwala ihu a tsorace har sae da muryarta ta fito don axaba, daukarta yyi ya daura kan gado, hade da rufe mata bakicikin sanyin murya yace "bbu abinda xan maki, amma kar ki sake min ihu," kai kadae ta gyada masa jikinta na rawa tana hawaye, ya mike ya shiga bathroom ya samu ruwa a heater ya hada mata ruwan xafi ya saka dettol sosae, ya maida wani ruwan a heater snn ya fito, tana nn yanda ya barta, kuka kam yinsa take kmr ranta xae fita, daukarta yyi ya shiga bathroom din ya saka ta cikin ruwan, ta fasa masa ihu "wayyo nashiga uku wllh da kwae xafi sosae yaya," cikin kuka take masa maganan sakamakon wani axababben radadi da taji bayan ya saka ta cikin ruwan, ya riketa ganin tana neman tashi yace"xae daina maki xafin rufe idonki," ba shiri ta kulle idon tana kuka, ruwan ya dinga ratsa ta, ya daura kanta bisa kafadarsa, sai da ya tabbatar ya gasa ta sosai, kuka kam tayi shi har ta gode Allah, don ita tun da take bata taba wahala hka ba, ya dauko tooth paste da tooth brush ya taimaka mata ta wanke baki, da kansa ya wanketa, snn ya taimaka mata tayi wankan tsarki ya nannadeta a towel ya fito da ita, jikinta ya dau xafi matuka, ya kwantar da ita bayan ya cire xanin gadon ya sa bargo ya lullubeta ganin yanda take rawan sanyi, sae da ya fara moppin din kasan tiles din dakin, snn ya dawo gefenta yana kallonta ya ga bacci take, hkn yasa ya dauki makullin motarsa ya fita siyo magani da allurori don bae da komai a gidan. Bayan kmr minti ashirin ya shigo gidan, sae da ya fara shiga kitchen ya hado mata tea snn ya hau sama ya shiga dakin wajen karfe bakwae da rabi, ya dago ta yace "ta shi ki sha tea fateema," da kyar take numfashi, jikinta kmr wuta, ya shiga lallabata ta sha tea taki, ita kam kukan bakin ciki take kawae, yyi lallashin amma a bnxa hkn yasa ya rungumeta yana cewa "bna son kukan nn fateema," lamo tayi a jikinsa tana ajiyar xuciya cike da tsanarsa, kofar dakin da aka murda yasa ya dago da sauri, ita ko ta fara kkrin kwace kanta daga rungumar da yyi mata don tasan xainab ce, da sllmarta ta shigo dakin tana cewa "wllh yarinyar nn kina ma yayana abinda kika ga dama a gidan nn, kamshin dettol har waje don ba ke kike siya ba ko," turus tayi a bakin kofar ganin yayan nata rungume da intisaar.Zainab ta juya xata bar dakin, Aliyu ya kirata da sauri, ta juyo ba tare da ta kallesu ba tace "ina kwana yaya," yace "lfya lau daga ina hka," tace"emm dama inna ce ta ce na kawo ma intisaar abincin break," ya gyada mata kai yace "cum in," ta karaso cikin dakin kanta a kasa ta durkushe gabansu ta ajiye basket da flask din dake hannunta,yace "meye a nn," tace " kunu ne da wainar shinkafada miyar taushe, sae dambu da kosae," yyi murmushin da bae shirya yi ba yace "yyi kyau, je dauko plate ki dibar mata wainar," tace "to" snn ta mike ta bar dakin, ya dago intisaar yana kallonta yace "me xaki ci fateema," ta kauda kanta da sauri, ta fara kkrin mikewa duk da yanda take jin jikinta kmr ba nata ba, ya rikota yace "ina xa ki," ta kwace hannunta snn ta mike tsaye, lkci guda ta fasa ihu tare da durkushewa kasa, sakamakon wani axababben xafi da taji a kasanta, ta kife kanta kan tiles, ya durkusa gabanta ya dago ta yace "menene,"bata ce komai ba sae hawayen dake xuba a idonta, ya dagota ya maido kan gadon, xainab ta shigo ta yiabinda yace mata snn tace xata tafi, yace "ok gyara mata bedroom sae ki wanke bathroom din tukunna,"tace masa to, ya mike tsaye ya dauka intisaar din kmr wata bby ya fita da ita daga dakin ya kaita nasabedroom din ya xaunar da ita kan gado, da kyar ya lallabata ta dan ci abincin da kunu, snn ya bata magani yyi mata allura shima da kyar, bbu abinda take yi sae aikin kuka, ya kwantar da ita tare da lullubeta nn da nn bacci ya dauketa, yana kwance kan kujera yana danna wayarsa xainab tayi sllma yace ta shigo, ta shigo tace yaya dama na gama ne xan tafi, yace mata ok snn ya bata dubu daya tayi kudin mota ta amsa tare da gdya ta fita, . lallai xa ayi ruwan sama da kankara yau, wae ya Aliyu ne har da bata kudi ta hau mota," tayi dariya sosae bayan ta fita, lallai intisaar ta gama mata da yaya jiya. Yinin ranar Aliyu bae fita ba yana gefen intisaar, duk wani motsi da xata yi a kan idonsa, dukda xxabin ya bar jikinta amma ta kasa sukuni don sae juye juye take, yasan ciwo ne ke cin ta, karfe biyar da wani abu ya fita siyo mata chips ganin taki cin duk abincin da xainab ta kawo mata (ko ya akayiyasan intisaar na son chips oho ma Haiydar) yana fita kuwa xainab ta shigo gidan da abincin dare, ta kasa shiga dakunan ganin level ya canxa a gidan, hkn yasa ta dinga rafka sllma amma shiru, ta sauka kasa ta samu maigadi ta tambayesa ko mutanen gidan na ciki, yace oga dae ya fita daxun nn, ta koma cikin gidan tayi hanyar dakin intisaar ta bude a hnkli bata ga kowa a ciki ba, hkn yasa tayi hnyar dakin yayan nata, xaune taga intisaar kan gado, ta kife kanta bisa gwiwwowinta, ta karasa dakin ta xauna gefen gadon tana kallonta, a hnkli intisaar ta dago kai tana kallon xainab din da idonta da ya gama rinewa alamar ta ci kuka, xainab ta girgixa mata kai ganin kukan take son fashewa da kuma ta rungumeta, ta ko fashe da kukan sosae cikin shassheka tace "xainab ya Aliyu mugune, ya cuceni,ya..." da sauri xainab ta rufe mata baki tace "sshii.. Ya isa hka, wnn sirrinki ne tsakaninki da mijinki," kuka sosae intisaar ta dinga yi xainab na lallashinta, suka ji an bude kofar Aliyu ya shigo dakin "wat," ya daka ma xainab tsawa yace "uban me ya kawo ki nn kuma," ta mike tsaye da sauri, ya daka mata tsawa ba da ke nke ba, ta xunburo baki tace "abincin dare na kawo maku," ya nuna mata kofa "xoki fita," . tayi hnyr kofar ba tare da ta kallesa ba tace inna tace ta fara girki daga gobe," yace"taji," snn xainab ta fice.. Cikin kwanaki biyun nn intisaar ta sami kulawa a wajen Aliyu sosae, don ynxu kam jikinta yyi sauki sosai, kuma duk wnn abinda yake mata baya bari su hada ido, ita kuwa dari dari take dashi don bata yrda Aliyun da ta sani bne wnn ga wani mugun tsanarsa da take ji a xuciyarta, sae dae kuma har lkcn bata iya takawa, yyi yyi ta bari ya dubata amma kememe taki, hkn yasa ya kira wata Dr Maryam warce suka yi karatu tare ta xo dubata, ya fita ya bar masu dakin, ita ma dae da kyar intisaar ta yarda ta dubatan. Bayan kmrminti talatin ta fito tana ma Aliyun wani irin kallo, yyi murmushi yace "ya akayi Dr," ta girgixa kai tace"amma wllh ka bn mamaki Dr, kai da kanka, kai da xaku dinga ba wasu shawarwari shine..." yyi dariya ya katse ta da sauri "gskya ne maryam, but tel me d truth don Allah, is it dat critical" ta galla masa harara tace "wnn kuma ya rage naka, though it's nt, idan na fita ynxu xan turo maid dita da drugs da injections da prescription dinsu sae ka mata, snn kadinga sa tana shiga ruwan xafi da dettol sosae, i will b on my way," yace "ok, bill dina fa Dr," ta hararesa tace " ae ba kai nayi ma wa ba, kanwata nayi ma, xan lekota xuwa jibi," yyi dariya yace "to ngd maryam," ta tabe baki tace "mugu kawae," snn ta fice, sunyi soyayya sosae da maryam suna sch, kuma lkci daya ya gujeta duk da irin son da take masa, shi kuma yana da dalilinsa nayin hkn. Ya haye sama ya shiga bedroom dinsa ya xauna gefenta yana kallonta, tana kwance idonta a lumsheduk da ba bacci take ba, shima kuma yasan ba barcin take ba. Cikin kwanaki ukun da intisaar tayi dakin Aliyu ta sami kulawa sosae daga gareshi don komai shi yake taimaka mata tayi, harta abinci shi da kansa yake bata, duk da tana yi tana dan noke masa, kullum da yamma sae Dr maryam taxo dubata har dae ta warware sosae tana iya yin komai da kanta, yana ganin ta warke kuwa ya fita harkarta ya daina tarairayarta kuma, snn yaki barin ta ta bar dakin nasa, tsakaninta da shi sae dae ya siyo mata abincin ya ajiye mata gabanta in ta so taci idan bata so ba ta barshi, ko kadan hkn baya damunta, ita dae 24hrs tana kallo abinta a dakin, shi kuma yana kan laptop dinsa, ta rasa dalilin da ya hanasa xuwa aiki ta tattara ina ta ina ta ta koma dakinta kafin ya dawo. Ranar friday, da yyi dae dae da kwanakinta biyar a dakinsa yana bathroom yana wanka ita ko tana kan gado tana kallo taga wayarsayyi haske, ta dan kalli kofar bayin, ta dauko wayar taxauna tana duba mai ya shigo wayan, msg din safeenah ne, ta bude tana yastine fuska ta karanta kmr hka,, Honey kwana biyu ka mance dani ko, naje har office aka ce ka dauki hutu, don kuji ddin cin amarcinku da matarka, ni dama nasan duk ddin baki kke min kawae Haiydar......" intisaar ta ja dogon tsaki ta cilla wayar ba tare da ta karasa karanta text din ba, can dae ta jawo wayan ta shiga yi masa binciken inbox na msg, msg din mata sun kai 50 a inbox din, to a ina ya sansu, hka ta dinga dudduba msg din har ya fito daga bathroom, ta tura wayar karkashinta a tsorace, ita dae tasan da wuya tsoran Aliyu ya rabu da ita lkci daya, sanye yake da farar t.shirt da 3quatre don duk xaman da tayi a dakinsa bai taba sa kaya gabanta ba, . hatta singlet baya tsayawa dashi a dakin, bae ko kalleta ba ya isa gaban mirrow ya dauki turare yana fesawa, wayarsa tayi kara, ya juya da sauri yana kallonta, gabanta yyi mugun faduwa ta ciro wayar daga karkashin kafanta, ta ajiye masa kan table din computernsa kmr munafuka, ya karaso ya dauka yana hararta yace "uban me kike da wayata" ta kauda kanta bata ce komai ba, kira ya sake shigowa, ya dde nn a tsaye yana hararta daga bisanni yyi kwafa ya daga kiran, "bbyna ykk, ayya ban manta dake ba wife, wllh abubuwa ne suka sha min kai, but gani nn xuwa ma ynxu, kiyi min fruit salad, kinji dear" yyi dariya snn ya kashe wayar, intisaar ta tabe baki tare da mikewa tsaye tayi hanyar fita, ya bita da kallo tare da daka mata tsawa, xo nn uban wa kike tabe ma baki hka," ta juyo tana masa wani irin kallo duk da irin yanda gabanta ke faduwa tace "ni na tabe baki ne," snn ta bude kofar, ya daka mata tsawa "ina xaki," ta juya tayi masa wani irin kallo snn tace "ae nn ba dakina bne," ya bude baki yana kallonta da mmki yace "da xa a kawo ki gidan nn a dauro maki daki daga gidan ku kin kawo nn ne," ta dan tabe baki bata ce komai ba ta kauda knta, "fice min a daki kar nayi ball dake a nn, raguwar bnxa kawae," ta fice daga dakin tare da jan dan guntun tsaki, ya bita da sauri yana cewa"uban wa kike ma tsaki," amma tuni ta shige dakintata kulle da makulli, tana jinsa ya ja motarsa ya fice daga gidan, . ynxu ita kadae tasan irin tsanar da takema Aliyu a xuciyarta, ranar dae har tayi bacci Aliyu bae shigo gidan ba, ga wani irin yunwa da take ji, dole ta tashi cikin dare ta shiga kitchen ta bude store taga kayan abinci, ta dauki indomie guda biyu da kwae ta dafa ta ci, sae a snn ta sami bacci. Tun daga lkcn kmr anyi ruwan sama an dauke Aliyu ya fita harkarta, tsakaninta dashi kallo, kuma shi ke kallon nata ba ita ba, don ko gaishesa bata yi a gidan, iyaka idan taji shigowar motarsa ta shige daki da gudu.. Randa ta ci ka sati uku a gidan tana kitchen ta gama wanke wanken kwanukan d a ta ci abinci da safe bayan Aliyu ya fita, tana sanye da dan jumper sae bum short, ta ji muryarsa ya shigo gidan, gabanta yyi mugun faduwa, shknn ta shiga uku, ta dan leka falon a tsorace taga ashe shi da safeenah ce ma, taga xae shigo kitchen ta buya bayan kofa da sauri, safeenar ta biyo bayansa tana cewa "honey irin coffee din nn naka xaka hada min ba tea ba," yace "ok bby," ta kwanta bayansa ya juya yana kallonta yace "ae sae ki sa na kasa hada coffeen bby, wait 4 me @ d parlor" ta kankamesa tana 'yar dariya tace "idan naki fa, wae ina matar gidan ne," tsit kke jin Aliyu, ta rungumosa ta gaba tana masa wani irin kallo gnn abinda take so knn tace "ya kayi shiru dear," tasan ba lallae bane ta samu amsa, hkn yasa ta daura bakinta kan nasa tana 'yar dariya, duk wnn abinda sukeyi intisaar da taji kmr numfashinta xae dauke na kallonsu ta bayan kofa, ita kam xuwa ynxu ta gama gane wanene Aliyu, ta gano weak point dinsa, ganin irin kiss din da yake ma safeenar tana mayar masa da martani yasa ta turo kofar ta fito, daga safeenar har shi sun tsorata, ta gabansu ta wuce tare da jan dogon tsaki tace uhum karuwancin ma har sae an biyo mutum gida don rashin sanin ciwon kai," can kuma sae ta juyo tana kallon Aliyun dake binta da kallo gabanta na mugun faduwa tace " ni dae malam kayi hkuri ka daina shigo min da karuwae gidana idan ba hka ba Allah xan hadaka da Abba,".... A fusace Aliyu ya fixgota da karfi yana huci cikin tsawa yace "me kika ce?" tuni jikinta ya dau rawa don tsoro, ya maimaita tambayr cikin tsawa, amma intisaar bata ce komai ba sae daure fuska ma da ta dada yi, hkn yasa ya makureta tana ganin hka ta fasa ihu mai kara tare da durkushewa a wajen, ya bi ta da sauri tare da rikota, a rikice ya fara tambayarta mai ya faru, ta sake fasa ihun hade da sakin kuka sosae, yace "subhanallahi, wae me ya faru fateema," ya shiga dudduba kafarta da jikinta a rude, ta buga masa hannu tare da mikewa tsaye, "to ba kai bne ba xaka wani dokeni bn maka komai," ta ja tsaki tare da juyawa ta fara barin wajen cikin tafiyarta mai jan hankali, Aliyu ya bi ta da kallo kmr wani soko, ya dan sauke ajiyar xuciya ya juya yana kallon safeenah dake kallonsa tamkar xata hadiye xuciya don takaici, ya wara mata manyan idonsa yace "ki kyaleta kawae, yarinya ce, ko ni kai na bana biye mata a gidan nn," tana huci tace "xata gane kuwa ita ba yarinya bace yau," ta yi hanyar stairs din da sauri kmr xata tashi sama, "ke ke kina da hnkli kuwa ina xa ki," amma tuni ta haye sama a fusace tayi hanyar dakin intisaar, ya bi bayanta da sauri yana kiranta, ta shige dakin bayan ta buga kofar da karfi, intisaar na kkrin cire kayanta ta shiga wanka ta shigo dakin, ta juya da mamaki tana kallonta, nn da nn taji gabanta ya fadi don safeena ba sa'arta bace ta girmeta nesa ba kusa ba, snn ita da take kmr wata bby don rashin jiki ta ya ma xata iya ma safeenah, amma ta dake tana mata wani irin kallo tace "uban me ya shigo dake dakina malama, kinga nn yyi kama da dakin karuwae," safeenah ta yo kanta tana huci, tana ganin hka ta fasa ihu tare da durkusawa a wajen gabanta na faduwa, ta rikota da karfi ta dago ta tace "yau sae kin gaya min ko da ubanki nake karuwancin," ta gaura mata mari, intisaar bata sn lkcn da ta rama har sau biyu ba snn ta riko gashin dokin dake kanta da karfi hkn yasa safeenah ta fasaihu sosai, Aliyu ya karaso dakin, ya finciko safeenar ya buga ta da bango snn ya shaketa yana huci yace"me na ce maki," intisaar ko ta xube wajen tana faman rusa kuka tana kiran abbanta, ya cilla safeenar gefe daya, snn ya dawo gaban intisaar ya durkushe yana kallnta yace "me tayi maki," tayi bnxa dashi tana ci gaba da rusa kukanta, sae da ya daka mata tsawa da ta raxana ta snn tace "dukana tayi," ya dago ta sama ya rungume snn ya soma rarrashinta, ta kauda kanta cike da tsanarsa ita kam wani irin mugun haushin Aliyu take ji, har lkcn safeenah na dakin tana kallon Aliyu da mamaki, cantayi murmushin mugunta ta mike ta fice daga dakin tana gyada kai kmr kadangariya, intisaar kadae ce ta lura da hkn, shi ko ya tafi duniyar runguma, intisaar ta turasa da karfi jin bakinsa a wuyarta hannunsa a gashinta, snn tayi tsaki ta dauko xani tafara cire jumpern dake jikinta, ta cire dan wandon ma snn ta daura xanin ta shige bathroom da niyar tayi wanka, duk wnn abinda take yi Aliyu binta kawae yake da kallo kmr soko tuni idonsa suka sauya launi ya rumtse idonsa xuciyarsa na harbawa da sauri, yana nn tsaye har lkcn idonsa na kan kofar bayin ta fito bayan kmr minti sha biyar daure da towel ganinsa a dakin har lkcn yasa ta wani hade rai, ta xauna gaban madubi tana goge gashinta da dan karamin towel, ya karaso gefen gadonta ya xauna tare da sauke ajiyar xuciya, yace"na taya ki shafa lotion din kanwata," ba karamin dariya hkn ya bata ba, wae ashe dae yasan ita din kanwarsa ce, ta juya tayi masa wani irin kallo snn tace "dnt bother," . ba sake ce komai ba amma ya kasa dauke idonsa daga kanta, ta dae gama shafe shafenta duk yana kallonta kmr xae cinyeta, snn ta mike ta dauko kananan kayanta riga da wando xata saka, ya mike da kyar ya karasa kusa da ita yace"lemme help yhu plss," tayi masa wani kallon rainin hade da sakin wani irin dariya duk da gabanta faduwa yake yi sosai tace "aa i can do it my self, ko da ka saba taya ni ne" ya fixgota da karfi tare da matseta jikinsa ya daura bakinsa kan kirjinta ya shiga mata wani irin kiss, ta fasa masa ihu a tsorace nn da nn jikinta ya dau rawa ta turasa da karfi jikinta na rawa tace "da'alla ka rabu da ni malam, meye hka," ya fada kan gadon tare da lumshe idonsa ya bude su da kyar snn ya mike ya fice daga dakin, tana ji ya ja motarsa ya fita daga gidan, ta sauke ajiyar xuciya tare da tabe baki tace"ae ka shiga uku a hannuna tunda na gano ka," ta gama shirinta snn ta sauko falo tayi hanyar garden da novel dinta a hannu.aleesat HaiydarKarfe tara da rabi na dare intisaar na shirin kwanciya taji shigowar motar Aliyu gidan, xuciyartaya kusan shigewa cikinta don tsoro, da sauri ta shige bargo ta kashe wutan dakin don dama ta sa kayan baccinta, ta lumshe idonta kmr mai bacci, har ta fidda rai da shigowar tasa dakinta bacci ya soma tafiya da ita taji ya bude kofar dakin, ta takurekanta cikin bargon gabanta na faduwa, tana ji ya kunna bedside lamp din ya xauna gefenta yana kallo, taji ya daura hannu kan fuskarta, kmr ta fasa ihu don tsoro amma ta dake tayi kmr bacci take, ya daura mata kiss a fore head dinta yace "gudnyt", snn ya kashe beside lamp din ya fice daga dakin, ta sauke ajiyar xuciya tana gode ma Allah a ranta. .. Washegari lahadi tana kitchen tana hada breakfast din da xata ci, shi kuma yana dakinsa, taji an danna kararrawar gidan, ta taka har bakin kofar tana lekanko waye, Hajiya ta gani fuskar nn tata a hade tana jiran a bude kofar gabanta yyi mugun faduwa, ta juya da sauri tayi hanyar stairs har gobe ita kam baxata daina tsoran wnn matar ba, a bakin stairs din suka ci karo da Aliyu, yau dae shaidanun nasa na kusa da alama, don wani mugun harara ya galla mata ya turata gefe ya sauka don a xatonsa safeena ce, ta bi sa da kallon mamaki, snn ta haye sama da sauri ta shige dakinta, yana ganin hajiyarsa ce sae da gabansa ya fadi shima, ya bude kofar a hankali ta shigo, cikin ladabi ya gaidata, ta galla masa wani mugun harara cikin tsawa kmr xatayi kuka tace "hka muka yi da kai son," yace "ki shigo ki xauna mana momy," ta girgixa kai tace "ba xama ya kawo ni ba, ynxu Aliyu duk irin alkawarin da ka daukar min ka watsar dasu knn, ni xaka bamakunya Aliyu, ina can na sake baki ba don hajiyar safeena taxo ba" sae kuma ta fashe da kuka sosai, duk ya rikice "haba mummy meyasa xaki dinga cewa hka, wllh bbu alkawarin da na saba cikin wanda na daukar miki, kuma in dae safeena ce ki kwantar da hankalinki ni nace xan aure ta vry soon, but gskya bansan yanda xan tunkari abba da wnn maganar ba dama munyi kmr shekara...." ta daka masa tsawa "bakin ciki ya kasheni kafin lkcn knn, ina ruwanka da wani abba, shi da ya jera mata uku uban wa ya hanasa, ko xae hanaka bin sunnar ma'aiki ne," ya gyada mata kai "hka ne mum, amma ki bari nn da sati 2 hka sae naje masa da maganar," ta goge hawayen idonta tace " amma Ali don Allah don annabi ko sau daya kar ka taba sake ma yarinyar nn, kasan munafukai ne masu bin boka da malamai, baka ganin yanda uwarta ta mallake ubanka, ko uwarsa baya sauraran maganarta sae na tsinanniyar matar nn tashi, har innar ma ta asirceta baka ganin inda ta tare gunta, ka rufa min asiri don Allah bna son nayi rashinka, kaga da kayi aurenka ko da wata uku ne sae ka sako ta... Aliyu yyi murmshi yace "in'sha Allah mum," ta sauke ajiyar xuciya tare da daure fuskarta tana kallon sama kmr tana ganin intisaar din tace "ina shegiyar 'yar take ynxu" ya girgixa kai yace "ban sani ba mum, daxun nn na shigo gidan nima," ta mike tsaye ta tabe baki tace "mu dai xuba ni dasu, Allah kadae yasan abinda na tanadar masu ita da uwarta da wnn makirar tsohuwar," Aliyu dae bae ce mata kmai ba sae gyada mata kai da yake, tayi kwafa tana huci tace "xo ka maidani gida, ynxun madaga gidansu safeenah nake," yace "ok bari na canxa kaya," snn ya haye sama, dakin intisaar ya fara shiga, tana xaune ta xabga tagumi hannu bibbiyu idonta a kan TV, duk tana jin conversation dinsu da uwar tasa, amma ko kadan hkn bae dameta ba, kawae dae tana mamakin hali irin na hajiyar ne, tunda ta taso gidan ko sau daya matar nn bata taba mata kallon arxiki ba, bata san me ta tsare mata a rayuwa ba da ita da Hajiyarsu kursum,ya durkusa gabanta yana kallonta yace "kinyi break ne," tayi masa bnxa don ko kallonsa bata yi ba idonta na kan plasma, ya daura hannu kan cikinta yace "ba kya ji na ne," ita abin ma dariya yake bata wllh, abu kmr wasan yara, lallai Aliyu bashi da kunya, ynxu ita abinda take son ta gane bae wuce dalilin muguwar tsanar da yake mata a gida ba tunda ta taso, don ko sau daya Aliyu bae taba mata kallon arxiki ba a gida kullum cikin daka mata tsawa da hantararta yake, lkci daya kuma ya nuna ya damu da ita, ita dae tasan yaudararta kawae yake, jikinta kawae yake so , ita kuma baxata basa ba, ta buge masa hannu ta hade rae tace "me ye hka," ya tabe baki ya mike tsaye yace "me naji kina soyawa a kitchen daxu," tayi kmr ba da ita yake ba, ya xauna gefenta ta matsa da sauri, yyi saurin rikota yace "me yasa baki fito gaida Hajiya ba," tai shiru bata ce komai ba tana kallonta, yace "don ba ki da kunya ko," ta fara fixge fixge daga rikon da yyi mata "da'alla ni ka rabu dani malam bana son hka," ya rungumeta suka fada kan gadon ya saka bakinsacikin nata ya fara kissn dinta, duk ta rude ta kasa kwatar kanta kuma, tun tana mutsu mutsu har ta gaji ta daina sae hawayen da ta fara yi, wayarsa dake aljihunsa ya fara ring, maimakon taga Aliyu ya kyaleta sae taga abu sae gaba yake yana neman cire mata kaya tuni ta rikice ita ba daman ta kwala ihu ba Hajiya na kasa, hka wayarsa ta dinga kara bae kula ba, duk ya fice hayyacinsa, ta tsorata sosae don bata manta daren ranar ba, kuka ta shigayi sosai tana rokansa ya rufa mata asiri yyi hkuri, yagirgixa kai da kyar yace "plss" cikin kuka tace"nashiga uku kasheni xaka yi ya Aliyu....." . muryar Hajiya suka ji a corridor tana kkrin bude kofar dakinsa tana cewa "son, ka fa shanya ni, ina ta kira kuma shiru" intisaar ta turasa da karfi don har lkcin taga bae da niyar daina abinda yake, ya fada gefenta yana maida numfashi ta mike xaune da sauri ta jawo xaninta, shima ya mike xaune yana kallon bakin kofar fuskarsa a daure, Hajiya ta bude kofar dakin nasa ta fito tana cewa "ikon Allah, to inaAliyu ya shiga," sae kuma ta bude kofar dakin baki nn ma ta shiga, Aliyu na jin hka yasan dole ta shigo dakin intisaar din ma ya mike da sauri ya fixgo intisaar din da gabanta ya dinga faduwa suka shigebathroom ya kulle kofar, idan ba ma rashin sanin yakamata ba mai xae shiga da ita dakinsa... . .Hajiya ta bude dakin Intisaar ta shigo, intisaar ta xaro ido a tsorace tana kallon Aliyun dake murmushi kawae, ya wara mata manyan idonsa ya rungumota, tayi lamo a jikinsa gabanta sae faduwa yake, to me take mata a daki hka, don taga shirun yyi yawa, Hajiya kuwa ta gama kare ma dakin kallotana tabe baki bakin ciki da takaici karara a fuskarta, can ta ja dogon tsaki tana murmushin mugunta tace "gidan nn ba gidan xaman ki bane yarinya, wllh ko hkn xae yi sanadiyar rasa raina sae na rabaki da son din, shegiya mara asali " tana kai wa nn ta fice daga dakin tare da banko kofar da karfi, intisaar ta shigatura Aliyun a hnkli jikinta a sanyaye daga rungumar da yyi mata, ya kankameta yaki sake ta, ta turasa a fusace cikin tsawa tace "meye hka malam, ka sakeni ni kar...." ya sa hannu da sauri ya rufe bakinta yana wara ido yace "Allah ya baki hkuri malama," tayi tsaki ta juya, ya fixgota ya hade rai yace"uban wa kike ma tsaki," nn da nn ta tsorata ta rike hannunsa tace "aa kayi hkuri, ba kai nayi ma wa ba," ya lakaci hancinta yyi murmushi yace "tun kina karamarki kike da tsoro," snn ya juya ya fice daga bathroom din, hkn yyi mugun bata haushi, ita bata ma san lkcin da ta basa hkurin ba da bata bashi ba, ita dae ta na nn a tsaye a bathroom bata san yanda suka kaya da Hajiyasa ba, taji fitar motarsa a gidan, hajiyace har garden neman Aliyu. Tana xaune a garden abun duniya ya isheta, ita kam ta gaji da xaman kadaici a gidan Aliyu, gashi har lkcn ya kibata waya bare ta dan dinga kiran gida tana jin ddi, ga kewar momynta da inna da take yi, xainab dama tuni ta daina xuwa gidan kullum ita knn kmr mayya a gida ko nn da gate bata xuwa daga dakinta sae garden, ta kife kanta bisa gwiwowinta bata san lkcn da ta fara hawaye tana tausayin kanta, taji an sakale hannu a wuyanta, ta mike a tsorace xata fasa ihu, taga Aliyu ne, ya hade rai yace "meye hka, me kike yi a nn," ta kaudakanta ta tabe baki bata ce komai ba, rabanta da ganinsa tun lstwk sunday da hajiyarsa ta xo gashi yau har sati daya, sae dae taji ya shigo gidan da daddare da asuba yyi ficewarsa, ta riga ta gama ganesa . in har ya kulata a gidan to ganinta yyi ta basa sha'awa, sae ya nemi ya biya bukatarsa ita kuma taki basa hadin kai, don har lkcn bbu abinda ya sake shiga tskaninsu tun bayan daren ranar, ita dae tasan Aliyu ba sonta yake ba kawaesha'awace, ta mike a fusace xata bar wajen ya fixgota ta fado kansa yace "kin rainani yarinyar nn, ko gaida ni bakya yi a gidan nn fa," ta fashe da kuka, don tasan abinda ya kawo sa wajenta ynxu, don a bnxa Aliyu baya sake mata fuska duk da ya daina dukanta ko yi mata tsawa, ya dago fuskarta yana kallonta, yyi dariya yace "in kin yarda ki kwana dakina yau gobe na kai ki gida," ta dago da sauri tana kallonsa tace "gida?"yace "yea," ta daure fuska tace "kmr ya na kwana dakinka," ya daura kansa kan kirjinta yace "kmr hka," ta turasa da sauri, ya kashe mata ido yace "am serious fa" tayi shiru gabanta na faduwa ga haushinsa da ya cikata, ta dago kai tana kallonsa wani mugun tsanarsa na yawo a xuciyarta, lalle ma ya rainata, lst thing da xata so a rayuwarta knn wae Aliyu ya kusance ta, Allah ya kyauta, ganin amsar ta yake jira ne don ya tsura mata ido yasa ta dan marairaice tace "to ka bari muje gidan yau mana, idan yaso da daddare idan mun dawo sae na kwana dakinka," nn da nn ya rikice mata "ki rantse fateema," ta dan fara kame kame, can dae taga meye to, axumi ne dae guda ukukuma xata iya, ta gyara xama da kyau tace "wllh wllh," ya rungumeta ta turasa da karfi don tsanarsa kara yawa yake a xuciyarta idan yana hada jikinsa da nata, ta mike tsaye tace bari naje na shirya. snn ta shige cikin gidan ya bi ta da kallo, shikam baya son ya kara forcin dinta ya kwana da ita. Yana tsayebakin motarsa yana jiranta don tuni ya gama shirinsa, ta fito sanye da shadda brown colour am mata dinki riga da skirt ya sha aiki, tayi daurin dankwalin nata kmr headtie, tayi mugun kyau, ta rike handbag dinta brown colour, snn ta yafa mayafi light brown, flat shoe ta saka don ita bata sa heel sbda tsayinta, tun fitowarta Aliyu ke kallonta har ta karaso kusa da motar, ya tabe baki ya kauda kansa, bata burgesa ba kam, shi ma shaddar ce a jikinsa brown colour, intisaar bata ji ddin hkn ba, shima taga alamar bae ji ddi ba, ya shige motar, ita ma ta shiga gaba, snn yaja motar suka bar gidan. Karfe sha daya suka isa gida, har wani bari jikinta yake yi tun kan ya gama parkin din motar, ya fixgota ya hade rai yace "bana son hauka, don kika yi provokin dina wllh sae na juya motar nn," bbu ko alamar wasa a tare dashi, nn da nn ta kame kanta suka fito daga motar, suna fitowa kuwa ta kwasa a guje tayi cikin gidan Aliyu ya bi ta da sauri amma tuni ta shige gidan, hknyyi mugun basa haushi yyi kwafa ya bi bayanta, intisaar na shiga kan momynta ta fara daura idonta,ta fito daga bangaren inna, tayi 'yar karar farin ciki ta karasa da gudu da murnarta ta rungumeta, momy tayi mamakin ganinta sosae, ta dago kanta tana kallonta tace "meye hka fateema, daga ina hka" tayi dariya tace "daga gida mana momy" shigowar Aliyu yasa momy ta turata gefe ta fara wucewa abinta, ta juya tana kallon Aliyun har ya karaso inda take ta kauda kanta, ya riko hannunta yace "can xa mu fara xuwa," ya fadi yana nuna matabangarensu, . ita dae bata ce komai ba ya ja ta har suka isa sashinsu, yyi sallama snn suka shiga falon, ihsaan ta fito daga daki tana ganin yayarta ta rungumeta tana mata oyoyo da murnarta, ya nemi kujera ya xauna, ita ma ta xauna rungume da kanwartata tana kallonta tace "momy fa ihsaan," ihsaan tace ta kwanta a daki, ta juya ta sace kallon Aliyun, shi ma yadan kalleta snn ya jawo ihsaan yana mata wasa, intisaar ta mike jikinta a sanyaye ta shiga dakin da sallama, ta karasa kusa da momyntata dake kwance tace "momy ki fito ku gaisa da ya Aliyu," uwar ta galla mata harara tace"fice min a daki," jikinta a mace ta fito daga dakin, taxauna gefensa ta kirkiro murmushi xata yi magana ya riga ta, "momy na bacci ko," ta gyada masa kai kawae, yyi murmushi yace "to xo muje gun inna, ltr sai mu dawo," bata ce masa komai ba ya jawo hannunta yana rike da ihsaan suka bar falon, ita kam bata ji ddin abinda momy tayi ma ya Aliyu ba, suna tafe ne gabanta na faduwa kar su hajiya su gansu, don tasan su kursum duk sun tafi islamiyya sae karfe daya, ya lura da ita yyi dariya yace "ae su hajiya basa nn sun tafi biki kaduna tun friday, ammayau xasu dawo," hkn yasa ma ya sami confident din kawo ta gida, ita dae bata ce masa komai ba har suka isa sashin inna, tana gaban TV a xaune kmr xata shige ciki wae nn kallo take, intisaar ta fixge hannunta daga na Aliyu ta fada falon da gudunta, har sae da ta tsorata innar, ta fasa ihu "innata kina ina," inna ta mike da sauri tana mitsike ido, sae kuma ta fashe da kuka ta xube kasa tana cewa,"ashe dae xasu kawo min ke 'yar nn, kullum sae na xubda hawaye a kanki a gidan nn da daddare, ga Bukar gantalalle yaki barin a kai ni gidan shi da 'yar banxan yarinyar nn Nafisa, . intisaar ta kankameta tana tuntsira dariya, ita ma ta fasa dariyan suka dinga yi, ihsaan na taya su, Aliyu kam jingina yyi jikin kofa yana kallonsu yana murmushi, can inna tadago tana kallonsa tana washe baki tace, karaso mana jikalle,shigo ka xauna, ni anya ma akwae abinci a gidanka kuwa Aliyu, naga duk yarinya ta fiffige kmr kaxa," ya galla mata harara yace "to ki siya ki kai min mana," snn ya harare intisaar din yace "nn da minti talatin ki shirya xamu wuce," inna ta mike a fusace tace "ku wuce gidan ubanwa, dagaxuwan yarinya xata shirya ku wuce, ae in kaga fitarta a gidan nn sha biyun dare ne yyi wllh" ta koma ta xauna tana huci, ya girgixa kai, ya fice ya bar mata falon, nn inna ta sa ta gaba bayan ta hadata da fura mai sanyi tana mata tambayoyi, cutar ki yake yi a gidan ko, da gske ne bbu abinci a gidan nasa ko, to me kike ci ni Rahmatu, ynxu ma nasan kila Bukar ne yace ya kawo ki nn ko, to wae a ina gidan yake sun ki gaya min da na ringa xuwa kullum da kaina, intisaar ta fara tarin karya ta buge innar tace "kae inna ae gashi kinsa har ina kwarewada wa innan tambayoyin naki, inna ta koma gefe da sauri tace "yi hkuri to gama tukunna," hka intisaar suka dinga cafter da inna dake ji kmr ta maida ta ciki har su Zainab suka dawo gidan, duk suka yi murnar ganinta sosae suka sa ta gaba sae kallo suke, kursum tace kai kinga yanda kika yi wani fresh da kyau intisaar, intisaar ta galla mata harara tace "a inda bbu fresh din da kyau ba," duk suka dinga dariya, ita kanta tasan tayi kyau sosae, ramewa kadae ne tayi, inna tace "ku rabu da ita ciki ne da ita" nn da nn intisaar ta hade rai tana kallon innar, suko sae tuntsira dariya suke, inna kuwa ko a jikinta sae tauna goranta take, suna xaune a hka Aliyu ya shigo falon duk suka yi tsit bayan sun gaishesa bnda intisaar dake ta xuba abinta bata kara kallon inda yake ba, ya daka mata tsawa yace"kina jiran abba yaxo ya same ki a nn ne, kafin ki gaida shi," ta mike da sauri tace "lah na manta," ta ja gyalenta tabi ta gefensa ta fice daga falon tayi bangaren Abba, ya bi ta a baya, su xainab suka kwashe da dariya inna na taya su. . Da fara'arta ta shiga falon Abba ta rungumesa tana dariya tace"Abbana ina yini," shima yyi dariya ya amsa yana kare mata kallo snn yace "baki da lafiya ne fateema," ya juya ya hade rae yana kallon Aliyun da ya nemi kan tiles ya xauna yace "bata da lafiyane," ya fara kame kame kmr munafuki yace "Abba lafiyarta qlau ka tambayeta," abba yace wae hka fateema, Aliyu ya gyada mata kai da sauri yana kallonta, ta galla masa harara, snn ta mairaice murya tace "ni Abba makaranta nke son na koma lkci yana ta wucewa,"Haiydar Abba ya juyo yana kallon Aliyu yace, "amma lst tym da ka xo nn nai maka maganar karatunta me kace min," Aliyu aka fara kame kame da shafa kai "No Abba dama fa, dama tun lkcn nayi mata magana tace min ba ynxu ba tukun shine yasa ma ban sake mata maganar ba," Abba ya juya yana kallon intissar da ta tsaya kallon Aliyun da mamaki, yace"wae hka ne fateema" Aliyu ya shiga gyada mata kai wae tace hkne, ita kam ta rasa dalilin da yasa taga Abba da Aliyunsa kmr basa shiri kmr da, don dae tasan duk iskancin da Aliyu yake da wuya abba yace masa komai sae dae yyi ta kallonsa, yau kumataga ya hade masa rae kmr wanda yyi masa babban laifi, ta kalle Abba tace "ehh abba ya taba min mgna sau daya," Abba yace "ok, wni makarantar kike so," tace "bayero Abba," "medicine kika ce xa kiyi ko," ta gyada ma Abba kai, Aliyu yace"ke din ce xaki iya medicine? Abba baxata iya ba" abba ya galla masa harara yace "kai din da kayi kai goma gare ka?" Aliyu bae ce komai ba ya kauda kansa, Abba yace "sae kaje kayi abinda ya dace, ta fara karatu vry soon, idan nace vry soon, i mean vry soon" ba tare da ya kalle abban ba yace "to abba," intisaar ta mike tsaye tace " Abba sae anjima, ngd" abba yace "yaushe xaku koma gida," ta dan sace kallon Aliyu tace "aa abba ni kwana xanyi dama" Aliyu ya juya da sauri yana kallonta, amma bae ce komai ba, abba yace "to shiknn nima fita xanyi sae na dawo, ina da magana dake " tayi ma abba Allah ya kiyaye snn ta fice daga falon. Aliyu ya mike yyi masa sallama shima ya fice, da sauri ya bi bayanta,amma tuni har ta shige falon inna, ya shiga falon shima ransa a hade yace "wllh xuwa karfe shidda kishirya kafin na dawo," ya fice daga falon, ta tabe baki, tana kallon inna da ta bude baki tana kallon bakin kofar da ya bari, intisaar tayi dariya tace "innarufe bakin," inna tace "ae abun ne kmr wani mahaukaci," ynxu irin xaman da kuke yi knn intisaar, intisaar ta tabe baki tace "wae don nace xan kwana shine wae baxan kwana ba," inna tace"to uban me xaki masa a gidan, manta dashi kawae ai in kin koma gidan nn ke da kanki kika ce xaki koma," intisaar ta dinga dariya da jin ddin abinda inna ta ce mata, nn suka dinga hira har dae intisaar tace ma inna bari taje wajen momy, snn ta yi bangarensu. Bayan sllhn isha'i Aliyu ya shigo gidan,intisaar har ta fidda rai da ganinsa ta yi xaton ya hkura ne, ya tsaya masu kmr soja a bakin kofa wae ta tashi su tafi, intisaar ta yi kmr bata gansa ba tanata kallo abinta, kiri kiri inna tace bbu inda xae je da ita, kwana da kwanaki xata yi a gidan, sae ta gaji don kanta tace xata koma, ya hade rai yana ta kallon intisaar din dake kwance kan kujera tana taunar cingam, ko kallon inda yake ma bata yi ba, yasauke ajiyar xuciya tare da kwantar da murya ganinba ihunsa xae sa inna ta basa intisaar ba yace "don Allah inna ki bari, akwae fa inda xamu ynxu," ya kalle intisaar din yace "kiyi mata bayani mana fateema, wllh xuwa nxt wk sunday xan kawo ki kiyi sati ma idan kina so," intisaar ta tabe baki tace "ka dae je kawae nxt wk sunday din sae ka xo daukata," snn ta mike ta shige bedroom, ta barsa nn a tsaye, inna tace "to ka dae ji," snn ta kashe wutan falonta tace "Allah ya bamu alkhairi nima kwanciya xanyi, sae da safe," snn ta shige dakin ita ma ta kullo kofar.aleesat HaiydarAliyu ya kasa cewa komai sae kofar dakin da ya tsura ma ido, ya dde wajen a tsaye, can dae ya juya ya fice daga falon ya rufe kofar, inna na jin fitarsa tace "munafuki kawae, ki kwantar da hankalinki, ke da barin gidan nn sae ran da kika ce xaki tafi," intisaar ta gyara kwanciyarta don dama har tayi shirin bacci tace "kin ma san mene inna, bari na yake ni kadae fa kmr mayya a gidan, kuma bae ma san ci na da sha na a gidan ba, sae nayi sati ban gansa ba ma," inna ta bude baki tana kallonta "ke 'yar nn da gske," ta tabe baki tace "uhum ke dae barikawae, wllh kuwa inna," inna tace "to ni ae ca nke ciki ne da ke," intisaar ta galla mata harara tace " kaji ana mgnar arxiki wnn tsohuwar wae ciki, cikin lafiya, ni bnda komae" inna tace "ikon Allah, kina nufin har ynxu bbu abinda ya shiga tsakaninku intisaar" intisaar tayi mata bnxa ta juya mata baya snn ja bargo ta gyara kwanciyarta, inna xata yi magana wayarta ya shiga ruri, . ta mike da sauri ta dauko tana cewa "ina xan danna ke," intisaar tace"kai inna shekararki nawa da wnn wayar amma har yau baki san ina ake dannawa ba," inna tace "aa wani lkcn rudewa nake yi ne wllh," da kanta tayi pick din wayar dan intisaar kin mikewa tayi, ta doka uban sllma tana tambayar wanene, can kuma tace"A'a Bukar ne, lfya? Ayyo na ba fateema, to ga ta nn," inna ta mika ma intisaar wayan, intisaar gabanta yafadi ta amsa a sanyaye tace "Na'am Abba," murya can kasa tace "to Abba," snn ta kashe wayan, sae tafashe da kuka, inna ta rude "ke lfya me ya faru?" cikin kuka tace "kina ganin inna hada ni da abba yaje yyi ko," inna ta hade rae "to uban me Bukar din yace maki ynxu," ta goge hawayen idonta tace "waenaje yana nemana," inna tace "to bbu inda xaki je yi kwanciyarki, ni nn Rahmatu nace bbu inda xaki je, idan Bukar din ya isa yaxo ya tunkareni" intisaar ta mike tsaye ta dauki hijab har kasa tasa tace "ba dani ba xa ayi wnn ba inna, Abbana na kirana xanje na amsa kiransa," snn ta fice ta bar ta nn a tsaye. A hankali tayi sallama falon abba ta shiga, suka yi idohudu da Aliyu dake xaune falon a kasa gefen abba, ta nemi guri ta durkusa ta gaida abba, ya amsa yana kallonta yace "ki shirya maxa ku wuce gida fateema," a sanyaye tace "to abba" don bata iya ma abba musu, abba yace "ynxu meye naki a wajen inna, xainab taje ta dauko maki," ta girgixa kai tana kkrin maida hawayen idonta tace "bbu komai, kawae jakata ne, wani lkcn xan dauka," Abba yace"yauwa fateema, maxa tashi kuje kuyi ma momyntaku sllma, ku kama hanya ku wuce gida," ta mike tsaye ba tare da ta bari abba ya ga hawayen da take yi ba ta fice daga falon bayan tayi masa saeda safe , Aliyu ya mike shima yyi masa sae da safe, ya bi bayanta, bae ce mata ba, ita ma bata ce masa ba har suka isa sashinsu, falo suka tarda momy, ya nemi kujera ya xauna ya gaidata kmr wani munafuki, ta amsa batare da ta kallesa ba, ita dae intisaar tv kawae take kallo, suka dde a falon a xaune momy na gyara ma ihsaan gashi na xuwa sch gobe, ganin har karfe goma ya wuce Aliyu ya kasa tashi ne yasa intisaar ta mike tana kallon momyn tace "momy xamu tafi sae da safe," tace"Allah ya kaimu, . *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Aliyu ma ya mike tsaye yyi mata sae da safe tayi kmr bata ji sa ba, ya ajiye ma ihsaan dubu biyar ta sha ice-cream snn suka fice, ita kam bata ga laifin momy ba. Har suka isa gida bbu wanda yyi magana tsakaninsu, shi dae ne ke ta waya da safeenah suna soyewa, yana parkin ta bude motar ta fice tayi cikin gidan da sauri, ya bi bayanta tun kan ta hau sama ya risketa ya fixgota, yace "direct bedroom dina xaki shiga, ba sae kin shiga naki ba," ta turasa tana masa wani irin kallon raini, "nayi maka uban me," bata rufe baki ba ya dauketa da mari, ta fasa ihu ta durkushe wajen, ya bita da sauri, ya rikota, kuka ta shiga yi tana ihu, dukya gigice ya rungumota yace " don Allah kiyi hkuri fateema, am vry srry," ko sauraransa bata yi ba taci gaba da rusa kukanta, ya dauketa cak, ya hau sama yyi bedroom dinsa da ita, duk irin yanda yaso intisaar ta basa hadin kai kin yrda tayi, don kuka ta dinga masa sosai tana rokansa yyi hkuri bata so, hkn yasa ya kyaleta kawae yyi kwanciyarsa bayan ya lallasheta yace tayi baccinta baxae mata komai ba, ta jima bata yi bacci ba sbda tsoro, gnin kmr Aliyun yyi bacci ne yasa ta dan kwantar da hankalinta ita ma ta fara baccin, duk da kuwa idonsa biyu ba baccin yyi ba, yana ganin ta fara bacci kuwa ya mike ya bar mata dakin ya kohaleesat HaiydarDa asuba Aliyu ya shigo dakin yin alwala, tayi shame-shame hankali kwance tana bacci, kallo daya yyi mata ya dauke kansa ya shige bathroom, yana fitowa ya bude fridge ya dauko ruwan gora mai sanyi ya bude ya xuba a hannunsa ya watsa mata, ta mike xaune a firgice tana kalle kalle, ya juya ya fice daga dakin ya wuce masallaci, ta yi tsaki, a xuciyarta tace Allah ya isa na, snn ta mike tsaye ta shige bathroom tayi alwala, tana idar da sallah tayi jigum a dakin, can dae ta mike xata fita idonta ya sauka kan wayarsa da yyi haske a gaban mirror, ta dan kalli bakin kofar snn ta karasa ta dauki wayar, taga msg ne, ta bude taga na safeenahne, ta tabe baki bata damu ta karanta ba ta fita daga inbox din kawae,. ta xauna gefen gadon wayar a hannunta ta shiga hotuna, duk hotunansa da na safeena ne, wasu yana rungume da ita, wasu tana kwance jikinsa, wasu suna kiss, gasu nn dae ba kyan gani, duk da ba son Aliyu take ba sae da taji baddi, wani bakin ciki ya dinga yawo a xuciyarta, tana nn a hka har Aliyu ya shigo dakin tayi saurin boye wayar cikin hijab dinta, ya galla mata harara yace"fice min a daki kar nayi ball dake," ta mike ta fice daga dakin ba tare da ta kallesa ba wayar tasa a hannunta, yyi kwafa yace "xaki gane kuranki ne yarinya," har Aliyu ya fita ranar bata ji yyi mata maganar wayarsa ba, gabanta kuwa sae faduwa yake kar yaci ubanta. Da yamma wajen karfe biyar tana kwance a daki tana kallo, aka bude kofar dakin ta mike xaune a dan tsorace tana kallonsa, daga bakin kofar yace "ina jiranki a falo, kuma kar ki fito min da shigar nn na iskanci," ta tabe baki ta ci gaba da kallonta kawae, bayan kmr minti goma ya sake dawowa, ta mike a dan tsorace yace "kina hauka ne,me nace maki," ta hararesa tace "gani nn xuwa," yyi murmushi ya juya ya wuce, ta dauko hijab dinta har kasa tasa ta sauko falon, dama tasan bako na falon tunda har ya kira shigar ta ta iskanci, da can da take sa wa bae san na iskanci bne, ta karaso falon ta xauna tare da gaisuwa "ina yini," ya dago yana kallonta yyi murmushi yace "lfya fateema, ya gida ya amarci," komai nata ya tsaya cak ganin faruuq, ta kasa dauke idonta daga nasa, shi kansa yanayinsa ya canxa duk da yyi kkrin boyewa, yyi yake yace "kai wnn kallon kmr kin ga dodo intisaar,"ta dauke kanta da sauri ta kasa cewa komai ga hawayen da taji na neman cika idonta, Aliyu yana danna wayarsa duk da hankalinsa na kanta yace "kikawo masa ruwa mana" da kyar ta mike jikinta a sanyaye tayi hanyar kitchen ta dauko faranti da cupta daura juice da ruwa a kai ta dawo falon ta dire gabansa, yyi murmushi yace "thank yhu fateema" . tajuya xata bar falon Aliyu yace ina xaki, hira yaxo kuyi fa, kin juyowa tayi sae da ya sake kiranta snn ta dawo ta xauna tana kirkiran murmushi, Aliyu ya mike ya bar falon yana mata wani irin kallo, ko lura da hkn ma tayi, faruuq ya dago yana kallonta yace"kinyi mamakin gani na ko," bata ce komai ba yyi murmushi yace "ya amarci," nn ma shiru tayi, "yace common fateema, baki yrda da kaddara bne, ki tuna fa matar mutum kabarinsa," ta gyada masa kai kawae, yace "cheer up kanwata," tayi murmushi kawae, yace "yauwa ko kefa," nn dae intisaar ta sake suka dinga hira da faruuq din kmr ba komai, Aliyu ya sauko ya xauna falon shi dae bae sa masu baki ba sae dae yyi murmushi, intisaar tace "yayanain xubo maka abinci to?" faruuq yace "haba dae sae kace jaki daxu fa muka ci da Aliyu," ta juya tana kallon Aliyun ya harareta ya dauke kai, faruuq bae bar gidan ba sae kusan maghrib, har bakin kofa ta rakasu da yake shi da Aliyun xa su fita kuma, tace"yayana ina da magana da kai fa," ya juya yana kallonta yace "ina jin ki kanwata," ta harare Aliyu daya xuba masu ido tace "ba da kai nke ba," yyi murmushi yyi gaba, faruuq yyi dariya yace "to ina ji,"tace "yayana dama nace don Allah don annabi, tunda Allah yyi ni ba matarka bace, to ka nemi 'yar uwata mana," ya juyo da sauri yana kallonta yace"wa?" tace "zainab," ya harareta da wasa ya juya xae wuce tace "haba yayana, abinda yyi zainab shi fa yyi ni, ni da xainab daya ne" yace "haba dae, da gske?" . ta lura yana son shashantar da maganar ne, ta dinga masa magiya kmr xatayi kuka, daga karsheyyi murmushi yace "shkkn kanwata xanyi shawara,"ta ce "haba yayana kasan fa ba talarta nake mka ba,tana da manema dayawa, kawae dae xumuncin mu nake so yyi karfi kuma...." yyi dariya yace "to shknn fateema, ngd da kulawarki sae da safe," ya juya da sauri ya bar wajen, tayi dariya ta daga masa hannu ta koma cikin gida. Bayan kwana biyu da xuwan faruuq intisaar na daki a kwance tana ta game da wayar Aliyu da ta mayar nata don har lkcn bata gansa ba bare ta sa ran xae mata maganar wayar tasa, hkn yasa ko da yaushe cikin kiran inna da Zainab take su yi ta hira don akwae kudi sosai a wayar, momy dai sau daya ta kirata suka gaisa, abun da ya bata mamaki bae wuce na rashinganin kiran safeena ba don jira kawae take ta kira tayi mata rashin mutunci amma har lkcn bata kira ba kuma bata yo tex ba, sau dayawa kiran abokanansa da 'yan mata kan shigo amma ko sau daya bata taba dagawa ba, ta goge duk hotunan haukan da sukayi da safeenah dake cikin wayar, snn tayi deletin tex din safeenar da na mata da dama a wayar, karar bell taji downstairs ta mike a dan tsorace don Aliyu baya dannabell, ita tun ranar ma da ya fita raka faruuq bata sake ganinsa ba, kar dae Hajiyarsa ce ta dawo don ita tsoran matar nn take, a tsorace ta sauko kasa cikin sanda ta isa bakin kofar ta dan leka ta glass taga Anty Nafisa ce, ta bude kofar tare da doka tsalle ta rungumota tana mata oyoyo cike da farin ciki, Anty nafisa tayi dariya tace "ni kar ki karya ni," suka shigo falon intisaar na tambayarta Maryam fa, meyasa har ynxu bata xo ba, Anty nafisa tace sun fita waje da abbanta ai, intisaar tace Anty mu hau sama mana, Anty nafisar tace "ina fitsararren mijin naki," intisaar tace "uhm baya nn," snn ta mike ta kawo mata lemo a fridge ta dire mata a gabanta tana tambayr ya su shaheed da ummi, Anty Nafisa tace suna nn lfya, snn ta mike ta hau sama tana cewa "bara naje naga dakin amarya," intisaar ta bi ta a baya tana dariya, hira suka dinga yi da Anty Nafisa tana bata lbarai, duk da anty nafisar taso jin irin xaman da suke yi da Aliyun, amma intisaar ta dinga shashantar da batun, karfe sha biya tace bari taje ta daura girki tunda yini Anty Nafisar xata mata, Anty Nafisa ta mike tana inspect din dakin tace "duk da dae nasan ke ba kaxama bace intisaar bari dae na dudduba ko ina, don randa naje gidan fadila duka ne kadae ban mata ba, gskya mijinta na kkri don fadila muguwar kaxama ce ta karshe," intisaar dae tayi dariya ta sauka kasa don ita kam tun tana karamarta take da kyankyani, kuma ko a gida ma inna na yaba tsaftarta, ko shakka bbu tasan Anty nafisa baxata ga datti ko kadan a dakinta ba, dama ko ina na gidan, lafiyayyar jollof rice da plantain sai farfesun kaza ta shiga girka ma Anty nafisa, ta dan hada mata cream salad kadan, snn tayi ginger drink, gidan ya kauraye da kamshin girkinta, tana jerasu a faranti don sama xata kai mata taji an rungumota ta baya, ta tsorata sosae xata fasa ihu ya juyo ta yasaka bakinsa cikin nata, ta turasa da karfi tana maida numfashi, "meye hka," ta tambayesa tana hararan sa yace "ni kika yi ma girki?" tayi masa wani irin kallo tace "kai a su wa," ya tabe baki yace "kinga ina cin ko wani girki? Ae wnn kaxanta ce kika hada," bata kara ce masa komai ba ta gama jera abincin a faranti ta dauka xata bar kitchen din, ya fixgota, saura kiris farantin ya fadi daga hannunta, ta xaro ido tayi saurin ajiye farantin kan table, "wae meye hka don Allah," ta tambayesa kmr xatayi kuka, yace "to dibar min nawa," ta galla masa harara tace "ban yi girki da kai ba, kai da ba ko wani girkikke ci ba," yace "to kuwa baxa ki bar kitchen din nn yau ba knn," ta ce " Anty Nafisa na jirana fa a sama," ya dan wara ido yace "Nafisa? metaxo yi?" muryar Anty Nafisar suka ji tana cewa "wae store din kitchen din kike girka min gaba daya e intisaar, wnn ae sae yunwar ta galabaitar dani," da sauri har yana neman faduwa ya shige bayan kofar, intisaar bata san lkcn da ta kwashe da dariya ba har da xubewa kasa, Anty nafisa ta shigo kitchen din tana cewa "ohh dariya ma na baki, ai gskya ne," intisaar tace"na gama anty ynxu dama xan kawo maki," ta dauki farantin, Anty nafisa tace "to ina na mijin naki fa," intisaar ta girgixa kai tace "ae shi ba ko wani girki yake ci ba Anty," nafisa ta tabe baki tace "sae irin na uwarsa Aisha yake ci knn," intisaar ta dinga dariya, Anty nafisa ta karbe farantin tace "ni bani kar ki xubar min da abinci, ae gskya na fada," suka bar kitchen din a tare suka wuce sama, ae ba karamin farin cikin saukowar Antynafisar intisaar tayi ba, kuma tunda ya shige bayan kofa baya son ta gansa tasan bae da gskya ne. Ni kam koma wacece ke ci min gaba da lbri gskya bn yafe mata ba, Inteesar.... . Karfe biyar saura anty nafisa ta fara shirin wucewa gida, intisaar duk sae taji wani iri tayi jigum tana kallonta kmr kar ta tafi, Anty nafisa tayi dariya tace "kar ki damu daughter, xan dinga xuwa a kai a kai ina duba ki, tunda dae ke Allah bae sa kinyi sa'an miji ba," dae-dae nn Aliyu ya shigo dakin da sallamarsa, nafisa ta xuge handbag dinta ta sakale a hannu tana kallon intisaar din fuskarta atsuke tace "daughter ni na wuce sae wani lkcn," snnta yi hanyar kofar ba tare da ta kalle inda Aliyun yake ba, da sauri ya shige gabanta yana dariya yace "haba momy, ina kika taba jin uwa na fushi da danta," ta galla masa harara tace "da'alla wuce ka ban waje malam," ya karbe handbag din hannunta yace "ina! Ai yau nn xaki kwana momy," tun tana gintsewa har ta fara dariya ganin yanda Aliyu ya maida ta kakarsa, ta koma ta xauna tace "sae ka fito da kudin mota tunda Allah ya kawo ka," yace"tab, ni ban da kudin mota sae dae na kai ki a motata," dole anty nafisa ta tilastasa ya bata dubu biyar kudin mota snn ya maidata gida a motarsa, bayan fitansu intisaar duk sae taji ba ddi ta xauna ita daya a daki tana rera kuka. Ranar friday daya yyidae-dae da sati daya da xuwan Anty Nafisa gidan kuma hkn yyi dae dae da wata biyu da sati daya da kawo intisaar gidan Aliyu, tana daki da daddare ta gama shirin bacci wajajen karfe tara, Aliyu ya shigo dakin nata ya tsaya bakin kofa, ta juyo tana kallonsa, ransa a hade yace "ki shirya xamu fita," snn ya juya ya fice daga dakin, ta dde a tsaye bakin madubinta tana tunanin to ina xasu je da daddaren nn, can dae tayi tsaki tayi kwanciyarta a xuciyarta tace bbu inda xani, can bayan kmr minti sha biyar ya dawo dakin, ya daka mata wani raxannen nn tsawa "wat? . Ina wasa da ke ne ko kin fara hauka ne?" ta mike a tsorace don har ta manta rabon da yyi mata irin wnn tsawar tun suna gida, jikinta ya dau bari ganin bbu alamar wasa a tattare dashi ta mike tsaye muryarta na rawa tace "kayi hkuri, ni bn ji ka da kyau bne," "baki ji ni da kyau ba?" ya tambayeta yana mata wani irin kallo, ta girgixa masakai, yyi kwafa ya fice, ba shiri ta dauko dogon rigarta na material ta saka snn ta dauki hijab dinta har kasa ta sa, ta feshe turare ta fito falon a sanyaye, yana tsaye ya dafa kujera yana jiranta, ya dauki makullinsa ya fita ta bi bayansa, suna fitowa ya rufe gidan yyi hanyar garage ya bude motar ya shiga, ta xaga ita ma ta bude ta shiga, ya ja motar suka fita daga gidan, sun yi nisa sosae, intisaar gabanta sae faduwa yake don bata san inda xae kaita ba gashi bata ga fuskar tambayrsa inda xasu ba, taga yyi park gefen titi, ya juyo yana kallonta fuskarsa a daure ya fara magana a hankali "kina jina," ta gyada masa kai a dan tsorace "wllh duk tambayar da xa a maki idan har kika nuna baki san komai a kan tambayar ba, xanyi gunduwa gunduwa dake, idan kuma kin yi tunanin am jokin dare me," gaban intisaar ya shiga faduwa sosai ta dinga gyada masa kai a tsorace... INTEESAR BOOK 3 Aliyu bae sake ce mata komai ba sae gudun bala'in da ya dinga yi kmr xae tashi sama, hankalinta yyi mugun tashi ta ma rasa mae xata ce masa don tsoro, ta dake daga karshe da kyar Muryarta na rawa tace "wae ni ya Aliyu ina xa ka kai ni ne don Allah," ya taka brake yyi arkin da sauri yana kallonta cikin tsawa yace "kika ce me?" ta tsorata ssae ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yyi mata wani mugun kallo yace "sayar da ke xanje nayi," bata dago kai ba bare tace masa komai yyi kwafa ya ja motar suka bar wajen, lkci daya hankalinta ya kwanta ganinsu da tayi anguwansu, yana gama parkin kuwa ta bude kofa xata fita da sauri yyi hanxarin fixgota yana hararta yace "kin dae ji me na ce maki, kuma wnn hawayen bana son ganinsa a fuskarki" ta fixge hannunta ta fice da sauri daga motar snn ta watsa masa harara hade da jan tsaki tace "ban ji ba," tana fadin hka tayi cikin gidan da gudu ya bita da sauri, tana isa gate cikin rashin sa'a tayi tuntube tayi gaba xata fadi yyi saurin rikota ta fado kansa, ta marairaice fuska a tsorace tace "don Allah kayi hkuri ba da kai nake ba," bae ce mata komai ba ya shiga janta kmr wata dabba tana biye da shi a baya har suka iso falon Abba, sae a snn ya juya yana kallonta fuskarsaa murtuke yace "Allah ya baki sa'a ki ki yin abinda nace maki, wllh sae na kusan sumar dake a gida yau," bata ce komai ba ya ja ta suka shiga cikin falon, Abba na xaune remote a hannunsa yana canxa tasha, Aliyu kadae ne yyi karfin halin yin sallama ita kam inteesar kasa wa tayi ji tayi hka kawae gabanta na faduwa, ta xauna Aliyu ya xauna gefenta snn ya gaida Abban nasa ba tare da ya kallesa ba, Abba ya amsa bbu yabo bbu fallasa snn ya kalli Inteesar da ta kirkiro murmushi tana gaishesa ya amsa da fara'arsa yana tambayarta ya gidan, ta sunkuyar da kai tace lfya lau Abba, murya can kasa Aliyu yace "ga ta nn Abba na kawo ta," ko kallonsa Abba bae yi ba ya fara magana kmr hka "tambayace kawae xan maki Fateemah, amma gskya kawae nake son ki gaya min kar kiyi min karya ban san ki dakarya ba," tayi shiru gabanta na faduwa tana kalln Abban, ya dan dau lkci snn yace "wae da amincewarki Aliyu xae kara aure?" ji tayi komai nata ya tsaya ta kasa dago kai bare ayi expectn amsa daga gare ta, nn da nn taji hawaye na neman cika mata ido, Aliyu ya kamo hannunta ya hade da nasa a boye, ta gane abinda yake nufi, suka ji muryan Abba na cewa "magana nake fateema kin yi shiru, sharri yyi maki ko?" da ganin Abba kasan ransa a bace yake, da kyar ta iya bude baki ba tare da ta kalli Abban ba tace "eh hka ne Abba da sanina," Abba ya girgixa kai yace "karya kike," tayi kkrin boye hawayenta tace "da gske Abba na sani ni ce nace yyi," Abba yyi shiru yana kallonsu gaba daya daga bisanni yace "to yyi yau, baxan hanaka kara aure ba Aliyu kuma ni kam bbu abinda xan ce maka da ya wuce Allah ya taimaka, snn abu na karshe da nake son na gaya maka shine ka tabbatar kafin kayi auren naka 'ya ta ta fara karatu tayi settle dwn idan ba hka ba wllh sae na wargaxa komai, ka tashi ka ban wuri" bbu ko dar bare damuwa Aliyu ya mike yace "ngd Abba," ya sace kallonta, ita ma kallonsa take hawaye cike idonta da ganinta ta shiga wani yanayi da baxa a iya fassarawa ba ya galla mata harara snn ya fice, Abba yyi shiruyana kallonta snn a hankali ya fara magana"kiyi Hkuri fateema, nayi dana sanin hadaki daAliyu da nayi, kuma ni ban isa hana shi kara aure ba, snn baxan ce kar ki bi mijinki ba amma idan har kin ga baxa ki iya xama gidan ba bayan auren nasa ni nn nace ki tattaro ki dawo gida," kai kawae take gyada ma Abba tana hawaye yyi mata nasiha ssae yana kwantar mata da hankali daga karshe yace ta tashi tashiga cikin gida amma kar ta ce da inna komai tukun, ta mike jikinta a mace tayi masa gdya snn ta fita falon tayi bangaren inna tana kuka ssae, tsaye ta gansa alamar ita yake jira, yana ganin tayi bangaren inna ya daka mata tsawayace "c'mon gida xa mu wuce ina kike tunanin xa ki," ko kallonsa bata yi ba ta saka gudu tayi sashin inna ya bi ta shima da sauri, Kursum da ta fito daga gun inna knn ta bi su da kallo baki bude, saura kiris ya kamata ta afka falon inna tana mayar da numfashi ta fasa ihu tare da xubewa tsakiyar falon, inna dake daki ta fito da gudu tana salati tace "me ya faru?? Daga ina hka?" shi ko ya fixgota a fusace ya shake ta hade da hada ta da bango yana huci yace "don ubanki ina wasa da ke ne?" inna tayo waje da ido snn tayi waje da gudu ta saki kuka cikin daga murya tace "jama'a yau naga ikon Allah xae kasheta gabana, Bukar Bukar ka taho kaga abinda dan ka ke shirin yi da daddaren nn" . Haisam ya karaso da sauri yana kallon inna yace "me ya faru inna," tana kuka wiwi tace "wllh Haisam ina daki na je ajiye kayan da kursum ta gama goge min naji ihu kmr xa a xaga falona, fitowar da xanyi wae sae ganin Aliyu nayi shake da Inteesar yana duka yana buga ta da bango, duk yyi mata kaca kaca ko motsin kirki wllh bata yi yanxu ban san ya ake ciki ba ka taimaka ka kira mun Bukar don Allah," tana kai wa nn ta fashe da wani kukan har da durkushewa kasa, Haisam ya girgixa kai ya shiga falon innar da sauri dai dai bakin kofa ya hadu da Aliyun rike da hannun inteesar yana janta tana kuka tana cewa "wllh ka kyaleni bbu inda xa ni," ya buge mata baki Haisam yace "wae kai wani irin mutum ne Aliyu 4 heaven sake" Aliyu ya watsa masa wani mugun kallo yace "da'alla can get out malam kar na buge ka," inna tayi cikin gida da gudu tana rusa kuka lkci daya tana kwala ma Abba kira, da sauri Aliyu ya ja inteesar suka fice daga gidan tana nonnokewa ya bude mota ya jefata ciki snn ya shige motar ya tada ta, dae dae nn inna ta fito kofar gidan Abba na biye da ita a baya tace "maxa bi shi Bukar ya tada motar," Abba ya girgixa kai cike da takaici yace "kina ma Allah da annabi ki daina daga min hankali a gidan nn baaba wnn wani irin bala'i ne," bae jira mai xata ce ba ya koma cikin gidan ransa a bace. Suna isa gida Aliyu yyi parkin ya bude motar ya fito yana kallnta har lkcin bata daina kuka da take ba ta hade kai da gwiwa, cikin tsawa yace "ko sae na jefar dake waje," taki dago kai bare ta tanka masa, ya fixgota ta fasa masa ihu tana cewa "wllh baxan shiga gidan nn ba ka mayar dani gida," cak ya dauketa ya rufe motarsa tana dukansa bae damu da hkn ba ya shiga gida da ita ya haura sama ya bude dakinsa, nn da nn ta saita kanta cikin muryar kuka tace "ni ka ajiye ni," bae kulata ba ya isa kan gado ya kwantar da ita ta mike da sauri ya turata da karfi ta fada kan gadon snn ya fada kanta, nn da nn ta hadiye kukan da take xuciyarta na bugawa a hankali tace "kayi hkuri ya Aliyu na daina kukan" ya dago yana kallonta da ganinta kasan a tsorace take, ta fara kkrin sauka daga kan gadon ya rikota yace "bbu inda xaki yau nn xaki kwana," kanta ce komai ya kashe wutan dakin, ta fasa masa ihu ya buge mata baki da karfi, ba karamin wahala ya bata ba, don duk sae da ya jagwalgwalata, ganin irin kukan da take da kuma yanda jikinta ke bari duk da bae ma kai ga yi mata komai ba yasa ya kyaleta tare da cewa "ki rufe min baki kar na baki mamaki," ba shiri ta hadiye kukan jikinta na rawa don duk ya tsorata ta, ya rungumota ssae, snn ya dauki wayarsa yyi dialin nmbr safeenah, kmr jira take yana ringin kuwa ta daga, murya can kasa yace "bbyna," ita ma a marairaicen tace "mijina," ya sauke ajiyar xuciya ya daura bakinsa kan gashin inteesar da ta rumtse ido xuciyarta na bugawa, yace "nayi missn naki ssae fa bby, i need yhu safeena," ta danyi dariya tace "matarka fa? Kaje ka sauke need din a kanta mana," ya yamutse fuska yace "me wnn take da shi da xata bani da ya wuce wahala, naki nake so bbyna," tayi dariya ssae snn tace "ka kusa samu dear na, ina amaryartaka," yace "ga ki nn bbynah," nn suka dinga xancen yanda 1st nyt dinsu xae kasance bbu kunya bare tsoran Allah, a hankali Inteesar ta shiga xamewa daga rungumar da yyi mata, ya matseta da karfi ta shiga kokuwa da shi, ya ki sakinta, ya kunna wutan dakin yana kallonta, hawaye ne kwance fuskarta, ta boye fuskar da sauri, bbu yabo bbu fallasa yace "nayi maki wani abu ne kike min kuka don munafurci?" tayi shiru bata ce komai ba har lkcn hawayen da take yaki tsayawa, ya dada rungumeta ya kashe wutan ya ci gaba da wayarsa, suna nn a hka yana ta hirarsa da safeenah har bacci ya dauke Inteesar . Karfe sha biyu da rabi ya kwantar da ita a hankali, snn ya shiga bathroom yyi wanka ya koma wani dakin yyi kwanciyarsa. Da safe taji an watsa mata ruwan sanyi ta farka a tsorace tana kallonsa da mamaki, ya galla mata harara yace "ke kafura ce ina ga ko," bata ce masa komai ba ta sauka daga kan gadon fuskarta a daure tayi hanyar fita daga dakin ya fixgota yace "ina magana xaki fita don baki da kunya," ta hararesa tace "to ca nayi maka banyi sallah bane" ya wara ido ya shaketa yace "ni kike kallo hka, wae me sa kika raina ni hka ne yarinyar nn?" ta girgixa masa kai kmr xata yi kuka tace "kayi hkuri baxan sake ba," yyi kwafa ya saketa yana kallonta tayi hanyar fita da sauri ya daka mata tsawa "ke! Uban wa xae gyara maki dakin?" ta juya tana kallon dakin snn ta dan yi tsaki ta dawo ta fara gyara gadon, ya bude Bathroom ya shiga wanka, tana gama gyara dakin ta fice da sauri tayi hanyar dakinta. Inteesar na jin muryarsa a kasa ta mike da sauri ta isa jikin window tana kallonsa yana tsaye jikin motarsa yana magana da masu gadi, ta juya da sauri hawaye ya cika idonta, jin ya tada motar ne yasa ta juya tana kallonsa har ya bar gidan snn ta dawo gefen gado ta xauna a sanyaye, tana nn a hka bayan fitarsa da kmr minti goma Zainab ta shigo gidan, Zainab ta ajiye mayafinta tana kallon Inteesar da ta kirkiro murmushi tace "lah daga ina kike da safen nn," Zainab tace "wae jiya da kuka xo gida da daddare da ya Aliyu me ya faru" Inteesar tayi shiru tana kallon Zainab snn tace"me aka ce ya faru?", Zainab tace "oho, Abba yace mu taho gida tare ynxu, ya kira Aliyu tun jiya ya ki dagawa," Inteesar tace "to ae baya nn," Zainab ta galla mata harara tace "to ina ruwana, Abba ca yyi mu taho gida ynxun nn da ke," Inteesar ta girgixa kai cikin confusion tace "to ki kira ya Aliyun ki fara gaya masa," Zainab ta bude baki tana kallonta tace "iyye sae na kirasa xa mu tafi," Inteesar tace "to ae bae sani ba," da mamaki Zainab tace "Ahh lallai," snn ta juya tace "sae anjima," Inteesar ta bi ta da sauri tace "ki tsaya don Allah Zainab," Zainab xa tayi magana wayar dake gaban madubi na Aliyu yyi ring, Inteesar ta karasa gaban madubin tana kallon wayar a tunaninta Safeena ce, ta daga wayar ta kara a kunne bata ce komai ba, "kina jina, idan kika kuskura kika fita gida ba tare da izinina ba xaki sha mamaki, just dare me, ki ga" yana kai wa nn ya katse kiran, ta juya tana kallon Zainab ta marairaice tace "yace kar na fita Zainab," ko kallonta Zainab bata yi ba tayi hanyar kofa, Inteesar ta bi ta da kallo har ta fice. Da yamma tana kwance abun duniya ya isheta tun tean data sha da safe bata sake cin komai ba ta rasa me ke damunta, jin an bude kofar downstairs ya sata mike da sauri a tunaninta Zainab ce ta kuma dawowa, ta xauna gefen gado tana jiran shigowartata, kamshin turarensa da taji yasa ta gane shi ne, ta koma ta kwanta a hankali tana kallon kofar dakin, ya tura kofar dakin ya tsaya daga bakin kofa yana kallonta, bata ce masa komai ba, ya tabe baki yace "wa ya shigo gidan nn daxu?" tayi kmr bata ji sa ba ya daka mata tsawa "ba da ke nake ba," xata yi magana taji ana kiransa da darlin, ya juya da sauri yace "srry bby, magana nake da wnn ballagaxar," Inteesar tamike tsaye da sauri tana kallon safeenah da ke lekota, ta karaso bakin kofar tanai ma safeenah wani irin kallo snn tace "karuwancin ne har sae kin biyosa gida don rashin sanin ciwon kai, ke kam kin banu banxa kawae sha sha sha," bata rufe baki ba Aliyu ya sauke mata mari ya fixgota ya jefar kan gado yana huci ya nuna ta da dan yatsa yace "ki shiga hankalinki wllh, don kika sake ce mata karuwa sae na illata ki, dabba kawae" ta sulalo kasa daga kan gadon ta fashe da kuka ssae tace "Allah ya isa ban yafe maka ba mugu kawae mara....." wani wawan marin ya sake kai mata hade da buge mata baki da karfi yana huci nn da nn sae ga jini, ta fasa ihu a gigice, safeena ta dafe kanta tare da sauke ajiyar xuciya tana yatsine fuska tace "kai bby ban cika son hayaniya ba wllh, muyi abinda ya kawo mu na bar nn plss," ya ce "srry bby," snn ya kamahannunta suka fita daga dakin tana ma Inteesar wani irin kallo tana murmushi, kuka Inteesar ta dinga yi kmr ranta xae fita ta hade kanta da gwiwa, tana nn a hka suka sake bude kofar dakin suka shigo, taji yace "nan fa bby?" Safeenah ta dan yatsine fuska snn tace "yauwa nn yafi dear, nn din nake so can bae yi min ba,". Aliyu yyishiru yana kallon safeenah, ta dan matso kusa da shi ta yi masa fari da ido tace "mun gama da wnn, kuma ni bna son irin paint din nn, mu jedear na fara jin yunwa," tana fadin hka ta juya xata fita daga dakin ya riko hannunta a hankali yace "meyasa baki son wancan dakin bby?" ta yatsine fuska tana masa wani irin kallo tace "can bai yi min ba nn nake so," ya juya yana kallon Inteesar da har lkcn ke kuka a hankali kanta kife a gwiwanta, ya maida kallonsa ga safeenah yace "to na bar maki dakina, ni sae na koma wancan," ta xaro masa ido tace "No! Ni wnn dakin nake so," yyi shiru yana kallonta, Inteesar ta mike tsaye ta dauki Hijab dinta ta sa ta ciro flat shoe dinta shima ta sa snn tayi hanyar fita, duk suka bi ta da kallo har ta iso inda suke tsaye tabi ta gefensa xata fita ya fixgota, "ke? Gidan ubanwa xaki," ta galla masa harara da jajayen idonta tace "gidan ubana xani," yace "ko?" tace "eh," ya aketa ya gyada kai yana murmushin mugunta yace "to tafi," cikin kuka tace "ni wllh sae na tafi," ya daka mata tsawa ya fixgota yana kallonta yace "ae shine nace ki tafi na gani," ta fashe da kuka ta xube wajen tana kiran Abbanta, safeenah ta dafe kanta tare da jan dogon tsaki tace "gosh! kaga nifa Hydar ban cika son hayaniya ba wnn abu hka sae kace ina kindergarten, don Allah ka taho muyi abinda ya kawo mu ka mayar da ni gida yau fa xan fara gyaran jiki" Inteesar ta mike tsaye da sauri tana mata wani mugun kallo tace "da'alla fice min daga daki rahama ya shigo, banxa da ke kawae jahila" Safeenah tayi wani dariya tana taunar cingam din yan iska tace "ae sae dae ki kira wani gun da dakin ki amma ba nn ba, don dis is myn, kuma kika sake ce min jahila wllh sae na kusan illataki kmr yanda mijinki ya gaya maki daxu, don wnn karan ba sae ya dukan min ke ba, ni da kaina xan nakade ki, ki san cewa ni ba sa'ar uwarki bace bare......" bata rufe baki ba Inteesar ta sauke mata tagwayen mari masu rae da lfya nn da nn fuskarta ya koma ja don axaba, ta dafe kuncinta a gigice tana kallon Aliyu da ya jingina jikin bango rungume da hannayensa yana kallon Inteesar da mamaki tace "wat? She slapped me Hydar" Inteesar tace "ae kadan ma kika gani," bata jira me Aliyu xae ce ba tayi kanta, inteesar na ganin hka ta fasa ihu a tsorace tayi hanyar bathroom, safeenah ta fixgota ta buga ta da bango ta shaketa tana huci snn ta shiga dukanta kmr an aikota Aliyu yyi kansu da sauri ya fixge safeenar ya watsa mata mari ya buga ta da bango yana huci yace "don ubanki kasheta xakiyi ne," Safeena tayo waje da ido tana kallonsa da mamaki, Inteesar ta sulale kasa gabanta na faduwa tana kallonsu, Safeenah ta girgixa kai ta fashe da kuka tana kallon Aliyun, ya saketa ya dafa bango tare da sauke ajiyar xuciya, can ya dawo gabanta a hankali yace "meyasa xaki kulata Safeenah baki ga yarinya bace warce bata san ciwan kanta ba, bbu abinda ta sani nn da kike ganinta she's just a kid," Inteesar ta mike tsaye tace "ku dae ne baku san ciwon kanku ba amma ni nasan ciwon kai na," Aliyu ya bude baki da mamaki yana kallonta, tayi hanyar bathroom da sauri xata shige ya bita ya fixgota a fusace, ta fasa masa ihu tare da durkushewa a kasa tace "wayyoo Abbana," ya durkushe shima da sauri gabanta yana kallonta yace "me ya faru?" ta dago tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "to ba kai bne xa ka doke ni . Aliyu yyi kwafa ya mike tsaye, ita ko ta ja da baya daga xaunen da take tana goge hawayenta, ya juya yana kallon Safeena dake hawayen takaici xae yi magana ta juya da sauri ta bar dakin yaji ta bude kofar dakinsa ya gane jakarta xata dauka a ciki ta bar gidan, ya juyo yana kallon Inteesar da ta bi ta da harara, ya sa kafa ya haureta yace "xan babbalaki a gidan nn wllh idan kika yi wasa," ta mike tsaye da sauri tayi tsaki can ciki ta koma kan gado ta xauna tana ci gaba da share hawayen fuskarta, danna bell din gidan da aka yi yasa ya juya ya fita daga dakin dae dae lkcn da Safeena ma ta fito daga dakinsa rike da handbag dinta, yace "haba bby ina kuma xaki?," ko kallonsa bata yi ba ta fara sauka daga stairs, ya bi ta da sauri yana kiran sunanta,tsaye suka ga Hajiya a falon tana kare ma ko ina kallo fuskarta a tamke, ya juya da sauri ya koma dakin Inteesar, tana nn yanda ya barta ya karasa gabanta yana kallonta ya kama hannunta ta fixge tana hararansa tace "meye hka," ya buge bakinta ya fixogata ya bude bathroom ya tura ta ciki snn ya kulle da makulli ya cire makullin yasa a aljihu, kofar ta shiga bubbugawa tana kuka, ya fice daga dakin ya sauka downstairs da sauri, tsaye yaga safeena kusa da Hajiyan tana mata magana tana kuka, ko me take ce mata oho, ya karaso yana kallonsu Hajiyar dake ta faman huci tayi hanyar stairs kmr xata tashi sama, ya juya yana kallon safeenar yace "me kika gaya mata," ta galla masa harara tace "meye baxan gayamata ba," yace "haba safeenah kin san fa ina sonki kuma dae kinga abinda na mata daxu a kan rashin kunyar da ta maki,yarinyar ce bata jin magana wllh ban san yanda xanyi da itaba," tace "dnt tell me dat kai dae kace ka fara sonta kawae,idan ba hka ba yarinyar dake mugun tsoranka kmr mutuwalkci daya xata rainaka hka idan ba wani abun ya shigatsakaninku bane kana xuwa gurinta da daddare karban sweet tunda dae kai a wnn bangaren baka da maraba da maye," yace "ya salam, haba safeena wllh bbu abinda ke shiga tsakaninmu me take dashi da xata bani, baki yrda dani bne, wllh Abbana ne yasa ta rainani hka ke ma kinsan ba wasa da ita nake ba," safeena taki cewa komai sae tabe baki da tayi, ko minti biyar ba ayi ba Hajiya ta sauka tana huci tace "kaban mamaki Aliyu ban xaci hka daga gareka ba," sae kuma ta fashe da kuka "ni dama nasan cika bakin naka na kwana biyu ne sae sun juya min kanka, na shiga uku ni Aisha," safeenah tace "no Hajiya shi ba ruwansa ae bae yi supportn din ta ba, har dukanta ma sae da yyi amma hkn bae sa ta daddara ba, ina ga kmr a gida ake xugata" Hajiya kmr xata hadiye xuciya don bakin ciki tace "to na shiga dakin ban ganta ba kuma ai," Aliyu yace "nima na shiga ynxu nace ta tafi gida ban ganta ba," Hajiya tace "xata ko ci ubanta shegiya tsinanniya, daxu fa a gabana Alhaji yace xainab taje tace ta dawo gida taki dawowa, ita ta samu gidan hutu ko to wlh ba gidan dana ba don ubanta kuma idan Allah ya yrda baxa ki shigo ki sameta a gidan nn ba Safeena," safeena tayi murmushi tace "to Hajiya naji ddin jin hkn," Hajiya tace "to ya shirye shirye safeena, kin xo ganin Aliyun ne, shi me ya hanasa xuwa" safeena tace "ehh dama yace na xo na xabi dakin da nake so ne, kuma nace wanda take ciki ne yyi min," Hajiya tace "to ae shknn sae yasa ta fiffito da kayan nata, abinda ma ba samunta xaki yi a gidan ba ae Alhaji ya nuna kawae ta dawo gida" Aliyu ya juya ya koma sama ya shiga dakin nata, ya ciro makulli ya bude kofar bathroom din, ta mike tsaye a tsorace da ganinta kasan kuka ta ci, ya karaso yana kallonta ya galla mata harara yace "uban me aka maki munafuka," ta girgixa kai a tsorace xata yi magana suka ji muryarsu alamar suna haurowa sama, ta shiga yarfe hannu tana hawaye tace "wayyo tsoro nake ji xata dawo," ya juya yana kallon kofar dakin, yaji safeenah na cewa "bari mu je dae ki gani Hajiya" da sauri Aliyu ya rufe kofar bayin ya sa makulli ya koma baya ashe tana dab da shi ya bugeta tayi baya xata fadi yyi hanxarin rikota ya rungumeta, taboye fuskarta a kirjinsa tana kuka a hankali har wani rawajikinta yake, su Hajiya suka bude kofar dakin suka shigo safeena na cewa "ban ma duba bathroom din ba wllh," Hajiya tace "ehh duk sae mu duba ynxu," xamowa Inteesar ta shiga yi daga jikinsa ya bita ya riketa yana mata wani mugun kallo, a hankali cikin muryar kuka tace "tsoro nake ji," ya mike tsaye ya dagota jin suna bude drawers dinta yasa ta girgixa masakai taki mikewa tsaye, taka kafarta yyi yana mata mugun kallo ba shiri ta mike har tana bugesa makullin hannunsa ya fadi, yasa kafa da sauri ya take amma duk da hka sae da yyi kara,ta toshe bakinta a tsorace tana harharde kafa ta rikesa tace "wayyo ya Aliyu fitsari xanyi," . Safeenah tace "ina ga kamar fa da mutum a bayin can," Hajiya tayi shiru tana kallon bayin snn ta karasakusa da bathroom din ta murda kofa ta ji shi a rufe, tana kallon safeena tace "a rufe yake ma," safeenah ta karaso ita ma ta murda taji shi a rufe, ta sa kunne ko xata ji motsi, Hajiya tace "to wae ma ina Aliyu yyi ne ban gansa ba," Aliyu ya tsura ma kofar ido yana kallo, ita ko Inteesar sae yarfe hannu take hawaye na bin kuncinta tanabubbuga kafa a kasa a hankali, har gobe ita dae tasan baxata daina tsoron Hajiyar nn ba, suka ji Safeenah tace "bari naje naga ko kofar iri daya ce da na dakinsa na dauko tasa makullin," Inteesar ta dafa sa a tsorace tace "nashiga uku wayyo Abbana," har wani bari jikinta yake, ya riketayana kallonta yace "xaki sha mari, idan baki rufemin baki ba," ta sa hannu ta toshe bakin jikintana rawa, hajiya kuwa na ta bude buden drawersdin dakin tana ta xage xage ita kadae harsafeena ta shigo rike da makullin, Hajiya tace "kinsamu," safeena tace "eh iri daya ne, bari mu budemu ga, munafuka kila tana ciki," Inteesar ta kamohannunsa hawaye ya gama wanke mata fuskamuryarta na rawa kmr mae rada tace "ya Aliyuwllh fitsari xanyi," ya jawota yana kallonta yashiga xuge mata xip din skirt dinta, ta rike skirt din da sauri tana xaro ido, ya galla mata harara murya can kasa kasa yace "ba fitsari xaki yi ba," ta girgixa masa kai sae kuma ta gyada kan da sauri kmr wata wawuya, ya xuge mata gaba daya Zip din ta rike hannunsa da sauri tana xaro ido, suka ji Safeena na kkrin saka keyn cikin kofa, ta rungumesa tana kuka a hankali tace "ya Aliyu wllh dukana xasuyi tsoro nake ji," shima ahankalin yace "ae gwara su doke kin ni da kaina ma xan bude masu kofar idan sun kasa," ta shiga girgixa masa kai cikin tashin hankali tace "A'a don Allah kayi hakuri ka kai ni gidanmu yau Abba dama yace na dawo," safeena dae na ta kiciniyar bude kofar Hajiya na taya ta, a hankali Aliyu ya bi skirt dinta da ya shiga xamewa daga jikinta da kallo har ya sauka kasan bayin, ya tsura ma laps dinta da kafafuwanta ido, don tsabar tsoro bata ma lura da hkn ba ganin wani irin kallon da ya shiga mata yasa ita ma ta kalli inda yake kallo, ta durkusa da sauri tace "na shiga uku," ya dagota, nn da nn yanayinsa ya canxa tace "wayyo Abbana......" a hankali kmr wan mashayi yace mata "ae baxa su iya budewa ba tunda ba makullin bane dnt...." bae karasa abinda xae ce ba ya shiga kissin dinta kmr xae cinyeta, ta shiga turasa da karfi suka xube kasa, bata san lkcin da ta fasa wani ihu a tsorace ba jikinta na rawa. Safeenah ta juya da sauri tana kallon Hajiya tace "ba nace maki tana ciki ba" Hajiya ta shiga buga kofar da sauri tana cewa "don ubanki fito ki bar gidan nn kar na kasheki shegiya munafuka, gidan da na yafi karfinki wllh" a tsorace cikin kuka ba tare da ta shirya ba tace "kiyi hkuri mumy xan....." buge mata baki Aliyu yyi da karfi ya mike tsaye yana kallonta ya sa kafa ya haureta, ta toshe bakinta ta koma baya da sauri hawaye na cigaba da bin kuncinta, safeenah tace "Hajiya kawae mu kira kafinta ne ya balla kofar don ba budewa xata yi ba," a fusace Hajiya tace "to wae ina Aliyu ne, ya xo ko xae iya ya bude don wllh wllh yau sae ta bar gidan nn don ubanta," safeena ta ciro waya tace "bari na kirasa," yana jin hka ya ciro wayarsa da sauri ya kashe, safeena tace "kinji tsiya wae a kashe yake," nn Hajiya da safeena suka dinga xaginta suna cewa ta bude kofar ta xo ta wuce gida kar su balla su kasheta, ita dae bata ce komai sae kukan da take yi a hankali, shi ko Aliyu na tsaye sae kallon kofar yake yana girgixa kai, sun kai kusan minti goma a dakin suna abu daya daga bisanni suka bar dakin Hajiya nacewa "ae yau da ta kwana gidan nn gwara gidan ya babbake, bari muje mu samo kafinta ya cire kofar kawae, shi kuma Aliyu don tsabar wlknci ficewa yyi ya bar gidan ga yar iska ta xo" Safeena tace "ni wllh Hajiya tsoro ma Aliyun nn yake bani," yana ji sun fita daga gidan gaba daya ya juya yana kallon Inteesar da ta xama kmr wata marainiya ya daga hannu xae xabga mata mari ta fasa ihu sae kuma ya fasa, ya fixgota yana mata mugun kallo yace "daga yau kika sake bara min wnn shegen bakin naki kmr na xaki a gidan nn sae na cire maki hakora wawiya kawae," yana kaiwa nn ya bude kofar ya fice ya bar ta nn durkushe tana kuka, direct gun mai gadi ya nufa yace "kar ka bude ma kowa gate ya shigo gidan nn, snn kar ka bari ta ciki ta fita" mai gadi yace "to yallabae, snn ya shiga motarsa ya bar gidan shima, hka Inteesar ta yini tana kuka ranar gashi mai gadi yaki barin ta fita, tsoranta daya kar su Hajiya su dawo, cikin ikon Allah kuwa bata ga sun dawo ba, har ta kwanta ranar Aliyu bae dawo gidan ba. Yau tana xaune ita kadae abun duniya ya isheta rabonta da Aliyu tun ranar da Hajiya ta xo gidan aka yi wnn draman gashi yau kusan kwana uku, budewar kofar dakinta yasa ta mike a raxane don ynxu ba karamin tsoron gidan take ba, Zainab ce ta karaso tana kallon Inteesar tace "wae dama ashe aure Aliyu xae yi Inteesar," jikin Inteesar yyi sanyi kmr lkcn ta fara jin xancen, tayi shiru bata ce komai ba, ganin Zainab ma tayi shiru yasa tace "wa ya gaya maki," Zainab tace "yau Abba ke gaya ma Inna wae ashe ma saura sati daya, tun safe inna ke kuka tana tsine tsine a gidan wae xamanta ya xo karshe a gidan," Inteesar ta xauna gefen gado bata sake cewa komai ba, Zainab tace "in ni ce ke Inteesar wlh baxan xauna gidan nn ba, infact na gama auren ma gaba daya, duka duka watanku nawa da auren ko three month fa bae cika ba," budewar kofar dakin yasa suka juya da sauri suna kallon waye, Aliyu ne ya shigo dakin yana ma Zainab wani irin kallo, nn da nn hanjin cikinta ya kada. . Zainab ta dauki mayafinta gabanta na faduwa ta kalli Inteesar tace "na tafi inteesar, inna tace na xo nace maki ki hada kayanki tana nn xuwa," tana kai wa nn ta juya ta dake tana kallonsa tace "ina yini yaya," bae tanka mata ba sae dae har lkcn kallonta yake, ta bi ta gefensa xata wuce ya cakumota ya watsa mata mari cikin tsawa yace "daga yau, na sake ganin shegun kafafunki cikin gidana wllh sae na ji maki," kuka ta fashe da tace "ni me nayi maka xaka mareni hka wlh sae na gaya ka da Abba," wani marin ya kai mata snn ya fixgota ya shiga janta har suka fita daga gidan, ita dae Inteesar bata ce komai ba sae kifa kanta da tayi kan gado tana kukan da bata san dalilinsa ba, suna isa gate Aliyu yace mamaigadi "kar ka sake barin yarinyar nn ta shigo gidan nn," mai gadi yace "to yallabae," snn ya jefar da ita waje ya rufe gate din ya koma cikin gida. Washegarin ranar da daddare Inteesar na gaban madubi ta fito daga wanka knn tana shafe shafenta gaban madubi wayarsa dakegunta yyi ring ta duba ta gane nmbrsa ce dayan, ta daga yace "ina jiranki downstairs," da kmraxa ta je ba sae kuma ta dauki Hijab dinta har kasa ta sa snn ta sauko downstairs yana xaune remote a hannunsa, yana daura idonsa kanta ya daka mata tsawa "ke daga yau kika sake sa irin wa innan hijaban a gabana sae na ci ubanki daga ke har hijabin, wawuya kawae get out," ganin bbu alamar wasa tattare da shi ya sa ta koma sama ta sa kayan barcinta mai dan mutunci don dama xani kadae ne jikinta snn ta sa gashinta cikin net ta sauko kasa fuskarta a daure, kallo daya yyi mata ya dauke kansa yace "ga kayanki nn ki kwashe su gabana," ta tsura ma akwatinan da ya nuna mata ido snn ta dake tace "na me," ya galla mata harara yace "na xubar wa, c'mon kin xo kin kwashe su gabana ko sai na bata maki rae" ta girgixa kai tana kkrin mayar da hawayenta tace "na yafe bana so, ka kara mata a nata," tana fadin hka ta juya da sauri ta koma sama, ya bi ta da kallo, kan gado ta fada ta fashe da kukan takaici tana data sanin kin bin Zainab da tayi ranan, don dae ko hauka yake baxae je yace xae daukota ba, Aliyu ya cuceta ya walakantata bakin cikin ta daya ynxu ya raba ta da budurcinta, hka ta kwana ranar tana abu daya. Washegari da safe ya shigo dakin yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "ki shirya anjima xa a raka ki registration na Jamb," yana kai wa nn ya juya xae fita ta mike da sauri tace "bbu inda xa ni wllh," ya juya yana mata wani mugun kallo yace "to sae me, me xa a fasa mutuwan ko hisabi, kar Allah yasa kije din jaka kawae" ta fashe da kuka tace "ni a jaka bace wllh, ka jira jaka na nn shigowa nnba da ddewa ba," ya karaso cikin dakin ya kwashe ta da mari ta fasa ihu tana kiran Abbatace "Allah ya isana ban yafe maka ba wlh mugu kawae," juyawa yyi ya fice daga dakin da sauri ta mike jikinta na rawa ta shige bathroom ta rufe da key. Karfe sha biyu saura taji ana ring din Bell, ta sauko gabanta na faduwa don tasan Aliyu baya danna bell, ta karaso kusa da kofar tana lekan ko waye, wani mutumi ta gani tsaye, ta ki bude kofar tace "waye," yace "ina yini madam, Yusuf ne, oga Hydar ne ya aikoni waexamu je registration da ke yau, shi yana buzy," tace "kaje kace masa ban xuwa," bata jira me xae ce ba ta koma sama abunta, da daddare Aliyu ya dawo gidan direct dakinta ya nufa ta hada tea knn xata sha, duk da ba karamin tsorata tayi ba amma ta dake bata nuna ba, kuma taki dago kanta, ya karaso inda take ya fixgota cikin tsawa yace "wani sako kika bada a kawo min daxu," ta shiga kikkifta ido a tsorace tace "ni ka kyaleni wllh," ya jefar da ita ya fice daga dakin ta bi sa da harara, ko minti biyar ba ayi ba ya dawo rike da belt, ta fasa ihu a tsorace ta mike tsaye tace "na shiga uku, wayyo Abbana," ya fixgota ya shaketa yana huci yace "na rantse da Allah idan baki kama kanki a gidan nn kinsan da wanda kike xaune ba sae na sumar dake watarana" yana kai wa nn ya buga ta da bango ya fice daga dakin, hka ta kwana kuka da ciwon kai ranan, Da safe yana fita ita ma ta shirya xata bar gidan amma mai gadi yaki bude mata gate ta dinga rusa masa kuka tana rokansa ya bude mata gate amma yace "to ko yau sae da yallabae ya kara jaddada min cewar kar na bari ki fita," ta fashe da kuka abun tausayi ta kasa cewa komai, kmr daga sama taji Muryar inna da karfi tana cewa "salama alekum, kin tabbata nn ne gidan kursum" . Inteesar na jin muryar inna ta fasa kuka tana kallon gate din, inna ta shiga bubbuga gate din tana cewa "lah nn ne kursum ga muryarta nn naji, a bude mana" Mai gadin yace "waye wnn," inna ta bude baki tace "nashiga uku amar ya waye? Waye ke min wnn tambayar," Inteesar tace "malam ka bude mata kakata ce fa," mai gadi yace "ko ma wacece yallabae yace kar na bude ma kowa gate," cikin daga murya inna tace "yau naga jaraba waye wnn kuma" kursum tace "mai gadi ne," inna tace "mai gadi? To ya ci ubansa ba a gaya masa ko ni wacece bane ni da gidan jikokina xae hana ni shiga," kursum ta fashe da dariya inna tace "ke ban san shashanci fa," sae kuma ta shiga kiran Inteesar," cikin kuka inteesar tace "Na'am inna yaki bude gate din," a fusace inna tace "yau ni naga jarababben dan iska gate din ta ubanka ce ko ko, kaji min mutum," dariya ma abun yaba mai gadin inna tace "shi Aliyun yana ina," Inteesar tace "oho nima ban sani ba," inna ta shiga buga gatedin da karfi tana duddura ma mai gadi xagi,shi dae yana xaune sae shan rakensa yake inteesar tace "wae kai wani irin mutum ne baka jin ka bude mata gate ne ka maida mutane mahaukata," inna tace "ki rabu da shege, kursum maxa kira min Bukar," kursum ta karbi wayar ta kira Abba ta mika mata tace "Bukar Bukar gani gidan Aliyu wani kato yahanani shiga, na kai awa biyu tsaye cikin rana Bukar," Abba yyi murmushi yace "to ae umarnin da aka basa knn baaba ku koma gida kawae," cikin kuka inna tace "kambu, Al'quran bbu inda xani sae ya bude min gate don uwarsa," nn ta shiga jijjiga gate din kmr xata cire tana tsine ma mai gadi, maigadi yyi tsaki ya ciro dan wayansa ya kira Aliyu "oga ga wata tsohuwa nn ta xo ta cika anguwa wae sae an bude mata gate," Aliyu yyi dariya yace "karka kuskura," snn ya katse kiran mai gadi ya mike yana fito ya shige dakinsa. Inteesar taji kmr ta shakesa ta karasa kusa da gate din tace "inna Aliyun ne fa yace kar ya bude maku wlh, ku tafi gida kawae ba budewa ae yi ba," inna ta yo waje da ido tace "me? To wllh bbu inda xani ina nn har sae an bude min gate din," cikin kuka take maganar, kursum kuwa sae dariya take har da faduwa,inna ta nemi dakali ta xauna tana sharbe majina, tace "ae yau bbu abinda xae hanani shiga gidan nn wllh sae na shiga" Inteesar ta gaji da tsayuwa ta shiga, ciki lkci lkci ta kan fito ta tarar suna nn, sae tausayin innan ya cika ta taji kmr ta dinga ihu don takaici lallai Aliyu ya cika mara mutunci, duk irin yanda ta lallaba inna ta tafi kin wucewa inna tayi, har aka kira azahar inna na nn xaune kursum ta gaji ta kama hanyar gida inna ta rakata da xagi, shegiya kawae ni ba mutum bace kuma ban san ciwon jikina ba sae ke ko, ganin har kusan karfe hudu inna na nn a xaune yasa inteesar ta fito da ruwa tana kallon mai gadi tace "don Allah don annabi malam ka dan bude gate din sae ka mika mata ruwan nn wllh tsohuwace," da kamr baxae tashi ba sae kuma ya mike ya karbi ruwan da take mika masa ya dan bude gate din yana lekota yace "ga ruwa kaka," ta mike tsaye tana kallonsa da shirin masifa ko me ta tuna sae kuma tafasa, ta karaso kusa da gate din kmr xata karbi ruwan ta bangajesa da karfi ta shige gidan da gudu. Me inteesar xata yi idan ba dariya ba, ta durkushe kasa ta dinga dariya kmr cikinta xae kulle, mai gadin ya bude baki yana kallon inna dake huci tace "don buhun ubanka ni xaka hana shiga gidan jikokina, mugu katon bnxa kawae, wllh baka sameni lkcn ina Rahmatu ba da yau bbu ubanda xae hanani faffala maka mari dan iska," Inna na kai wa Aya ta yi hanyar garden kmr xata tashi sama tana huci Inteesar ta bi ta da sauri tana ci gaba da dariya tace "ba nn bane hanyar shiga inna," Mai gadin ya sauke ajiyar xuciya yana bin inna da kallo, bae taba ganin tsohuwa da karfi hka ba, har suka shiga falo Inteesar bata daina dariyar da take ba inna ta hade rae tace "ke ni fa ban san tsiya meye abun dariya a nn, wlkncin da katon can yyi min ko me" kan Inteesar tace komai inna ta rike haba baki bude tace"A'aah bene kuma cikin gida ni Rahmatu naga abinda ya ishe ni," Inteesar tace "kuma shi xaki hau muje daki ba," inna tace "ni ina xan iya," inteesar na dariya ta ja ta suka haura sama tana mitan kafafunta na ciwo, sae da inna ta fara sllh snn Inteesar ta kawo mata abincin da ta dafa kmr dae tasan inna xata shigo gidan daga karshe, inna aka xauna aka bubbude kafa tana ci tana xagin mai gadi da Aliyu, sae da inna ta gama cika cikinta snn Inteesar ta xaga da ita ko ina na gidan har dakin Aliyu sae da suka shiga, inna sae washe hakora take tace "ashe dae xan ga wnn rana da xan taho gidan jikokina ni rahmatu, ae Bukar bae yi ba, ni ban san meyasa yake min hka ba gidan jikokina ma ya hanani xuwa sae da ixininsa sae kace ubana, daba dan hka ba ae sae na dawo nn ma gaba daya gani ga ku, ni dae ynxu 'ya yana nake son gani duk da bamu san gawan fari ba, xan so naga yayanku da Aliyu," Inteesar dae bata ce komai ba a xuciyarta tace Allah shi kyauta na Haihu da Aliyu, inna ta juya tana kare mata kallo tace "wae ni ya naji shiru ne har ynxu Inteesar ga fadila can da ciki, anya kuwa bakwa shan abu yaran nn, barin ke, nafi tausaya maki don shegen yaron nn kai ki xae yi ya baro ki" Inteesar ta hade rae tayi gaba ta barta nn tsaye, inna ta bita a baya tana cewa "to ni dae banga abun bata rae ba a nn daga fadan gskya" suna komawa daki inna ta xauna ta hade rae tana kallon Inteesar tace "ki maxa ki hada kayanki tafiya na xo yi dake dama, wae ashe gantalallen yaron nn aure xae yi ban sani ba," sae kuma ta fashe da kuka tace "sakayyar da xae mana kenn, wllh sae ya baki takardar ki ba rasa masoya kika yi ba," Inteesar tayi shiru da mamaki tana kallon inna kmr ba ita ba kuma mai son ganin ya'yansu, inna ta gama ta mike ta koma kan gado tace "bari na dan runtsa kafin nn kin gama hada kayanki," Inteesar dae bata ce mata komai ba har ta fara bacci, ta kalli agogo ta ga biyar ya gota ta mike a sanyaye ta shiga kitchen tana tunanin abinda inna ta gama gaya mata ynxu, to ynxu knn hada kayan nata xatayi gaba daya su koma gida, jikinta ba kwari ta shiga girka mata tuwan shinkafa da miyar vegetable don tana da kayan girkin gaba daya a deep Freexer, sae kusan Maghrib ta gama komai snn ta koma daki tayi wanka tayi alwala ta fito ta tada inna tayi sllh, karfe bakwae da rabi ta shigo ma da inna abinci inna tace "uban wa yace kiyi girki mu da xamu bar gidan ynxu, kin gama hada kayan naki" ta hade rae tace "to inna ki ci abinci dae tukunna mana," inna ta sauko tace "Atoh don xaman ki ya xo karshe a gidan nn yyi ta xama da amaryar tasa, wae in tambayeki wnn me sa kayan 'yar bbyn mai kaman xabiyar nn ce xae auro," Inteesar ta gyada mata kai kawae, inna tayi kwafa tace "xasu ci ubansu," snn ta fara kai loman tuwo, a tare suka gama cin abincin da inna ta kwashi kwanukan ta kai kitchen ta shiga wanke wanke ta gama ta fito knn Aliyu ya shigo gidan, suna hada ido ta dauke kanta da sauri tayi hanyar stairs yana yatsina fuska yace "wa yace kiyi girki da kifi a gidan nn, kinga ina son jin warin kifi?" tayi masa wani mugun kallo ta haura sama ta bar sa nn tsaye, ko da ta koma ta tarar inna na shafa'i da wutr, ta shiga bayi ta wanke baki snn ta fito ta xauna gaban madubi tayi shafe shafenta ta saka kayan barcinta ta kwanta don tayi isha, inna na idarwa tace "to ynxu dae tunda dare yyi, sae mu bari gobe da sassafe mu bar gidan nn, shi kuma wnn yaro dama baya dawowa gida ne naji shiru har ynxu, ko dama ke daya ke rayuwa cikin gidan," Inteesar bata tanka ta ba tana ta game da wayar Aliyu, inna ta tabe baki tace "to Allah shi kyauta, ynxu dae kije ki hado min tea don idan ban sha ba bana jin ddi" Inteesar tace "kai inna duk tuwon da kika ci," inna tace "naga dae ba ke ke siyowa ba jikana ke siyowa," inteesar ta harareta ta mike tayi hanyar fita xata je hado mata tean, tana bude kofar ta kusan cin karo da Aliyu dake labe jikin kofar, shi ma xuwansa knn, suka xaro ido a tare xata fasa ihu don ba karamin tsorata tayi ba kuma bata yi xaton ganinsa gurin ba yyi saurin fixgota ya rufe kofar . . Inteesar ta turasa xata koma cikin dakin ya rikota da sauri ya toshe bakinta ya ja ta suka shiga bedroom dinsa ya tura kofan ya jingina jikin kofar yana mata wani irin kallo, tace "meye hka ni ka bude min kofa na fita," yace "hakkina nake so ki bani yau," ta xaro ido gabanta na faduwa tace "meye hakkinka kuma," yace "bari na nuna maki, yyi kanta ta koma baya da sauri tana cewa "wllh xan maka ihu idan baka bude min kofa ba," a tsorace tayi maganar ya galla mata harara yace "kiyi mana," ta girgixa masa kai kamr xata yi kuka tace "don Allah kayi hkuri tea fa xanje na hada ma inna,"yyi murmushi yana kare mata kallo, rigar bacci ne sky blue mara nauyi iya gwiwa a jikinta mai hannun singlet, ta saka gashinta cikin net, ya lumshe ido yace "bani hakkina tukun sae kije ki hada mata kitchen din gaba daya ma," xata yi magana ya daga ta sama kamr wata yar bby sae kan gado, ba karamin tsorata tayi ba cikin muryar kuka tace "ya Aliyu don Allah ka bari ni ban san me kke nufi ba," ya cire jallabiyar jikinsa yana kallonta ya ajiye yace "xan gwada maki abinda nake nufi," xata sauko daga kan gadon ya danneta tace "wayyo na shiga uku," kissin dinta ya shiga yi yana rungume da ita, duk ta gigice ta shiga turasa amma yaki sakinta ya shiga romance dinta, kuka ssae ta shiga yi ganin abun nasa ba na wasa bne, suka ji inna ta bude kofar dakin Inteesar din ta fito tana cewa "yau naga rayuwa daga xuwa a hado min tea shiru har ynxu," inna ta rike haba tace "lau ko dae shafe shafen nn da naga tana yi daxu gun mijinta xata" sae kuma ta fita ta samu mai gadi tana kallonsa tace "kai mara mutunci mai gidan ya dawo ne," da kmr baxae kulata ba sae kuma yace "ehh" tace "amma yarinyar nn anyi yar bnxa gun mijinta ta tafi ta barni," ta koma ciki ta hada tean da kanta ta koma daki tace "ikon Allah, amma wnn anyi munafuka" Inteesar na jindawowanta cikin kuka tace "kayi ma Allah ka kyaleni na kai mata abinda ta aikeni," Aliyu bae ma san tana yi ba lkci daya yanayinsa ya canxa ya xaman mata kmr wani xautattce, duk ita ma ya bi ya kashe mata jiki ganin ya soma rabata da kayanta yasa ta kankamesa jikinta na rawa tace "don Allah ka bari ya Aliyu ka tausaya min wllh tsoro nake ji," ya girgixa kai da kyar yace "plss fateema ni ma ki tausaya min," cikin kuka tace "wllh baxan iya ba," murya can kasa yace "don Allah fa nace maki," ta shiga turasa jikinta na rawa tana kuka tace "wayyoo tsoro nake ji don Allah kajitausayina wllh bna so," ya fada gefentayana mayar da numfashi, ganin tana nemansauka daga kan gadon yasa ya fixgota ya rungumeta, cikin shessheka tace "don Allah kaji tausayina ka bari," da kyar yace "bbuabinda xan maki," duk da hkn bata kwantar da hankalinta ba sae kuka take, shi dae yana rungume da ita idonsa a lumshe, hkn yasa tayi shiru sae ajiyar xuciyar da take,suna nn a hka har bacci ya dauketa, ya kwantar da ita ya lulluba mata bargo ya koma dayan side din jikinsa a mace ya kwanta, hka ya kwanta ranan a wahale da ciwon ciki, ita ko tana ta bacci abunta, cancikin dare ganin bacci ya gagaresa yasa ya mike ya koma falo ya sami lime ya sha ya kwanta, da asuba ruwan sanyi gora guda ya tashe sa . Aliyu ya mike xaune da sauri yana kallon inna a fusace yace "meye hka," tace "so nake kasan naxo gidanka," yyi tsaki ya mike tsaye yyi hanyar stairs ya bar ta nn tsaye tana dariya, yana shiga dakinsa ya tarda Inteesar ta fito daga wanka knn, ya kalli agogo yaga biyar saura minti goma, ta kasa karasowa cikin dakin dan towel dinsa ne jikinta, bata so ya shigo ya tarda ita a dakin ba kuma wae nn ita dubara xata ma inna kawae sae dae ta farka ta ganta kwance dakin, bae sake kallonta ba ya shige bathroom, ko me ya tuna sae kuma ya fito da sauri ita ko har ta isa kan gado ta sa hannu xata dauki rigar baccinta ta sakasae ta koma dakinta, ya karasa kusa da gadon shima ya daura hannu kan rigar baccin yana kallonta, ta cire hannunta ta mike tsaye ya dauki rigar da net dinta yyi hanyar bathroom da shi ya bude washin machine ya jefasu ciki snn ya rufe kofar bayin, duk tana kallon abinda yake yi taji kmr ta fasa ihu, tasan iskanci kawae yake son mata, ta kalli towel din jikinta ynxu haka xata fita, ita gashinta dake jike ma yafi damunta, Allah dae yasa inna bata tashi ba, ganin kmr tana bata lkcn ta kar inna ta tashi yasa ta fita da sauri ta bude kofar dakinta a hankali ta shiga, xaune ta tarda inna kan darduma da casbi a hannu ta saka Tv a gaba ko ya aka yi ta kunna oho, inteesar taji kmr ta nutse don kunya inna ta kalleta ta tabe baki tace "ban san baki da kunya ba Inteesar sae yau, idan ba rashin kunya ba kina ganina a gida ki tafi turakar mijinki ki kwana daga cewa ki kawo min tea, da kika tashi dawowa kuma sae ki dawo mun daure da tawul," Inteesar ta galla mata harara tace "ku ji min tsohuwar nn me xan maki idan ban tafi gurin mijina ba to," inna ta bude baki, Inteesar tayi dariya ta dauki xani ta cire towel din jikinta ta daura, inna tace "ae ba dan jiya dare yyi ba da baxa ku tashi ku tarar dani gidan nn ba, inteesar bata tanka ta ba ta dauki Hijab ta sa ta tada slh, ko da ta idar ta gaida inna maimakon ta amsa sae ca tayi "ni tashi ki hada min kayan karyawa nayi na bar gidan nn tun kan na fara ganin abinda yafi karfina," inteesar xata yi magana Aliyu ya bude kofa ya shigo dakin yana kallon inna, daga tsayen yace "an tashi lfya," inna ta galla masa harara tace "ban tashi ba, hka kke gaida uwarka," Aliyu yace "har gida xan xo na rama abinda kika min daxu wllh," Inteesar ta mike ta fita daga dakin ya bi ta da kallo ya tabe baki yana kallon inna yace "yar nn bakuyi mata trainin me kyau ba a gida, bata san ta tashi ta gaida mutum ba da safe," inna tace "ae gun uwarka ta gaji hka, wae ni Aliyu ya naji shiru har ynxu ban ganta da ciki ba," Aliyu yace "ita ce tace bata son Haihuwa,shine ma yasa xan auro warce ke son Haihuwan" inna tayo waje da ido tace "kmr yaya," xae yi magana wayar inna ta cika daki da ruri ta daga da sauri tare da cewa "salama alekum," ya mike ya fice daga dakin, kitchen ya sameta tana hada ma inna break, ya karaso kusa da ita yana kallonta yace "ke gidanku ba a koya maki idan kin tashi da safe kiyi gaisuwa ba ko," ta tabe baki bata ko kallesa ba bare ta basa amsa, kmr xae yi magana sae kuma ya fasa ya matsa dab da ita yace "gobe xa a xo ayi ma amaryata danki, kuma tace dakin da kike ciki take so don hka nake so kije ki fara fiffito da kayayyakin dakin ki xaba wani dakin ki xuba su ciki," tayi yar dariya bata ce komai ba, yace "hope dats clear," tayi masa wani mugun kallo ta juya xata fita daga kitchen din ya kamo hannunta. Inna na xaune a daki tana kallo bayan ta ci tayi kat, inteesar kuwa na wanke Bathroom Aliyu ya shigo yana kallon inna yace "inna xo mu je indan xaga dake gari mana tunda ina gida yau," inna na kallonsa da mamaki don daxun nn suka gama fada tace "kai da gske? Amma fa ba tukin nan taka ta ganganci xaka yi dani ba fa," yace "wllh a nutse xan tuka ki," ta mike da sauri tana gyara daurin dankwalinta tace "to ita Inteesar ita kadae xa mu bari gida, wae ma to wa xae je ya kwaso min kayana ne," yace "ehh xan kira Zainab ta kwaso maki, inna tace "Inteesar ke baxa ki je bane, Aliyu yace "ki dae gaya mata me xata girka maki kafin mu dawo," inna tace "to kiyi min tuwan semo da miyar kubewa," inteesar ta fito tana kallonsu, ko kallonta inna bata yi ba tace "sae mun dawo," ta fice Aliyu ya juya ya galla mata harara snn ya fice shima, mai gadi na bude masu gate tace "yauwa Aliyu wnn ba mutumin arxiki bne jiya kokuwa ya dinga yi dani ka koresa," yace "to inna," suna ta tafiya suna hira inna sae kyalkyale dariya take duk da Aliyu bae ga abun dariya ba don hiran ma ba ganewa yake ba, tafiyar kusan minti talatin suka yi snn yyi parkin yana kallon inna yace "to fito in siya maki nama," inna ta fito da sauri tace "yauwa dan albarka" tana kare ma inda suke kallo bakinta a wangale, can sae fara'ar dake fuskarta ya bace tace "nn ae anguwansu farida ne Aliyu," yace "yauwa ashe kin gane, *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** kuma nasan xaki iya gane gida daga nn kina shan kwana xa ki ga gate, in kin koma sae kice da Haisam ya siya maki naman don ban fito da kudi ba" yana kai wa nn ya shige motarsa yyi gaba inna ta fasa ihu tana salati, mutanen dake gun suka taho da sauri suna tambayar lfya. Inteesar na kwance da daddare ya shigo gidan ita dae tasan bbu maganar dawowan inna gidan, tana ji ya bude dakinsa ya shiga, ta mike xaune ta rafka tagumi tana naxarin abinda yace mata daxu da safe ita har lkcn ta kasa gaskata wae Aliyu aure xae yi nn da kwana hudu, tunanin hkn yasa hawaye ya cika idonta, tana nn xaune har kusan karfe daya ganin bacci ya kaurace mata yasa ta mike a sanyaye ta shiga bathroom ta dauro alwala ta fito ta fara sllhn dare. Da safe tana gaban madubi tana gyara fuskarta ya shigo dakin, 1st tym in history Aliyu ya shigo mata daki da sallama ta amsa ba tare da ta kallesa ba yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "kina jina, ki kama kanki safeenah xa su xo gidan nn anjima don nasan baki da kunya, infact bance ki fita ba ma," tace "akan me baxan fita ba? Wllh bbu abinda xae hanani fita," yace "shknn, ni kuma xan ce mata duk abinda kika yi mata tayi min maganinki" ya juya ya fice daga dakin bayan kmr minti goma ya dawo yana kallonta yace "kinga dakina yyi kama da dakin kaya, c'mon kin wuce kin dauke min kayanki da kika ajiye min a ciki ko sae na bata maki rae," xata ce wani kaya sae ta tuna kayan baccinta dake dakinsa ta mike fuskarta daure ta fita tayi hanyar dakin ya bita a baya tana shiga dakinsa ya jawo kofan yasa key, ta juya da sauri tana kallon kofar ta shiga bugawa tana cewa "meye hka," yace "hka xaki tsaya har sae na dawo," ya rufe nata dakin ma da key snn ya fice ya bar gidan, kuka ta fashe da ta durkushe tana kare ma dakin kallo, sae a snn ta lura da kayan tea da cakes din da ya ajiye mata kan fridge sae plantain chips, karfe sha biyu taji ana shigowa gidan da motoci ta mike da sauri don bayan ta gama cin kukanta ta gaji kwanciya tayi, ta karasa jikin window taga manyan motoci shake da kaya har kusan guda uku, wasu lafiyayyun motoci suka shigo gidan, manyan mata kusan su goma suka fito suna daddaga hanci, sae ga wata motar ma ta shigo safeena da kawayenta suka fito daga cikin motar tana gwada masu ta inda xa su bi su shiga gidan, tuni aka fara sassauke lafiyayyun funitures din da aka shigo da, Inteesar ta sake labulan a sanyaye ta koma kan gado tayi kwanciyarta tare da lumshe idonta da taji na neman kawo kwalla, duk suka cika gidan da hayaniya wasu na sakin magana, ana ta shigo da kaya. Ko minti sha biyar ba ayi da shigowarsu ba Anty Nafeesa da Zainab suka shigo gidan, suna shiga falo duk aka juya ana kallonsu, batare da Anty Nafeesa ta kallesu ba tace Sannunku fa, Zainab kuwa dama ko kallonsu bata yi ba, Safeena dake kwance kan kujera da kawayenta suna ta hira da shewa ta bi su da wani irin kallon raini hka ma iyayen nata, cikin daga murya Anty Nafeesa tace "to ina uwar gida sarautan mata kuma ran gida take ne," Zainab tace "ina xata iya da wnn hayaniyar Anty, kila tana can cikin daki," . Safeenah da 'yan uwanta suka bi su da kallo har suka haura sama Anty Nafeesah na cewa "gskya kam ina xata iya da wnn hayaniyar," wayar Zainab yyi ring ta duba ta ga ya Aliyu, tace "ashe dae ya Aliyu na da nmbrna," ta daga yace "ki fito waje ki karbar maku makulli," tace "na me," yace "ban sani ba snn ya katse kiran" ta kalli Anty Nafeesa dake buga kofar inteesar tana kiranta tace "wae yaya naje na karba makulli a waje," Anty Nafeesa tace "na me, ko tare suka fita da Inteesar din ne," Zainab tace "kila, ina xuwa na karbo keyn," ta fice da sauri, yana cikin mota yana jiranta ta karasa ya mika mata keyn dakinsa da na Inteesar, tace "to ina inteesar din," yace "in kun bude xa ku gani," ya ja motarsa yyi gaba, ta tabe baki ta koma cikin gidan, dakin Inteesar suka fara budewa bbu kowa ciki, snn suka bude nasa, tana xaune ta hade kai da gwiwa, suka karaso cikin dakin Anty Nafeesah tace "amma Aliyu dan rainin wayo ne kulle ki yyi a daki don ya isa," Zainab ta dago kanta tana kallonta, kuka take, Anty Nafeesa ta galla mata harara tace "ban san shashanci kukan lfya" ita dae bata ce komai ba ta gaida Anty Nafeesa, Zainab tace "meye na kuka Inteesar" Anty Nafeesah tace maxa tashi kije ki gyara fuskarki kiyi kwalliya kar na bata maki rae ke dae baki gajiya da wnn shegen kukan naki komai kuka komai kuka, ita dai bata ce komai ba suka bar dakin Aliyu Zainab ta kulle suka koma nata dakin, sae da ta sake wanka snn Anty Nafeesa ta sa ta gaba ta tsantsara kwalliyanta snn ta fito mata da wata shaddarta dogon riga maroon colour ta saka Nafeesa tayi mata dauri mai kyau, Zainab tace"waw yan matan yayanmu kin ga yanda kika xama kmr wata balarabiya," inteesar ta galla mata hara, ba karamin kyau tayi ba duk da ta rame ssae, Anty Nafeesa tace "to akwae abinci ne a gidan? Don ni yunwa nake ji," Inteesar tace "sae da na girka maku," Anty Nafeesah tace "to da dae yafi," ta ce "toAnty suna falo kuma," Anty nafeesa tace "to ina ruwanki da su ae don su ganki da kyau nake son kije kiyi mana girkin," ta mike ta dauko mata takalmikalan shaddar ta ajiye mata snn ta feshe ta da turare tace "maxa sa ki tafi indomie kawae xaki girka mana," Zainab tayi dariya tana kallon Anty Nafeesa, Inteesar kam murmushi tayi ta sa takalmin gabanta na faduwa ta fita xuwa kitchen, duk suna xaune falon har da safeena kusan su goma banda wa inda ke ta jere a daki, Inteesar bata ko kalle inda suke ba a nutse cikin takunta mai jan hankali ta nufi kitchen ta bude kofar kitchen din tana yatsine fuska don duk sun dauki cups sun sha lemo da shi, ta dan tabe baki ta shiga kitchen din, duk kawayen safeena suka juya suna kallon safeena da yanayinta ya sauya lkci daya xuwa bacin rai tana kallon kofar kitchen din, inteesar ta kunna gas ta daura ruwa snn ta fito falon ta shiga kwala ma Zainab kira cikin wani irin tsiga, da sauri Zainab ta sauko tana cewa "na'am yan matan yayanmu wnn kira hka," inteesar ta galla mata harara da wasa tace "ban fa son iskanci indomie nawa kike ga xae isheku," Zainab tace " wani irin tonan asiri ne wnn, ko ma dae duka nace ae gidan yayana ne nn bbu uban da ya isa ya hana," Inteesar tayi dariya ssae tace "ikon Allah to shigo ki girka maku kinsan dae ni ba daga nn ba ban gaji rowa ba kuma duk yanda nace hka xa ayi a gidan nn bare kice kina tsoran wataran ki xo...," a fusace safeena ta mike tana nuna Inteesar da yatsa tace "ke ki kama kanki kar ki kaini bango don dukan tsiya xan maki wllh wllh kuma sae dae mijikinki ya gode min idan ya dawo," Zainab ta yo waje da ido tace "wa xa a duka ni Zainb" Inteesar tayi dariya tace"tambayan min ita don ni kaina ban gane inda ta dosa ba," Safeena ta ciro wayarta da sauri ta shiga kiran Aliyu, "Aliyu Aliyu ka ja ma ballagaxar da ka ajiye a gida kunni wllh ta fita harkata idan ba hka bakafin na bar gidan nn yau sae na yi mata kaca kaca, kuma wnn shegiyar kanwartaka ita ma kaja mata kunne," Zainab tace "wllh ni ba shegiya bace sae dae kece shegiya," Inteesar ta ja ta suka shiga kitchen suna dariya, safeena tayi shiru tana sauraran abinda Aliyu ke ce mata tana bubbuga kafa, sun gama dafa indomien knn xasu wuce samaAliyu ya shigo gidan, ba karamin tsorata inteesar tayi ba tayi hanyar stairs ba tare da ta kallesa ba, Zainab tace "ke kar ki bada kanki mana ki tsaya ae Anty nafeesa na nn," Aliyu na kallonta yace "ke xo nn," ta galla masa harara tace "nayi maka me," karasowa kusa da ita yyi ta dake xuciyarta na bugawa, duk yan falon suka xuba masu na mujiya, ita kanta Zainab karfin hali tayi ta tsaya, Safeena kosae taunar cingam take tana jujjuya ido xuciyarta fal murna ita nn kawayenta suka yanda ta isa da Aliyu, yana isa kusa da inteesar ya kama hannunta ta fixge tace "da'alla malam kyaleni," ya tsaya kallonta da mamaki bae ce komai ba,ya juya yana kallon Zainab yace "je dauko mata mayafinta ko ki bata naki," Zanab ta cire mayafinta ta mika ma Inteesar taki karba, shi ya karba snn ya sureta kmr wata bby suka fita daga gida . Inteesar ta tsorata ssae murya can kasa tace "don Allah kayi hakuri ka saukeni wllh ita ce ta fara,"Safeena kam binsu tayi da kallo da mugun mamaki don tsabar mamaki kasa rufe bakinta dake bude tayi, ita nn jira take taga ya rufe ta da duka, Zainab kuwa dariya tayi tace "kai irin wnn soyayya hka, ko me Inteesar ke ma yayana hka oho," ta haura sama tana ci gaba da dariya, bayan mota ya jefata snn ya xaga ya shiga motar ya ja ta, ita ko kallonsa kawae take gabanta na faduwa ko ina xae kai ta, sun yitafiya ssae snn taga yyi horn aka bude gate ya shiga yyi parkin, ya bude mata kofa yace "fito kar na mareki," ta fito tana kare ma wajen kalloduk da tasan inda ya kawota don ta taba xuwa, lallai ma Aliyu asibiti ya kawota, yyi gaba tana biye da shi a baya kmr xata yi kuka, nurses duksuka kama kansu ganinsa, suka bi inteesar da kallo suna masu sannu da xuwa, bae ko kallesuba sae ita ce ta gaishesu ganin yanda suke kallonta, can last flour office dinsa yake kusa dana aminin dad dinsa don shine mai asibitin wato dad din Sadeeq, ya bude office dinsa ya shiga, ganin taki shigowa yasa ya fixgota, ta shiga karema office din nasa kallo, ba karamin haduwa yyi ba kmr ba office ba ita fa bata taba gskata Aliyuna aiki ba duk da tasan da sassafe yake barin gida ya dawo late, ya shiga dakin da ke cikin office din ita dae tana nn tsaye har ya fito bayan kmr minti goma sanye da kayan surgery, green colour yana kkrin sa hand gloves alamar theatre xae shiga, ya galla mata harara yace "kada Allah yasa ki xauna kuma idan lkcn sllh yyi kar kiyi," snn ya fice, tayi tsaki kmr xata yi kuka ta xauna kan kujera tana kare ma office din kallo, ko minti goma ba ayi ba da fitarsa wata nurse ta shigo rike da abinci a rufe da lemo ta ajiye mata tace "sannu madam," snn ta fita. Hka inteesar ta yi ta xama kamar gantalalliya a office kmr tayi kuka, abincin da aka kawo mata ma kin ci tayi, ta gaji da xama ta kwanta kan gadon da ake duba pregnant women tayi kwanciyarta sae bacci, ko da ta farka taga biyar ya kusa ita da ta kwanta tun kusan daya da rabi, bata damu ba don dama bata sllh, ta bude abinci daxu ta yatsine fuska ta rufe, aka bude kofa wasu nurse biyu suka shigo da jarirae har biyu suka yi ma inteesar sannu, snn suka daura su kan gadon yara dake office din daya ta kunna wani wuta mai haske dae dae fuskarsu snn suka fita, inteesar ta wara ido tana kallon yaran kyawawa dasu, ta karasa kusa dasu da mamaki tana kallonsu tace "yan biyu," a hankali dayan ya shiga kuka yana tsotsan hannunsa dayan ma ya karbe taji kmr ta daukesu don tana bala'in son yara, ta rasa yanda xata yi dukta rude ganinsu tayi can tayi nn, aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo ta juya da sauri tace "ya Aliyu yan biyu ne?" ya cire abun bakinsa yace "ehh" ba tare da tasani ba tace "waw a ina kukasamo su" ya karaso kusa da gadon yana kallonsu yace "daxun aka cirosu daga cikin mamansu, bata farfado ba har ynxu ma" inteesar ta juya da sauri tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "theatre aka mata," xae yi magana daya yaron ya tsala ihu tace "wayyo ya Aliyu in daukeshi," ya harareta yace "basu da lafiyasuma," tayi shiru tana kallonsu kmr xata yi kuka.Ya dauki dayan a hankali ya mika mata yana kallonta. . A hankali Inteesar ta sa hannu ta karbi bbyn da yake mika mata tana murmushi, tace "ya Aliyu ni ina son twins ssae" yana kallonta yace "kina sonki haifi twins knn," da sauri tana kallonsa tace "eh mana ina so," ganin irin kallon da yake mata yana murmushi yasa taji kunya ta kauda kanta da sauri, wae Aliyu take ma wnn maganar? Ita bata ma sani ba, ya matso dab da ita ya tsaya har tana iya jiyo numfashinsa a bayanta ya rike kugunta yace "wnn waist din naki xae iya daukar twins?," ta bar wajen da sauri nn da nn ta tsorata xae yi magana ta riga sa da sauri tace "Yaya yunwa fa suke ji ko," bae ce komai ba sae kallonta da yake, ta daga bbyn xata yi kiss dinsa ya dakatar da ita da sauri, snn ya karbe shi ya kwantar gefen dan uwansa, tace "yaya baxa a basu abinci ba," yace "sae xuwa karfe sha biyu na dare," ta wara ido tace "sbda me yunwa fa suke ji," yace "eh xa ayi ta basu ruwa" kmr xata yi kuka tace "to waye xae dinga basu kace mamarsu bata farfado ba," ya daka mata tsawa "ke da'alla kar ki dame ni" yyi tsaki ya shiga daki, ta bisa da kallo snn ta tabe baki ta koma kujera ta xauna, wata nurse ta shigo rike da mug a rufe tana kallon Inteesar tace "doctor fa? Ya shigo?" a dari dari take tambayar, Inteesar ta gyada mata kai, nurse din ta ci gaba da tsayuwa har ya fito sanye da kananan kaya, yana kallonta yace "wathappen" tace "coffee sir," ya daka mata tsawa "to kaina xaki daura ko me," ta karasa kusa da table ta ajiye ta fita sum sum. Ya bude abincin da aka kawo ma inteesar yana kallonta yace "meyasa baki ci ba," tayi kamr bata ji sa ba, ya rufe ya koma kan table dinsa ya xauna kan kujera ya bude coffeen ya shiga sha, hka yaran suka dinga kuka Inteesar taji kmr ita ma tayi kukan, ta kasa jure kukan nasu tace "yaya kuka fa suke," ya kalleta yace "cnt yhu see they re under medication," bata sake cewa komai ba bayan kmr minti sha biyar ya kira nurses su kashe wutan su fita da su, inteesar ta bi su da kallo kmr xata bi su suna fita ta bata rae ta juya tana kallon Aliyu taga kallonta yake yana murmushi, ta dauke kanta da sauri, karfe takwas da rabi suka bar asibitin bayan ya kaita ta kara ganin yan biyun da mamarsu, ya biya ta eatry ya siya masu abinci snn suka kama hanyar gida, gidan ba kowa duk sun watse sae kamshin turaren wuta ke tashi, ta haura sama ta bar sa nn falo shima ya bi ta a baya, spare key Aliyu ya dauko ya bata na dakinta don su Anty Nafeesa sun tafi da shi, dakin safeena ma a kulle yake ta tabe baki, ta bude kofar dakinta, ba shiri ta koma baya da sauri tana kallon dakin da mamaki kadda cikin dakinta aka yi ma safeena jere, ta juya tana kallon Aliyu da ya fito daga dakinsa yana kallota yace "Abba ne ya ba kansa wahala ya bata kudinsa shi me 'ya," ya sauka kasa ya barta nn, sababbin funitures masu rae da lfya wanda suka fi na da ne a dakin nata, ashe su Anty Nafisa abinda suka xo yi knn, ta karasa cikin dakin a sanyaye, bbu abinda ba a canxa ba a dakin. Tanaxaune gefen gadonta bayan ta fito daga wanka ta sa kayan bacci tayi jigum ta ma rasa abinda ke damunta ya shigo dakin ya ajiye mata ledan abinci ya fice. Ranar friday da yyi dai dai da Ana gobe daurin auren Aliyu da safeena ranar da kuma xa suyi dinner, Inteesar na kwance a daki da rana duk ta rasa kanta kmr wata mara lfya, rabonta da Aliyu tun ranar da ya ajiye mata abinci ya fice sae dae taji shigowarsa da fitarsa, Zainab da kursum kadae ke xuwa debe mata kewa, taji an bude kofar dakinta a xatonta su ne, Aliyu ya shigo dakin ya xauna gefen gado yana kallonta yace "mantawa nayi jiya bamu je party da ke ba" bata ko kallesa ba bare ta basa amsa, ya tabe baki ya ajiye mata dan box karami irin na jewelries yace "tunda kince ba kya son kaya ga wnn, don banso in shiga hakkinki," ta juya tana kallon box din ya bude mata, Zinari ne dan kunne da sarka har da xobunaye biyu, tayi tsaki tace aikin bnxa me xanyi da wnn gantalin kadae je ka kara mata don wanda ubana ya sa min a kayana ma ba damuwa nayi dasu ba bare wnn, ku wnn ya dama" ya mike tsaye fuskarsa daure yace "ni kike gaya ma magana," ta fashe da kuka tace "an gaya maka din wlh ka fitar min a daki," yyi murmushi ya dauki box din ya fita daga dakin, tasulale kasa tana kuka ssae da bata san dalilinsa . ba, karfe bakwae suka shigo gidan da abokanansa suka shirya suka wuce dinner. Har Aliyu ya shigo gidan karfe daya idon Inteesar biyu, ta kasa bacci, hka kawae ta samu kanta da fashewa da kuka har da shessheka, har kusan karfe biyu tana xaune bbu alamar bacci a tare da ita, taji an tura kofan dakinta a hankali ta juya da sauri suka yi ido hudu da shi ta kauda kanta da sauri ta mike xata shiga bathroom yyi hanxarin rikota ta fashe masa da kuka ya rungumeta . Inteesar ta shiga turasa yaki sakinta, har suka isa kan gado ya xaunar da ita shima ya xauna yana kallonta ya dago kanta a hankali yace "me ya hanaki bacci har ynxu," ta dauke kanta har lkcn tana hawaye ta mike xata bar wajen ya rikota, a hankali ta shiga rera masa kuka ya rungumeta yace "ina son jin kukan ki har wani ddi nake ji idan naga kina kuka," ta turasa da karfi xata mike ya rike ta gam yace "not until yhu tel me y yhu re cryn," ta fashe masa da wani kukan abun tausayi ya daga ta ya kwantar da ita kan gadon ya kwanta gefenta ya rungumota snn ya kashe wutan dakin, ajiyar xuciya kawae take, a hankali yace "don xanyi aure shine kike kuka," xata yi magana ya rufe bakinta da sauri, yace "warce xata haifa mana 'yan biyu xan auro, kinga sae kiyi ta raino tunda kina son su," bata ce komai ba ya daura bakinsa kan gashinta yana kissin dinshi, a hankali ya kai hannunsa kan cikinta yana shafawa kmr mae mata rada yace "xaki iya na baki yan biyun ynxu?" a tsorace ta rike hannunsa da sauri tace "A"a wllh baxan iya ba," a hankali yace "plss," muryarta na rawa tace "No plsss" ita kam 1st nyt dinsu kawae take tunawa da irin wahalar da tasha har da suma har abada bata fatan ya sake kusantarta, ya kankameta murya can kasa yace "to yi baccin ki," suna nn a hka har bacci ya dauke ta, ranar dae a hka suka kwana tana jikinsa kuma ranar ce rana ta farko da ya kwana a dakinta, washegari da yyi dae dae da ranar daurin aurensu da safeena, da asuba ya kwantar da ita a hankali ya shiga bathroom dinta yyi alwala, ko da ya fito ya tarda ta xaune kan gadon tayi tagumi, ta mike ba tare da ta kalleshi ba ta shiga bayin ita ma tayi alwala ta fito ta tar da shi yana jiranta, a tare suka yi sllhn, rana ta farko knn da ta bude baki da safe ta gaishesa ba tare da ta kallesa ba yana murmushi ya gyada mata kai kawae, ta mike xata bar dakin ya kamo hannunta yace "ina xa ki," ta sunkuyar da kanta bata ce masa komai ba, ya saketa ta fita, falo ta sauka ta shiga mrnin duties dinta, ba ita ta koma sama ba sae kusan karfe tara,ta tarda shi kwance yana bacci, wanka ta shiga ta fito ta gama shirinta ta fita daga dakin ta koma downstairs, bata ba kanta wahalan hada breakfst ba don bae taba cin girkinta ba, tayi kwanciyarta a falon don neman yunwa tayi ta rasa, karfe sha daya taji mai gadi ya bude gate ta mike ta isa jikin kofa taga ko waye ya shigo, motoci biyu ne suka shigo gidan abokanansa kusan su biyar suka fito, da yake kofar a bude yake komawa kawae tayi ta kwanta, suka shigo gidan da sallamarsu duk suna sanye da fararen shaddodi, ta kara volume din Tv ta mayar da hankalinta kan TV, tsokanarta suka shiga yi suna dariya "uwar gida ke kika rike ango har ynxu yaki fitowa kuma kika sa ya kashe wayoyo ko to ayi hakuri a sakar mana shi muje gun daurin aure," bbu yabo bare fallasa tace "ku dae tambayesa wanda ya rikesa," ta mike fuskarta a daure ta haura sama ta bar su nn falo, a step duka hadu da Aliyu ya galla mata harara, don me baki tashe ni ba, ita ma ta galla masa hararan tace "sbda baka isa ba," tayi gaba ta bar sa nn tsaye, ya sauko suna ta tsokanarsa wae tsoron uwargida yasa ya makara, dole suka jirasa yyi wanka snn ya fito shima sanye da farar shaddar, ba karamin kyau yyi ba don ko hmm bari dae, ya shiga dakin Inteesar tana xaune gaban madubi, kallo daya tayi masa ta madubin ta dauke kanta yace "kinyi break," tayi bnxa da shi, ya daga kafada yace "sae na dawo kiyi mani adduar Allah yasa ayi a sa'a," ya juya xae bar dakin ta fashe da kuka ba tare da ta shirya ba, ya juyo yana kallonta, ya karaso cikin dakin yace "an maki wani abu ne ko kawae jin ddin kukan ne ke damunki," bata tanka sa ba, ya tabe baki ya juya ya fita, suka fita gaba daya da abokan nasa suna masa mitan ya bata lkci dayawa ko mantawa yyi yau ce ranar daurin aurensa da sahibarsa shi dae bae ce masu komai ba har suka shiga mota suka bar gidan, suna fita daga gate yace "kun san wani abu ku je kawae gani nn xuwa, ina son na kai fateema can gida daga can sae na wuce," namesake dinsa yace "wae meye hka kke yi ita bata san hanyar gidan ba sae an kaita baka ganin saura yan mintoci," Aliyu yace "ni dae kuje kawae ina nn xuwa, ya bude motar ya koma cikin gidan," suka yi tsaki kusan gaba dayansu suka yi gaba, yanda ya barta hka ya dawo ya tarar da ita, ya dauki hijab dinta ya mika mata yace "tashi to na kai ki gida," bata yi musu ba ta mike ta karbi hijab din tasa takalminta suka fita, motarsa ya fito da ta bude sit din baya ta shiga, bai ce mata komai ba ya ja motar suka bar gidan, suna isa gida bata jira ya gama parkin ba ta bude mota ta fice, ya dakatar da ita da sauri ko kallonsa bata yi ba ta shige gidan da gudu sae sashin inna, hkn yyi mugun bata masa rae kuma yasan da mutane cikin gidan shi yasa bae bi ta ba, ya ja motar kawae yyi gun daurin aure, mutanen dake tsakar gidan har da su Hajiya suka bi ta da kallo murna fal cikinsu, umma ko ta dinga tuntsira dariya tana guda kawayen Hajiya na taya ta. ta xube jikin inna ta fashe mata da kuka, a rude inna ta shiga tambayarta "meye faru, ke da waye," ta kasa cewa komai, inna ma ta bare baki ta fashe da kukan, Anty Nafeesa ta fito daga daki da sauri tana kallon Inteesar tace "wa ya kawoki," inteesar tayi kkrin tsayar da kukanta tace "shi ya kawo ni," Nafeesa tace "ynxu kuwa muke shirin tafiya can gidan, kukan meye hka kike yi, ke dae baki ji ddi ba wllh," a fusace cikin kuka inna tace "ban son iskanci ke uwar wa yyi maki kishiya," inna ta mike ta daga inteesar tana share hawayenta suka shiga daki tana cewa "ki rabu da shi, bbu abinda xaki koma gidan nn kiyi, kuma bbu uban da ya isa yace ki koma tunda nace baxa ki ba, ina nn ina jiransa daga shi har ubansa," Anty Nafeesa tayi murumushi ta bi su cikin dakin. Gida ya cika fal da yan uwan su Hajiya da umma da abokanan arxiki ana ta shagalin biki har da su Dj a gidan, inna na daki xaune gefen Inteesar da ta kwanta tana bacci tana mata fiffita ita ma tana gyan gyadi, jin kide kide yasa inna ta farka ta fito da gudu har Anty Nafeesa da wa inda ke falonta suka tsorata suka dinga tambayar lfya, ko kallonsu bata yi ba ta fita xuwa tsakar gida da gudu, Anty Nafeesa ta ma xaci abu ne ya sami Inteesar suka shiga dakin da sauri suka tarar baccinta take, wasu kuma suka bi inna da sauri a baya suna tambayar wae Hajiya mai ya faru, inna na isa tsakar gidan cikin daga murya tace "nashiga uku uban wa ya gayyato wa innan shaidanun gidan nn" ta fadi hkn a fusace tana nuna masu Dj da kayan kide kiden nasu, aka kashe wakar dake tashi, Umma tace "to naga dae yau ranar farin ciki ne inna kuma dae daga yau ba sake ganinsu xa ayi ba," inna tace "kin ci ubanki mai dattin hula, kaji min rubabbiyar yarinya," ta karasa kusa da masu dj tana huci ta shiga bubbuga speakers din tana cewa "ku fitar min dasu kar na babbake su, gidan da na ba gidan yan iska da shaidanu bane" ba shiri Hajiya tasa aka shiga kwashe su a barrow ana fita dasu, hka ma canopies din duk sae da tasa suka fita dasu tana jaraba an cika gidan dan'ta da tarkace, hka mutane suka dinga kallon inna wasu na dariya can ciki ciki, "kuma duk shegen da ya xauna kusa da flawowin da na ban yafe masa ba duniya da lahira tunda dae ba shi ya dasa masa ba, ko tsinke kuma kar a wurgar a tsakar gidan nn," ta fadi tana huci kmr kirjinta xae fashe, Hajiya dae shigewa daki tayi kunya kmr ta nutse, wae juyawar da inna xata yi sae ganin momy tayi xaune suna hada salad, ta saka salati kmr xata yi kuka tace "Allah ya wadaranki Zainabu, ynxu uban me ya kawo ki cikinsu idan ba shisshigi da neman suna ba, ca suka yi maki yi suke dake mara xuciya kawae wahalalliya, ni dama nasan tun ba yau ba kika tsani yarinyar nn kike son ganin karshenta, idan ba hka ba taya xaki kwaso kafafuwa ki taho nn cikinsu, wllh daga yau kar ki sake nuna kin san Inteesar, ita ma bata sanki ba wllh, shi yasa ma da ta xo daxu bata nufi inda kike ba dan tasan ba sonta kike ba" ta karashe maganar da kuka ssae har da tari, ta bar wajen tana cewa "kuma yau bbu ubanda ya isa ya bar min tsakar gidan da' na hka, duk sae an wanke shi an goge wllh," dariya wasu har da xubewa kasa, ranar dae a dari dari su Hajiya suka yi shagalin bikinsu, jefi jefi inna kan fito taga ko an xauna kusa da flowern da tace kar a xauna, bbu wanda yyi gigin xama kuwa. Da Magrib bayan kowa ya watse inna ta tasa su Hajiya gaba sae da suka wanke tsakar gidan su Zainab da kursum da Maryam din Anty Nafeesa dariya kmr cikinsu xae fashe, dama momy tun daxu ta shiga ciki amma sae da inna taje ta fito da ita wae har da ita yar bakin ciki maxa su gyara ma dan ta tsakar gidansa, sae da taga sun kusa gamawa snn ta koma sashinta tana cewa "wahalallun bnxa kawae" karfe takwas abba yyi kiran Inteesar falonsa, ta karasa falon a sanyaye tayi sallama ta shiga, Zaune ta tarda Aliyu a falon yana sanye da shadda brown colour, ta nemi gefe ta xauna tana kallon Abba tace "ina yini Abba," Abba ya amsa yana kallonta yace "ya gidan," ta sunkuyar da kai tace "lfya Abba," Abba ya nisa yace "ranar da nace ku taho da Zainab don me kika ki bin ta," ta daga kai tana kallon Aliyu dake kallonta, Abba ya gyada kai yace "to yyi kyau, kuma har ynxu baki fara karatun ba ko?" a hankali tace "Abba na kusan farawa," Abba yyi shiru yana kallonta snn yace "to Allah yasa, ki tashi ki bi mijinki, a cigaba da hakuri, Allah yyi maku albarka" Aliyu ya mike yana kallon Abba yace "nagode Abba," ko kallonsa Abba bae yi ba, Inteesar ta yi shiru kmr xata yi kuka tace "Abba inna tace ba ynxu......." Abba ya hade rae yace "inna tace me, tashi maxa ki koma dakin ki, kuma bance ki shiga cikin gida ba," bata san tayi mugun ba Abba haushi ranar da ya aika Zainab kiranta taki xuwa ba, a sanyaye Hawaye na kkrin sauko mata ta mike tace "Abba sae da safe," yace "Allah ya tashe mu lfya," Aliyu ma yyi masa sai da safe ya bi bayanta suka bar falon . .. Suna fita Aliyu ya kamo hannun Inteesar da sauri ganin bata son jerawa da shi, ta juya tana kallonsa yace "mu fara shiga na gaida momynki," tayi masa mugun kallo tace "ae ko baka fada ba dama momyta ce bance taka ba," bai ce mata komai ba yana rike da hannunta suka isa sashinsu, shi yyi sallama ganin tsaya kawae tayi ta rike kugu, duk da ita yaso tayi sallamar, Ihsaan ce ta amsa ya shiga falon tana biye da shi a baya, suna hada ido da momy ya kauda kai da sauri ya nemi kujera ya xauna, ita ma ta xauna kusa da ihsaan da ta kankameta, momy dae na rike da assignment books din ihsaan, ba tare da ya kalleta ba yace "ina yini," ita ma tana neman page din da aka ba ihsaan bbu yabo bbu fallasa tace "kalau," Inteesar ta mike ta koma kusa da momynta tace "assignment ku ke yi momy," momy ta gyada mata kai, tace "bari nayi assistn dinta momy," momy ta bar mata buk din, ihsaan tace "Anty ae na iya," Inteesar tace "to xo kiyi," ta mika mata buk din ta karba ta shiga yi, momy ta mike ta shiga daki, inteesar ta juya tana kallon Aliyu da ya bita da kallo, ko kadan ba ta jin ddin yanda momy ke masu, ta mike a sanyaye ta bi ta daki, shi kuma ya dawo kusa da kanwartasa yana kallon abinda take yi, tana ganinsa ta daina rubutun, yana kallonta yace "y did yhu stop," tayi shiru taki cewa komai ya mike xae koma inda yake taji tsoro ssae don ta xaton dukanta xae yi, yyi murmushi yyi xamansa yace "to na bar maki wajen," ta ci gaba da abinda take, da Haisam ne jikinta na rawa xata fada kansa, amma da yake shi ya koya mata tsoransa shi yasa bae damu ba, to a gidan nn ma waye baya tsoransa, yyi murmushi tuno hka da yyi, yana nn xaune har kusan karfe tara da rabi snn inteesar ta fito bayan sun dan yi hira da momy, ta xauna gefen kanwarta tana kallon abinda take, murya can kasa yace "ki ce ma momy xa mu tafi," ta mike ba tare da ta kallesa ba ta shiga dakin, sae ga ta ta fito a sanyaye tace "tace to," hkn ya sa ya gane baxata fito ba knn, ya mike yana kallon ihsaan yace "bby gud Nyt," ta kauda kanta bata ce komai ba tana kallon inteesar kmr xata yi kuka tace "Anty ni xan bi ki," Aliyu yace "je ki tambayi momy to," ta shiga daki da gudu, sae ga ta ta fito kmr xata yi kuka tace "tace a'a," yace "je ki ce mata plss," ta koma da gudu sae ga ta ta dawo da hawaye tace "tace xan je sch," yyi shiru yana kallonta snn yace "i promise xan xo na dauke ki nxt wk kin ji, sae ki dinga tafiya sch daga can," ta gyada masa kai kawae ya ciro dubu biyar ya mika mata tayi masa gdya snn ta daga masu hannu suka fita daga falon Inteesar na murmushi, da kansa ya bude mata gaban motar ta shiga snn ya xaga ya bude driver sit ya ja motar suka bar anguwar, bae ce mata ba bata ce masa ba, suka yi nisa ssae snn taga yyi parkin ya fita ta bi sa da kallo, tasan me xae siyo ganin inda suka tsaya, ba a wani dau lkci ba ya dawo rike da ledoji har biyu ya bude motar ya shigo snn ya ja ta suka bar gun suka kama hanyar gida, suna isa yyi horn mai gadi ya bude ya shiga yyi parkin snn ta bude motar ta fita shima ya fito ya kulle motar ya bi bayanta suka shiga gidan, kamshi ne mai ddi ke tashi a gidan, ta kalli agogo taga karfe goma da kusan rabi ta haura sama ta bude dakinta ta shige, ya dde xaune falo snn ya mike shima ya haura sama da ledojin a hannunsa yana kallon kofar dakin safeena ya bude nasa dakin ya shiga, ba a dau lkci ba ya fito sanye da jallabiya ya bude kofar dakin safeenar ya shiga, tana xauna sae taunar cingam take tana kallo ta wurgar da mayafinta gefenta, ya karaso yana kallonta yyi murmushi ya ajiye ledar hannunsa yace "amarya bakya laifi," ta galla masa mugun harara tace "daga ina kke Aliyu xaka shanya ni nn, har kawayena sun gaji da jira sun wuce," ya xaune gefenta ya rungumota yana shafa bayanta yace "Abbana ne ya bata min lkci bbyna kiyi hkuri," ta dan marairaice kmr xata yi kuka tana shafar fuskarsa tace "har naji haushi wllh angona," yyi kissin din goshinta yace "nasan kina jin yunwa bari na kawo plate da cup na xuba maki chicken da yogurt din da na siyo maki, tayi kissin din lips dinsa tace "to mijina," snn ya mike ya fita, dakin inteesar ya bude a hankali, tana kwance kan gado ta tsura ma Ac ido, yana kallonta yace "kinci abinci can gida ne," tayi bnxa da shi ya karaso kusa da ita ya hade rae "ba magana nake maki ba," nn ma taki ce masa komai sae dae me, ya lura kuka xata fara ta yanda tayi da fuska ya xauna gefenta da sauri yace "wae ke wace irin mutum ne da shegen kuka sae kace marainiya," yyi tsaki ya ce "saura idan na kawo maki abincin kar ki ci," snn ya fice, sae da ya fara shiga kitchen ya dauko plate da cups snn ya koma dakin safeenar, ita ma ta fito daga bayi knn sanye da dogon hijab ta xauna gefen gado, kaji uku ne taga ya ajiye daya gefe da yogurt biyu, ta sauko tana kallonsa tace "wnn fa dear," yana xuba mata kajinta a plate yace "na warcan ce" ta jingina jikinsa ta marairaice tace "xafi nake ji bby," yace "to cire hijabin mana, a hankali ta shiga cire hijabin tana masa wani shu'umin kallo . Aliyu ya dauke kansa da sauri ganin wasu shegun kayan baccin dake jikinta ya ci gaba da abinda yake, har ya gama ya ajiye mata nata snn ya dauki na Inteesar ya mike xae fita ya kai mata, safeena da ta koma kan gado ta xauna ta daura cinya daya kan daya tayi yar kara ya juya da sauri yana kallonta yace "me ya faru bbyna," kamr xata yi kuka ta shiga nuna masa bayanta ya karasa kusa da ita yana kallonta yace "me ya samu bayan dear," cikin tsigar shagwaba tace "nima ban sani ba," ya dafa ta ya dan duka yana duba bayan da take nuna masa ta turasa da sauri ya fada kan gado ya wara ido kan yace komai ta fada kansa ta shiga yi masa wani mahaukacin kiss tana shafa kirjinsa, turata ya shiga yi yana cewa "wait wait bbyna bari na kai mata abincinta stop it," ko kulasa bata yi ba ta karbe ledan hannunsa ta ajiye snn ta kashe wutan dakin ta shiga masa wasu abubuwa masu rikitarwa da kashe jiki nn da nn ya fara dauke wuta, shima ya shiga biye mata, haukatasa ne kadae safeena bata yi ba daren ranar don sumbatu kawae ya dinga mata, kamar yanda ta basa wahala hka shima ya wahalar da ita, ta shiga rera masa kukan kissa, bae sarara mata ba har sae da komai ya wakana ta dde jikinsa tayi lamo har sae da ya dawo nml snn ya turata gefe ya mike tsaye ya kunna wutan dakin yana mata wani mugun kallo yana huci, tana kwance kamar wata macijiya a kan gadon, ya girgixa kansa ya juya da sauri ya fice daga dakin ya shiga nasa dakin yyi wanka snn ya sauko falo ya kunna Ac duk da da sanyi garin yyi kwanciyarsa kan doguwar sofa ya lumshe idonsa xuciyarsa na harbawa da sauri ga wani mugun takaici da ke masa yawo a kai," hkn yasa ya dafe kansa yana kiran Allah a xuciyarsa, ya mike xaune ganin kwanciyar baxae masa ba, ya harde hannuwansa yace "Godforbid," ya kai minti talatin a hka a xaune snn ya mike yana kallon agogo karfe biyu da qtre yyi hanyar kitchen ya hado coffee ya dawo ya xauna ya shanye snn yyi kwanciyarsa, sae a snn bacci ya daukesa a falon. Da Asuba a bayin dake falo Aliyu yyi alwala ya tafi masallaci ya dawo yyi kwanciyarsa a falo, ganin bae jin komawa bacci yasa ya dauki remote ya kunna TV ya rage volume din yana kallon tashar Animaux, karfe bakwae yaji an bude kofa can sama, ya juya yana kallon stairs din daga kafafuwanta da yanda take tafiya ya gane ko wacece, ta sauko kasa tana sanye da rigar bacci iya gwiwa, tana tafiyar nn nata mai jan hankali, ita bata ma lura da shi ba sae da ta shigo falon, kallo daya tayi masa ta dauke kanta da sauri tayi hanyar kitchen ya bi ta da kallo har ta shige kitchen din snn ya sauke ajiyar xuciya ya ci gaba da kallonsa, aka bude kofa kuma ya bi stairs din da harara sanin ko waye, sae ko ga Safeena ta sauko tana mika da hamma sanye da kayan bacci iya cinya, nonuwanta rabi duk a waje, murya can kasa kmr mara lfya tace "shine sbda ba ka da imani Aliyu xaka tafi dakinka jiya ka kwanta bayan ka gama biyan bukatanka ka bar ni da wahala, wllh ban samu bacci ba jiya, bayan hka kuma gari na wayewa naji ka bude kofa ka sauko kasa ashe kwanciyarka ka xo kayi sbda baka damu da halin da ka sani ba ko," a tunaninta budewar kofar da taji na dakinsa ne bata san Inteesar bace, Aliyu ya mike a fusace yyi kanta ya shaketa yana huci yace "kika ce me?" ta xaro ido a tsorace tace "meye hka kke yi Aliyu," yana mata mugun kallo ya jinginar da ita jikin bango a nutse yace "ina kika kai Virginity dinki safeenah," ta hade rae tana kallonsa tace "kamr ya? Ban gane wnn tambayar taka ba Hydar, kana nufin ka kusance ni ne jiya don kaci xarafina, ko kai makaho ne baka gane ma idonka ba, ko so kke budurcin nawa ya fito yyi maka magana," daga ita har shi cikin natsuwa suke maganar don hka ba lallai bne wanda ke sama yaji me suka cewa sae dae mutum na downstairs ne, ya saketa yana mata wani irin kallo yace "prove it ynxun nn cewar ke Virgin ce," ta hararesa tace "ok," snn ta haura sama, yyi murmushin takaici sanin abinda xata je ta dauko masa ya bi ta da kallo xuciyarsa na tafarfasa, sae ko ga ta ta fito rike da xanin gadon jiya da ya bace da jini ta jefa masa gabansa tana masa mugun kallo, ya daga xanin gadon yana kallo, snn ya jefa mata a fuska yace "kin yaudari ubanki," ta wara ido ta dafe kirji tace "ubana fa kace Aliyu," yace "shi fa, ni xaki yaudara da fake Hymen, me kika maidani safeena kin manta ko wanene ni? Kin ci darajar ina sonki da bbu abinda xae hanani baki takardarki yau, ni ba maxinaci bane don hka Allah ne kawae ya kaddaro min aurenki," tayi shiru gabanta na faduwa kmr kirjinta xae fito tana kallonsa, dae dae nn Inteesar ta fito daga kitchen rike da cup din tea, safeena ta juya da mugun mamaki tana kallonta, tana wani irin taku mai jan hankali ta xo ta wuce su tana ma Safeenar wani mugun kallon wlknci tana murmushi, Safeena taji kmr kasa ya bude ta shige, lallai Aliyu ya tona mata asiri idan har dae yarinyar nn taji abinda suke cewa, sbda tsabar iskancin dake cin Inteesar bata ma san ta isa bakin stairs ba ta kusan faduwa ta rike karfen da sauri kofin hannunta ya fadi ya fashe ruwan tean ya malale kan tiles din falon ta fasa ihu tana cewa "wayyoo xafiii,", da sauri Aliyu ya karaso wajen ya dauke ta ya koma baya yana kallonta yace "ke makauniyace," ta marairaice kmr xata yi kuka tace "to ban sani ba, ido ne yyi min yawa," ya ajiye ta kasa ta ce "wayyo xafi kafar ke min," ya daga ta yana kallon kafar sae yarfe hannu take, yyi tsaki ya dauketa ya haura stairs din suka bar Safeena nn a tsaye, kallon safeenar take yana rike da ita tana murmushi, suna kaiwa karshen stairs tayi mata wani kallon bnxa tana kallon xanin gadon dake gabanta a yashe, Safeena taji kmr taji a mafarki ne hkn ke faruwa, hawaye ya cika idonta tana huci ta shiga kiran layin uwarta, bugu biyu ta daga cikin muryar kuka tace "momy mun bata kudin mu ne kawae a bnxa ya gane ni ba budurwa bace, ya ci xarafina momy ya walakanta na gaban yar iskar yarinyar nn duk taji cin mutuncin da yake min," a rude uwar tace "kashe kashe kar su jiki, xan kira ki anjima" ta katse wayan tana kukan takaici, kai amma Aliyu bashi da mutunci ko kadan, Aliyu na shiga dakinsa rike da Inteesar ya kwantar da ita kan gado yana duba kafar nata ko kwalba ne ya shiga, ganin yana ta ba kansa wahala yasa a hankali tace "ni ba komai a kafata," ya daga kai fuskarsa daure yana kallonta ya mike tsaye yace "fita ki ban waje," ta hararesa ta mike ta bi ta gabansa ya bi ta da kallo har ta fice daga dakin, a corrido taga safeena na kkrin shiga dakinta ta fashe da dariya ba tare da ta shirya ba har da faduwa . ... Safeena tayi kanta a fusace tana huci, da gudu ta sake komawa hanyar dakin Aliyu ta kwala ihu, ya fito da sauri yana kallonta yace "me ya faru," kmr xata yi kuka tana nuna safeena tace "ba ita bace ba," ya juya yana kallon safeenar fuskarsa a daure yace "tayi maki me?" Inteesar tana kallonsa tace "wae ta wani yo kaina kmr wata lioness xata dokeni sae kace uwata," ta karasa maganar tana hararan safeena, yana kallonsa safeenar yace "to ki doketa tunda yar ki ce," Inteesar tayi tsaki ta wuce su ta bude dakinta ta shige tana xaro mata ido, safeena taji kmr a mafarki hkn ke faruwa ta kasa cewa komai sae kallon Aliyu da take, shima yyi tsaki ya koma dakinsa ya bar ta nn tsaye. Inteesar na daki bayan tayi wanka ta shirya cikin wani less mara nauyi mai shegen kyau an mata riga da skirt lafiyayye, kwance take tana game da wayar Aliyu, taji ya buga kofar dakinta ta dago kai tana kallonsa yace "uwar wa xae gyara maki falon da kika yi litter da tea da kwalabe," ta xumburo baki ta ci gaba da game dinta, yace "ba magana nake maki ba," ta mike tsaye fuskarta daure ta bi ta gefensa ta fice ya bita da kallo, ya sauke ajiyar xuciya, tana sauka ta shiga kitchen ta fito da mop da bokiti da tsintsiya da parker ta rasa ta inda xata fara gyaran ga shegen tean shima ya malale har cikin falon, ya sauko yana kallonta yace "ohh tsayuwa kika ma yi knn," kmr xata yi kuka tace "to ni ban san yanda xanyi ba" ya tsaya kallonta, ta karyar da kai ita ma tana kallonsa, sae abun ya kusan basa dariya, yyi kwafa ya karbe broom din daga hannunta ya duka ya fara tattara broken mugs din, tana tsaye tana kallonsa, ya dago yana kallonta yace miko min abun kwashe sharan kmr xata yi kuka tace "baka ga kwalba a wajen ba xan taka," ya tsaya kallonta ya kasa cewa komai, dae dae nn Safeena ta sauko da dogon hijabinta xa ta kitchen hado tea ganin yunwa na neman hallaka ta, yace "miko min abun kwashe dirt din can Safeena," bata yi masu ba ta dauka ta mika masa jikinta na rawa, a tare ta taimaka masa suka gyara falon Inteesar na tsaye tana kallonsu, safeena na goge falon ya daka ma Inteesar tsawa yace "get out kar na mareki, meye amfanin ki a nn" ta ja dogon tsaki ta haura sama daga shi har safeenar suka bi ta da kallo, yyi kwafa kawae, da daddare ya hadasu a falo xae yi masu magana, Inteesar dae nata kallonta abunta, yana kallon safeena yace "kina ji na Safeena," safeena da ta xama kmr marainiya ko kuma nace ta kirki tun daga jiya, kanta a duke tace "ina jinka," ya kalli Inteesar da ta bar kallonta tana hararanta, yace "kema kina jina," ta yi bnxa da shi ta ci gaba da kallonta, ba karamin daure ma safeena kae abinda Inteesar ke yi yyi ba, lallai xata yi maganin shegiyar nn nn ba da ddewa ba, Aliyu bae damu da bnxan da inteesar tayi masa ba yace "ke kika xo kika sameta a gidan nn safeena don hka ki sani gaba take da ke a gidan nn, bana son wani tashin hankali a gidana ku kame kanku, kar wanda yyi kishi kaina ban aikesa ba, kowa tasa ta fishshesa," ya juya kan Inteesar "ke kuma fitsararriya ki rike fitsararki, ki sani safeena ta girmeki nesa ba kusa ba, ke din yaushe kika balaga ma kika san me duniya ke ciki, yarinya dake sae shegen rashin kunya ki tambayeta shekararta nawa ta fada maki kiji, u had beta respect ur self coz she's nt ur mate, snn girki as frm nxt wk duk every 2dayz xaku ke yi, bana son tashin hankali a gidana i repeat my self kuyi respectn kanku" Inteesar ta mike tsaye tana gyara daurin dankwalinta ta ja dogon tsaki tace "sannu balagaggu, kuma ba girmata ba har haifata Safeena tayi," tayi masu kallon bnxa xata haura sama ya bita da sauri ta saka gudu amma duk da hka sae da ya kamota ya shaketa yace "uban waye sa'anki a nn," ta fashe da kuka tana kiran Abbanta ya jefar da ita kan kujera yana kallon safeena yace "in ta maki ki gyara mata xama ni na sa ki," xata mike daga kan kujerar yace "in kika tashi sae na watsa maki mari," ganin bbu wasa a tattare da shi yasa ta koma tana kuka, yana kallon Safeena yace "kije ki shirya mu siyo abinda kika ce," murna fal cikinta ganin abinda aka ma Inteesar tace "ni a shirye nake," ya ciro makullin motarsa, ta mike ta bi bayansa suka fice daga gidan tana ma Inteesar wani irin kallo tana jujjuya ido. Basu dawo gidan ba sae kusan karfe sha biyu, inteesar na kwance bayan ta gama cin kukanta har lkcn bata yi bacci ba, muryar safeena taji tana cewa "bby ka bari mu shiga ciki mana don Allah ka bari," cikin kissa take maganar, Inteesar ta mike ba tare da ta shirya ba kuma bata san dalili ba ta shige bathroom ta kulle . Yau safeenah ta cika sati uku gidan Aliyu ko sau daya kallon kirki bae taba hadata da Inteesar da ta xame mata jaraba a gidan ba, gashi ba dama tayi mata ko da kwakkwaran kallon bnxa Aliyu ya hau ta da bala'i don yace mata baya so, ta kyaleta kawae yarinyace kuma yarinta ke damunta, bbu yanda Safeena ta iya don tana mugun son Aliyu kmr rayuwarta duk abinda Inteesar tayi mata sae dae ta gaya masa, wani lkcn ya shareta wani lkcn kuma ya samu Inteesar din ya tsoratata ko kuma ya sa ta kuka, shima ta lura ba a son ransa yake yin hkn ba, ko sau daya Inteesar bata taba shiga kitchen tayi masu girki a gidan ba ko da kuwa ranar girkinta ne sae dae Safeena tayi a bisa umarnin da Aliyu ya bata, don ca yyi ta rabu da ita kawae ta dinga girki kullum, littafin girki kadae ne ke taimakonta don bbu abinda ta iya da ya wuce tafasa ruwan xafi, cikin ikon Allah kuwa idan tayi sae ya dan yi ddi da taimakon littafin, ta adana littafinta ssae, iyaka idan ta fito inteesar ta shiga ta dafa indominta ko taliya, ganin rashin amfaninta a gidan yasa Aliyu ya kai ta da kansa tayi registratn din jamb ana saura sati daya a rufe, kila idan ta fara xuwa makaranta xae samu kwanciyar hankali don bata tsinanasu da komai sae tashin hnkli a gidan, wani lkcn yakan yi mamakin ashe yarinyar nn na da baki hka, kuma fitsarewarta lkci daya da rashin tsoran kirkin da take masa yana mugun basa mamaki shi dae ba wasa da ita yake bare yace kuma tunda ya auri safeena bae nemeta ba, gaba daya ta daina tsoransa sae taga yyi kanta xae doketa ta marairaice masa tana kuka, gashi abu kadan sae ta bara masa baki ta fasa masa ihu a gida ba gaira ba dalili, shi kuma yana kyaleta ne kawae sbda Abbansa don ko kadan Inteesar bata gabansa don bbu abinda Safeena ta rage shi da barin a wajen kwanciya shi yasa yake ji da ita, duk da yakan yi murmushi idan ya tuna 1st nyt dinsu da Inteesar, da yanayin da ya shiga da har yau bae ji hkn gun Safeena ba, darajar da Inteesar ke ci kadae a gunsa knn banda hka da bata isa ta taka masa matarsa da yake ji da ba, Safeena kanta na mamakin yanda Aliyu ke share Inteesar duk da iskancin da take xuba masa, ita bbu abinda yafi daga mata hankali ma irin mugun rainata da Inteesar tayi, amma tasan duk Aliyu ne ya ja mata tunda ga irin tonan asirin da yyi mata washegarin ranar da aka kawo ta gidan, wani lkcn takan yi murmshin takaici tace nasan tanadin da nayi maki yarinya kiyi yanda kike so lkcn ki ne ynxu. Ranar da ya kaita tayi registratn din jamb can ya barota ya bata kudin mota ya wuce office, bata bari adai daita sahun ya shigo da ita layinsu ba ta sauka ta basa kudin don yau tana son ta kare ma anguwar kallo tunda dae ba fita take ba, tana isa bakin gate dinsu taga wata yarinya da baxata wuce ta ba rike da wani kyakkyawan yaro a hannunta tana waya, Inteesar ta dauke kanta ganin sun hada ido, yarinyar tace "sannu fa," inteesar tace "yauwa, ngdd," ta danna bell mai gadi ya bude mata ta shiga, taji yarinyar ta burgeta yar kyakkyawa da ita, safeena na kwance a falo da kawayenta ta wucesu tana yatsine fuska ta haura sama, bayan kwana biyu Aliyu ya hadata da driver taje ganin centre dinta, tana dawowa ta sake haduwa da yarinyar a bakin titi ita ma xata karasa layin da kafa tana rike da danta, bayan sun gaisa Yarinyar tace "amma aure kike a gdan nn ko," Inteesar tayi murmushi tace "eh," yarinayr tace "to ya sunanki," inteesar ta gaya mata yarinyar tace "ni kuma sunana Aneesah," Inteesar tayi murmushi tace "to yaron ki fa," yarinyar tace "sunansa Abdush-shakur," Inteesar ta karbi yaron tana murmushi tace "fyn shakur," har suka isa dai dae gidajensu, yarinyar tace "kina da kyau ssae, ina son mu xama kawaye," inteesar tayi dariya tace "to ai kema kina da kyau," Aneesah ta bata wayanta tace "sa min nmbrki to inteesar," Inteesar tace "wllh wayan mijina ne a hannu na ki bari idan na samu waya," Aneesah tace "to mu shiga kiga gidana mana" inteesar ta xaro ido tace "mai gidanki baya nn," Aneesah tace "A'a a Abuja yake aiki sae wkend yake dawo wa," inteesar ta bi ta suka shiga gidanta, gidane babba kmr nasu bbu abinda ya xama bakonta a gidan don duk suna da shi a nasu gidan, har bedroom ta shiga da Inteesar, inteesar ta shantake suka dinga hira kmr da can sun san juna, ta girka masu abinci ta kawo masu dakin suka ci suna ta hira tana ba Inteesar labarae kala kala, Inteesar taji kmr kar ta bar gidan, karfe shidda saura ta rako Inteesar har bakin gate kmr kar su rabu, har shakur ya saba da Inteesar don har da kukansa, wae sae da ta isa jikin gate tukunna gabanta ya shiga faduwa a xuciyarta tace "Allah yasa ya Aliyu bae dawo ba," mai gadi ya bude mata gate ta shiga taga motarsa a parke a garage xuciyarta yyi mugun bugawa da kyar tana jan kafa ta shiga gidan. Batatarda kowa cikin falon ba tayi sum sum ta haye sama ta bude kofar dakinta a hankali ta shige, xama tayi kan gado ta sauke ajiyar xuciya, jin an fara kiraye kirayen sllh Mahgrib yasa ta mike ta tashiga cire kayan jikinta xata dauki xani ta daura ta shiga wanka don bata sllh taji an bude kofar dakinta, ta tsorata ssae tace "wayyoo Abbana," ta durkushe da sauri tana kare kirjinta da hannunta don undies kadae ne jikinta, ya karaso cikin dakin yana kallonta yace "daga ina kike," taki cewa komai kuma taki dago kanta tana durkushe inda take, ya karasa gabanta ya dago ta ta shiga nonnokewa a tsorace tace "wayyo ya Aliyu ban sa kaya ba," ko kulata bae yi ba ya jinginar da ita jikin bango yana mata wani irin kallo nn da nn yanayinsa ya canxa, duk ta tsure tana son durkusawa yaki barinta ta fashe masa da kuka, ya sauke ajiyar xuciya ya sake ta ya fice daga dakin ta tajawo xaninta da sauri ta shiga wanka, tana fitowa ta gama shafe shafenta ta saka kayan baccinta, ta saka gashinta cikin net ta fita dafa indominta, xaune ta tarda Aliyu a falo safeena na jingine jikinsa suna kallo, ya bi ta da kallo har ta wuce su tana tabe baki ta isa kusa da fridge ta dauki five alive ta bude ta sha ta rufe ta mayar da sauran don bbu mai shan five alive a gidan sae ita, ta juya ta watsa masu harara ta shige kitchen yin abinda ya sauko da ita ya mike da sauri safeena na tambayarsa inda xa sa bae kulata ba ya haura sama ya shiga dakinsa bae dau lkci ba ya fito rike da kwayoyi har uku a hannunsa, bae bari safeena ta lura da komai ba ya shiga kitchen Inteesar na duke cikinta ya hanata sakat, ta mike da sauri ta koma baya a tsorace, bae ko kalleta ba ya dauki cup ya fice, ta dan yi tsaki ta bude tukunyar indomienta tana dubawa, yana fita falo yyi hanyar fridge safeena sae binsa take da kallo, ya juya mata baya ya ciro drink din five alive din da inteesar ta bude ta sha ya xuba kwayoyin a ciki ya rufe ya mayar ya ajiye snn ya fito da hollandia yogurt ya xuba a cup din da ya dauko a kitchen ya rufe ya mayar da sauran a fridge snn ya dawo falo ya xauna gefen safeena yana shan hollandia yoghurt dinsa, Safeena tace "ae da kayi magana na kawo maka shine ka ba kanka wahala," yace "bana son ki ba kanki wahala ne," bata sake cewa komai ba ta kwanta jikinsa tana shafa shi, shi dae idonsa na kan Tv ganin irin abinda take masa yasa ya hade rae yace "stop it am nt in d mood," tayi shiru bata ce komai ba amma bata ji ddin hkn ba don tana jin ddin Aliyu ya iya sa mace ta manta hanyar gidansu gashi yau a matse take, Inteesar ta fito daga kitchen rike da plate din indomienta ya juya yana kallonta har ta isa kusa da fridge ta bude ta ciro Five alive dinta a xuciyarta tana cewa ni da cikina ma ke ciwo, ta dan tabe baki ta rufe fridge din, juyawar da xata yi suka hada ido da Aliyu ya kauda kansa da sauri ta tabe baki ta haura sama, ya sauke ajiyar xuciya har safeena na tambayarsa lfya, bae tanka mata ba yana ta kallonsa har kusan karfe sha daya snn ya mike yana kallonta yace "xanje in kwanta sae da safe," ya haura sama ya bar ta nn xaune, tasan tunda bae nemeta ba yau idan ta kai kanta walakanta ta xae yi, don hka sum sum ta mike ranta bae so hkn ba don tana bukatansa yau ta shige dakinta ranta a bace. Shi kam yana haurawa sama dakinsa ya shiga ya hada coffee yasha don shi mayen coffee ne, snn yyi wanka ya canxa xuwa nyt wears dinsa ya bude kofar dakinsa yyi hanyar dakin Inteesar, xaune ya tarda ta a dakin ta jinginar da kanta jikin gado idonta a lumshe, ya karasa gabanta ya durkusa yana kallonta, ta bude idonta da ya kada yyi jajur a hankali tana kallonsa. . *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Aliyu yyi murmushi yana kallon cikin idonta ya daura goshinsa kan nata har tana iya jiyo numfashinsa a fuskarta ta lumshe idonta ya dagota ya xaunar da ita kan gado ya dago kanta yana kallonta, a hankali kmr mai rada yace "kina bukatan wani abu ne," kin cewa komai tayi ta koma can tsakiyar gado xata kwanta, bae hanata ba ya barta tayi kwanciyarta snn ya dawo gefenta yana shafa fuskarta yace "to yau baki tsorona" idonta lumshe bata ce komai ba ya dagota ya rungumeta ya shiga kissn din wuyanta yana shafata, da kyar ta turasa muryar ta can kasa tace "ka bari," shima murya can kasa yace "shkkn tunda ba kya so," ya sake ta ya mike ta rikosa da sauri ta fashe masa da kuka, ya rungumeta cikin rada yace "to duk me nayi maki kiyi mani ke ma," xata yi magana ya daura bakinsa kan nata a hankali yace "kiss me," ta lumshe idonta ta shiga kissn dinsa, he could'nt belive it, ya kankameta, ta dauke bakinta daga nasa tana mayar da numfashi kmr xata yi kuka, a hankali ya shiga cire mata kayan baccin jikinta yana kissn dinta, ya shiga romancin dinta kmr xae hadiyeta ita ma lkci lkci takan mayar masa da martani ganin yana neman xautar da ita gaba daya yasa ta kankamesa tana mayar da numfashi tace "plsss" bae tanka ta ba har sae da yaga ta fara kuka snn ya shiga rabata da sauran kayan jikinta, turata yyi ba tare da ya shirya ba, ya fada gefen gado yyi rub da ciki yana mayar da numfashi ta fada kansa tace "no, plss ya Aliyu," duk ta xama kmr wata mara hankali, da kyar ya dago ya rungumota murya can kasa yace "u re nt clean," ta rikesa tana girgixa masa kai tana hawaye ta kasa cewa komai sae mayar da numfashi da take, ya mike da kyar ya fice daga dakin, ta fada kan gado tana kuka a hankali tunda take bata taba shiga irin yanayin da ta shiga ranan ba, ta ma rasa meke damunta kawae, wnn abun dae da take mugun tsoro yau taji take mugun bukata kmr xata yi hauka, ta rasa inda xata sa ranta, ta dukunkune waje daya kmr mai jin sanyi, Aliyu ya bude dakin ya shigo ya karasa kusa da gadon rike da kofi a hannunsa ya dago ta, ta fada kansa tana kuka tace "don Allah ya Aliyu," ya kai mata kofin baki ta dauke kanta da sauri yace "magani ne" ta maida kanta jikinta na rawa ta shiga shan abinda ke kofi, ruwan lime ne, sae da ya tabbatar ta shanye snn ya kwantar da ita ya lulluba mata bargo ta xama kmr wata mara lfya, yaji tausayinta ssae gashi har uku ya xuba mata, da kyar ta samu bacci ya dauketa, snn ya mike ya dauki juice din ya shiga bathroom ya xubar ya fice daga dakin, dakin Safeena ya shiga ya biya bukatansa. Da safe tana wanka ya shigo dakin, ta kasa fitowa daga bathroom din duk da ta gama wani mugun kunyarsa take ji, to wae jiya wani jaraban ne ya sameta ita kam, tunda take bata taba experiance din abinda taji jiya ba, ya gaji da xamansa a dakin ya fice duk da yasan ta gama wankan fitowa ne kadae baxata yi ba gashi ta sa key, yana fita ta fito da sauri ta kulle dakinta da key, tana shiryawa gaban madubi taji muryarsa da safeena can kasa, ta mike da sauri ta bude curtain din window tana kallonsu, tana sanye da wasu shegun matsatsun kaya, ya bude mata mota ta shiga ya xaga shima ya shiga snn ya ja motar suka bar gidan, ta sake labulen ta koma gaban madubinta amma ta samu kanta da kasa yin komai kuma, ta mike ta koma kan gado tayi kwanciyarta tare da lumshe ido, har rana basu dawo ba, hkn yasa ta mike ta dauki Hijab dinta tasa snn ta sa takalminta ta fice daga gidan, mai gadi yace "ina xa ki," tace "bae gaya maka inda da exams yau ba," ya bude mata gate din ta fice tayi gidan Aneesah. . Aneesah tayi farin cikin ganinta ssae ta kai ta har bedroom ranar ma , snn ta kawo mata lemo, Aneesah tace "to ni yaushe kike son na shigo gidan ki kawas," Inteesar ta tabe baki tace "ae ni ba ni kadae bace, ni da kishiyata ce," Aneesah ta yo waje da ido tace "da gske, ke ce ta farko ko ta biyu," Inteesar tace "ta farko," Aneesah ta bude baki tace "shekaranku nawa da auren? Ko don baki haihu bne har ynxu," Inteesar tayi murmushi tace "watanmu biyar knn da aure," Aneesah ta dafata da mamaki tace "kai Inteesar, to dama ba auren soyayya kuka yi bne ko kuwa kinsan ba ke kadai bace," Inteesar tace "kusan auren xumunci aka mana, baya sona bana sonsa," Aneesah tayi shiru tana kallonta snn ta sauke ajiyar xuciya tace "ke xaki koya masa sonki Inteesar namiji fa wawa ne cikin lkci kalilan xaki ga kin mallake abunki sae kace ba mace ba Inteesar," Inteesar ta tabe baki tace "tabdi me xanyi da shi, hanyar jirgi daban ta mota daban, baya shiga harkata bana shiga tasa," Aneesah tace "to amma kuna plannin ne ko," Inteesar tace "kinga ni ki rabu dani da hirar nn, ina shakur?" ba don ran Aneesah ya so ba suka bar xancen suka kama wani hirar, ranar ma a gidan ta ci abincin rana, bata bar gidan ba sae kusan karfe shidda ta shiga ta tarar sun dawo, safeena na kitchen da dan littafinta da take boyewa tana hada masu girki shi kuma yana xaune falo yana kallo, ta hade rae xata wuce sama ya daka mata wani mugun tsawa da ya raxanata ta tsaya daga inda take tana masa mugun kallo ya mike ya karasa kusa da ita fuskarsa daure yace "daga gidan ubanwa kike," ta tabe baki tace "aikena kayi to," bata rufe baki ba ya watsa mata mari ta fasa ihu ta durkushe wajen tana kiran Abba, safeena ta leko tace "haba cweety nace ka rabu da ita yarinya ce bata san ciwon kanta ba tukun yarinta na damunta, meye kuma na dukanta, nasiha ya kamata kayi mata dear," Inteesar ta mike tana kuka tace "don uwarki sae ki xo kiyi min nasihar munafuka kawae jaka" yyi kanta ta fasa wani ihun ta saka gudu ta bar wajen ta haura sama tana ci gaba da rusa kuka kmr xata tsaga gidan, ranar hka taci kukanta ta koshi bbu mai lallashi ta gaji ta kwanta tayi bacci ba tare da ta ci abincin dare ba, karfe goma ya shiga dakin nata, ko wanka bata yi ba bare ta canxa kayanta karewarta ma kasa tayi kwanciyarta, ya daga ta ya cire hijabin jikinta snn ya mayar da ita kan gado yana kallon fuskarta, ya lulluba mata bargo ya kashe mata wutan dakin ya fita. Washegari kin fitowa tayi daga dakinta tana ta xaune har axahar bata karya ba, ya shigo dakin ya tarar da ita xaune kan darduma ta idar da sllh, ta mike ta shige bathroom ta bar sa nn tsaye, yyi tsaki ya fice daga dakin, ranar ma hka suka fita suka barta ita kadae a gidan, taci kukanta ta fito ganin yunwa na neman hallakata ta nemi abinda xata ci, har da na dare ta tanada don ba fitowa xata sake yi ba, Ana gobe xata je ta xana jamb dinta tun safe take ta karatu har kusan sha biyu bata karya ba, ta rufe biology text book din dake hannunta ta fito xuwa falo don neman abinda xata ci a xuciyarta tana cewa inda wnn mutumin kirki ne da ba shi xae koya min abubuwan da na manta a chemistry ba, tayi tsaki ta shiga kitchen ta tarar safeena ta daura girki amma bata kitchen din littafin da take amfani da tana koyan girki na kitchen din a ajiye da alamar tuwon shinkafa da miyar egusi xata yi ganin irin kayan miyan da aka jera a kitchen din ko wanne a cikin dan plate, inteesar ta girgixa kai tace "dakikiya kawae ynxu ina dauke littafin nn bbu abinda xata iya yi a nn," xata daura indomie kawae wata xuciyar tace ta dauke littafin kawae ta boye, ba shiri ta dauke littafin ta ma fasa girkin gaba daya ta fice da sauri ta haura sama a stairs suka hadu da safeena, safeena tayi mata wani kallon banxa tana karairaya, inteesar tayi dariya can ciki ciki a xuciyarta tace "i jez dey laf," ta shige dakinta, safeena na shiga kitchen ta nemi littafi ta rasa ta fito da sauri ta koma sama ta buga kofar dakin inteesar, inteesar ta fito tana gyara daurin dankwalinta a walakance tace "lafiya," safeena tayi mata mugun kallo tace "maxa fito min da kayana kar na nakada maki shegen duka a nn," inteesar tayi dariya tace "meye kuma kayanki," safeena na huci ta kasa cewa komai don wnn ae abun kunya ne a gunta anata tunanin, inteesar tayi tsaki tana yatsine fuska xata rufe kofar safeena ta fixgota ta kai mata mari, ta fasa ihu tace "wayyoo Abbana, wlh sae na rama," safeena ta kai mata wani marin, inteesar ta fasa wani kukan tace "don uwarki me nayi maki xaki dokeni, bnxa kawae dakikiya, karuwa da ke," Safeena tayo waje da ido tace "ni kike ce ma karuwa," Inteesar tace "ance maki din karuwa yar iska, uban waye bae san kinyi karuwanci ba," tayi kan Inteesar ta rufeta da duka dai dai nn Aliyu ya shigo gidan, ya haura sama da sauri da mamaki yana kallonsu ya fixge Safeena a fusace yace "ke jakar wace gari ce" tana huci tace "karuwa fa tace min Aliyu," ya watsa mata mari yace "ta ce maki din, sharri tayi maki, ko bakiyi karuwancin bane. Safeena ta bude baki da mamaki tana kallon Aliyu, cikin tsawa yace "get out kar na taka ki a nn, don uwarki idan kika ji mata ciwo kice baki sani ba ko me? Yar ki ce xaki kamata da duka hka ko sharri tayi maki" tsui tsui Inteesar ta bude dakinta a hankali ta shige tasa key, Safeena da hawaye ya gama wanke mata fuska don takaici ta kasa cewa komai ta juya ta bude dakinta ta shige da sauri, yyi tsaki ya bude dakinsa shi ma ya shiga, dariya Inteesar ta dinga yi kmr wata tababbiya a daki, kai Aliyu bae yi ba ko ke wacece ya disga ki gaban kowa ba komai bane a gurinsa, girkin da Inteesar bata yi ba knn ta ci gaba da karatunta da ta tuna abinda ya faru sae ta fashe da dariya, Safeena kam xamanta tayi a daki bayan ta kira uwarta ta gaya mata abunda ya faru girki kam ta fasa shi har taje takashe gas din ta komo sama, tana xaune tana naxarin abinda uwarta ta gama gaya mata tana murmushin mugunta Aliyu ya shigo dakin ta dauke kanta ya karaso kusa da ita ya xauna yana kallonta cikin lallami yace "haba bbyna, meyasa xaki kulata bayan nace ki daina, i've told yhu times wit out nmbr yarinyar nn ba ishasshen hankali gareta ba wllh, ni kaina tsoro take bani" Safeena ta mike a fusace tace "dnt tell me dat Aliyu, ynxu so nake kawae ka tashi ka maidani gidanmu," ya mike ya kamo hannunta yace "haba safeena wllh ina sonki kema kin san da hka, dukan yarinyar nn da kika yi ynxu baki san xae iya xaman min jaraba ba,"xata yi magana ya saka bakinsa cikin nata ya shiga kissin dinta ya dago kanta yana kallonta yace "yhu knw i luv yhu dear, ki bari ynxu xanje in mata magana," ya xaunar da ita ya fice daga dakin ta bi shi da kallo, ita kam Allah ya daura mata son Aliyu, tayi shiru xuciyarta na tafarfasa tanatunanin abinda xata yi masa taji ddi yau, ta sauke ajiyar xuciya tace "xanyi maganinka kuwa yau," shi kam yana fitaya buga kofar dakin Inteesar ta mike da sauri duk da tasan waye tace "waye," yace "ni kike tambayr waye," tayi tsaki ta koma tayi kwanciyarta, yyi shiru yana kallon kofar snn yyi kwafa ya shiga dakinsa. Ganin mugun yunwan da take ji yasa inteesar ta bude kofar a hankali ta fita xuwa falo, kitchen ta tarda shi tsaye shima yana hada tea ta juya da sauri xata koma ya fixgota, tace "wayyoo ni ka kyaleni," ya cakumota yace "ke kince kunnen kashi gare ki ko?" ta bata rae kmr xata yi kuka tace "ni ka kyaleni" yyi kwafa ya saketa yace "ni nasan maganinki," snn ya fice, itama tean ta hada taxo ta wucesa a falo tana takunta mai jan hankali ya bita da kallo, a dae dae stairs ta hadu da safeena, ta wuceta da sauri kmr mara gskya, safeena dae bata ce mata komai ba ta sauko kasa. Ganin ba girki safeena xata yi ba kuma yasan yyi mata laifi yasa Aliyu ya fita ya siyo masu abinci da daddare, bata nuna masa komai ba ta xauna suka ci abincin bayan ya kaima Inteesar nata, karfe tara tace masa xata je tayi wanka ta barsa nn falo ta haura sama sae da ta fara shiga dakinsa ta bude drawer dinsa ta dauki kwalin wani magani ta cire pills har guda hudu tana murmushi sanin ko na menene ta fice daga dakin ta shiga nata, tana jin ya bude dakinsa ta fito daga nata dakin da sauri ta shiga nasa yace "shine kika bar ni ni daya a falo ko bbyna," ta danyi murmushi bata ce komai ba ta xauna gefensa, ta kalli agogo tace "yau baxa ka sha coffee ba bby," ya duba agogo karfe sha daya saura yace "to kawo min dear," ta mike tana rangwada da shegun kayan baccin dake jikinta tace "ok bby," snn ta fita daga dakin, tana gama hada coffee din ta watsa kwayoyin dake hannunta a ciki tana murmushi ta koma sama ta kai masa, ya karba ya ajiye yace "tnks dear bari sae nayi wanka," tayi kwanciyarta kan gado ya mike ya shiga bathroom yin wanka, tana nn kwance ya fito yyi shirin kwanciya snn ya jawo system ya dan yi danne dannensa snn ya dauki coffee din ya fara sha, sae satan kallonsa safeena take ta gefen ido, a hankali ya dinga shan coffeen har ya shanye ya ajiye cup din, snn yyi rub da cik kan gadon ya kwanta tare da lumshe idonsa, tana ta kallonsa har na kusan minti talatin snn taga ya mike da kyar ya dawo gefenta ya kwanta ya jawota jikinsa, bata hanasa ba ya shiga shafata yana kissn wuyarta, ta fara mayar masa da martani itama, sae da ta bari ya gama ficewa hayyacinsa gaba daya ya xama kaman wani mashayi har wani rawa jikinsa yake yana neman fara aiki snn ta turasa da karfi tace "me kuma xaka yi da karuwa banda abinka," ya kankameta kmr wani tababbe yace "no plss kar kiyi min hka safeena, plsss," tayi dariya ta turasa da karfi ta mike ta saka kayanta tace "aa . . Duk yanda Aliyu ya so Safeenah ta basa hadin kai kememe taki yarda da shi sae dariya take ta tana masa kallon rainin wayo tace "kaje gun warce ba karuwa ba, ni kam karuwace," tunda ta shigo gidan dama ta lura da bbu abinda ke shiga tsakaninsa da Inteesar don kullum ita kadae ke kwana dakinsa sae randa baya bukatarta ne xae hade rae yace tana damunsa ta koma nata dakin, kuma shi da bakinsa ya taba gaya mata baya forcin mace ta kwanta da shi, komin nacinsa gwara ya hakura kuma ta lura da gskya yake fada mata ba karya ba, ta mike tsaye tana karairaye tana kallonsa tace "gud nyt dear," snn ta fice xuciyarta fari tas ae sae dae ya mutu yau, binta kawae yake da kallo ya ma rasa abinda xae ce mata ya mike xaune da kyar ya dafe kansa yana kiran Allah a xuciyarsa, shi daya kadae yasan yanda yake ji a jikinsa, ya ma rasa wani tunanin xae yi, inteesar ta fado masa ya girgixa kai sanin halinta ya koma kan gado ya kwanta yana mayar da numfashi, tsam ya mike kmr wanda aka tsikara ya fice daga dakin ganin yana neman hallaka kansa yyi hanyar dakin Inteesar, tana xaune gefen gado ta kunna bedside lamp chemistry textbook a hannunta tana karatu don gobe xata xana jamb, ta mike da sauri jin an bude kofar dakinta, ta koma da sauri ta xauna ganin Aliyu don dan karamin kayan bacci ne jikinta, gani tayi ya xube tsakiyar dakin, ta mike tsaye da sauri ta dauki xaninta ta daura ta karasa gabansa da sauri ta durkusa tana kallonsa da mamaki, a durkushe kansa yake, nn da nn ta rude kmr xata yi kuka tace "me ya faru ya Aliyu," ya dago da kyar ya riketa, idonsa ya kada yyi jajur da kyar yace "fateema don Allah kar kice kina tsorona yau, i beg u plss ki tausaya min," ta yo waje da ido a tsorace ta mike da sauri xata bar wajen yyi hanxarin fixgota ta fado kansa ya rungumeta yana mata wani irin kallo, kuka ta fashe da a rude tace "na shiga uku, don Allah ka sakeni bana so," muryarsa na rawa yace "baki tausayina fateema," cikin kuka tace "wllh wllh tsoro nake ji ya Aliyu kayi hakuri," ya mike da kyar ya fada kan gadonta ta mike tsaye ita ma ta bisa tana kuka xata yi magana ya jawo ta jikinsa yace "kar ki ce min komai fateema, taimakona xaki yi," bae jira tace komai ba ya shiga rabata da kayanta, duk da rawan da jikinta ya fara yi kmr ana kada gangi bata hanasa ba amma kuka ssae take, ganin da gske ashe yake yasa ta fasa ihu ya toshe bakinta da sauri ta shiga turasa a gigice tana cewa "wayyoo wlh bana so ka bari don Allah nake rokanka baxan iya ba," kuka take kmr ranta xae fita, ya saketa yana mayar da numfashi taga ya mike da sauri yyi hanyar bathroom a nn bakin kofa ya xube kasa ya kasa karasawa ciki, ta mike da sauri ta dawo kusa da shi jikinta na rawa tana kuka tace "kayi hakuri ya Aliyu, gani baxan sake maka kukan ba," cikin tashin hankali take maganar, ya rungumota ta runtse idonta da sauri jikinta na ci gaba da rawa, bata sake hanasa yi mata komai ba kuma tayi kkrin hadiye kukan da take sae ajiyar xuciya, ranar ta ci axaba wajen Aliyu, don bata ga bambancinsa da ranar da ya fara saninta ba, tayi kuka tayi rokan amma Aliyu bae sarara mata ba bae ma san tana yi ba, ya wahalar da ita ssae ba kadan ba, bae kyaleta ba sae da yaga numfashinta na neman daukewa, ya kankameta duk ya rikice mata yana kiran sunanta, sun fi minti goma a hka snn yyi namijin kkrin daga ta ya mayar kan gado, kuka take don tsabar axaba muryarta ma bae fitowa, duk ya rasa yanda xae yi da ita, ya rungumeta abun tausayi ya shiga lallashinta yana bata hakuri, ajiyar xuciya kawae take tana kwance kan kirjinsa duk ta wani langwabe don wahala nn da nn jikinta ya dau xafi, wanka ya fara yi mata snn ya bata magani ta sha, ya kwantar da ita kan gado daga nn bacci ya dauketa wajajen karfe hudu na Asuba. . Da kyar Aliyu ya iya tashi yyi sllhn Asuba, shima duk baya jin ddin jikinsa, har lkcn bacci Inteesar take ya dawo gefenta ya xauna yana kallonta cike da tausayinta, a hankali ya shiga tada ta, ta bude idonta da ya kumbura don kuka a hankali tana kallonsa yace "tashi kiyi sllh, xa ki iya?" ta kauda kanta da sauri bata ce komai ba snn ta mike xaune, ya daura hannunsa a goshinta yaji da xafi, yace "xa ki iya kuwa," bata ce masa komai ba ta mike da kyar gabanta na faduwa ko xata ji irin abinda taji wancan ranar amma bata ji ba sae jiri kawae da take gani ta shiga bayin ya bita da kallo, yana nn xaune ta fito ta fara sllh, tana idarwa, ya dawo kasa kusa da ita ya xauna yana kallonta ta sunkuyar da kanta, yyi murmushi yace "mrning," ta hade rae ta mike xata bar wajen tayi baya xata fadi yyi saurin rikota ya karasa da ita kan gadon ya kwantar da ita, kuka ta shiga yi a hankali ya kwanta gefenta yana kallonta yace "ki fada min gskya fateema, jiya kin ji xafi ne," ta dago kai tana kallonsa don takaici ma kawae sae ta fashe masa da kuka ya dagata suka mike xaune yace "ni bance kiyi min kuka ba," ta turasa cikin kuka ssae tace "tambayata ma kke ko, to wlh daga yau ka sake min irin hka sae na gaya ka da inna" ya rungumeta yana murmushi, ta dinga kuka har da shessheka, a hankali yace "sae kice ma inna nayi maki me," taki cewa komai sae dae har lkcn kuka take, ya kwantar da ita ya rufa mata bargo yace kiyi baccinki, ya koma daya side din ya xauna, nn da nn bacci ya dauketa, yana nn xaune har kusan karfe takwas, yaga ta xabura ta mike xaune ya juya da sauri yana kallonta, ta kalli agogo ta mike tsaye da sauri tayi baya xata fadi ya mike da sauri kan ya karasa kusa da ita har ta buge da bango ta fadi kasa, ta fashe da kuka ya durkushe gabanta da sauri ya dagota, jikinta yyi xafi ssae, ya xaunar da ita kan gado yace "to da ina xaki," tana kallon agogo tace "yau ne exams dina," yyi shiru yana kallonta yace "xaki iya," ta tsaya kallonsa snn tace "kmr ya," yace "naga baki jin ddi ki bari nxt yr kawae, kmr gobe..." bata gama sauraran abinda xae ce ba ta mike ta shige bathroom abinta tana daddafa bango, yana nn xaune ta fito ta shirya, yace "break fst fa," tana rike da chemistry dinta da kyar tace "tea xan sha kawae," ta gane xaxxabi ne ke neman rufeta, da kansa ya hada mata tean ya bata, ta shiga sha, har ta sha rabi ta ajiye sauran snn a hankali tana nuna masa wani calculatn a chemistry textbuk dinta tace "ni na manta wnn formula din," ya karba yana kallo abinda take nuna masa, ya dauki takardar da take calculatns jiya ya shiga solve din mata questn din yana mata explanatn, wai daga kan da xae yi sae ganin ta yyi ta jingina jikin gado tana bacci, yyi shiru yana kallonta, yasan jiya kam bata samu baccin kirki ba, a hankali yace "fateema," ta bude ido da sauri tana kallonsa tace "kace me," yace "ki bari nxt tym kiyi jamb," kmr xata yi kuka tace "ni ka kyaleni, idan baxa ka koya min ba in tashi in tafi," ya daga kafada ya shiga koya mata har ya gama yace kin gane tace eh, ta mike ta sa Hijab dinta ya bi bayanta, sae da ya fara shiga daki ya dauki makullin motarsa snn ya fito ya bude mata motar ta shiga shima ya xaga ya shiga suka bar gidan, hka ta dinga bacci a motar har suka isa, yace "ke baki jin magana nace ki bari wani yr din, ki ci gaba da islamiyya kin ki ko," ko kallonsa bata yi ba ta bude motar xata fita ya mika mata dubu biyu yace xan xo daukarki anjima, snn ya ja motarsa ya wuce, ita kuma ta shiga ciki. A daddafe ta gama exams din don xaxxabi ne ssae ya rufeta, ta fito ta nemi guri ta xauna tana jiransa, jiran minti talatin tayi masa taga bae xo ba ta tsayar da tricycle ta hau abinta ta wuce gida, ko da ta isa gidan bata tarda kowa ba mai gadi yace mata sun fita shi da Safeena, ta tabe baki ta koma ciki tayi kwanciyarta, sae kusan yamma xaxxabin ya sake ta ta sauko kitchen ta dafa indomie ta koma sama abunta ta ci, ba su suka shigo gidan ba sae kusan karfe goma na dare, ya shigo dakin yana kallonta yace "srry fa, mamar Safeena ce bata da lfya shine muka je gidan," ta ja dogon tsaki ko kallonsa bata yi ba ta mike ta bude bathroom ta shige ta barsa nn tsaye, yyi kwafa ya fice kawae. Bayan kwana biyu aka turo mata da scores dinta na Jamb, ya isa har yyi yawa ta karanta Medicine abunta, a falo take gaya masa ranar yyi mata mugun kallo yace "ke ce xaki iya wani karanta Medicine salon na bata kudi na kawae, wae an gaya maki cin tuwo ne," ta galla masa harara tace "to ina ruwanka ka shiga kwakwalwata ne?," ya mike tsaye yana kallonta yace "xan fa babbalaki wataran a gidan nn yarinyar nn," tayi tsaki ta juya ta koma sama tana cewa "ni wllh abba xanje na gaya ka da abba, ina ruwanka da abinda xan karanta, kai wa ya hanaka karanta medicine" Safeena da aka siyo sabon takardar koyon girki ana kitchen ana girki tace "sae hakuri dear, ta xata wasan yara ne medicine din Honey," yana hararanta yace "ke kuma wa yasa bakinki a nan, Bayan sati daya inteesar na kwance ita kadae a daki wajen karfe sha biyu na rana, safeena ma na dakinta waka sae tashi yake kmr xae tsaga gidan, Aliyu ya fita aiki, inteesar ta gaji da kide kiden da safeena ke sa wa gashi ba daman tayi mata magana ta ci ubanta Aliyu baya nn, ta mike ta dauki Hijab dinta ta fita daga gidan, mai gadi yace "oga yace kar na bari kowa ya fita," ta yi shiru tana kallonsa kmr ta shakesa, can dae tace "bae ce maka xan je duba jarabawa bne," mai gadi yace "aa ni bae ce min hka ba," ta galla masa harara ta isa kusa da gate din tace "to sae ka kirasa kaji," ta bude gate din ta fice daga gidan, gidan Aneesah ta shiga, ta tarar tana ta karatun littafin hausa, taji ddin ganin Inteesar ssae tace "kwana da yawa 'yar uwa ina kikaboye gashi ba daman na shiga gidanku,"inteesar tayi dariya tace "ina nn ke dae, ba nace maki xan xana jamb ba," Aneesah tace "ohh hka fa ya scores yyi kyau?" inteesar tace "ehh wllh, shakur fa," Aneesah tace "yana bacci wllh, wae meye sirrin yan mata naga kin kara kyau kinyi haske" Inteesar ta harareta tace "ban fa son cin fuska," Aneesah tayi dariya ssae tace "wllh kuwa da gske, baki duba kanki a madubi ne? ko dae...." inteesarta tabe baki tace "ko dae me," Aneesah tayi dariya tace "oho," ta mike ta kawo mata ruwa da lemo, nn suka dinga hirar rayuwa, ganin Aneesah bata boye mata komai game da rayuwarta yasa inteesar ta bata lbrin nata rayuwan tun bata yi aure ba har ixuwa aurenta da Aliyu, da irin xaman da suke da shi har ya auro safeena, Aneesah tace "tab lallai ba shi da mutunci, kuma Abba bae kyauta maki ba da yyi maki hka da ma Haisam din ne, ke ma da naki ae, taya xaki dinga shiru kina cutar kanki inteesar, na tabbatar da tuni kin gaya Abba irin xaman da kuke da ya raba ku ynxu wllh, to wae ma don me baki son na shiga gidan naku sbda wata safeena, tsoranta kike ko me, shi kuma Aliyun ba kiyi niyar gyara masa xama bne wllh, tab," Aneesah tayi kwafa taji kmr ita ce Inteesar, inteesar tayi murmushi tace "to mu je gidan namu ynxu, ae ya fita office," Aneesah ta mike kmr jira take tace "bari na dauko Hijab," ta wuce sama Inteesar ta bi ta da kallo tana murmushi, ba ajima ba ta sauko sanye da Hijab tana rike da Shakur da kwalban turare a hannunta, ta mika ma Inteesar tace "mum dita ce ta aiko min da turaren nn na dibar maki yana da kyau ssae wlh," Inteesar ta karba tayi mata gdya suka fita daga gidan, inteesar ta danna bell mai gadi ya bude masu gate suka shiga, xaune suka tarar da Safeena da uwarta a falo ta cika ta da kayan drinks da nama sae hira suke suna shewa kmr kawaye, safeena ta bi Aneesah da kallo hka ma uwarta dake kallon inteesar cike da tsana, Aneesah tace "kai amma falonki babba ne Inteesar, nake ga kmr ma yafi nawa," inteesar tayi dariya tace "kai Aneesah kallon tsoro dae kika ma falon nawa," safeena ta mike tana hararan Inteesar tace "falonki? Amma ke jaka ce da kika yi wnn tunanin uban wa ya baki falo," Hajiyarta ta mike tace "wllh kin ban mamaki safeena da har xaki iya xama yarinya karama ta raina ki hka, yaushe kika yi laushi hka safeena, dubi fa kallon da take maki," inteesar tace "to falonki kike son nace da, ni dae naga ko gaban mai gidan kika kira nn da falonki wllh gwale ki xae yi, dama kun saba, ni ko sae na fadi hkn ya xauna" Aneesah ta fashe da dariya, inteesar tace "Atoh ae gskya ne Aneesah, jiya fa daga tace kofarta ya fara samun matsala ya hauta da masifa kmr xae maketa wae ta shigo masa da kofa gidansa ne da xata ce kofarta, bare wnn mae gaba daya wae falonta" dariya Aneesah ta dinga yi ssae, safeena tayi kan Inteesar ta haura sama da sauri ta bar Aneesah nn tsaye, safeena ta cakumi Aneesah tana huci tace "don ubanki me ya shigo dake gidan nn," Aneesah ta ajiye shakur ta watsa mata mari tace "meye hadina dake don uwarki da xaki rikeni hka," haba kan kace komai fada ya kaure tsakaninsu, inteesar ta kasa saukowa don shegen tsoro, da kyar tayi shahada ta sauko ganin dambe suke ssae, safeena dake cin uwarta hannun Aneesah ta fixgo inteesar, uwarta ma ta taho da gudu xata sa hannu Aneesah ta jefar da ita gefe daya ji kke rigijib a kasa, nn inteesar da Aneesah suka hadu suka nakada ma Safeena shegen duka sae ihu take shakur ma na ihu, sae da suka mata laga laga snn inteesar ta ja Aneesah suka haura sama rike da shakur ganin uwar safeena tayi kitchen da gudu, inteesar ta saka key a kofar bayan sun shiga. Ihu safeena ta dinga rusawa a gidan ta dauki wayarta ta kira kawayenta gaba daya su xo wae sae sun kashe Aneesah yau, ita kuma inteesar mijinta baxae ganeta ba, inteesar duk ta tsorata ganin kawayen safeena na ta shigowa gidan, Aneesah kam ko a jikinta, suka dinga bubbuga kofar kmr xasu cireta, inteesar kuka shakur kuka, Aneesah tace "kin ban mamaki wllh inteesar meye abun tsoro a kishiya, ba dole ta maida ki yar ta ba tayi ta duka taga kina tsoranta," inteesar tana goge hawayenta tace "to ko na kira ya Aliyu ne wllh cire kofar xa suyi," ta fashe da kuka tana neman wayar Aliyu dake wajenta. . Inteesar tadauki wayar jikinta na rawa ta shiga kiran Aliyu, dontsabar takaici Aneesah kasa daukar Shakur dake ta tsala ihu tayi, sae kallon Inteesar take kmr ta maketa, Aliyu na daga wayar ta fashe masa da kuka, ya mike tsaye da sauri yace "me ya faru," cikinkuka tace "ko ba Safeena bace wae xata kasheni ta kira kawayenta da yawa a gidan har da mamarta gasu nn xasu cire kofar wae su kasheni," Aneesah ta girgixa kai cike da takaici ta kinkimi danta tayi hanyar kofa xata fita da gudu inteesar ta karasa kusa da kofar ta rikota tace "wayyo so kike su kashemu, don Allah ki bari ya dawo," da sauri inteesar ta cire makullin, Aneesah ta ma rasa me xata ce mata, su safeena har lkcn basu fasa buga kofar da suke suna xage xage ba, Aneesah ta shiga mayar masu ita ma, hka suka dinga xage xage ta uwa ta uba, sum sum inteesar tayi jikin window har lkcn a tsorace take ta tsaya tana jiran shigowar Aliyu, ko minti sha biyar ba ayi ba ya shigo gidan da motarsa, tayi gun Aneesah da ke ji kmr ta cire kofar ta fita suyi ta takare tace "Aneesah ya dawo," Aneesah ta galla mata harara tace "da'allah ja can kin ban waje, kin ban mamaki inteesar," Aliyu ya hauro sama yana kallon safeena da kawayenta kusan su biyar uwarta ma na tsaye cikinsu, wani mugun tsawa ya daka ma kawayen nata yace "b4 d count of 3 duk ku fice min a gida kar na sa a kulle min ku karuwan bnxa kawae yan iska nn din gidan ubanku ne ko na uwarku, kaji min bitches " tuni jikin safeena ya dau rawa, kawayen nata kuwa sum sum suka shiga sauka kasa yana binsu da kallo yana huci, ko kallon uwar safeenar bae yi ba yyi kan safeena ya fixgota ya kai mata mari yace "gidan nawa xaki mayar joint din yan iska? To maxa ke ma dauko gyalenki ki bi su bana son na bude ido na ganki cikin gidan nn, get out" cikin tsawa ya karasa maganar, Hajiya na kallonsa da mamaki tace "Aliyu a kan idona kke walakanta min 'ya ta," ya juya yana mata mugun kallo yace "an walakantata din, ae dama a walakance kika bani ita, kuma a walakance na sameta ko kun manta ne," yyi tsaki ya shiga buga kofar Inteesar, inteesar na hararan kofar tace"waye?" yace "uwarki ce, kin xo kin bude min kofa ko sae na taka ki," inteesar tayi tsaki tace "to baxan bude ba," Aneesah ta bude baki da mamaki tana kallon kofar, a lallai wnn gantalallene shi kuma ba shi da gwani, a fusace ya juya ya shige dakinsa, safeena ta fito sabe da gyale tana matsar kwalla tana kallon uwarta, uwar tace "ke ina xaki maxa koma ita kanta naga ba kyaleta yyi ba, hka yake dama," safeena tace "hka yake wllh...." fitowar Aliyu yasa safeena tayi tsit, ko kallonsu bae yi ba ya isa jikin kofar inteesar da spare key a hannunsa, inteesar na jin ya saka key cikin kofar ta mike tsaye da sauri tana kallon Aneesah ta nuna mata bathroom murya kasa kasa tace "ki shiga bayi kafinya shigo," ko kallonta Aneesah bata yi ba, har ya bude kofar ya shiga dakin, da sauri inteesar ta juya xata bar wajen ya fixgota a fusace ta fada kansa ta fasa masa ihu a tsorace tace "wllh xan gaya ka da Abba," idonta ya tsaya kallo da alamar mamaki, ya sa hannu ya dago kanta yana kallonta da kyau, a hankali ya shiga kare mata kallo snn taga ya sake ta, Safeena da uwarta na bakin kofa suna kallon dukabinda ke faruwa, har ya juya xae fita ya juya yana mata mugun kallo yace "wnn wacece," ta hararesa tace "kawata ce," yyi shiru yana kallonta, shakur ya karaso kusa da shi yana cewa "daddy," da maganarsa da bae gama fitowa ba, ya sunkuya yana kallonsa snn ya shafa kanshi yace "hw re yhu dan daddy," snn ya juya ya fita shakur na biye da shia baya, sum sum safeena da uwarta suka bar wajen, bbu yabo bbu fallasa Aneesah tace "dauko min yarona na tafi gida" Inteesar tace "lah har xaki tafi ki bar anjima mana ko ruwa fa baki sha ba," Aneesah ta harareta tace "ae wllh kin bada mata Inteesar, ni dauko min yaro na na bar gidan nn," safeena da uwarta na shiga daki uwartata ta kira Hajiyar Aliyu, tace "maxa maxa ki taho ki ga irin rikon da danki ke ma 'ya ta Hajiya, hka muka yi dakudama ya dinga dukan safeena," Hajiya ta bude baki tana salati tace "wllh Alhaji ya hanani xuwa gida Aliyu ban san dalili ba, amma kar ki damu xan kirasa ynxun nn Hajiya" inteesar na shirin kwanciyawajen karfe goma Aliyu ya shigo dakin, bata ko kallesa ba ta gama abinda xata yi ta shige cikin bargo, ya dawo gefenta ya yaye bargon yana kallonta, ta hararesa tace "meye hka," ya dan marairaice mata yace "yau ma tausaya min xaki yi kanwata," nn da nn ta fara kuka kmr jira take tace"ni wlh wllh ka fitar min a daki ina gaya maka," yyi dariya ya dawo gefenta ya kwanta yana shafa cikinta yana murmushi xae yi magana sae kuma ya fasa, ta turasa tace "ni fa bana son iskancin nn ka fitar min a daki," yana ci gaba da shafa cikinta yace to wacece wnn yarinyar da na gani daxu a gidan nn,inteesar ta buge masa hannu tace "kawata ce," yace "a ina kika samo ta," tayi masa bnxa, ya rungumota ssae, sae da ya jagwagwalata snn ya fita daga dakin ganin irin kukan da take a tsorace . Inteesar na kwance a daki tun safe take ta bacci ta kasa tashi, da ta farka xata koma taji dae yunwa ya isheta ta mike xaune ba shiri tana kallon agogo, taga karfe daya, ta tabe baki ta jingina jikin gadonta bbu wanda ya damu da ko ta karya ko bata karya ba a gidan, kuma ranar lahadi ne Aliyu na gida, ta sauko daga kan gadon da kyar idonta na juya mata ta dauki xani ta daura kan rigar baccinta ta bude kofa ta fita tana jan kafa, xaune ta tarda shi da safeena kan dinnin suna lunch sae hira take masa tana dariya, shi kam sae dae yyi murmushi yana cin abincinsa, da wuya kaga dariyan Aliyu, inteesar ta tabe baki ta shige kitchen suka bi ta da kallo, Aliyu ya girgixa kai yace "yarinyar nn dae bata da amfani a gidan nn," safeena ta dauke kanta ta ja bakinta tayi shiru don ta san tana iya magana ya gwaleta ynxu ba karamin aikinsa bne, inteesar taji bata jin cin indomie, ta dan bude tukunyar safeena tana lekar abinda ke ciki, cous cous ne da miyar hanta, ta dan yatsina fuska duk da hka kawae taji abincin ya shiga ranta, ta rufe tukunyar a hankali tayi xamanta a kitchen din tana tunanin me xata dafa, indomien dae at lng lst tayi decide ta dafa ta mike tsaye ta daura ruwan, ta bar shi ya fara tafasa snn ta shiga xuba abubuwan da xata xuba, hka kawae taji bata jin cin kwae, indomien na fara dafuwa taji xuciyarta na mugun tashi, ta koma baya da sauri tana rike da cikinta da ya hautsine nn da nn, ji tayi amai na neman xubo mata ta toshe bakinta da hannunta da sauri ta fice daga kitchen din da gudunta tayi hanyar stairs har tana tuntube, duk suka bita da kallo Aliyu ya mike ya bi bayanta da sauri yana tambayarta me ya faru ya ma yi xaton yankewa tayi, safeena bata yi gigin binsa ba don tasan halinsa, da kyar Inteesar ta iya karasawa dakinta ta bude kofar bayi da sauri ta durkushe nn bakin kofar ta shiga kwarara amai kmr xata amaye hanjin cikinta. Aliyu ya shigo dakin da sauri ya karaso bakin kofar bayin yana kallonta, har lkcn amai take ssae gashi bbu komai cikinta, ya durkusa gabanta a hankali ya dafa ta yana mata sannu, buge masa hannunsa tayi, tayi xaman dirshan a bakin kofar tana mayar da numfashi ta fashe da kuka ta jingina jikin bango duk ta rasa inda xata sa kanta, juye juyeta shiga yi a bakin kofar tana kuka tana kiran Abbanta, ya fixgota ya daka mata tsawa "kina hauka ne," ko kallonsa bata yi ba ta rarrafa jikin gado ta xauna ta jinginar da kanta tana ci gaba da kuka tana mayar da numfashi, ya mike ya dawo kusa da ita yana kallonta ya dafa ta xae yi magana ta mike da sauri ta koma bayin ta durkushe ta shiga kwararo wani aman kmr xata shide har wani rawa jikinta yake, lkci daya jikinta ya dau xafi, ya riketa yana mata sannu, ta langwabe masa ta fada kansa sae kiran Abba take tana mayar da numfashi, ta fara kkrin mikewa ya rikota yace "ina xa ki," tana girgixa masa kai ta kuma fadawa kansa tace "wayyo kwanciya xanyi na gaji," ya dago ta ya shiga da ita bayin ya wanke mata baki ya dauketa ya maidota cikin dakin ya kwantar kan gado ya rufa mata bargo yana kallonta sae rawan sanyi take, ya koma ya gyara bathroom din, snn ya dawo gefenta ya xauna yana kallonta duk ya ma rasa wani tunani xae yi, ya jinginar da kansa jikin bango a hankali ya lumshe idonsa "no! Wnn me shegen rakin baxata iya rainon ciki ba ynxu, nd bae tashi haihuwa da ita ba tukun, da ma safeena ce wnn kam takuran da yake samu a gida a kanta xae kara yawa ne ma, to ma wani moranta yyi har xata dauki ciki ynxu" yyi tsaki ya bude ido yana kallonta bacci take amma da gani ba me ddi ba sae juye juye take, ya girgixa kai ya mike ya fice daga dakin, makullin motarsa ya dauka ya sauko falo, safeena da ta fito daga kitchen knn bayan ta kashe gas din da Inteesar ta kunna tace "me ya sameta Dear," ya galla mata harara yace "ban sani ba," ya fice, ta bi sa da kallo, ita kam halin Aliyu ya isheta a gidan nn, gashi sae bata kudinsu suke a banxa a kansa, amma abu sae kara gaba yake, tayi kwafa ta haura sama, yana shiga motarsa ya kama hanyar asibiti, bae damu da gaisuwan da nurses ke masa ba har ma da patients ya haura sama kawae ya wuce office dinsa, ya bude glass din da magunguna suke ya shiga xaban wanda ya kawosa, tabs kala biyu ya dauka da ruwan allura daya ya rufe glass din ya fito ya rufe office din, ya sauko kasa xuwa reception, sae a snn ya shiga amsa gaisuwan patients din da ke gaishesa, yyi murmushi ganin matar da yyi ma theatre kwanakin baya da yaranta da babansu, ya karasa kusa dasu yana kallonsu yace "madam me ya sami twins" matartace "wllh tari suke doctor, ya aiki?," ya karbi dayan yana masa wasa yace "aiki Alhmdllh anyi attend din maku ne," tace "A'a ynxu dae xa a duba mu, madam fa," yyi murmushi yace "tana lfya," tace "to a gaida min ita, yau kana wkend ko," yace "wllh kuwa, Allah ya sauwake, i wil b on my way," ya ba mijinta hannu suka yi sllma snn ya juya, yana isa kofar fita sai da ya juya ya sake kallon kyawawan yan biyun da suka girma ssae, ya dauke kansa da sauri ya fice ya shiga motarsa ya bar asibitin. . Aliyu na shiga gida ya tarda Safeena kwance a falo tana kallo, ta bisa da kallo har ya haura sama snn ta mike xaune tana bubbuga kafa a hankali ta shiga maganar xuci "lallai its high tym she wake up frm her slumber, ya kamata ta tashi tsaye daga xaunen da take ynxu, Aliyu ya gama kawota bango, xata cire sonsa ta ajiye gefe guda tayi abinda uwarta ta dde tana son tayi taki yi sbda so ya rufe mata ido, ita kuma inteesar ynxu suka sa kafar wando da ya da ita" tayi murmushin mugunta ta mike ta haura sama xuciyarta na tafarfasa. Aliyu na shiga dakin ya tarda ta tana bacci ya xauna gefenta yana kallonta ya ciro magunguna da alluran da ya dauko a asibiti yana kallonsu, snn ya juya yana kallonta tayi wani irin haske ta kuma kara kyau, yyi murmushi ya shafi gefen fuskarta ya mike ya dauko syringe a dakinsa ya dawo ya shiga hada alluran, sunansa yaji ta kira, ya juya da sauri yana kallonta ta sake maimaitawa "ya Aliyu," sae kuma yaga tayi murmushi ta juya, ya ajiye alluran hannunsa ya dawo dab da ita ya xauna yana shafa labbanta da yatsa yace "fateema," cikin baccin ta amsa "na'am," yyi murmushi ya daura mata kiss a bakinta, murmushin yaga ita ma tayi, yyi still yana kallonta, to wae meyasa yake son xubar da cikin nn, shi dae yana son yara kuma xae so yaga kyakkyawan bbyn da xata haifa masa mai kama da ita, ya dauke kansa ya daura hannu a goshinsa kan na juya masa, y? Meyasa yake son xubar da bbynsa gudan jininsa, ya girgixa kai yace "No," da sauri yaga ta mike xaune ya kamo ta ta fara turasa xata sauka yaki sakinta yana tambayarta mene, amai ta shiga kwarara masa a jiki yana rike da ita har lkcn, sae da ta gama snn ya dauketa ya shiga da ita bayi, sae kuka take tana cewa ita ya kaita gida, wanka yyi mata ya nannadeta cikin towel ya fito da ita ya cire xanin gadon snn ya kwantar da ita, shima wankan yyi don duk ta bata masa jiki ya saka xanin gadon cikin washn machine da shirt din jikinsa snn ya fito daure da towel, ranar ce rana ta farko da ta taba ganinsa daure da towel don ko singlet Aliyu bae yrda ta gansa da shi bare short nicker, ta rufe idonta da sauri, shima bae ce mata komai ba ya kwashi magunguna da alluran da ya hada ya fita da su, dai dai lkcn da Safeena ta fito daga dakinta, ta bi sa da kallon mmki shi kam ko kallonta bae yi ba shiga dakinsa. Alluran da yyi mata bayan ya tilasta ta sha tea ne ya tsayar mata da aman, amma duk da hka sae da ta gwammace dama aman ta dinga yi taji ddi, don rasa inda xata sa ranta tayi sae kuka take tana juye juye, ya rungumota cike da tausayinta yana lallabata tayi bacci, da kyar ta samu baccin ya dauketa, yyi shiru yana kallonta duk ta rame lkci daya, da yamma wajajen karfe biyar ya fita pharmacy siyo mata magunguna da drips din da xae sa mata.Yana fita ko minti goma ba ayi ba Zainab ta shigo gidan ko kallon safeena dake ta busar da gashinta da hand dryer bata yi ba ta wuce sama, safeena ta bi ta da kallo snn ta ja dogon tsaki, bacci ta tarar Inteesar ke yi ta shiga tashinta da xolaya tana cewa "ke kasa kinyi bakuwa maxa tashi" inteesar ta shiga juye juye ta mike xaune da kyar tana kallon Zainab, Zainab tace "hmm lbri na xo maki da mai ban kunya," inteesar xata yi magana taji yawu cike bakinta, ta mike tsaye da kyar ta shiga bayi ta xubar da yawun ta dauraye bakinta da freshner ta dawo, Zainab tace "meye hka," Inteesar ta langwabe da kyar tace "bana jin ddi ne," Zainab ta bude baki "iyye kar dae bby xa a samo mana," inteesar tayi shiru da mamaki tana kallonta snn tace "bby kuma, wani bby," Zainab tayi dariya tace "lalala kinga yanda kka yi wani irin haske da kyau kuwa, shknn xa a sama ma yayana bby," inteesar ta hade rae xata yi magana taji yawu kuma a bakinta ta mike da sauri taje ta tofar wnn wani irin jaraba ce, ta tambayi kanta, kuka ta fashe ma Zainab ganin Zainab ta kuke sae murna take xa su samu bby, tace "ni fa bana son hka Zainab wllh bani da komai," Zainab tace "ki daina wllh, ga signs a jikinki," kuka ssae take tana cewa na shiga uku ni Zainab ki bari bani da komai yarinya da ni xaki ce ina da ciki, Zainab tayi dariya ssae tace "tunda ko kina kwana daki daya da yayana ai ke ba yarinya bace," dai dai nn Aliyu ya shigo yana ma Zainab mugun kallo yace "ke wae wace irin mutum ce, ban hanaki shigowa gidana ba, xo ki fita," cikin daga murya ya karasa maganar ta mike da sauri tana xumburo baki ta dauki mayafinta ta bi ta gefensa ta fice ya kai mata rankwashi, inteesar ta hade kanta da gwiwa tana kuka, ynxu ciki ne da ita yar yarinya da ita, to da wani ido ma xata kalli su inna, ae Allah ma ya kyauta kuma ya rabata da haihuwa ynxu kuma ma wae dan Aliyu. Ta mike da sauri tun kan ya shigo dakin xata yi hanyar bathroom jiri ya debeta ya shigo dakin da sauri ya kamota ta fada kansa suka xube kan gado, ya fada gefenta da sauri ganin ynda take mayar da numfashi ya dagota ya rungumeta yana mata sannu, cikin kuka tace "wllh ka cire min cikin nn bana so," ya toshe bakinta da sauri yana kallon cikin idonta yace "ni ina son abu na . Kuka ssae Inteesar ta shiga rera masa, shi kam saekallonta yake yana murmushi, ta fara kkrin mikewa xata sauka daga kan gadon ya riketa da sauri yace "ina xaki," cikin kuka tace "wllh sae ka cire min cikin nn bana so," ya rufe bakinta ya hade rae yace "kar ki sake cewa na cire maki bbyna, sae kace wani kaya," ta buge masa hannu, ya harde kafarsa cikin nata tayi yar kara, ya rungumota yana kallonta ya shiga shafa mata cikinta yace "me xaki ci, dubi fa yanda kika rame tun kan ba mu je ko ina ba, a hka xa muyi rainon cikin kika san ma ko yan biyu ne kanwata," ta fashe masa da kuka tana kiran Abbanta, ya rankwashi kanta yace "ki daina min kmr ihsaan a nn, ke baki san kin girma ba tunda ga bby nn cikin cikin ki" bata san lkcn da ita ma ta rama rankwashin ba tana kukan da xa a iya kiransa da na shagwaba duk da har ga Allah ba shagwaba take ba, ya wara ido yana kallonta, ta koma baya da sauri nn da nn ta tsorata ya lakaci hancinta ya ja kunnenta yace "kin ci sa a bbyna na jikinki da yau na maki shegen bugu, ya Aliyu kike rankwashi " bae jira me xata ce ba ya kwantar da itaya mike ya fita, ta mike xaune da sauri ta hade kanta da gwiwa ta fashe da wani sabon kukan ynxu wae ciki ne da ita da gske yar yarinya da ita, ba a dau lkci ba ya dawo dakin rike da kofin tea yace "maxa tashi ki sha na saka maki ruwa aman ya tsaya," kallon tean kawae tayi taji xuciyarta na tashi ya kai mata baki ta mike da sauri sae cikin bayi ta shiga kwarara amae, ya isa kusa da ita ya durkusa ya dafata yana kallonta yana mata sannu, sae da ta gama snn ya gyara mata jiki ya maidota cikin dakin, a hankali ta kamo hannunsa tana hawaye tace "don Allah ya Aliyu ka tausayamin ka cire min cikin nn bana so," ya galla mata harara yace "wllh idan kika sake gaya min wnn maganar sae na bata maki rae, ki cire ynxu na gani mana," tayi shiru tana kallonsa xuciyarta na tafarfasa, ita ko ta fi sa iskanci xae gani kuwa, ta juya tayi kwanciyarta tana mayar da numfashi, tean da bata sha ba knn har bacci ya dauke, sae kusan sha daya na dare ta farka yana gefenta a kwance, shima amai ne ya farkar da ita, ya cire mata ruwan dake hannunta ganin a gigice ta farka tana neman sauka ya raka har bayin ta shiga kwarara amae, gashi dae ba komai cikinta, ya xuba mata ruwa a kai ya fito da ita, daga ita har shi ranan basu yi baccin kirki ba, jikinta yyi xafi ssae ta rasa inda xata sa ranta sae kuka take masa yana rungume da ita, da kyar bacci mai nauyi ya dauketa kusan asuba. Washegari monday bae je aiki ba sbda ita, tana kwance jikinsa bayan ya lallabata ta sha tea kadan yyi mata allurorinta wajen karfe goma safeena ta kwankwasa kofar tare da sallama, yace ta shigo, ta bude kofar ta shigo sae da xuciyarta ya kusan harbawa yanayin da ta gansu, shi singlet da 3qtre ne jikinsa, ita kuma rigan bacci iya cinya, ta kirkiro murmushi ganin allurori a bedside drawer tace "Ayya bata jin ddi ne dear," ba tare da ya kalleta ba yace "eh, ya akayi?" tace "Allah sarki, Allah ya sauwake fateema sannu," inteesar ta dago kai da kyar ta watsa mata harara, ta mayar da kanta, safeena ta dauke kanta da saurixuciyarta na tafarfasa tace "yauwa dear Momy ce ciwonta ya tashi shine xanje ynxu, amma ba ddewa xanyi ba dan da sauki," yace "ita kuma kullum ciwon nata ke tashi, baku da abinci ne a gida, ae yunwa ce ke kawo ulcer " tayi shiru tana kallonsa ya tabe baki yace "Allah ya sauwake, ki duba side drawer can bedroom dina ki dauki dubu goma," tana murmushi tace "to ngd dear," snn ta juya ta fice tana murmushin mugunta. Da yamma safeena ta shigo gidan, har lkcn Aliyu na dakin Inteesar, lkci lkci yakan yi tunanin ko dae kawae ya rabata da cikin nn ne ta huta shima ya huta, don ba karamin wahala yaga take sha ba tun kan cikin ya kai ko ina, ynxu ma da kyar ta samu bacci ya dauke, irin masu shegen laulayin nn ne me wahala, ya dan yi tsaki, ita ma ragwancinta ne kawae yyi yawa, duk ta fige lkci daya sai kace wacce tayi wata tana ciwo, safeena ce ta bude dakin ta shigo ya daga kai yana kallonta, tayi murmushi tare da lumshe ido tace "Aliyu so nake kaje duba mum dita ynxu, kuma ka tafi mata da wnn maganin nn da ka bata ranan nn wae taji ddinsa," yyi shiru yana kallonta,snn taga ya sauke ajiyar xuciya yace "wae ynxu?" ta dan yi fari da ido murna fal cikinta, amma ta hade rae tace "to da yaushe kke tunani," yace "ok," snn ya kwantar da Inteesar dake jikinsa ya mike tsaye ya juya yana kallonta bacci take, kan yace komai safeena tayi saurin cewa "to kaxo ka wuce," ya juya ya fice daga dakin, ta bisa da kallo tana murmushi, dakinsa ya shiga ya shirya snn ya fito da makullin mota, tana hararansa tace "to haka xaka je mata hannu rabbana," ya koma ciki sae gashi ya fito da kudade, ta rakasa har jikin mota snn ta manna masa kiss a baki, yyi murmushi ya lumshe idonsa yace "sae na dawo bbyna," snn ya ja motar ya fice daga gidan, ta doka uban tsalle tashiga kiran layin uwarta cikin murna tace "wayyoo mum, saura naki gashi nn xuwa. Aliyu na fita gidan ya wuce wani babban super market ya yayiwa mum din safeena siyayya bata wasa ba akalla ya kashe kusan 50k. Ya fito ya shiga motarsa ya dau hanyar gidan mum xuciarsa duk a cushe ya rasa dalili,gashi yana son kiran inteesar a waya ta wayar sa dake hannunsa amma ya kasa a haka dai ya cigaba da driving har Allah ya kai shi lpy. Yana isa gidan su safeenar maigadi ya bude masa get yana washe baki kasancewar aliyu na hannun damansa ne yana da yawan kyau,ko kula da gaisuwar da me gadi yake yi masa bai yi ba ya mika masa 2k aiko maigadi ya hau godia da kiraki hannu kawai ya daga masa yai hanyar parkin shade dinsu ya ajiye motarsa ya duba seat din baya cikin magungunan daya ajiyewa a a first aid box dinsa ya dauki na ulcer ya jefa a cikin ledar magunguna da safeena ta bashi. Sallama yayi cikin nutsuwa ya shiga falon dai dai lokacin mum ta fito aiko ganin aliyu yasa ta dan yatsina fuska shiko jiki na bari kamar yayi gamo ya sauko dg kan kujera yana kwasar gaisuwa,fuska ba yabo ba fallasa suka gaisa yai mata ya jiki sannan ya mika mata ledojin hannunsa ya mike xai mata sallama kenan tace "aliyu baxaka tsaya ko ruwa kasha ba?" Sai ya tsinci kansa ya kasa yi mata musu alhalin bai taba cin komai na gidan ba. Komawa yai ya xauna xuciarsa na cikin dumuwa yana buqatar ya duba inteesar kuma ya san by nw ta tashi dg baccin da ya barta tanayi. Tunanin haka yasa ya ajiyar xucia tare da fesar da iska mai xafi hade da lashe labbansa da suka bushe. Mum ce ta shigo riqe da jug a akan tray da cup da roban ruwan c'est bon,ta tsiyaya masa xobon ta mika masa ya kai hannu biyu tare da yin godia.... zai kai bakin shi kenan wayarsa tai ringing hakan ya dakatar dashi da sauri ya ajiye xobon ya karkace ya xaro wayar dg aljihun jeans dinsa duk a tunaninsa ko inteesar ce ta kira shi... Sae da Aliyu ya fara xuwa asibiti ya dauki maganin da xai kai ma mamar safeena snn ya ja motarsa ya kama hanyar gidan jikinsa a mace, ya na isa yyi parkin a waje, ya fito da maganin yana kare ma gidan kallo snn ya shiga, suka gaisa da mai gadin ya karasa balcony ya danna bell, yar aiki ta bude masa kmr jira take ya shiga falon ta nuna masa kujeran da xae xauna da sauri shima kmr wnda ake contrl ya xauna inda ta nuna masa yana bin ko ina na falon da kallo, yar aikin tayi sama kiran Hajiya, yana kallo Hajiyar ta shigo falon ya dan dukar da kansa ya gaisheta ta amsa da fara'a kmr gske snn yyi mata ya jiki, ya bata maganin da ya kawo mata, ta amsa tana gdya tana jujjuya maganin, ya ciro kudin da ya dauko daxu ya mika mata yace "ni xan koma Hajiya" ta karba da sauri tana gdya ta mike tace to bari na kawo maka ruwa kasha mana, yace "A'a Alhmdlh ae daga gida nke," tace "to bari na baka sako ka kaima safeena," yace "to," ta mike ta yi sama, sae ga ta ta sauko da dan wani parcel, ya karba yyi mata sallama, ta rakosa har bakin kofa tana sa masa albarka snn ta koma murna fal cikinta, yana barin anguwar yaji hka kawae yana son ganin abinda ke cikin parcel din, parkin yyi gefen titi snn ya shiga budewa, wani ruwa ne ya xuba jikinsa ya matsar da parcel din daga jikinsa da sauri amma duk da hka sae da ruwan ya taba kayansa da farko wari yaji, ya yatsine fuska kawae kuma sae yaji wni mugun kamshi me ddi ya xiyarci hancinsa, ya rufe da sauri ya ajiye parcel din ya ci gaba da drivin dinsa. Safeena ta kasa xaune ta kasa tsaye sae kaiwa take tana komowa a falo, wayar uwarta ya shigo nata ta daga da sauri jikinta na rawa tace "ya xauna kan kujerar mumy, kuma ya karbi ledan," uwar ta kyalkyale da dariya tace "wllh kuwa dota, ynxu fatanmu kawae Allah yasa ya bude," safeena ta doka tsalle tace " Alhmdllh amma naji ddi momy, budewa kuma ba matsala bace ko a gida xan sa ya bude bare ina da yakinin ma ya bude naji sighn din da mutumin yace xan ji a jiki na," budewar gate din da safeena taji yasa tace "wayyoo momyna ya dawo xamu yi waya anjima," ta katse kiran tana murmushin mugunta, shknn ynxu sae yanda tayi da Aliyu," yana shigowa gidan ta karasa cikin kissa ta rungumesa ya dagata sama ya manna mata kiss a goshi yace "bbyna sae kyau kike karawa kullum," ta hararesa tace "sae yau ka sani," yace "A'a bbyna ina sane," kinsan me bbyna na dan maki barna wllh momy ta ban turare na kawo maki da karambani na na bude ya xuba jikina," ta kankamesa ta rasa inda xata sa kanta don murna, tace "da gske bbyna, wllh sae ka biya ni," yyi hanyar stairs da ita yana cewa "naji xan biya bby nawa ne," inteesar kam na xaune ta jinginar da kanta jikin gado, ji take kmr ba ita ba duk ta rasa inda xata sa ranta taji ddi, ga alluran hana aman da yyi mata duk ya bi ya dameta, tana neman yin aman ma ko xata samu sauki amma ta kasa, yunwa take ji ssae amma bbu abinda ke ranta, ko wani abinci ta tuna sae taji amai na taso mata jikinta yyi mugun xafi ga kishin ruwa da take ji kuma tana tsoron shan ruwa, ta sauko kasa da kyar ta kwanta kan tiles din dakin ko xata ji ddin ranta, kasa daure kishin tayi ta mike xaune tana mayar da numfashi ta rarrafa ta bude fridge dinta taga ba ruwa ciki sae lemo, tana daddafa bango ta fita daga dakin ta sauka kasa da kyar ta bude fridge ta dauki ruwa ta sha, snn ta koma sama, dae dae kofar dakinta taji amai frm no where ta xube wajen ta shiga kwarara aman kmr ranta xae fita, suna daki shi da safeena duk ta gama rikitar da shi, ya turata da karfi ya mike tsaye ya karasa kofa ya bude ya fita safeena ta bi bayansa da sauri, durkusawa yyi gabanta yana kallonta, ta fashe masa da kuka abun tausayi ta xube jikinsa muryarta na rawa tace "don Allah ya Aliyu ka kai ni gida, ni wllh na gaji ko ina ciwo yake min wayyoo mutuwa xanyi," ya rungumeta cike da tausayi xae yi magana safeena tace "dear," ya juya da sauri yana kallonta, kallonsa kawae ta tsaya yi bata ce komai ba, ya sauke ajiyar xuciya yana kallon Inteesar yace "ke kuma mahaukaciyar wace gari ce xakiyi ma mutane amai a nn, idan kina jin amai ba sae ki shiga bathroom din ki ba, wnn ae kaxanta ce," Inteesar ta daga kanta tana kallonsa, da kyar ta shiga kkrin mikewa daga inda take wani aman ya taso mata ta shiga kwarara sa a wajen, kuka ssae ta fashe da ta jingina jikin bango tace "wayyoo Abbana," kallonta kawae ya tsaya yi ya kasa cewa komai, ta rarrafa ta shiga dakinta ta xube kan tile tana mayar da numfashi, safeena da sae kallon inteesar take da mugun mamaki lkci daya jikinta yyi sanyi ta ma rasa tunanin da xata yi, a xuciyarta tana cewa amae kuma? to me hkn ke nufi, ta sauke ajiyar xuciya tana kallon Aliyu tace "me ke damunta???? . Aliyu ya mike tsaye yana kallon safeena yace "bata jin ddi ne," bae jira me xata ce ba ya bude dakinsa ya shiga sae ga shi ya fito da mop ya gyara wajen aman, safeena ta koma daki da sauri hannunta na rawa ta shiga kiran uwarta, tana dagawa tace "momy wlh ina ga fa kmr cikine da yarinyar nn," uwar ta mike daga xaunen da take da sauri tace "mene? Ke wa ya gaya maki," a rude safeena tace "gashi nn tana ta amai," uwar tayi salati tace "bari xan kiraki," ta katse kiran. Da daddare Inteesar na kwance kan tiles ya shigo dakin ya durkusa gabanta yana kallonta yace "tashi ki sha kunu na karbo maki a gida," ta kasa dagowa ya dagota yana kallonta ya kauda kansa da sauri, ya kai mata kofin baki, ta kauda kai da sauri muryarta na rawa tace "xafi," ya girgixa mata kai yace "ba xafi," ta maido da kan jikinta na rawa ta daura hannunta kan kofin taji ba xafi ta kai bakinta yana rike da kofin ya shiga bata, da sauri ta cire bakinta tace "baxan yi amai ba? ya gyada mata kai ya ci gaba da bata, yunwa take ji ssae don hka rabi tasha ta koma tayi kwanciyarta kan tiles, yace "kin koshi ne ta gyada masa kai tace ruwa xan sha, yace "aa baxa ki sha ba," bata ce komai ba ya dago ta mayar kan gadon duk abinda suke safeena na lekensu, ta koma da sauri daki har da hawayenta ta kira uwarta tace "kai ni momy wllh na gaji, gashi can wajenta yana lallabata yana bata koko," uwar tace "yi shiru safeena, daxun nn na dawo daga wurin mutumin, ca yyi wae duk abinda xa muyi masa a kantabaxae taba tasiri ba sbda yana mugun son cikin nn dake jikinta," safeena ta dafe kirji tace "ynxu ciki ne da ita da gske ina xaune momy," uwar tace "ki tsaya ki saurareni mana," safeena na share hawaye tace "to ina ji momy," uwar tace "yauwa, to ynxu ca yyi dole sae an lalata cikin in har muna son muga aiki yyi mugun tasiri a kansa, ynxun ma ba wae bae yi tasiri bane, don xae dinga lallaba ki kuma sae abinda kika ce masa xe yi, sae dae fa hankalinsa gaba daya na gunta sbda wnn shegen cikin, kuma fa baki isa ki hanasa xuwa gunta ba amma, don hka kawae ki kwantar da hankalinki jibi ki xo mu koma kauyen yace yana jiranmu, ciki kuma kmr ya bare ne," safeena ta share hawayenta xuciyarta fal murna tace "to ngdd momyna," ta katse kiran tana murmushin mugunta. Da safe Aliyu ya bae ma safeena i.v din bikin Zainab, ta tabe baki tana hararansa tace "to ca nayi maka ban sani bane," yyi shiru yana kallonta snn yyi murmushi yace "to Allah ya baki hkuri bbyna, amma ni dae ban san me nayi maki ba kika canxa min kwana biyu," ya mike ya karasa kusa da ita ya xauna yana shafa gashinta yace "haba yan matana," ta hararesa tare da buga masa hannu tace "ni ka rabu dani," ya rungumeta yace "haba bbyna," kmr xata yi kuka tace "to ba kai bne ba baka ma damu dani da lamarina ba a gidan ba," yace "inji wa yace maki hka," kakarin Aman inteesar yaji, ya saketa da sauri ya mike tsaye ya fice daga dakin, safeena ta bi sa da kallo xuciyarta na mugun kuna, kasan dakin ya tarar da ita tana ta amai ya kamata har ta gama snn ya gyara mata jikin ya gyara dakin ya kwantar da ita kan gado, ta rikesa muryarta na rawa tace "sanyi nake ji yaya," ya lulluba mata bargo snn ya dauki I.v din da ya ajiye gaban madubinta xae fita ya juya yaga kallonsa take, ya dawo yana kallonta yyi murmushi yace "kina san wani abu ne," ta girgixa masa kai yace "kinsan bikin Zainab saura kwana goma ko," ta mike xaune da sauri tace "da gske yaya, ni ba a gaya min ba to," ya kamo hannunta yace "ae sun san baki da lfya, ki bari nxt wk sae mu tafi gidan kafin nn jikinki ya kara kwari," ta marairaice kmr xata yi kuka tace "to ba kila xuwa tayi ranan ta gaya min ba ka koreta," yace "ba ta ji ne," tace "to yaya wa xata aura" yana kallonta yace "faruuq," ta wara idonta ta fada kansa cikin jin ddi tace "don Allah da gske yaya, kai amma naji ddi wllh, ka bani nmbr ya faruuq din" yace "to anjima xan baki, xanje gida ynxu me xan ce inna ta girka maki?" tayi shiru sae kuma ta bata rae ita da ba ma son cikin take ba, yace kinyi shiru, tana hararansa tace "kace mata ina da ciki ne," ya daga hannayensa da sauri yace "A'a" yana girgixa kai, ta koma ta kwanta tace "dan wake nake so ni," yace "to, sae na dawo, kar ki sha ruwa kar amai ya takuraki," bata ce masa komai ba yayi hanyar kofa, duk wnn abinda suke safeena na labe tana jinsu, tana jin xae fito ta bar wajen da sauri ta shige dakinta tana murmushin mugunta, yana fitowa ya shiga dakin safeenar . Bayan kwana biyu safeena ta samu ta lallaba Aliyu wae xata gun wata yar uwarta, ya ko barta har da bata kudi da makullin mota dayake ta iya drivin tana ta murna a xuciyarta tana cewa lallai sae yanda tayi da Aliyu, ynxu kam ta yrda yana tafin hannunta amma dae ba duka ba, tunda bata isa ta hanasa xuwa gun Inteesar ba, amma komai ya kusan xuwa karshe, ta fada a fili tana murmushi, cikin kwanakin nn Aliyu na da aiki ssae a clinic don hka ya gwammace da ya bar Inteesar kadae a gida gwara ya dinga tafiya da ita don tana bukatar kulawa ssae, hka ko ya dinga yi kullum shi xae shiryata da safe yyi ma safeena sallama su wuce asibiti, hkn yyi mugun tada ma safeena hankali to ta ya xa'a yi ta aikata abinda suka sha wahala kafin su samu bayan baya barinta a gida., ita kam Inteesar ko kadan abinda Aliyu ke mata baya burgeta don dai dae da second daya bata son cikin jikinta, kuma tasan sbda cikin yake mata hka, wani mugun tashin hankali ke xuwa mata idan ta tuna cikin Aliyu ne jikinta, Ana saura kwana uku bikin Zainab ya kai ta gida duk da ba a son ranta ba don bata son su san tana da ciki, amma ashe duk ya gaya masu uwarsa ce kadae be gaya ma ba sae umma, inna duk ta rikice masa wae cutar jikarta kawae yake gashi duk ta fige ba kyan gani, shi dae bae tanka ma inna ba ya fice, Inteesar dae na kwance falo sae mayar da numfashi take don da kyar ta iya karasowa cikin gidan bayan sun sauka daga mota, kuma da asibiti ne baya barinta ta taka da kanshi yake daukarta su shiga ciki, inna tace "to wae wani irin jarababben cikine wnn dake neman kashe min ke," ta mike xaune tana hararan inna kmr xata yi kuka tace "wae ni nace maki ciki gareni ne," bata jira me inna xata ce ba ta shiga daki tayi kwanciyarta, inna duk ta daga hankalinta ganin irin laulayin da Inteesar take mai tsanani, bbu wanda bae san ciki ne da ita ba a gidan, ko da yaushe cikin amai da kasala take, ko maganan kirki bata son yi sae in Aliyu na yasa ta gaba ko yana tambayarta me take so, duk tausayinta kawae yake, Hajiya da hankalinta yyi mugun tashi bata ga fuskar da xata ma Aliyu magana ba da ya shigo da ya fice daga gidan, tab aiko gwara ta nemo yanda xa ayi da cikin nn, ynxu Aliyu dama sae ya iya kwana daki daya da yarinyar nn duk cika bakinsa, hka aka yi biki hankalin inna rabi na gurin Inteesar rabi na gun bikin, duk aka yi abubuwa masha Allah, amma inteesar na kwance tana fama da kanta, safeena ma ta xo ranar bikin tana daddaga hanci ita matar Aliyu inna ta kunyatata gaban lodin jama'ar biki su kursum dariya kmr xasu shide, ko minti daya bata kara a gidan ba tayi gaba ba shiri jikinta a sanyaye har ga Allah tsoran tsohuwar nn take, ran Hajiya yyi mugun baci amma bbu yanda ta iya da inna, washegarin ranar da aka kai Amarya da daddare Aliyu ya shigo falon inna bae ko kalli innar ba ya durkusa gaban inteesar dake kwance idonta biyu, ya daura hannu a goshinta yace "amma yau bakiyi amai ba ko," a fusace inna tace "kaji gantalalle wani irin bata yi amai ba, ae hanjin cikinta ne kadae bae xaxxago ba yau har tsorata nayi nace to ko su ne ke shirin fitowa" Aliyu yyi mata mugun kallo yace "to ke kuma wa ya somo bakin ki nn, iyayi kawae," sae abun ya ba Inteesar dariya ya dago ta yana kallonta yace "Abba na neman mu, xaki iya ko na daukeki," ta marairaice tace ynxu, ya gyada mata kai, ita mugun kunyan Abba take ji har ma da momynta, duk shigowar da momy take ta gaisheta kar inna ta xaxxageta tace taki xuwa, Inteesar yi take kmr tana bacci, inna ta mike tsaye da sauri tace "bari kawae na kama hannunta mu je," Aliyu ya bude baki yana kallonta yace "wae meyasa kike son shiga tsabgar da ba taki ba ne," bae jira me xata ce ba ya harareta ya sa ma Inteesar hijab dinta ya dauketa suka fice, inna tayi kmr xata yi kuka tace "ni ban san meyasa yaron nn ya rainani da tsufa na da furfurata ba," a hanya ya ajiye ta dalilin rokansa da ta dinga yi ya ajiyeta suka karaso falon yana rike da hannunta, da kyar ta iya bude baki ta gaishe da Abba kanta a kasa, ita kawae kunyarsa take ji, yace "ya jikin fateema," kanta a kasa tace "da sauki Abba," yace "to Allah ya sauwake, kina son komawa dakin ki ne ko xaki xauna nn gun inna sbda condition dinki" ta dago kai a hankali tana kallon Aliyu, shima kansa a kasa yake, tayi shiru ta rasa me xata ce don ita kam bata da burin cikin nn ya kara girma a jikinta, Aliyu yace "Abba da dae na tafi da ita xan fi kula da ita a can kuma ba gida ma nake barinta ba tare da ita nake xuwa clinic, nn ko xae yi min nisa kuma xan takura kaina," Abba xae yi magana inna ta fado falon, ashe tana labe tana jin duk abinda suke cewa tana huci kmr xata yi kuka tace "amma munafurcinka dayawa yake Bukar, hka muka yi da kai? To ni Rahmatu nace bbu inda yarinyar nn xata je aje a kashe min ita da abinda ke cikinta a banxa a hofi a barni da wayyo Allah, don idan an kashe su ma ni nayi hasara ba ku ba". .. Aliyu ya dan yi tsaki ya kauda kai, Abba kam shiru yyi yana ta kallon inna, ita ko ta tsaya masu kmr soja a bakin kofa, can dae Abba yace "to ki hada kayanki sae ki bi su," tayi kwafa tace "ko da naji," snn ta juya ta fice da sauri, Abba ya girgixa kai yace "tashi ka dau matarka ku tafi," Aliyu ya mike yana kallon Inteesar, ita ma ta mike tsaye suka ma Abba sallama snn suka fita, yana rike da hannunta yace "mu je mu gaida momyn ihsaan ne," tayi kmr bata ji sa ba shima bae sake ce mata komai ba har suka fita ya bude mata mota ta shiga shima ya xaga ya shiga suka kama hanyar gida, ko da suka isa tayi bacci ya fito da ita daga motar yana rike da ita kmr bby, safeena na kwance falo ta bi su da kallo ya sakar mata murmushi yace "bbyna," tayi tsaki ta dauke kanta tacigaba da kallonta, sae da ya kai Inteesar sama ya kwantar da ita snn ya sauko ya sameta, ta mike tayitsaki ta haura sama ta bar sa nn ya bita da kallo snn yyi mmrshi yabi bayanta. Washegari sae da safeena ta sa ya makara xuwa office, wanka kawae yyi ya shirya ya dauki makullin motarsa ta rakasa tanai masa shagwaba ya manna mata kiss ya ja motarsa ya bar gidan, ta sauke ajiyar xuciyan jin ddiyau dae ya manta shegiyar gaba daya, ta koma cikin gida murna fal cikinta, tana shiga daki ta fito da kullin maganin da aka basu su sa ma Inteesar a ruwan sha ta tsura ma maganin ido tana murmushi,dukiya fa knn a hannunta, ruwan fridge ta kwashe gaba daya ta bar guda biyu ta xuxxuba maganin cikisnn ta rufe fridge din ta koma sama, ta lura kasa Inteesar ke saukowa shan ruwa bbu ruwa a dakinta kuma bata ga alamar an siyo ba, tana ta kwance a daki tana jiran jin saukowar Inteesar amma shiru, ita ko tana kwance daki ta rasa inda xata sa ranta sae juye juye take ga yunwar da take ji tun safe ta gane Aliyu ya bar gidan hkn yasa ta daure ta mike ta sa ma kofar ta key, kishin ruwa duk yabi ya ishetagashi ba karfin sauka kasa, da kyar ta rarrafa ta shiga bathroom ta bude tap ta sha ruwa ta dawo tayi kwanciyarta kan tiles. Washegari ma abinda ya faru knn Aliyu bae shigo ya ga halin da take ciki ba ya bar gidan da sassafe, duk da jiya don ita ya dawoda wuri amma safeena ta gusar masa da hankalinsa ya manta me ya dawo da shi, ganin yunwa na neman yi mata lahani yasa ta dinga daurewa tana hada tea a nn dakinta da ruwan sanyita sha, shima tana sha ta amayo, duk ta kara xabgewa bata da aiki sae na kuka ita daya a daki, wani lkcn sae taji kmr ta dauki waya ta kira inna kawae sae ta fasa don bata ga amfanin kiran ba don rabuwa kawae take son yi da cikin, ita safeena bbu abinda yafi daga mata hankali irin yanda taga ruwanta na nn ajiye ba a taba ba, hkn yasa da daddare da Aliyu ya dawo ranan tace "anya kuwa kana shiga duba baiwar Allahn nn dear, gashi ita bafitowa take ba, na kan shiga na dubata wllh, amma ba ddewa nake ba kar ace xan yi mata wani abun ne" Aliyu ya mike da sauri kmr an tsikaresa yyi hanyar stairs ta bude fridge ta dauka ruwan da sauri ta bi sa tana cewa "gashi ka kai mata ruwa naga kmr jiya ruwan dakinta ya kare na fanfo take sha, ni kuma kar na kai mata ta xata wani abun ne," ya karba ya haura sama ya bude dakin ya shiga rabon da ya ganta yau kwana uku tun ranar da sukadawo daga gida, ya karaso gabanta ya durkusa yana kallonta a hankali yace "ya jikin fateema, kin daina aman," tayi tsaki ta juya abinta, ya bude fridge dinta ya ajiye mata ruwan yace "me xaki ci," tayi bnxa da shi, yyi shiru yana kallonta, ta juya cikin kuka tana kallonsa tace "wllh tllh idan baka cire min wnn shegen cikin ba...." bae jira ya karasa jin maganarta ba ya xuba mata mari, "don uwarki kika sake min maganar cire ciki sae nayi mugun saba maki kina ma da hankali kuwa, to ki je ki cire tunda ke mahaukaciya ce," ya mike a fusace ya fice daga dakin ta bisa da kallo dafe da kuncinta. Ranar bata yi bacci da daddare ba, kawae Allah Allah take gari ya waye, gari na wayewa ya shigo dakin kafin ya tafi aiki, tea me kauri ya hada mata ya ajiye matagefenta, snn ya dauko goran ruwan da safeena ta basa jiya ya ajiye mata gefenta safeena ta shigo dakin tana murmushi tayi ma Inteesar ya jiki ko kallonta inteesar bata yi ba suka fice tare da mijintata rakasa ya shiga mota ya manna mata kiss snn yaja motar ya bar gidan, safeena ta koma gidan xuciyarta fari tasa ganin goran ruwan da ta ba Aliyukusa da inteesar yau dae xa ayi ta ta kare, ta shige dakinta tana dariya. Inteesar ta mike tsaye ta dauki Hijab dinta ta saka, duk irin wahalan da take sha ko sau daya wanka bae taba wuce ta da safe ba dole sae ta daure ta shiga tayi, ta fito tana ganin jiri mai gadi ya tsaya xae mata maganar bnxa ta fixgo gate din ta fice abinta ta barsa nn tsaye, gidan Aneesah ta shiga, tana xaune tana ba shakur Indomie, tana shigowa ta kwanta kan kujera tana mayar da numfashi, Aneesah tace "lah daga ina hka Inteesar daxun nn nagama xancenki a xuciyata wllh" Inteesar xata yi magana taji yawu bakin ta mike da kyar taje bathroom ta xubar Aneesah tace "A'aah kice oga yyi aiki" . Inteesar ta harare Aneesah snn tayi tsaki tace "ni don Allah taimako naxo kiyi min Aneesah," Aneesah tayi dariya tace "to kawas ina jinki amma cikin nn na baki wahala gskya, kinga yanda kika rame kuwa," Inteesar ta dawo kasa kusa da ita tace "don Allah don Annabi Aneesah kinsan inda ake abortion?" Aneesah tayo waje da ido da mamaki tana kallonta snn tace "kina da hankali kuwa inteesar," inteesar ta jinginar da kanta jikin kujera hawaye ya cika idonta, Aneesah tace "kinyi shiru," inteesar ta share hawayen idonta tace "wllh xubar da cikin nn xanyi kin dae ji na rantse in ma xaki gaya min ki gaya min," Aneesah ta gyada kai tace "to tashi ki fita a gidana, ni bana hulda da maras tsoran Allah," inteesar ta juya tana kallonta tayi shiru snn ta mike tayi hanyar fita daga gidan, Aneesah ta bita da sauri ta kamo hannunta tace "haba inteesar bafa kiyi kama da jahila ba," kuka inteesar ta fashe da tace "baxa ki gane ba Aneesah wllh bana sonsa bana son cikinsa, bae damu dani ba sae wahala nke ta sha," Aneesah ta xaunar da ita tana kallonta da tausayi tace "ni na tabbatar maki kina haife wnn cikin xaki ga tsantsan so gun mijinki, ni banga rashin son da mijinki yake maki ba inteesar nafa ga abinda yyi ma kishiyarki ranar sbda ke, don me xaki walakanta kyautar da Allah ya baki yar uwa," inteesar tayi shiru tana ta sauraran Aneesah tana ta wa'axinta da nasiha, har ta kai Aya snn inteesar ta kirkiro murmushi tace "to ngdd Aneesah, ta dauki shakur tana ta wasa da shi yana mata dariya, tace "amma a gida kika haife yaron nn ko Aneesah," Aneesah tace "me kika gani," inteesar tayi yake tace "aa kawae tambaya ce nayi don ni dae ina tsoran Haihuwa," Aneesah tayi dariya tace "A'a a asibiti na haifesa," inteesar tace "wani asibitn?" Aneesah tace "A'a tender care na haifesa, ai kin san asibitin bbu wani nisa," Inteesar tace "A'a" Aneesah ta gaya mata inda asibitin yake kuma dama abnda kawae take son ji knn, ta mike xuciyarta fal murna ta bar gidan. . Inteesar na fita daga gidan Aneesah ta koma gida cike da jin ddi ta shiga dakinta tana haki kmr warce tayi gudu, ta tabe baki jin wakan da ke tashi dakin safeena, sae da ta huta na kusan minti goma snn ta mike ta dauki purse dinta ta fita daga dakin, dakin Aliyu ta bude a hankali ta shiga ta bude drawer din da taji yace Safeena ta bude ta dauki kudi ranan, taji ta a kulle, tace "na shiga uku," ta mike ta fara kalle kallen cikin dakin kmr xata yi kuka, to ina xata samu kudin xuwa asibitin ynxu, drawers din dakin ta dinga bubbudewa gaba daya ko xata ga kudi amma bbu, duk ta gaji sae haki take, tuni ta fara kuka tana cewa "Allah ka taimakeni in ga kudi" ta bude lst bedside drawer din taga wani babban book an rubuta my diary a gaba, tayi tsaki ta ajiye ta mayar da drawern, ta mike ta isa wardrobe din da yake ajiye kayansa na sawa ta bude ta lumshe idonta sakamakon wani kamshi me ddi da ya bugi hancinta, ta gama bincikenta nn ma ba ta ga kudi ba ta rufe ta xube kasa ta daura hannu a ka tace "wayyoo Abbana wllh ni na gaji," ko ina ta bude daga taga Allura sae taga magunguna da dae kayan asibiti kmr tsiya wnn wace irin jaraba ce, kmr ance ta mike ta daga filo taga dubu daddaya karkashin filon har da Atm dinsa ta wara ido tace "wayyo Allahna," ta kwashi kudin ta shiga kirgasu da sauri hannunta na rawa taga dubu sha biyu ne, ta dan marairaice fuska to xae isheta taje asibitin ma kuwa, tayi tsaki ta bude purse dinta ta xuba kudin snn ta juya xata fita daga dakin taje dakinta ta sha ruwa don mugun kishi take ji don tsabar son taje ta cire cikin ta nemi xaxxabin dake tattare da ita ta rasa sae kasala kawae, har ta isa bakin kofa ta dawo da sauri tuna baxae rasa ruwa a dakinsa ba da tayi ta bude fridge dina ta ko ga ruwa ta dauka ta bude ta sha snn ta rufe fridge din ta dauki sauran ta fita daga dakin, duk wnn abinda take safeena bata sani ba, tana daki kwance tana ta shan kida cike da jin ddi, jiran jin ihun Inteesar kawae take a ko wani lkci, Inteesar kam har ta fita daga gidan rike da purse dinta cikin Hijab, mai gadi dae bae ce mata kala ba ta bude gate ta fice abinta sae da ta isa bakin titi snn ta tsayar da tricycle tayi masa kwatancan asibitin da Aneesah ta gaya mata yace ta bada dari biyu, ta shiga tace mu je. Wasa wasa asibitin shegen nisa ne da shi, yyi parkin dae dae gate din asibitin ya juyo yana kallonta yace "mun kawo Hajiya," ta fito tana kare ma asibitin da ma anguwar kallo, ta bude purse ta ciro dubu daya cikin kudin ta basa kudin ya rage dubu sha daya, ya bata canjinta ta karasa cikin asibitin gabanta na faduwa, wnn dae da ganin asibitin nn ba na talakawa bne, anya kuwa xasuyi mata abortion a dubu sha daya kuwa ta dan karyar da kanta abun tausayi, da Addu'arta ta shiga asibitin, babba ne ssae ta karasa cikin reception ta xauna ganin patients dayawa a xaune, ta shiga kare ma reception din kallo, ta kai kusan minti talatin a xaune ba a xo kanta ba duk ta gaji, taji kwanciya kawae take son yi ga amai dake taso mata, ta daura kanta a cinya taji kmr ta rusa ihu duk ta rasa ina xata sa ranta, wata nurse ce ta dafa ta ta dago da sauri tana kallonta, Nurse din tace "yhur card nmbr Madam," inteesar ta shiga kalle kalle xata yi magana taji yawu ya cika bakinta, nurse din ta lura da hka ta nuna mata bayin dake kasan reception ta karasa ta xubda yawun ta kora ruwa snn ta dawo, nurse din ta debo vitamin c ta mika mata ta sa a baki tayi mata gdya ta karba, tana kallon Nurse din tace "i dnt have a card in here," Nurse din tace "to dole sae kin yanki kati," Inteesar tayi shiru snn tace "nawa ake yankan katin," nurse din tace "family card dubu biyar, na mutum daya dubu 2 da dari 5," inteesar tayo waje da ido tana kallonta, ganin xata bata ma nurse din lkci ga kuma patients dayawa suna jira yasa tace "to ki yankar min na mutum daya," nurse din tace "ok" snn tayi gaba, a hankali inteesar tace "na shiga uku, to ai kudin ya kare," ba ajima ba nurse din ta fito daga wani dan daki ta mika mata katin snn wata nurse ta daddubata ta duba har da weight dinta tayi rubutu a file tasa nurse ta rakata bayi aka xuba mata ruwa a kanta don temperature dinta yyi sama, ita dae binsu kawae take, a xuciyarta tace ko da yake basu san me ya kawota ba shiyasa suke bata lkcnsu, ita dae ynxu likita kawae take son gani, wata nurse ce ta gwada mata office din doctor din da xata shiga a sama, tana rike da file dinta ta haura sama da kyar ta karasa office din tayi knock. A hankali Inteesar ta tura kofar bayan an mata ixinin shigowa office din, cak ta tsaya daga bakin kofa tana kallon likitar, doctor din ma ta mike tsaye tana kallon Inteesar da mamaki tace "fateema," inteesar ta kirkiro murmushi gabanta na faduwa ta karaso office din a sanyaye, ta nuna mata kujera ta xauna, doctor din tace "daga ina kike hka fateema, me ya kawo ki nn," ta rasa karyan da xata mata, da kyar bakinta na rawa ta ce"banda lfya ne," doctor din ta hade rae tace "shi Aliyun fa," inteesar ta rasa me xata ce ga xuciyarta sae tashi yake, likitan ta dawo kusa da ita tana kallonta ta dago kanta tana kallon cikin idonta tace "ciki gare ki fateema," inteesar tayi shiru bata ce komai ba, doctor din ta ciro wayarta ranta a bace ta shiga neman layin Aliyu, da sauri inteesar ta dakatar da ita gabanta na faduwa tace "A'a don Allah doctor kar ki kirasa wllh ya sani kuma yana dubani nice dai bana son shi ya duba ni, Allah yana kula dani doctor kawae ni ce bana so, idan yaji na xo nn xae bata min rae don bae sani ba," doctor din tace "haba fateema, to ma don me xaki fita ba tare da ixinin mijinki ba, kuma meyasa baki son ya duba ki," inteesar ta fashe da kuka tace "wllh ni bana sonsa doctor," doctor din ta tsaya da mamaki tana kallonta snn tace "sbda me fateema, gashi har rabo ya shigo kice baki son mijinki," Inteesar ta sunkuyar da kai tana hawaye, doctor din tayi shiru tana kallonta, can ta koma sit dinta ta xauna ta shiga yi mata nasiha kan cewar ta rungumi mijinta ta cire duk wani rashin sonsa a ranta, ita dae bata ce komai ba sae kukan da take a hankali, Doctor din tace "yyi maki scan ne?" inteesar ta girgixa kanta tace "A'a nace masa bana so," doctor din ta harareta tace "to karki sake yi ma mijinki musu baki san aljanarki na karkashin kafarsa ba," inteesar ta dan tabe baki kanta a kasa ba tare da ta bari doctor din ta lura ba, doctor din ta yagi wani takarda ta danyi rubuce rubuce snn ta danna bell wata nurse ta xo da sauri, ta mika mata takardar tace "scan xa ayi yi mata sisterna ce," doctor din ta kalli Inteesar tace "tashi ki bita," inteesar ta mike a sanyaye ta bi bayan nurse din har sun kai bakin kofa ta juya tana kallon doctor Maryam tace "don Allah doctor kar ki kirasa wlh xae bata min rae,"doctorn tayi murmushi tace "baxan kirasa ba ki kwantar da hankalinki" bayan kusan awa daya inteesar da nurse din suka shigo da sakamakon a hannun nurse din, ta mika ma doctor maryam ta fita, doctorn ta bude takardar tana dubawa, inteesar dae kallonta kawae take ranta a hade, ba shiri taga doctor maryam ta mike tsaye da sauri tace "waw Ahmdllh, twins 4 Aliyu, Allahu akbar," ta rungume inteesar tace "Allah ya raba lfya kanwata, kinga ma yan biyu ne" inteesar ta sunkuyar da kanta da sauri hawaye ya cika idonta, hka doctorn ta dinga mata surutu cike da murna kmr ita xata haifa ma cikin, ita dae bata ce mata komai ba daga karshe ta hada mata magunguna, da allurori a office dinta ta xuba mata su a leda da takardar scan din tace "to maxa tashi ki koma gida sae ki kai masa takardar scan din, sae ya fada maki yanda xaki sha magungunan yyi maki alluran," Inteesar ta mike da sauri kmr jira take tace "ngdd ssae doctor," har gate doctorn ta rakota snn tayi mata sallama bayan ta kara jaddada mata ta hakura ta xauna da mijinta, ita dae inteesar sae gdya take mata har ta koma ciki snn ta kama hanyar titi inda xata samu tricycle, a cikin wani flower ta watsar da magungun da injectns din dake cikin ledar dake hannunta ta bar takardar scan din kawae, ta isa titi xuciyarta na suya, ta tsayar da tricycle tace "malam don Allah idan kasan ko wani asibiti a nn wajajen ka kai ni," yace "to shigo muje akwae wani can gaba," ta shiga da sauri ya ja machine din suka kama hanyar asibitin, ae ko yan goma ne a cikinta ba yan biyu ba sae ta xubar da su yau wllh . Wani babban Asibitin aka kuma kawota, ta fito tana kare ma asibitin kallo snn tace "nawa xan baka," yace "ki bada ko nawa ne," ta ciro dari biyu ta mika masa tayi hanyar gate din shiga asibitin, gabanta ya shiga faduwa ganin asibitin bana wasa bane don har yafi wanda taje da xu, tana isa reception bata tarar da patients da yawa ba aka xo kanta, nurse din tace "yhur card nmbr madam," Inteesar tace "i dnt have a card in here, nawa ne katin," nurse din tace "family card dubu biyar, na mutum daya dubu uku, na Anti natal, dubu biyu," Inteesar ta ciro dubu uku ta mika mata, matar tace "sunanki fa," inteesar tace "Fateema Aliyu," matar tace Address fa? Da date of birth, Inteesar ta bata fake address da date of birth dinta, matar ta juya ta wuce, ba ajima ba ta dawo ta mika mata katinta snn aka dubata wata nurse ta rakata da file dinta a hannunta xuwa office din doctor, yana xaune yana ta rubuce rubuce farin glass a idonsa, sae da gabanta yyi mugun faduwa don sae taga kmr ya Aliyu barin yanda ya hade rae da tsukekken bakinsa, shima kyau kam ba a magana, ta karasa office din xuciyarta na ci gaba da bugawa ta ajiye masa file din a gabansa ta xauna kan kujera a sanyaye tana kallonsa, yana ta rubuce rubucensa har lkcn bae dago ba, hkn yasa ta dan marairaice a hankali kmr me shirin kuka tace "doctor," sae a snn ya dago yana kallonta yace "srry ina dan abu ne," ya jawo file dinta gabansa ya bude, tana kallonsa a sanyaye tace "don Allah don annabi taimako naxo ka min doctor," ya dago yana kallonta yace "taimakon me fa," nn da nn hawaye ya cika idonta ta rasa me xata ce, yace "tok 2 me mana yan mata, taimakon me kike nema, baki da kudine kika xo a dubaki," ta girgixa kai ta fashe masa da kuka tace "A'a," ya kauda kansa yace "ni karkiyi min kuka a nn, ki fadi abinda ya kawo ki, mijin ki fa?" a hankali muryarta na rawa tace "ni banda miji," ya wara ido yana kallonta yace "wat? Amma kin san kina dauke da juna biyu kuwa," ta fashe da matsanancin kuka tace "ka taimaka min ka tausaya min ka cire min don Allah abinda ya kawo ni knn," yace "kina da hankali kuwa ca aka maki ana xubar da ciki a nn," cikin kuka tace "nasan ka iya doctor, ni taimakona nake son kayi don Allah," ya girgixa kai yace "me ya aike ki kanwata, meyasa kika xabi ki..." da sauri ta katsesa tace "rapin dina aka yi, kuma har yau ba a sani ba a gida," yace "innalillahi wa inna'ilaihi raji'un, to don me baki fada ba a gida" tana kuka tace "ba yrda dani xasu yi ba wlh," yace "to waye yyi maki," tayi shiru kmr me tunanin abinda xata ce nn kuma amai ne ke taso mata, ta daure tace "saurayina ne," yyi shiru yana kallonta, mikewa yaga tayi da sauri shima ya mike, yaga ta toshe bakinta ya bude mata bayi da sauri ta shiga ta fara kwarara amai, yana tsaye gefenta tausayinta ya rufesa ganin yanda take aman kmr xata shide amma bae taba ta ba har tagama ya bata ruwa ta wanke bakinta ta xuba ruwa a wajen ta fito da kyar ta xauna kan kujeran ta kifa kantakan table dinsa abun tausayi, yace "to sae mu ce ma Allah me, wllh ban taba xubar ma mace ciki ba kanwata," ta dago tana hawaye tace "plss ka taimakeni kuma ka fadi nawa xan baka ko ba yau ba xan biyaka don kudin hannuna ya kare," shi dae yyi shiru bae ce komai ba, har dae daga karshe ya mike ya fito gabanta yana kallonta yace "takardar meye a hannunki," ta kalli takardar snn tace "na scan da nayi ne," ya karba yanadubawa snn yace "Mrs Aliyu kuma aka sa," kmr xata yi kuka tace "kunya nake ji, ace bani da miji kuma gani da ciki," bae ce komai ba ya maida idonsa kan takardar yace "ya salam, yan biyu ne ae," ta gyada masa kai tana hawaye, ya koma ya xauna ya dafe kansa, yace "anya kuwa xan iya taimakon nn kanwata, rae biyu fa kuma har kusan 2mnth," ta fashe masa da wani sabon kukan tace "don Allah ka rufa min asiri," ya mike shima da ganin sa kasan jikinsa yyi sanyi, ya bude wani show glass din magunguna ya shiga xaban wasu magani har kala uku, snn ya dawo yana kallonta rike da maganin yace "amma xan maki allura a nn," kai kawae ta gyada masa tana kallonsa ya hada alluran ya juyo yana kallonta tace "ni ba kai xaka min ba ka ba nurse su min," yana kallonta yace "ok ni xan rufa maki asiri, ke kuma ki tona min nawa ko," da sauri tace "A'a wllh," ta bude cinyarta yyi mata snn ya dauko magungunan ya bata ya gwada mata yanda xata sha, tayi ta masa gdya har da kuka, nn dae yyi mata nasiha ssae akan matsalar da ta tsinci kanta a ciki, ya nuna mata ita ce me babban laifi, ita dae hawaye kawae take har yyi mae isar sa, yyi shiru, a hankali tace "to nawa xan biyaka doctor," yyi shiru yana kallonta snn ya sauke ajiyar xuciya yace "bana bukatan komai tunda ba aiki me kyau nayi ba, kawae dae nmbrki xaki bani don Allah," da sauri tace "to xan baka amma a kashe yakesae na koma gida na kunna," ta basa tsohon layinta, snn ta dada masa gdya ssae ya rakata har gate, ya koma, ta shiga ticycle xuciyarta fari tasa kmr an mata albishir da aljanna ta kama hanyar gida da magungunanta. . A gajiye Inteesar ta shiga gida bayan ta biya mai adai-daita sahu kudinsa, xaune ta tar da Safeena a falo tana cin Ayaba da gyada tana kallon American film sae kyalkyale dariya take ita daya kmr tababbiya, bata ko kalli inda safeena take ba ta haura sama da sauri gabanta na faduwa kar ta biyo ta ta ci ubanta, don mugun tsoranta take idan su biyu kadae ne a gida, in ko Aliyu na nn fitsara sae wanda bata tuna ba, dat was den, lkcin da take da lafiya knn, ynxu kam ta kanta take ba ta tsiwa ba, Safeena ta bi ta da kallon mamaki baki bude, dama yarinyar nn bata gidan ashe, shine take ta xaune kmr yar iska tana jiran jin ihunta, to ina ma taje, ranta yyi mugun baci ta kasa cin ayaban gabanta, tunawa tayi cewar tunda ta kwaso rana 1st abinda xata fara bukata shine ruwa, hankalinta ya kwanta tunanin hkn da tayi, to amma Allah yasa a fridge ruwan yake kar taga abinda ke ciki don inda sanyi baxata taba lura da komai ba, inteesar kam na shiga daki ta ajiye magunguna da takardar scan dinta a kan gado, katunan asibitin dama tun a hanya ta watsar da su, ta bude fridge dinta da sauri tana haki xata dauki ruwa ta sha taga bbu ruwa, ta yarfe hannu kmr xata yi kuka to ynxu ya xata yi ga wancan mayyar a falo taje tayi mata duka a bnxa, ta juya xata shiga bayi tasha ruwan ganin bata da wani alternative ta hango goran ruwan da safeena ta ba Aliyu ya kawo mata a bedside drawer, ta karasa da sauri ta dauki ruwan taji shi kmr ruwan dumi, bata damu ba ta kai bakinta xata sha taga abubuwa na yawo a ciki kmr an xuba kasa, idan ma baka kura ido ba baxa ka lura da hkn ba, ta dauki dayan ma tana kallon kasan ruwan ta gansu kwance ta girgije ta ga suna ta yawo, ta yatsine fuska ta isa bathroom dinta ta tsiyaye duka ruwan guda biyu a bath tub snn ta koma daki ta dauko cup ta dibi ruwa a famfo ta sha ta koma ta kwanta a gajiye, a hka bacci mai nauyi ya kwasheta ba tare da ta shirya ba, shafa cikinta da taji ana yi a hankali ne yasa ta bude idonta da sauri suka yi ido hudu da Aliyu xaune gefenta ta shiga kkrin mikewa xaune ya taimaka mata yana kallonta yace "kin ci abinci kuwa don yau na xo duba bbyna ne hope kin shirya?" ta juya ta kalli agogo da sauri taga karfe takwas na dare, mikewa tayi da sauri taje ta xubar da yawun bakinta ya rikota yace "ina xa ki," ta buge masa hannu ya saketa ta karasa bakin kofar bayin ta juya tana hararansa, magungunanta ta gani kan gadon kusa da shi, ta yo waje da ido a tsorace da ganinta kasan bata da gskya, ya tsaya kallonta yace "me ya faru," sanin cewa xae juya ya kalli inda take kallo ne yasa ta tofar da yawun bakinta nn bakin kofa da sauri ta fasa wani raxanannen ihu tana tsalle, har ya juya ya kalli ledan kan gadon kuwa ya mike da sauri ya karasa kusa da ita a rude ya riketa yana tambayarta lfya, jikinta ya dau rawa ta fashe masa da kuka tace "wayyoo cikina ke min ciwo har da kaina," da mugun damuwa yace "cikinki kuma" ta gyada masa kai jikinta na ci gaba da rawa, ya daga ta xae kwantar da ita kan gadonta ta fasa masa ihu a gigice tace "wayyoo ni ka kai ni dakinka, xafi nake ji," duk ta rikitasa ya dauketa da sauri ya bude dakin ya fita, sae kuka kuwa take jikinta na rawa, safeena dake fitowa daga dakinta knn ta bisuda kallo xuciyarta na bugawa "kai wayyoo ddi, ta sha ruwan," ko kallonta Aliyu bae yi ba, ita ko inteesar sae kuka take kmrgske, ya kwantar da ita kan gado bayan ya kunna AC yana kallonta yace "ina kika ce ke maki ciwo," a hankali tace "ya daina, wanka kawae xanyi da ruwan xafi," ya shiga bayinsa da sauri ya hada mata ruwan, yana shiga ta mike har tana tuntube ta fice daga dakin da sauri suka kusan cikin karo da safeena dake labe bakin kofa, safeena ta koma baya a tsorace tayi xaton Aliyu ne, inteesar ta watsa mata harara tace "an dae ji kunya," tayi tsaki ta bude kofar dakinta da sauri ta kwashe magungunan kan gadon ta xuba su cikin handbag dinta jikinta na rawa, tana xuba su ta fice da sauri taga safeena tsaye har lkcn kwakwalwarta a jagule to ko bashi tasha bane, inteesar ta wuce ta ta shige dakin Aliyu, dae dae nn ya fito ya tsaya kallonta da mamaki, xae yi magana ta rigasa "ruwa, amm ruwa naje sha," yana mata mugun kallo yace "get out," ta yi kmr xata yi kuka ya daka mata tsawa "ni kike raina ma hankali ko, fitar min a daki munafuka," tayi tsaki ta juya ta fice daga dakin tare da sauke ajiyar xuciya. Bata samu shan maganin ba ranar da daddare har tayi bacci don ido Aliyu ya sa mata, washegari sunday yana gida yana xaune dakinsa na'ura gabansa, safeena ko na daki kwance abun duniya ya isheta, inteesar ta gama duk abinda xata yi da kyar don xaxxabi ne ssae tare da ita, ta rufe dakinta da makulli ta ciro maganin da likitan ya bata jiya ta debo ruwa a bathroom don har lkcn ba ruwa a dakinta, ta xauna kusa da gado, ta fiffito da magungunan daga kwalayensu ta daddauki yanda yace mata, ta tsura ma kwayoyi shiddan dake hannunta ido, ita bata ma taba ganin irinsu ba, ta rumtse idonta ta xuba su a bakinta ta kora da ruwa da sauri ta hadiye su. TAMMAT ALHAMDULILLAHI. INTISAAR BOOK4 Inteesar tayi shiru a dan tsorace bayan ta hadiye maganin tana jiran jin me xata fara ji a jikinta, har na kusan minti goma bata ji komai ba hkn yasa ta mayar da hankalinta ga TV dake ta aiki shi kadae tana kallo, taji ta fara jin bacci amma har lkcn bata ji ko da ciwon kai a jikinta ba, hkn yyi mugun daga mata hankali, tace na shiga uku kar dae cikin baxae xube ba, ta dauko magungunan ta shiga balla su kuma xata sha yanda ta sha daxu hankalinta a tashe, ta ciro su knn ta jawo kofin ruwanta xata sake korawa taji wani matsanancin ciwo a mararta da bata taba ji ba, tayo waje da ido a tsorace gabanta na faduwa, a hankali cikinta ma ya fara ciwo ya hade da na maran, tunda take bata taba jin irin wnn ciwon a jikinta ba, kankame cikinta tayi ta shiga mutsu mutsu daga xaunen da take tana buga tiles da hannunta, taga xama ya gagareta ta kwanta kasa tana rike da cikin tana juye juye, ita nn tana ga xata iya jure ciwon har ya gama cikin ya fita, da marar ta yyi wani irin murda mata ta daura hannu a ka taji kmr mutuwarta ce ta xo, bata san lkcn da ta fasa wani axababben ihu ba tana rike da cikin, lkci daya ta hada xufa, ta shiga kwala ihun axaban da take ji a gigice, a tare Aliyu suka fito da Safeena ya karasa kusa da kofar a rude ya murda yaji a rufe, bubbuga kofar ya shiga yi yana kiranta, ta fashe da wani matsanancin kuka da kyar tace "wayyo mutuwa xanyi ya Aliyu," ya koma daki a rikice ya shiga neman spare key, safeena kam da gudu ta koma dakinta ta dinga tsallen murna shknn ta sha ruwan, ya karaso jikin kofar jikinsa na rawa ya bude kofar ya afko cikin dakin yana kalle kallen inda xae ganta, can kusa da gado ya ganta kwance tana juye juye ya karasa gabanta da sauri ya durkushe ya dago ta a rude yana tambayarta me ya faru, kasa cewa komae tayi sae juye juyen da kawae take a hannunsa, a rikice ya shiga cewa "don Allah kiyi min magana fateema me ya same ki," duk da mugun axaban da take ji hannunta na rawa ta shiga tura kwalin magungunan karkashin gado tana mayar da numfashi da kyar wae kar ya gani, ya lura da abinda take, ya rike hannunta da sauri yana kallon kwalin yace "meye wnn," girgixa masa kai ta shiga yi tana neman xamewa daga jikinsa ya daga kwalin tabs din yana kallo baki bude, a rude ya jefar ya shiga cewa "innalillahi wa inna ilaihi raji'un meye wnn," wani ihun ta kuma fasawa ta kankamesa tace "wayyoo ya Aliyu, cikina, mutuwa xanyi wllh," yana jijjigata cikin tashin hankali ya shiga cewa "ki gaya min shi kika sha fateema?" kasa cewa komai tayi sae jujjuya kanta da take cikin axaba, ya ga farar takardar scan din dake gabanta ya dauka da sauri hannunsa na rawa ya bude, jefar da takardar yyi ya fixgota cikin mugun tashin hankali yace "wayyo fateema ki gaya min magungunann nn kika sha? Plss kiyi min mgna," a rude yake maganar, ita ko da kyar ta shiga gyada masa kai tana jawo numfashi kmr me shirin suma, ya dafe kansa yana kallonta yace "nashiga uku, oh my God," saketa yyi da sauri ya fice daga dakin, ta dinga ihu tana birgima cikin axaban ciwo tana kiran Abbanta, ya dawo dakin da sauri rike da allura, kwance ya ganta cikin jini, yyi wani kara a rude ya jefar da alluran hannunsa ya karaso kusa da ita da sauri yace "ya salam, innalillahi wa inna ilaihi raji'un, fateema fateema" kuka take ssae tana juye juye kmr ranta xae fita jini sae malala yake ta kasanta, ya dagota ya kai mata wani wawan mari a gigice ya shaketa yace "kika kashe min yarana, yhu kill my kids" ta kankamesa tace "wayyo mutuwa xanyi na shiga uku," wani marin ya kuma kai mata ya dagota ya buga ta da bango, tunda take bata taba ganin yanayin da Aliyu ya shiga ranan a tare da shi ba, idonsa ya kada yyi jajur muryarsa na rawa yace "ki gaya min ubanwa ya baki maganin nn, wani asibiti kika je," ya wurgar da ita ya buga bango da hannayensa biyu yace "ya salam," juyowa taga ya sake yi ta fara kkrin fita daga dakin ya fixgota ya shaketa yana huci yace "me yarana suka maki kika kashe su fateema," ta rike hannayensa biyu cikin kukan tashin hankali tace "no plss kayi min rae ya Aliyu cikina xae kasheni," bugata yyi da bango da karfi ya fice daga dakin tasan be gama da ita ba, tayi karfin hali ta rarrafa ta fito daga dakin da kyar tana neman inda xata safeena ta fito da sauri ta ja ta suka shige dakinta ta rufe kofar da sauri, inteesar ta xube kasan dakinta tana mayar da numfashi har lkcn jinin dake xuba jikinta bae tsaya ba . Aliyu ya fito kmr wani mahaukaci daga dakinsa ya shiga nata a rikice bae ganta ba, ya fito ya shiga buga kofar Safeena da karfi ganin trace din jini tun daga kofar Inteesar har nata, alamar nn inteesar ta shiga, cikin tsawa yace "baxa ku bude min kofar ba" cikin sanyin murya Safeenah tace "haba dear ka sa ma xuciyarka ruwan sanyi mana, so kke kayi kisan kai, ka bar ta da halin da take ciki mana xaka dinga dukanta kuma," ya daka mata wani raxanannen tsawa yace "na rantse da wanda numfashina ke hannunsa idan ban hada dake ba kada Allah ya bani abinda yake nema, baxxa ki bude min kofa ba" ya karasa maganar yana huci, ta bude baki da mamaki tana kallon kofa, A'aaah lallai abun babba ne yau, to fa, ta dan tabe baki tace "to ni ko sae dae kar ya baka, don baxan tsaya hka kawae ina ji ina gani ka kashe yar mutane gabana ba," bae sake cewa komai ba ya juya da sauri kmr xae tashi sama ya koma dakinsa yana huci, inteesar kam na durkushe dakin sae kuka take tana juye juye kmr ranta xae fita, kila karshenta ne ya xo yau, gashi har lkcn jini bae tsaya mata ba sae bulbulowa yake, duk kayan jikinta ya baci da jini hka ma dakin safeena, safeena ta dauko Zaninta da sauri ta mika mata a xuciyarta tana cewa "yau ai sae dae jininki ya tsiyaye ki mutu yarinya baxan bude kofar ba bare ya taimaka maki," inteesar ta kasa karban xanin, sae cewa take mutuwa xanyi, safeena tace "baxa ki mutu ba," key suka ji Aliyu ya saka a kofar, Inteesar ta fasa ihu jikinta na rawa taji kmr ta sume ynxu ta samu saukin abubuwan dake faruwa ynxu "wayyo kayi min rae ya Aliyu wlh yau mutuwa xanyi, don Allah kaji tausayina" ya afko dakin rike da kwalin tabs din da ta sha yana huci, idonsa ya koma jajur kmr gauta, kanta yyi ya fincikota da karfi ya dago ta, muryarsa na rawa yace "wllh wllh baki gaya min wanda ya baki magungunan nn ba, sae na kashe ki kema yau," jikinta na rawa ta shiga girgixa masa kai hawaye na bin kuncinta, ya shaketa da karfi, cikin tsawa yace "baxa ki gaya min ba," ta yo waje da ido a tsorace, da kyar muryarta a shake tace "xan gaya maka," ya watsa mata mari yace "uban me kike jira," ta fashe da wani matsanancin kuka ta juya tana kallon safeena tace "ita ce ta kaini aka bani," Safeena ta yo waje da ido ta dafe kirjinta tace "na shiga uku yarinya xata min sharri, a ina kika ganni," cikin kukan Axaba Inteesar tace "ita ce ya Aliyu, ka tausaya min cikina kasheni xae yi wllh," a hankali Aliyu ya saketa ta sulale kasa ya juya yana kallon safeena da ta xama kmr mara gskyar gske, duk ta rude, sae rawa bakinta yake ta kasa cewa komai, ta fashe da kuka tace "wllh wllh sharri tayi min Aliyu, a ina ta gan ni yau da har xan kai ta a bata magani," wani kara yyi ya karasa kusa da safeenar kmr xaki ya shaketa hawaye cike idonsa yace "ku ka kashe min yarana, me suka maku safeena," bae jira me xata ce ba yyi wani irin buga kanta da bango ya saketa yana huci, sae ga jini, a hankali ta sulale kasa ta fadi sumammiya a wajen, juyawa yyi bae sake ganin Inteesar ba a dakin . Inteesar na fita daga dakin dama falo ta sauko tayi hanyar kofar fita waje da sauran karfinta don dk jikinta yyi weak, tana isa tsakiyar falon jiri ya debeta ta xube kasa ta kasa tashi kuma, dae dae nn shima ya sauko kmr an hankadosa ta fasa wani gigitattcen ihu ta fara kkrin mikewa tsaye amma ta kasa cikin kuka ta dinga cewa Noo plss ya Aliyu ka tausaya min," ganin ya yo kanta ne yasa ba tare da ta shirya ba ta sulale wajen sumammiya, ya xube gabanta ya kife kansa kan tiles cikin tashin hankali yace "Nooo" da kyar ya dago kansa yana kallonta hawaye kwance fuskarsa, ya dagota ya rungumeta muryarsa na rawa yace "y fateema, meyasa xaki min hka, me yaran nn suka yi maki kika gwammace ki kashesu, y?" ganin har lkcin jini bae tsaya mata ba yasa ya dauketa da kyar ya haura sama da ita ya bude dakinsa ya kwantar da ita yana tunanin me xae mata, duk wata baseera ta bace masa kmr ba likita ba ya rasa yanda xae yi da ita sae bincika ruwan allura yake ya rasa wanne ma ya kamata yyi mata, da kyar ya jawo wayarsa jiki ba kwari ya shiga neman nmbr wani abokinsa doctor yaji a kashe, ya kira Dr maryam ma yaki shiga, hkn yasa ya kira nmbr faruuq bugu daya ya daga, da kyar ya iya cewa "plss faruuq ka taho gidana ynxun nn i need yhu help," ya katse kiran ya ajiye wayar har lkcn inteesar na jikinsa, ko minti sha biyar bae cika ba faruuq ya iso gidan don a xatonsa Aliyun ne bae da lfya, yana shiga compound ya kira Aliyu yace gashi nn ya xo, Aliyu yace ya shigo falo ya hayo sama, bbu abinda ya daga ma faruuq hankali illa ganin jini da yyi ta ko ina a gidan, kasa karasa cikin dakin yyi bayan ya bude dakin Aliyu, har lkcn kuma yana rungume da inteesar jikinta duk jini, da kyar faruuq ya iya cewa "meye hka Aliyu, me ya sameta," Aliyu ya kasa cewa komai sae girgixa kansa da yake, faruuq yyi karfin hali ya karasa cikin dakin yana kallon Inteesar xuciyarsa na bugawa, da kyar 4 d second tym ya sake cewa "me kayi mata Aliyu," Aliyu yyi karfin halin cewa "Abortion tayi faruuq, she killed my children," hawaye ne ya biyo bayan maganr tasa, Faruuq yace "innalillahi wa inna ilai'hi rajiun, ix she alryt, suma tayi ko me, she's still bleedn" ya karaso gabansu da sauri ya durkusa ya daga hannunta yana feel din pulse dinta, ya sauke ajiyar xuciya snn ya karbeta daga hannun Aliyu ya kwantar da ita, yace "kana da kayan aiki ne a gida," Aliyu ya nuna masa inda komai yake, ya shiga hada alluran da xae mata da sauri, da kyar ya samu jinin nata ya tsaya, shi dae Aliyu kallonsu kawae yake yana gefe xaune, faruuq yace "ka gyara mata jiki sae ka mayar da ita kan gado, bari naje xan siyo drip din da xan hada mata," Aliyu bae ce masa komai ba ya fice da sauri, da kyar Aliyu ya iya tashi ya tafi dakinta ya dauko mata wani kayan da abubuwan da ya kamata, ya koma dakinsa ya shiga gyara mata jikinta har ya gama ya sauya mata wani kayan ya dauketa ya kwantar kan gado, snn ya shiga aikin goge gogen jini a gidan, a hka faruuq ya dawo ya samesa, faruuq ya gama mata duk abinda ya kamata snn ya fito yana tambayar Aliyu safeena fa, Aliyu dake xaune ya takure a falo xaxxabi na neman rufesa dakyar yace ka duba nxt room din i thnk ita ma suman tayi" faruuq ya tsaya kallonsa ya kasa cewa komai, ya juya ya shiga dakinta ita ma yyi mata duk abinda ya kamata ya fito yace Aliyu yaje ya mayar da ita kan gado. Har dare inteesar bata farfado ba, safeena kam an farfado amma bata yi gigin fitowa ba ba karamin fashewa kanta yyi ba ta dinga kuka ita daya a daki faruuq ya shigo gidan bayan sllh magrib ya shiga ya duba inteesar ya sauko yana kallon Aliyu yace dole sae an kara mata jini, Aliyu bae yi masa musu ba suka tafi asibiti aka diba jininsa don dai dai ne da nata, shi dae komawa yyi kmr wani mara lfya suka dawo gida faruuq ya sa mata jinin, ko da faruuq ya bude dakin safeena bae ganta a ciki ba, ya sauko kasa yana gaya ma Aliyu, Aliyu yace "tafita knn," ita ko tana jin fitarsu dama tayi gidansu ba shiri. A daren Aliyu ya tafi gida, yasa Abbansa a gaba kmr wani karamin yaro yana hawaye ya gaya masa abinda inteesar tayi, Abba kasa yrda yyi, hka ma Haisam dake falon duk jikinsu yyi sanyi, Abban yace "ita fateemar, innalillahi wa inna ilaihi raji'un" frm no where suka ji muryar inna tana salati tashigo falon Abba da gudu kmr an jefota a rude tace "Bukar Bukar wae ji nayi ance Inteesar ta xubar da cikin jikinta," duk suka yi tsit suna kallonta, a fusace tace "kuji min mutane kmr kurame, wae ba magana nake maku ba xaku mayar dani yar iska" Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "nima ynxu Aliyu ya xo yake sanar min," inna ta fasa ihu tare da fashewa da wani matsanancin kuka ta daura hannu a ka tace "wayyo na shiga uku ni Rahmatu, amma wnn anyi gantalalliyar muguwar yarinya, don ubanta dan nawa ta xubar, tasan burin da na ci akan dan nn," Aliyu ya mike da kyar yana kallon Abba muryasa can kasa yace "sae da safe Abba," inna na huci tace "maxa muje ka kaini wajenta ynxu" Abba yace "A'a baaba, gobe ya taho min da ita ko. Karfe goma da rabi Aliyu ya shigo gida, ya kulle gidan ya haura sama a sanyaye ya bude kofar dakinsa ya shiga, kwance ya tarda ita idonta biyu, ledan jinin hannunta ma kiris ya rage ya kare, kallo daya yyi mata ya dauke kansa, ya cire shirt din jikinsa da dogon wando, ya rage daga shi sae singlet da gajeran wando, ta dauke kanta a hankali ta lumshe idonta, bae taba tsayawa gabanta hka ba sae sau daya, ya karasa kusa da ita ba tare da ya kalleta ba cire mata alluran hannunta ya soka jikin ledan jinin ya xaga yyi kwanciyarsa can karshen gadon ya juya mata baya, ita kadae tasan me take ji a jikinta, ko ina na jikinta ciwo yake mata, gashi har lkcn marar ta bae dena damunta ba, ga mugun yunwar da take ji, don rabonta da abinci tun safe, a hankali ta fara kkrin sauka daga kan gadon ko tea ta hada ta sha don yunwar yafi karfinta, jiri ya debeta ta xube kasa, ya juya da sauri yana kallonta sae kuma ya dauke kansa, ta fara kkrin mikewa amma ta kasa, a hankali muryarta na rawa tace "yunwa nake ji ya Aliyu," ya juya yana kallonta kmr ya rufeta da duka ya girgixa kansa xuciyarsa na suya, cike da takaici yace "ta kasheki," snn ya juya yyi kwanciyarsa. Da rarrafe ta fita daga dakin ta shiga nata ta hada tea jikint a na rawa, amma duk yunwan da take ji sae ta kasa shan tean, hka ranan ta kwana a wahale. Washegari monday bbu yabo bbu fallasa ya shigo dakinta da safe yace ta shirya xasu gida, gabanta ya shiga faduwa, tana kallonsa daga kwancen da take tace "baxan iya ba ya Aliyu" wani tsawa ya daka mata yace "kada Allah yasa ki iya din, jahila kawai, Allah ya baki sa'a na dawo naga baki shirya ba," ya fice daga dakin, kuka ta shiga rerawa a hankali, ta kasa tashi daga kan gadon duk jikinta yyi tsami, cikin ikon Allah ta mike da kyar ta shiga ta wanke baki ta canxa pad, don bata da karfin wanka, ta fito jikinta na rawa ta xura doguwar rigarta snn ta saka hijab ta sauko yana falo yana jiranta bae ko kalleta ba ya mike yyi hanyar fita tana biye da shi a baya kmr iska xae kadeta ta fadi, duk tayi mugun rama daga jiya xuwa yau, a sanyaye ta bude bayan mota ta shiga bae ko kalleta ba ya shiga driver sit ya ja motar suka fita daga gidan, har suka isa gida bae ce mata ba ita ma bata ce masa ba, gabanta ya shiga faduwa don bata san me xata shiga ta tarar ba, da kyar jikinta a mace ta fito daga motar ta jira shima ya fito, bae ko kalleta ba ya nufi gate xuciyarta na harbawa da sauri da sauri ta bi bayansa suna shiga gidan falon abba taga ya nufa, ita dae tana ta biye da shi a baya kmr jela, a bakin kofar Abba suka ci karo da momy xata fito daga falon, inteesar ta koma baya da sauri kuma a tsorace, momy ta bi ta ta cafketa, ihu ta fasa a tsorace momy ta shiga xuba mata mari tana duka kmr an aikota, kuka ta dinga rusawa tana ihu a gidan Abba ya fito da sauri yana kallon momy a fusace yace "kina da hankali kuwa Zainab, meye hka kike yi," ko kallonsa bata yi ba sae jibgarta take tana tumble da ita, ita ko bata fasa ihu da kukan da take ba, Aliyu ya dauke kansa ya koma gefe ya tsaya ya lumshe idonsa, su Hajiya da umma duk suka fiffito daga dakunansu su Rahma duk sun tafi sch, duk irin masifar da Abba ya dinga yi ma momy ransa a bace kan ta sake inteesar kin sakinta tayi, har sae da ta kai ta kasa, su Hajiya da umma dae na tsaye sae murmushi suke, Hajiya na cewa "to wnn abu dae idan bakintsa mata aka yi ba taya yar mitsitsiyar nn tasan wani cire ciki" daga nisa suka ji Muryar inna tana tahowa da gudu tana cewa "muryar waye nake ji hka kmr ta Inteesar uban me ake mata," ta karaso tana haki, tana ganin abinda momy ke yi ma inteesar tayo waje da ido ta fasa ihu "meye hka xan gani Zainabu, akuya kika samu ko me? kashemin ita xakiyi don uwarki," sae a snn momy ta saketa, inna ta fashe da kuka tana kallonsu gaba daya tace "amma dae Allah ya isa ban yafe maku ba, ynxu Bukar har da kai aka taru xa a kashe yar mala'ikan Allahn nn don ta xubar da wani wahalallen cikin Aliyu dake neman aikata lahira, to duk shegen da bae fasa dukanta ba bae haifu cikin uwarsa ba " ta dago inteesar dake ta rusa kuka ita ma tana nata kukan ssae tace "Allah ya isar maki kuma ciki kin isa ne yasa kika xubar da shi, mu je ga ruwa can na daura xan maki wanka" taja ta tana dingishi suka yi sashinta tana huci, Aliyu ya juya yana kallon Abbansa da ya bi su da kallo shima, snn ya girgixa kai kmr xae hadiye xuciya yyi hanyar fita daga gidan Abba ya kirasa. Allah sarki Babana Aliyu, but ol d same Allah shi kara, na ma tuna ko waye kai da. . Inteesar na xaune falon inna tana cin tuwa da lafiyayyan miyan vegetable da inna tayi mata yaji nama da kifi da ganda, sae tura abunta take, ga farfesun kayan ciki da na kai gabanta ga fura mae sanyi shima duk a gabanta, inna ko na xaune gefenta tana tayi mata hira tana kyalkyala dariya, inteesar dae hankalinta na kan abincinta har ta manta rabon da ta ci tuwo sae indomie kmr mayya kullum, tun safe da inna ta ja ta tayo sashin ta da ita bbu wanda yaga fuskar xuwa ya samesu har Abba, Aliyu kam Abba ne ya hanasa xuwa don yasan halinsa, Haisam ma baram baram suka yi da inna daga yaxo yi ma inteesar fada, ransa a bace ya bar falon, sallamar faruuq yasa inteesar ta jawo hijabinta da sauri don daga ita sae yar shimi, suka amsa masa sallaman inna na washe baki ya nemi guri ya xauna ya gaida inna ta amsa cike da jin ddi ta mike ta kwaso masa lemo a fridge dinta, inteesar ta gaishesa tana murmushi ya amsa ba tare da ya kalleta ba, tace "ya faruuq Zainab fa?" yace "tana lfya," ta ci gaba da cin tuwonta inna nata yi masa hira mara tushe sae binta yake da uhm, sae da ya jira don kanta tayi shiru snn ya hade rae yana kallon inteesar yace "inteesar wajen ki naxo," ta dago tana kallonsa hka ma inna, yace "am vry disappointed in yhu inteesar, never knew yhu 2 b foolish...." da sauri inna tace "meye wnn kke cewa, ka fada wanda xanji mana," ya juya yana kallon inna yace "Haba inna, ynxu abinda inteesar tayi ta kyauta knn da ba ki son a mata fada, rae biyu fa ta hallaka dan wauta irin nata, kuma ace baxa a mata magana ba" a fusace ya karasa maganar, inna ta dafe kirji kmr xata yi kuka tace "rae biyu fa kace, dama yan biyu ne knn?" faruuq yace "au ke da duk abinda ake baki sani ba inna," inna tayi narai narai da ido tace "ni ina nasani, ynxu yan biyu ta xubar faruuq, ko daya bae rage ba," ta juya tana kallon inteesar dake ta tura tuwanta abunta fuskarta a daure, can ta juyo tana kallonsa tace "to hka Allah ya kaddara sae a dau na annabi, yarinya dae bata gama mallakar hankalinta ba bare ace xa a mata fada ynxu, kawae sae dae ace Allah shi kyauta, su kuma Allah ya ji kansu," faruuq don takaici kasa cewa komai yyi, can dae yace "meyasa xaki dinga cewa hka inna, inteesar din ce yarinya ynxu," inna ta hade rae tana kallonsa tace "naga dae alamar kaima ka fara xama munafuki, tashi ka ban waje idan har wnn maganar ce ta kawo ka, to jefar da ita kuke son nayi kome, dama Allah yyi yaran baxa su wuce wata uku a cikinta ba, don hka ku shafa ma jikata lfya" faruuq ya mike ransa a bace yace "to inna, Allah ya baki Hkuri ni xan koma," tace "eh Allah ya kiyaye," ya juya ya fice daga falon, inna ta ja dogon tsaki tace "munafukan bnxa kawae, ci ki koshi kije ki kwanta ina fatan dae jinin ya tsaya gaba daya ynxu." Da daddare inteesar na kwance gefen inna duk da fankan dake aiki a falon tana tayi mata fiffita suna hira, Abba yyi sallama, inteesar ta mike xaune da sauri tana kallon inna, inna tace "tsaya tsaya kar ka shigo min," ta juya tana kallon inteesar murya kasa kasa tace "maxa tashi ki shiga daki," da gudu inteesar ta shige daki ta rufe kofa, inna ta rungume hannuwanta tana sakace hakori tace "yauwa xaka iya shigowa" Abba ya shigo dakin da sallamarsa ya xauna ya gaidata yana kallonta, ta amsa bbu yabo ba fallasa, yyi shiru na kusan minti biyar snn yace "baaba fateema fa" inna ta hade rae tana kallonsa tace "ya aka yi," cikin fada Abba ya fara magana "haba baaba, ni ynxu kina gwada ma yaran nn bani da iko da su ne kome, ya yarinya tayi laifi irin wnn nasa a kawo min ita gida ki kunshe ta a daki bbu wani bayani, kuma ke ba yi mata xaki yi ba, ynxu kina gwada mata abinda tayi tayi dai dai knn kome," inna ta marairaice ganin yanda ransa ya baci tace "to wae Bukar maganar nn bata wuce bane ko me, naga dae ya ya ba dawowa xasuyi ba," Abba ya shiga kiran inteesar a fusace "fateema fateema," kmr munafuka ta fito da hijab har kasa, inna se ca take baxata fito ba koma inteesar, Abba yace "maxa ki wuce falona ki jira ni," a fusace yyi maganar don hka bata saurari inna ba ta fice kmr munafuka gabanta na faduwa, inna tace "to wllh sae na bi ku," bae tanka ta ba ya fice, ta fixgi gyalenta da sauri ta fice ta bi bayansu, gaban inteesar yyi mugun faduwa ganin su Hajiya da ma momynta har ma da Anty nafeesa da ta bi ta da harara a falon ashe ta xo gidan, ko inna ma bata sani ba, inteesar ta saci kallon Aliyu dake xaune gefen Haisam, ta rasa inda xata xauna don kowa haushinta yake ji a falon, Abba ya shigo ya xauna yana kallonta ta sunkuyar da kanta har lkcn tana tsaye, cikin ikon Allah sae ga inna ta shigo falon tana haki, tana kallon Hajiya tace "ke tashi ki ban waje in xauna," Hajiya bata yi musu ba amma in ranta yyi dubu ya bace, ta mike inna ta xauna tace "xo xauna nn inteesar," inteesar ta xauna gefen inna, Hajiya kuma ta nemi wani wajen ta xauna ranta a bace. Inteesar ta daga kai a hankali ta saci kallon Aliyu taga kallonta yake, duk ya koma kmr wani mara lfya, ta dauke kanta da sauri shima hka . A nutse Abba ya kira sunanta "fateemah," ta dago a hankali tana kallonsa, ya sauke ajiyar xuciya yace "ko da yake ma bari na fara ta kanki baaba," inna na kallonsa tace "eh ina ji," yana kallonta yace "Baaba kar ki fara magana nn ba tare da ance kiyi ba, duk me xaki ji a nn don Allah karki bude bakin ki, idan ana bukatar cewar ki xa'a sanar da ke, don Allah dae nace," inna ta tabe baki tana girgixa kafa, ya maida dubansa ga Inteesar da ta sunkuyar da kanta yace "fateema," wnn karan kasa dagowa ta kallesa tayi, bae damu ba ya ci gaba "Ashe ke dama mara hankali ce bansani ba," inna tayi karaf tace "kmr yaya," Abba ya hade rae yana kallonta, ta daga hannu da sauri tace "to nayi shiru," Abba na kallon Inteesar yace "ynxu abinda nake so dake shine kawae ki gaya min asibitin da kika je," Hawaye ya cika idonta ta kasa cewa komai, cikin daga murya Abba yace "ba magana nake maki ba," a hankali Aliyu yace "ae Safeena ce tayi mata jagora wae," a fusace inna tace "ga magana nn xaku tsaya kuna wani lauyewa, ni dae nasan jikata baxata iya aikata wnn danyan aikin da kanta ba" Abba yyi shiru yana kallon Aliyu snn yace "kae wa yaga maka hka," Aliyu yace "ita da bakinta ta fada," inteesar ta watsa masa harara tace "ni ba muyi hka da kai ba, kuma safeena bata yi min ko wani jagora ba ni da kaina na tafi inda naje, hasalima bata sani ba," Aliyu ya yo waje da ido da mamaki yace "kika ce me?" ta xaro masa ido tace "ehh" ya dafe kansa yace "innalillahi wa inna ilaihi raji un, kika sa naje na ba yar mutane takarda ashe sharri kika mata" Abba yace "takardar ka kai mata?" Aliyu ya kasa cewa komai sae kallon inteesar da yake, a rude Hajiya tace "kana da hankali kuwa Aliyu, ka saketa fa kace?" Abba yace "saki nawa kayi mata," Aliyu ya sauke ajiyar xuciya yace "daya," snn ya ciro pen daga Aljihunsa ya mike ya shiga dakin Abbansa duk aka bi sa da kallo ya fito rike da farar takarda ya isa study desk ya duka xae yi rubutu Abba yace "meye hka kke yi Ali," ya dago bbu yabo bbu fallasa yace "ita ma rubuta mata nata xanyi Abba" Abba ya daka masa tsawa "kana da hankali kuwa, a gabana don baka da kunya xaka dauko takarda kana gaya min maganar bnxa," cikin daga murya Abba yace "dawo nn ka xauna," Hajiya tace "kambu, ae wlh baka isa ba Alhaji, ita wancan din da ya saka ance maka gata ne bata da, ae ita ma Wllh sae ya rubuta mata nata, na rantse," Abba ya mike a fusace yace "fice min a falo Aisha, nace ki fita," ta mike tace "ae ko baka fada ba fita xanyi, amma wllh kmr yanda tayi makirci tasa ya saki matarsa ta arxiki ita ma sae ya saketa, ae dama idan bata xama makira ba sae Allah ma ya tambayeta, abu a jini," ta fice tana huci, inna tace "shegiya yar wahala, ae in Aliyu ya saki Inteesar yau duk kuma sae nasa dana ya rubuta maku takardarku wllh wllh," inteesar ta fashe da kuka tace "Abba ni ka bar shi ya rubuta min takardata don Allah don Annabi," Abba ya daka mata tsawa a fusace "rufe min baki, stupid" Anty Nafeesa kam kasa cewa komai tayi sae kallon inteesar take, momy dama hankalinta na kan TV, Abba yyi shiru na wani dan lkci snn yana kallon Aliyu yace "sae kaje ka mayar da matarka," Aliyu bae ce komai ba sae da har lkcin kansa a kasa yake da ganinsa kasan ran maxa ya baci, Abba ya hade rae yana kallon inteesar yace "ynxu dalilin cire cikin jikinki kawae nake son ki gaya mana gaba daya mu ji," hawaye ya cika idon Inteesar tayi shiru kanta a kasa, har sae da Haisam ya daka mata tsawa, "ba magana ake maki ba," a fusace inna ta mike tace "ohh ni yau naga tsiya xasu kashe min jika, kuma sun hanani magana " ta fashe da kuka xata bar falon, Abba yace "haba baaba ki dawo muji daliin da yasa tayi hka, ae bbu wanda yyi mata wani abun a nn," da kyar aka lallaba inna ta dawo ta xauna tana share hawaye, Abba yace "muna jin ki Fateema," inteesar ta dago kanta a hankali tana kallon Aliyun, taga shima kallonta yake, ta kauda kanta tace "sbda bana sonsa shima kuma baya sona yasa nayi hkn Abba," ta fashe masu da kuka ssae tace "Abba tunda na taso ya Aliyu ke cutata a gidan nn, tun ban san kaina ba, ban san me nayi masa ba ko dan ba gidan ubana bne, ya tsaneni kuma baya son bude ido ya gan ni cikin gidansu, ko uwar da ta haifeni ma bae bari ba, idan an manta randa ya daga hannu xae mareta to ni ban manta ba, kuma har gobe baxan manta ba, ban san me muka yi masa ba, duka bbu wanda ban sha a hannun Aliyu ba, idan ba a manta ba wani rashin lfya da nayi na kwana da kwanaki shi shine sanadin sa, amma ban fada ma kowa ba, har ka hada mu aure Abba, kuma tunda ka hada mu abba ko sau daya ban taba jin ddin xaman gidansa ba, sae nayi sati biyu ban daura idona a kansa ba, bae san ci na ba bae san sha na ba, kullum a wahale nake cikin gidan, to a hka yake son na haifa masa yara, wllh Abba bana sonsa ka taimakeni kasa ya bani takardata ynxun nn, biyayya kawae yyi maka yake xaune da ni gida daya a matsayin matarsa," ta fashe da matsanancin kuka takasa ci gaba, tun da ta fara magana Aliyu ke kallonta baki bude. Ganinbbu wanda ya iya cewa komai a falon dondukjikinsu yyi sanyi ya sa inteesar ta tsagaita kukan da take ta cigaba "snn Abba ni bada yardana ya sake aure ba, hasalima ni ban san xae yi aure ba sae ranar da ya kawo ni gunka da daddare kke tambayata ko nasani, to a nn ne ma nasan aure xae yi, kuma dama tun a hanya yyi threatn dina kan cewar ko me xaka tambayeni nace nasani, kuma Abba har yau yaki daukar batun karatuna da muhimmanci da nayi magana sae ya dinga hantarata wae baxan iya course din da nace nake so ba, kuma Abba da yake cewa na xubar masa da ciki a tambayesa ko kula dani da cikin yake, Abba sae nayi kwana uku ban gansa ba gashi bbu abinda nake iyawa kullum a wahale nake kwana nake yini a gidan ga kuma yunwa, tunda ba iya girkin nake ba," tayi shiru tana share hawayenta snn a hankali tace "lastly Abba kayi hakuri ba rashin kunya nake maka ba, amma ka tausaya min kayi masa magana ya sauwaka min, don baxan koma gidansa ba wllh na gama aurensa," Aliyu ya mike yana mata wani mugun kallo yana huci yace "munafuka, makaryaciya kawae, ki xo ki shake ni na baki takardar taki kuma wllh sae kinyi da kin sanin xubar min da ciki," ya juya xae bar falon Abba ya dakatar da shi a fusace, inteesar ta fashe da kuka tace "wllh Abba kace ya bani takardata bana auren kuma, bana sonsa," Abba yana kallon Aliyu yace "dawo ka xauna," ya kai minti kusan biyar a tsaye kmr baxae xauna ba, sae da Anty Nafeesa tace "ba magana ake maka ba ka tsaya ma mutane kallon rainin wayo," ya juya ya kalleta, snn ya koma inda yake ya xauna yana ma inteesar wani irin kallon, da ganinsa kasan ran maxa ya gama bacewa, Abba yace "cikin maganganun da Fateema tayi a nn akwae wanda xaka karyata," ya kauda kansa bae ce komai ba sae huci da yake, Abba yace "gud, dama tun ba yau ba nasan halinka, na kuma san xaka iya aikata duk abinda fateema ta lissafo a nn, kai kam ban san wani irin mutum bne Aliyu, kuma gwara da Fateema ta gaya min abubuwan da ta dde tana boyewa a cikinta tana cutar kanta," ya juya yana kallon Inteesar yace "amma fateema ke abinda kika aikata a ganin kinyi dai dai knn, me xaki ce ma mahaliccinki, ashe dama karamin tunani gare ki ban sani ba" inteesar dai kanta na kasa tana hawaye ta kasa cewa komai, Abba ya ci gaba, "a nan kin nuna kmr rashin kulawar da yake nuna maki ne yasa kika aikata abinda kika aikata, to Fateema baki san hanyar gida bne, ko in kin xo akwae wanda xae ce maki don me" a hankali tace "Abba banyi wnn tunanin ba," Abba ya girgixa kai yana kallon Aliyu yace "to malam rubuta mata takardarta, Allah ya hada kowa da rabonsa, ni nayi kuskure tun farko na baka auren fateema duk da ka nuna min baka sonta" Aliyu ya juya yana kallonta, ita ma kallonsa take, ya maida dubansa ga Abbansa yace "srry ba rashin kunya nake mka ba Abba, amma taxo ta shake ni ta kwata, ko kuma ta saki kanta da kanta," yana kai wa nn ya mike yana huci xae bar falon, Abba ya daka masa tsawa yace "don uwarka ni nayi maka magana ko fateema" Inna ta mike a fusace tace "yau naga tsiya, yarinya tace bata son aurenka ka sallameta mana ko ana yi dole ne, ae ba rasa manema tayi ba, ko gobe ta fita titi santalelen yaro me katuwar mota wanda ya fi ka komai ne xae biyo ta wllh, yo tsami gaye da kai idan ba tsautsayi ba ma me xae kai ta aurenka sai tsayi ba hankali kmr bishiya," abun dariya abun takaici, a walakance Aliyu na kallon inna yace "ae sae ki rubuta mata sakin ki bata, ko kuma ku hadu ku shake ni ku karba," yyi tsaki a fusace ya juya xae fita Abba yace "kar ka kuskura ka fita daga falon nn, kanka rawa yake Aliyu, ita mahaifiyar tawa kke gaya ma magana" inna ta fashe da kuka tace "yo sabon abu ne wnn, ae sae Allah ya mana hisabi da Aliyu" Haisam ya mike ya fice daga falon, hkn ma Momy, ran Abba a bace kuma a nutse yana kallon Aliyu yace "bani takardar Fateema ynxun nn Ali kar na nuna maka d odza side of me," cikin tsawa ya karasa maganar, Aliyu yyi shiru yana kallonsa yana huci, inna tace "ba magana ake maka ba salubabbe kawae," ya juya yana kallon inna tace "daina kallona Munafuki kawae," inteesar dae kanta na kasa, ya juya ya kalleta snn yyi huci me xafi ya ciro takardar da ke Aljihunsa da pen ya daura takardar kan hannun sofa, snn ya duka ya fara rubutu a jiki. Inteesar ta dago a sanyaye tana kallonsa hawaye na bin kuncinta, Abba ma kallonsa yake ko kiftawa baya yi, hka ma Anty Nafeesa, inna tayo waje da ido ta dafe kirji tace "lah rubutawa xae yi Bukar" . .. Inna ta fashe da kuka ta mike tsaye tana cewa "Bukar kayi shiru, kaga fa rubutawa yake, lah ha ila ha ilallahu mahammadur- rasulillahi sallallahu alaihi wassallama, Bukar kayi wani abu mana" Abba kam kasa cewa komai yyi sae kallon Aliyun yake, Anty Nafeesa ta jinginar da kanta jikin kujera tana kallon ikon Allah, har Aliyu ya gama rubutunsa ya mayar da pen din cikin aljihunsa yana kallon Abbansa yace "gashi nn na rubuta mata," Abba yyi murmushin takaici yace "to ka kyauta," ya dauke kansa ya shiga linke takardar neatly yana kallon inteesar dake kallonsa har lkcn tana hawaye, ya karasa gabanta yana mata mugun kallo ya jefa mata takarda snn ya juya xae fita inna ta bi sa da gudu ta cakumi kwalarsa tace "don uwarka jikartawa ka mayar baxawara, to Allah ya isa bamu yafe maka ba, sae Allah ya saka mana," Abba yace "ki rabu dashi baaba," inna tace "naki din, dama nasan har da hadin bakinka ae," ta fashe da wani matsanancin kuka ta xube wajen tana daddaga hannu sama, Aliyu yyi yar dariya rainin wayo ya juya ya fice daga falon, sae a snn umma dake xaune har lkcn bata ce komai ba ta mike ta bar falon xuciyarta fal murna don dama abinda take jiran gani knn, kuma ta gani, ynxu kuma xa taje tayi break din ma Hajiya gud News din, Abba ya sauke ajiyar xuciya yana girgixa kansa, Anty Nafeesa ta mike ta nufi gaban inteesar ta dauki takardar da Aliyu ya jefa mata ta koma ta xauna tana warware wa, inteesar kam hade kanta tayi da gwiwa tana rera kuka a hankali, Anty Nafeesa ta gama karanta content din takardar ta ajiye kan kujera kusa da Abba ta mike ta fice daga falon, inna ta mike ta dago inteesar tace "tashi mu je, sae me don ya sake ki, abinda ynxun nn kina fita masu mota xa su biyoki, uban waye xae kalleki yace kin taba aure idan ba dan bakin ciki ba, ae gwanda da kika kwabar da cikin don da ganin jarababbun yara ne, mu je kawae Allah ya isar mana" sae a snn inteesar taji sanyi ta mike tsaye inna ta shiga share mata hawayenta, Abba kam idonsa na kan takardar da Nafeesa ta ajiye masa bayan ya dauka, yana gama karanta cntent din ya sauke ajiyar xuciya tare da jinginar da kansa jikin kujera yace "gashi nn fateema," inna ta ja hannunta xasu fita tace "rabu da shi da'alla muje me xaki yi da shi su da suka sa shi ya sake ki ae sae su cinye," Inteesar ta kasa bin inna ta koma a sanyaye ta karbi takardar a hannun Abba, Abba yace "kiyi hkuri Fateema ni na ja maki komai," ta kirkiro murmushi ta karbi takardar inna tayi tsaki ta ja ta suka fice daga falon tana cewa "yo idan bata yi hkurin ba ya ake son tayi dama bayan an gama cutarta," inteesar dae jikinta a mace suka isa falon inna, inna ta karbe takardar hannunta da ta kasa dubawa har lkcin, tayi michi michi da ido tana kallon rubutun ita nn karatu take kmr tasan me aka rubuta jikin takardar tayi tsaki ta cukuikuye takardar ta jefar bakin kofa tace "shege kawae rubutun ma kmr ta agwawa," ta juya tana kallon inteesar da ta xauna kan kujera ta kura ma TV ido tace "maxa je ki kiyi wanka ki xo ki kwanta, kar ki sa komai a ranki kinji" a sanyaye inteesar ta mike ta shiga dakin inna tayi kwanciyarta kan gado kawae don baxata iya yin wankan ba. . Washegari da safe inna na share falo ta ga takardar da ta jefar bakin kofa, tace "na share wn shegen takardar Inteesar," inteesar da har lkcn ke kwance a daki tayi shiru kmr baxata ce komai ba sae kuma tace "ki ajiye kawae kar ki share," inna na gama sharan ta hada mata ruwan wanka ta kai mata bayi duk tana kwance, inna tace "maxa ki tashi kije kiyi wanka kadda ruwan ya huce," ta mike xaune da kyar ta fara cire kayan jikinta xata shiga wankan inna tace "to me xan hada maki na kalaci kan ki fito," inteesar ta dan yatsine fuska tace "ni waina kawae xa a siyo min," inna tace "yo ae wnn ba wani abu bne bari na kira kursum kan su tafi makaranta su siyo maki," inteesar na shiryawa a dakin inna taji muryar momynta ta xo gaida inna, ta hanxarta ta gama abinda take ta fito da sauri don ta gaidata don ba xuwa sashinsu xata yi ta jibgeta ba, gefen inna ta xauna tace "ina kwana momy," ba tare da ta kalleta ba ta amsa da "lfya lau," inna tace "ya kina amsa mata kmr ana tilasta ki," momy ta dan yi murmushi ta mike tsaye tace "bari naje na gama kimtsa ihsaan inna," inna ta tabe baki bata ce komai ba momy ta fice, inna tace "wannan wannan da ba dan a gabana ta haife ki ba da sae nace ba uwarki bace, bata sonki ko kadan, to wae da wanne xaki ji," inna tayi tsaki tace "Allah shi kiyaye," inteesar dae bata ce komai ba tana ta kallo abinta, can ganin inna tayi shiru yasa tace "inna ni ina son xuwa gida in kwaso kayana bani da kaya ko daya a nn da xan sa," inna tace "Aa ba sae kin je ba, xan sa su kursum su je su kwaso maki kawae, me xae kai ki gidan nn kuma" inteesar ta hade rae tace "to sanin me da me xasu kawo min xasu yi, ni wllh da kaina xanje bbu wanda xae je dauko min kayana," inna ta bude baki tana kallonta, can ta rufe bakin tace "ke dae wahalalliya ce wllh, don ubanki idan kika je kika hadu da shegen kiyi ya?" inteesar tace "meye ruwana da shi an dde bamu hadu ba, bari ma kiga ynxun nn xan shirya na tafi wllh, kuma kiyi ma Abba maganan yaushe xa a kwaso min kayan dakina gaba daya" inna tayi shiru tana kallonta snn ta tabe baki tace "to ni dae ba ruwana, ki tsaya kuma ki karya," waina uku inteesar taci ta wanke hannunta tace ta koshi, inna tace "to ni dae banda ko sisin da xan baki kudin mota," inteesar tace "ai kam sae ki nemo shi don nima bani da kudi," inna tace "bari naje gun Zainabu na ranto dari biyar to," inteesar tace "oho ni dae ki nema ki bani, kuma fa karki ce mata nice xanyi amfani dashi" inna tace "to," snn ta fita xuwa ranto dari biyar, ko minti goma ba ayi ba ta dawo rike da dubu daya tace "gashi nn har dubu daya na samu," inteesar tace "yauwa innata shi yasa nake son ki," ta karbe kudin ta saka takalminta ta fice daga gidan inna ta rakata har gate snn ta koma ciki. A dai daita sahu ta dauka har gidan, tana sauka ta tambayesa nawa xata bashi yace "dari biyar," bata damu ba ta mika masa dubu dayan ya bata canji, ta juya tayi hanyar gate, tana danna bell maigadi yace "waye," tace "ka bude min malam," ya bude gate din ta shigo tayi balcony abunta, bude ta tarar da kofar shiga falon, ta shiga cikin falon tana kalle kalle, kamshin soye soye ke ta tashi a kitchen din ta dan karasa kitchen din a hankali ta leka, taga Safeena ce ke ta soye soye tana waka, ta dan tabe baki tayi hanyar stairs duk cikin sanda take tafiyar, a hankali ta bude kofar dakinta ta shiga ta rufe snn ta sauke ajiyar xuciya, ta shiga bude boxes dinta tana cire kayayyakin da xa ta dauka, a dan babban box ta shiga xuba kayan, ta kwashe kayan make up dinta da turarruka duk ta xuba ciki har da jewelries, snn ta koma kan takalma suma ta fara xaban wa inda xata dauka, kofar ta taji an bude, ta juya a tsorace suka yi ido hudu da Aliyu, gabanta yyi mugun faduwa ta dauke kanta ta dake ta cigaba da harhada kayanta, shi ko ya rungume hannayensa ya jingina jikin kofar ya harde kafaffunsa yana mata wani irin kallo yana murmushin mugunta, da kyar ta gama kwasan abubuwan da xata kwasa don duk gabanta faduwa yake, ta xuge xip din ta daga akwatin, snn ta dauki hijab dinta ta sa, ta shiga jan akwatin tayi bakin kofa, tana isa bakin kofar ya sauke kafarsa, ya gyara tsayuwarsa a bakin kofar, ta hade rae tace "xan wuce. Aliyu yyi murmushi yana kallonta daga sama xuwa kasa yaki cewa komai kuma yaki bata hanya, ta hade rai tace "Magana fa nake, ka bani hanya in wuce," yyi dariya irin ta mugunta yace "bi ta kaina ki wuce," ta galla masa harara a fusace tace "wnn wani irin iskanci ne, ka bani hanya nawuce mana," ya fixgota yana mata wani shu'umin kallo, ta tsorata ssae, ya shigo dakin yana rike da ita ya kulle kofar tare da sa key, ta yo waje da ido a tsorace, a hankali ta saita muryar ta dan marairaice masa tace "Haba ya Aliyu me hka kke yi, kaji tsoran Allah mana wnn ba girmanka bane," ba karamin dariya ta basa ba, don bae san lkcn da dariyar ma ta kubce masa ba, tayi tsaki ta buge hannunsa daga rikon da yyi mata ta rike handle din akwatin ta xata yi hanyar kofa, ya fixgota yace "ae in kin ga kin bar gidan nn yau to wasu yan biyun sun dasu a mahaifarki ne," tace "auxubillahi minash shaidanir rajeem, meye hka kke cewa ya Aliyu," dariya yyi yace "ae sae dae kece shaidaniyar a cikin dakin nn," ta fashe da kuka tace "me yasa xaka dinga abu kmr ba musulmi ba, ni don Allah kaji tsoran Allah ka rufa min asiri ka bar ni na fita," yyi murmushi yace "iyye, sannu musulma me tsoran Allah" tayi tsaki ta turasa da karfi ta ja akwatin ta, ya kuma fixgota ya jefar da ita kan gado, a gigice ta fashe masa da kuka tace "na shiga uku na lalace, wayyoo Abbana don Allah ya Aliyu ka bari," ta mirgina ta dayan side din da sauri ta sauko daga kan gadon tayi hanyar bathroom da gudu, ya sha gabanta yana mata wani irin kallo yace "in ma xaki tsaya ki tsaya kar na wahalar dake," ta durkushe wajen ta fashe da wani matsanancin kuka tace "wayyoo Allahna na shiga uku, don Allah ya Aliyu kaji tsoran Allah ka kyaleni in fita," dagota yyi ya jinginar da ita jikin bango yana mata wani irin kallo ya cire hijab din jikinta ta shiga dukansa tana kiran inna, wani gigitattcen mari ya kai mata nn da nn tayi still marin har cikin kwakwalwarta, riga da xani ne jikinta ya cire xanin, ta rumtse idonta jikinta na rawa hka ma muryarta tace "wayyo Allahna, ya Aliyu" wani mahaukacin kiss ya shiga mata kmr xae cinyeta, jikinta sae rawa yake kuma bata yi gigin hanasa ba, ya dauketa cak ya kwantar kan gado ya rabata da kayan jikinta ya shiga mata abubuwa masu rikita lissafi, nn da nn ita ma ta fara dauke wuta, da kyar ta shiga turasa muryarta na rawa tace "ka bari ya Aliyu, bana so, tsoro nake ji," bae ma san tana yi ba duk ya fita hayyacinsa, ya kankameta kmr mae rada dab da kunnenta yace "plss kar kiyi min kuka fateema baxa kiji xafi ba," jikinta ya dau rawa a tsorace tace "A'a tsoro nake ji yaya xae min xafi," ya girgixa mata kai da kyar yace "rufe idonki," da sauri ta rumtse idonta ta kankamesa, ba shiri ta sakesa tayi yar kara, yana rike da ita da sauri yace "kinji xafi ne," kmr xata yi kuka tana mayar da numfashi tace "A'a," snn ta kankamesa. To ni dae da gudu na fita don ba ruwana, anjima na dawo. . Aliyu bae sarara mata ba sae da ya ga ta fara kukan gajiya, snn ya fada gefenta ya rungumota yana kissin din wuyarta, a hankali ya rada mata a kunne, "u re different Fateema, so so cweeeet," ta turasa da karfi ta fara kkrin mikewa, ya matse ta jikinsa yace "ae baki isa ba, bayan na gama biya maki bukatarki xaki kawo min iskanci, dama abinda ya kawo ki knn," ta fashe da kuka tace "Allah ya isa na, ni wllh ka sakeni," ya saka bakinsa cikin nata yana kissin dinta, turasa ta shiga yi ya dan gatsa mata cizo a labbenta, tayi kara, ya kankameta yace "last round sae na bar ki kiyi tafiyarki da kayanki," a fusace kmr xata yi kuka tace "da'alla ni ka kyaleni, wllh xan maka ihu" ya ki sakinta kuma yaki cewa komai sae wasa da gashinta da yake, a hankali ya shiga romance dinta kuma yana kallon cikin idonta, ta fashe da kuka tace "don Allah ka bari ya Aliyu wllh na gaji," ya ki sauranta ya ci gaba da abubuwan da yake mata, hkn yasa tayi shiru ta lumshe ido bata sake yunkurin hanasa ba, a hankali taji mararta ya fara ciwo, murya kasa kasa tace "ya Aliyu ka bari cikina na min ciwo," bae masan tana yi ba, ita ma bata wani yi serious wajen hanasa abubuwan da yake mata ba, wani mugun murdawa taji mararta yyi, bata san lkcn da ta fasa ihu ba, ya fada gefenta da sauri yace "me ya faru," ta shiga nuna masa mararta tana yarfe hannu tace "ciwo yake min," xae yi magana ta sake wani karan ta fashe da kuka tace "wayyoo ya Aliyu ciwo yake min ssae," ba shiri ya mike ya shirya ya dawo gabanta, yace "dama yana maki ciwo ne," ta kasa cewa komai don axaba ta sauko daga kan gadon da kyar ta durkushe kasa tana rike da marar cikin kuka tace "nashiga uku wllh ciwo yake min ssae ya Aliyu," ta fasa ihu a gigice ta rikesa tace "don Allah ka taimakeni, ciwo yake min" ya ma rasa me xae mata duk ya rude, in dae kan inteesar ne rudewa ba komai bne a wajensa nn da nn yake rudewa ya rasa abun yi, ya riketa ya jinginar da ita jikin gado a rikice yace "ina xuwa," kuka kawae take tana juye juye rike da marar, ya mike da sauri yyi kofa xae fita yaji tayi wani kara a wahale tace "wayyoo Abbana, ya Aliyu mutuwa xanyi," ya juya ya ganta xaune cikin jini ta rike gado tana kuka, ya dawo da sauri ya xube gabanta a rude yace "innalillahi wa inna ilaihi raji'un, fateema" kuka take ssae tana kiransa tana jijjiga kanta, ya rasa abun yi yana rike da ita sae kallonta yake a rikice, wayarsa dake kan gado ya dauko da sauri jikinsa na rawa ya shiga neman layin Dr maryam, bugu daya ta dauka yace "don Allah doctor i need yhur help ynxun nn, be fst plss," ya ajiye wayar ya mike da sauri, xani ya dauko mata ya shiga gyara mata jikinta, kuka kawae take tana rike da mararta tana kiran Allah, ko minti talatin bae cika ba doctor maryam ta iso gidan, kasa tsayawa a dakin yyi bayan ya dauko mata kayan aiki a dakinsa, ya koma falo ya xauna ya dafe kansa, to wat's d meanin of dis, Safeena ce ta sauko rike da handbag dinta ta tsaya gabansa fuskarta daure tana kallonsa tace "xan fita," da kyar ya dago yana kallonta snn yace "Allah ya kiyaye," ta juya fuu tayi kofar fita, duk tana sane da abinda ya faru a gidan, don tana gama hada break ta haura sama taji muryarsu, kuma ta gane abinda suke yi, ta dde labe jikin kofa tana jin duk me suke fada takaici yasa ta koma dakinta da sauri ta fada kan gado tana kuka, can ta kira uwarta ta sanar da ita komai, uwar ma ta rude don a xatonsu ae ya saki inteesar kmr yanda Hajiyarsa ta gaya masu, uwar tace maxa ta taho gida su san abun yi, hkn yasa ta shirya ta sauko ta kuwa samesa a falo, kuma yana ce mata Allah ya kiyaye kuwa tayi gaba, don dama tayi niyyar ko yace bbu inda xata tace bae isa ba kuma ta fita, Aliyu ya mayar da kansa bayan ya bita da kallo don bae da lkcnta, bayan kmr minti talatin doctor Maryam ta sauko tana kallonsa ta gaya masa magungunan da xae siyo da Allura snn ta koma sama, ya mike da kyar ya haura sama ya shiga dakinsa ya dauki makullin motarsa da Atm ya fita, bayan kmr minti ashirin ya shigo gidan rike da ledan abubuwan da ta lissafo masa, yana shigowa falo ta sauko ta karba ledan ta koma sama, ya kwanta kan kujera ya lumshe idonsa ya rasa gano abinda ke damunsa, karfe sha biyu da kwata doctor Maryam ta sauko, rike da makullin motarta da glass alamar tafiya xata yi, ya mike tsaye da sauri yana kallonta yace "ya ake ciki doctor, bleedn din ya tsaya," ta dan tabe baki tana hararansa tace "ni dae na kusa fara kiranka quack doctor wllh, dama likita na da rudewa hka? Ni kam ban taba sani ba sae a kanka," Aliyu yyi murmushi ya kasa cewa komai tace "to ynxu dae da sauki Alhmdllh, don har ta samu bacci kuma jinin ya tsaya, kuma tana da karancin jini wllh, ka dinga sa ta tana cin vegetables da dae abubuwan da ya kamata kae sae kace ba likita ba, ni abubuwan ka na bn mmki Hydar, nd lstly please n please doctor kayi hkuri ba dan ni ba ka dan sarara mata har bbies dinta su kara kwari don Allah," . Da mugun mmki Aliyu yace "wat? Kina nufin ciki na jikinta doctor?" Doctor maryam tayi masa kallon rainin wayo tace "kai kuma kana nufin kace min baka san tana da ciki bne ko me," Aliyu ya girgixa kai duk yyi confuse da sauri yace "ok ok, doctor ngdd ssae," ya juya da sauri ya haura sama, likitan ta tabe baki,tace "Allah ya shirye Aliyu," snn ta fita daga gidan tana murmushi, ynxu da ita ce xata haifa masa yan biyun nn amma Allah bae yi ba, ta kaudar da tunanin da sauri daga ranta, coz bygones re already bygonea, ta shiga motarta mai gadi ya bude mata gate ta fita daga gidan. Aliyu na shiga dakin Inteesar ya tarda ta kwance tana bacci, Maryam ta lullubeta da bargo ga drip a hannunta, ya karasa a hankali kusa da ita ya xauna yana kallonta, ya ma rasa irin farin cikin da xae yi, a hankali ya cire bargon daga jikinta yana kallonta, yes ga signs of pregnancy a tare da ita, a hankali ya daura kansa bisa cikinta muryarsa na rawa yace "plss Fateema, ki gaya min me kike bukata daga gareni, don Allah kar ki cire min cikin nn kuma, i beg yhu fateema ki bari na ga jinina a duniya plss," duk ya rikice mata har da hawayensa kmr idonta biyu, ita ko baccinta kawae take amma da gani ba me ddi ba hka ya gama haukansa ya dawo gefenta ta baya ya kwanta ya rungumeta yana shafa cikinta, ya kai minti kusan sha biyar a hka snn ya mike da kyar ya shiga bathroom dinta yyi wanka yyi alwala ya fito, nn dakin yyi sllh, ya dde xaune yana Adduar Allah yasa kar Fateema ta kuma yunkurin cire masa ciki, ganin tana ta mutsu mutsu ita kadae ya sa ya mike da sauri ya dawo gefenta ya riketa yace "fateema, me ya faru," cikin baccin tace "cikina," ya daura hannu a mararta yace "sannu xae daina kinji," ya daga kai yana kallon ruwan dake hannunta yaga ya kusa rabi, ya gyara mata kwanciyarta ganin ta koma baccin ya dawo bayanta ya kwanta ya rungumota, yana shafa mararta, a hkn shima yyi bacci yana rungume da ita, sae kusan la-asar ya farka ya mike xaune da sauri yana kallonta, bacci take har lkcin, ya kalli ruwan hannunta ya ga ya wuce rabi, ya mike ya shiga bayi yin wanka kuma kafin yyi sllh, ko minti biyar ba ayi ba da shigar sa bayi ta farka, ta fara kalle kallen dakin da mmki ta mike xaune da sauri kmr warce ta tuno abu tana kallon ruwan hannunta, ynxu kam marar ya daina mata ciwon sae kasala, ta kalli agogo ta ga hudu saura, ta kalli kofar bayi ta gane wanka yake, da sauri ta mike tsaye ranta a dagule, tayi baya xata fadi tayi saurin dafa bango, jiri ssae take gani, ta cire alluran hannunta ta dauki kayanta da kyar ta mayar jikinta, snn ta dauki Hijab dinta ta saka, tayi hanyar kofa ta bude a hankali ta fice daga gidan, tafiya take kmr wata mashayiya har ta isa bakin titi, ikon Allah ne kadae ya kai ta titin, ta tsayar da mai tricycle ta gaya masa inda xata ta shiga da sauri ba tare da ta jira me xae ce ba tana mayar da numfashi, a wahale ta isa gida bbu kudin ba mai mashin, da kyar tace "yi hkuri bawan Allah bari na shiga gida xa'a fito maka da kudinka ynxu," da lst strength dinta ta isa falon inna ta xube kan kujera ta lumshe idonta tana mayar da numfashi, inna ta fito da sauri daga daki tana cewa "wani gantalallen ne xae fado min gida ba sallama kmr katon arne," inteesar dae bata tanka ta ba, inna ta rufe bakinta da sauri tace "lah ai ban san ke bace ba, daga ina hka? ina kayan? me ya tsayar da ke tun safe hka? A'a me ya sameki," duk a rude ta jero mata tambayoyin, inteesar tayi tsaki tace "ni da'allah ki rabu dani inna, ga me keke napepcan a waje ki kai masa dari biyar dan Allah," inna tace "ina naga dari biyar, ba daxu gabanki na ranto dubu gun Zainabu ba, ina kudin motar da na baki," inteesar ta juya mata baya tace "ki nema ki kai masa dan Allah, yana waje yana jira," inna ta fita da sauri tana cewa "to bari naje gun matsiyatan can ko xasu bani," tana isa tsakar gida cikin daga murya tace "Aisha ko shafa cikin ku wani ya ranta min dari biyar kan Bukar ya dawo," umma ta leko ta taga da mamaki tana kallon inna, "magana fa nake yi ko basa ciki ne," a tare suka fito umma tace "wllh inna ni dubu ce a hannuna," Hajiya ta fito da dari biyar din ta mika ma inna tace "gashi ina da canji inna," inna tace "yauwa dama me keke napep xa ku mika ma a waje, inteesar ce ta tafi anguwa ta xubar da kudin ta a titi, ynxu bata da wanda xata ba ma mai mashin din nima kuma banda canji, fita ki mika masa yana waje," umma ta juya tana yar dariyar keta, don dama tana dashi ta hana sae ita Hajiya me neman suna, Hajiya kam ji tayi kmr ta hadiye xuciya don takaici, a fusace inna tace "ya hka ina magana kin tsaya kmr wata sokuwa, ki fita ki mika masa mana," sum sum Hjiya ta karasa gate ta mika ma mai keke napep dari biyar din ranta a bace, ta komo cikin gidan, inna ta juya tayi gaba ba tare da tace mata komai ba, ummata shige daki ta dinga kyalkyala dariya, inna na komawa falonta tace "shegu sun ba shi,A'aah jinin meye wnn a xanin ki inteesar" arude tayi tambayar ta karaso kusa da inteesar da sauri tana gwale ido. Inteesar ta juya da sauri tana kallon xaninta taga duk ya baci da jini, inna ta saka salati kmr xata yi kuka xata yi magana inteesar ta riga ta da sauri tace "al'ada ce ta xo min a hanya," inna tace "haba," inteesar ta gyada mata kai kawae, inna tace "to Alhmdllh, ciki kam sae dae lbri tunda ga al'ada har ta xo, ynxu Haisam ya dawo ya raka ki kuje ayi maki wankin ciki, don naga bbu shegen da ya damu da hka a gidan tunda ba lfyarsu bace," inteesar ta kuma juya mata baya don ita kadae tasan yanda take ji a jikinta," inna tace "to wae ina kayayyakin naki," ba tare da ta kalli inna ba tace "ba kowa a gidan," inna tace "shegu, to ki tashi kije ki gyara jikinki mana kin wani kwanta kaman rubabbiya ko gantalallen can ya koya maki kaxanta ne, ni dae ban san ki da kaxanta ba sae dae in gunsa kika koyo", inteesar ta juya da sauri tana kallonta tace "kema dae kinsan sharri kawae xaki masa amma ya Aliyu karshe ne wajen tsafta," inna ta wage baki tana kallonta, inteesar ta mike da sauri ta shiga daki don ita ma sae taji xancen yyi mata wani iri a baki to ina ruwanta ma da har xata wani kare masa, wanka ta shiga bayi tayi taga jinin ya tsaya, ta hada ruwan xafi tayi wankan snn ta fito ta shirya cikin gown, har ta kwanta abinda ya faru daxu ya fado mata, ta lumshe idonta, can ta mike xaune da sauri tana kallon bakin kofa tace "inna ina kika ajiye takardar daxu da safe?" inna dake ta goge goge a falo tace "oho kaman yana cikin durowa, me xakiyi da shi," inteesar bata tanka ta ba ta mike ta bude drawern ta dauko takardar ta koma ta kwanta, ta dan lumshe ido ta bude snn ta bude takardar tana kallon cntent dinsa "Ni Aliyu ynxu na fara aurenki Fateema, ke din bnxa baki isa kice na sake ki ba tare da na sa kaina ba, amma fa ban tilasta ki dole sae kin dawo gidana ba kiyi ta xama a gidanku don baki da amfani a gu na dake da rashinki duk daya ne a gurina, kuma muna nn da knki xaki kwaso kafafuwarki ki xo ki same ni, wawiya kawae Jahila," inteesar ta dafe kanta hawaye ya cika idonta "Allah ya isa bata yafe masa ba kusantarta da yyi daxu, ita da tasan abinda ke takardar nn da baxata fara xuwa gidansa ba, ta fada kan gado tana hawayen takaici, ita ko xata yi maganinsa. Aliyu na fitowa daga bathroom ya nemi Inteesar ya rasa duk ya rikice hankalinsa yyi mugun tashi, Allah dae yasa yarinyar nn ba gida ta wuce ba, abinda ya fada knn a xuciyarsa, yyi sllh da kyar snn ya shirya cikin three qtr da fara shirt ya dauki makullin motarsa ya fita daga gidan, karfe shidda ya isa gida, ya tarda mum dinsa a tsakar gida xaune da umma, ya xauna kan wani dan dakali ya gaishesu, Hajiya tace "son yana ga duk ka rame baka da lfya ne," ya dan sauke ajiyar xuciya yace "lfyata lau," umma tace "to ynxu me ka xo yi gida kai da sae muyi wata bamu ganka ba," Hajiya tace "shi dae na gani, daga ina kke ynxu," ya mike yana ma umma wani irin kallo yace "don naxo gidan ubana shine laifi," bae jira me xasu ce ba ya dan yi tsaki yyi sashinsa, khadija ya kira a waya ta shigo sashin nasa yace "khadee yarinyar nn ta xo gidan nn?" khadija ta dan tabe baki tace "ehh ae dama tana nn, ynxu ma inna ta kira ya Haisam wae ya xo ya rakata asibiti ayi mata wankin ciki," ya yo waje da ido ya mike tsaye da sauri yace "wani cikin, ina Haisam din," khadija tace "ae bae dawo ba," ya girgixa kai cikin tashin hnkli yace "tafi kawae," ta juya ta fice, baya san mum dinsa ta xargi komai shiyasa bae nufi bangaren inna ba ya shiga nasa, ya dan leko ko suna nn, yaga kuwa suna nn xaune har lkcn, yyi tsaki ya koma. Sae da aka kira Maghrib snn duk suka shiga sashinsu, yyi alwala ya fito ya tafi masallaci, bakwae da kusan kwata ya shigo gidan ya nufi bangaren inna, a hanya suka hadu da Momyn Inteesar ya kauda kansa da sauri kmr baxae gaisheta ba har ta wucesa snn yace "ina yini," bata ko kalli inda yake ba bare yasa ran xata amsa, yyi murmushi ya isa kofar falon inna xae yi sallama ya fasa, ya je kusa da window yana lekan falon, inna na xaune tana dama fura tana ta xuba da kursum dake kwance tana karatun Novel, inteesar kuma ta fito daga daki knn ta durkusa kusa da inna tace "inna xuge min xip," inna tace "yau naga jaraba, me kuma xakiyi ba daxun nn kika yi wanka ba," inteesar tace "ni dae ki xuge min," inna ta tabe baki ta xuge mata, inteesar kam sae bin falon take da kallo, wayar kursum yyi kara ta mike tace "inna sae da safe," ta fice daga falon saurayinta ne ya kirata, inna ta tabe baki tace "wnn mummunan saurayin naki me shegen rowa da baya shigowa gaida mutane," ihu suka ji kursum ta kwala ganin Aliyu da tayi jikin window ya galla mata mugun harara ya daura yatsunsa a labbensa alamar tayi shiru, da sauri inna tace "menene" kursum tace "mage na gani," snn tayi gaba da saurinta. Inteesar ta mike bayan inna ta xuge mata xip din ta cire doguwar rigan jikinta ya rage daga ita sae undies, inna tace "bokiti na waje kisa hijabi ki dauka, da na ce kursum ta shigo maki da shi, inteesar ta sa Hijab dinta ta nufi bakin kofar xata je dauko bokiti . .Inteesar na kaiwa bakin kofa tayi still kmr me tunanin abu, inna tace "me ya faru," bata dae ce mata komai ba amma ita kamshin turaren Aliyu take ji kuma ssae, to duk yanda aka yi yana tahowa ne, hkn yasa ta ki fita, shikam kallonta kawae yake yana murmushi ya gane me yasa ta tsaya, ya karaso bakin kofa cikin sanda ya bude kofar da sauri ya fixgota ya fito da ita, ta fasa ihu a tsorace hka ma inna da tayi waje da gudu ita ma, tana cewa"na shiga uku waye wnn," janta ya shiga yi tana nokewa cikin kuka tace "wayyo inna kice ya kyaleni," inna ta shiga binsu da gudu tana cewa"lahh yau naga iskanci ina xaka kai min ita don uwarka, Bukar Bukar," ganin inna tara masa jama'argidan kawae xata yi a tsakar gida yasa ya sake ta tun kan su karaso tsakar gidan, ta karasa gun inna da gudu tana kuka, inna na nunasa da dan yatsa tana kakkane ido tace"Aliyu ka fita harkata Aliyu ka fita harkata, wae shin ni kakar kace xaka dinga wasa da hankalina hka ko yaya ne," ya harareta ya xo ya wucesu yyi bangarenta, cikin daga murya tace "Wllh tllh kar ka shigar min falo, xan fa tara maka jama'ar anguwar nn da daddaren nn," dariya kawae yyi ya shige falonta abunsa, inna tace "maxa je ki falon Zainabu kiyi xamanki," inteesar ta make kafada tace "ni baxan je ba," inna tace "to mu xaunamu jira ubansa a nn," jikin wani flower ta ja ta suka xauna wae suna jiran Abba, Haisam ya shigo gidan yana kallonsu da mamaki yace "me kuke yi a nn inna," tace "yo wancan katon bnxan ne ya shigo mana falo ba dole mu fito mu bar masa ba, Bukar nake jira yaxo ya fidda min shi," Haisam yyi dariyar takaici yyi bangarensa kawae . A wani cafe taga Haisam yyi parkin, tace "ya Haisam me xa muyi a nn," ba tare da ya tanka mata ba ya bude mota ya fita ita ma ta fito, sae da suka shiga cafe din snn yace "ko baxa kiyi post utme bne," tace "ohh na manta, a nn xamuyi registration din" yace "ehh," nn suka gama komai cikin minti ashirin snn suka tafi banki ta jirasa a mota ya biya kudin registratn din ya fito, taga sun kama hanyar gida, a hankali tace "ya Haisam asibitin fa," bae kulata ba ya ci gaba da tukinsa har suka isa gida, ranta yyi mugun baci, yana gama parkin ta bude mota tayi cikin gida, ya bita da kallo ya girgixakansa lallai Inteesar ta girma, tana shiga falon inna inna tace "ya har kun dawo, amma abun ba wuya, amma bbu xafi inji dae," inteesar ta xauna ta rungume hannayenta fuskarta a tamke tace "kokai ni ma yyi," inna tace "sbda me, ina kuka je to," inteesar ta tabe baki tace "wae wani registratn ya kai ni," inna tace "kyaleni da shi," snn ta mike ta fice a fusace tayi bangarensa, ranta a bace ta dawo tace "ki rabu da yan iska so kawae suke ki mutu da dattin ya ya a cikin ki, yara duk sun bi sun rainani don ina wasa da su, ki rabu dasu kawae gobe da sassafe xan rakaki muje a wanke maki, tunda dae ni ba nakasashiya bace bare wani ya kawo min rainin wayo don na aikesa. Washegari da safe Abba ya aiki kursum ta kira masa Inteesar, inna tace "me xata yi masa da sassafe hka," inteesar da gabanta ya fadi tana kallon kursum tace "ni kuwa," kursum tayi tsaki tace "ni," snn ta fice, inna tace "maxa saka hijabi muje," inteesar ta dauki Hijab dinta inna na biye da ita a baya suka kama hanyar falon Abba, suna shigowa Abba ya hade rae ganin inna a bayanta, inna ta shigo falon ta hakikince kan kujera tace"kace a kira maka Inteesar Bukar, ga ta nn" Abba yace "to fisabilillahi baaba don nace a kira min ita sae ki biyo ta, wae meyasa kike yin hka ne baaba," inna ta mike ta marairaice tace"Allah ya baka hkuri," snn ta fice daga falon kmr xa tayi kuka, yyi tsaki yana kallon inteesar yace "daga yau bana son kina kwana a bangaren inna, kina ji na," ta sunkuyar da kanta ta kasa cewa komai, ganin yy shiru yasa ta gaishesa a sanyaye, ya amsa snn yace "fateema kinje walakanta abinda Allah ya baki sae ga shi kuma ya nuna maki ishara, nakan yi mmkin sauyawan ki lkci guda Fateema, ynxu abinda nake so dake shine ki koma gun ummar ki ki xauna bana son xaman ki tare da inna, snn wani asibiti da take cewa xata kai ki kar ki kuskura don ciki na nn jikin ki," inteesar ta dago a sanyaye tana kallon Abba gabanta na faduwa, hawaye ya cika idonta, wani cikin kuma bayan ta xubar, Abba ya katse mata tunani ta hanyar cewa "jiya Aliyu ya shigo ya sameni ya kuma badahkuri akan yana son ki koma dakin ki, though ban nuna masa na amince da hkn ba don ina son na fara jin ta bakin ki, kina sha'awan komawa dakin ki?" inteesar ta share hawayen da ya gangaro mata tace "Abba don Allah don Annabi ka sa shi ya sallameni, ni bana son auren kuma ka yi mani adalci abba," Abba yyi shiru yana kallonta snn yace "to kiyi hkuri ki bari har sae kin sauka lfya, na maki alkawarin xan sa ya baki takardarki ko yaki ko yaso," muryarta na rawa tace "ngdd Abba," Abba yace "kya iya tafi amma bana son xaman ki tare da inna, ki koma gun ummanki ynxun nn kuma," kai kawae ta gyada masa ta mike xata fita, Aliyu yyi sallamaya shigo falon, ta hade rae ta bi ta gefensa ta fice, ya bi ta da kallo snn ya xauna inda ta tashi, ya gaida Abbansa, Abba ya amsa yana duba newspaper, yyi shiru na dan lkci snn a hankali yace "Abba kayi mata magana," Abba ya dago yana masa mugun kallo yace"wani maganan xan mata," Aliyu ya sunkuyar da kansa bae ce komai ba, Abba yace "ae ni na gaya maka baxan mata dole ba, kajekayi xamanka da dayar matarka tace baxata koma ba," Aliyu yyi shiru da ganinsa bae ji ddin maganar ba, ganin Abba ya maida hankalinsa kan abinda yake yasa yace "to Abba kayi mata maganarkar ta sake yunkurin xubar min da ciki," Abba yace "tashi ka ban waje, nonsense kawae" Aliyu bae ce komai ba ya mike yyi masa sallama ya fita daga falon ba tare da Abba ya amsa ba. Dakin Haisam ya nufa, ya samesa ya gama shiri xae fita office, Haisam yace "daga ina da sassafe hka," Aliyu yace "taimako nake son ka min Haisam, kasan yarinyar nn na jin maganarka don Allah kace mata ta yi hkuri ta koma dakinta, ni wllh bana son wani abu ya sami yaran nn ne, kasan yarinta yyi mata yawa, ga inna kuma ba tsohuwar arxiki ba ko ita xata rakata su fake idon Abba suce xasu je cire cikin kuma" haisam yyi yar dariya yace "da knn Inteesar ke jin maganata ba ynxu . Aliyu yadafasa yace "plss ka gwada kaga Haisam, wllh bana son xamanta a gidan nn," Haisam yace "shknn xan gwada yi mata maganan ltr idan na dawo," Aliyu yace "thank yhu," a tare suka fita da Haisam kowa ya kama hanyarsa. Inteesar na komawa falon inna, inna ta mike da sauri ta dawo kusa da ita tace "me Bukar din yace maki," inteesar tayi shiru da ganin idonta kasan tayi kuka, inna ta mike a fusace tace "xan ko ci mutuncinsa, da wnne xaki ji," tana fadin hka ta fixgi mayafi a fusace tayi waje, da sauri inteesar ta bi ta ta riko hannunta tace "ni inna bbu abinda aka min kin wani kwashi kafafuwa ina xaki," inna tace "to kukan me ki ke yi ba ayi maki komai ba," inteesar tace "ni ki rabu dani," ta shige bedroom ta bar ta nn tsaye, inna ta bude baki tace "au" can ta tabe baki ta ci gaba da aikinta. Karfe tara saura tace ma inna xata gun momynta, inna tace "yau kuma, to ki tsaya ki sha kunun da na dama maki tunda kin ki shan tean" inteesar tace "xan dawo inna," snn ta fice daga falon tayi sashinsu a sanyaye duk sae taji bata jin ddin jikinta, wanke wanke ta tarar momynta nayi a bakin famfo, ta karasa tace "sannu da aiki momy, kawo na karasa maki," momy tace "A'a bar shi kawae," inteesar bata ce komai ba ta shiga falo ta karasa bedroom din momynta tayi kwanciyarta, duk jikinta a sanyaye yake wae mayen cikin nn na jikinta duk axaban da ta sha, hawaye ne ya shiga bin kuncinta, ta dde tana kuka a hankali daga bisanni bacci ya dauketa, karfe goma momy ta shigo dakin ta tada ta tace "kin karya ne," inteesar ta gyada mata kai tace "ehh" momy ta juya ta fita daga dakin, baccinta ta ci gaba da yi har kusan sha biyu, xaxxabi ya fararkar da ita, sanyi ssae ta dinga ji ta mike da kyar ta dauko bargo ta lulluba, biyu saura momy ta shigo dakin tace "kinyi sllh ne," ta girgixa mata kai da kyar tace "ynxu xanyi," momy ta karaso jikin gadon tana kallonta ganin yanda ta takure kanta tace "me ya same ki," da kyar inteesar tace "bana jin ddi ne," momy bata ce komai ba ta fita, can bayan kmr minti goma ta shigo dakin rike da kulan abinci tace "ki tashi ki ci abinci, kina shan magunguna ne," kai kawae inteesar ta gyada mata ba don tana shan maganin ba, ta sauko da kyar momy ta xuba mata abincin ta fita, tuwan shinkafa ce da miyar bitter leaf tayi mata, inteesar ta mike da kyar ta shiga bayi ta kurkure bakinta ta wanke hannu ta fito ta jawo tuwan gabanta ta shiga ci a hankali, loma uku kawae ta ci taji xuciyarta na tashi ta rasa inda xata sa kanta, lkci daya aman ya xo mata ta mike da gudu ta fada bayi ta shiga kwarara amai, momy dake falo ta shigo dakin da sauri ta shiga bayin tana kallonta, har ta gama aman snn ta taimaka mata ta gyara jikinta suka fito, momy tace "ina magungunan da kike sha," ta kwanta tana girgixa kai ta kasa cewa komai sae mayar da numfashi da take, momy ta shiga bayin ta gyara inda tayi aman ko da ta fito inteesar tayi bacci, don hka ta rufe tuwan ta ajiye mata a gefe. Karfe shidda Haisam ya shigo falonsu ya gaida momy dake koya ma ihsaan assignment, ta amsa da fara'arta tana tambayrsa ya aiki, yace "Alhmdllh momy, inna tace min inteesar na nn," momy tace "eh tana nn," Haisam yace "wajenta na xo momy," momy tace "eyya sae dae kuma bacci take wllh tunda safe take amai, tama ki cin komai, nayi mata maganan magungunanta tace suna gida," Haisam yace "subhanallahi momy ae da sai kiyi magana, ko Abba ki kira a san yanda xa ayi," momy ta mike tace "bari na taso maka ita to," da sauri yace "A'a ki bar ta kawae, na dawo anjima," momy tace "to shknn," ya mike ya fita yana ma ihsaan wasa. Yana komawa sashinsa kiran Aliyu ya shigo wayarsa, ya daga Aliyu yace "ya dae brother kayi mata maganan," Haisam yace "ynxun nn ma na dawo daga gunta, amma sae dae ban samu ganinta ba ma, bata da lafiya wae tun safe take amai inji momy," Aliyu yace "amai kuma, God! Bari xan shigo ynxu," kasa sukuni Aliyu yyi har sae da ya iso gidan wajen karfe tara saura don aiki yyi masa yawa a clinic, sashinsu ya nufa, yana isa kuwa ya kasa shiga ya dde tsaye bakin kofa daga bisanni ya dake yyi sallama, ihsaan ce ta amsa ya bude kofar ya shiga, momy na xaune suna cin abinci da ihsaan, kansa a kasa ya shigo falon ya nemi kujera ya xauna yana kallon Ihsaan kmr ita yake gaisarwa yace "ina yini," momy ba tare da ta kallesa ba tace "qlau," bae sake cewa komai ba ya shiga kallon TV, momy ta mike da sauri jin kakarin aman inteesar, Aliyu ya bi ta da kallo ransa a dagule don shima ya ji, ya rasa me xae ce mata ne, momy na shiga bedroom din ta sameta bakin kofar bayi tana amai, ta kamata tana yi mata sannu, kuka kawae take tana juye juye, momy ta gyara mata jiki ta mayar da ita kan gadon, snn ta gyara wajen ta koma falo ta ci gaba da ba ihsaan abinci. Aliyu ya dauke kansa da sauri daga kallon da yake ma bakin kofar kmr ya shiga, ya kai kusan awa daya xaune a dakin idonsa na kan TV, daga bisanni ya mike da kyar ganin momy nata harkan gabanta yace "na tafi," ba tare da ta kalli inda yake ba . .. Aliyu na fita Haisam yaje ya samu a sashinsa, Haisam yace "ya dae har ka shigo," ya xauna bae ce komai ba, Haisam ya ci gaba da abinda yake, can Aliyu yace "don Allah Haisam kaje ka ma Abba magana su bani matata in tafi ni fa ana min abinda aka ga dama a gidan nn," a fusace ya karasa maganar, Haisam yace "uhm Aliyu knn, har ka manta rashin mutuncin da kayi wks bck knn," Aliyu yace "to ba su suka nema ba, ni don Allah ka rabu dani," Haisam ya daga kafada yace "da kuna shiri da Hajiya inna da da gudu xata sa a baka matarka, ynxu kam ita da kanta xata xuga a hanaka," Aliyu ya kasa cewa komai, Haisam yace "to ynxu ka shiga ka duba ta ne," da kmr baxae yi magana ba yace "wani dubata xanyi bayan kasan halin mamanta, yi tayi kmr bata san me ya kawo ni ba, hasalima barina tayi nata xama kaman mara aikin yi a falon, ni kuma ban san me xance mata ba," Haisam yyi dariya, Aliyu ya galla masa harara yace "wat's funny," Haisam yace "to ae in dae momy ne ma kadan ka fara gani ynxu," dariya Haisam ya ci gaba da yi, Aliyu ya mike xae fita ya riko hannunsa da sauri yace "to bari muje in rakaka sae na ari bakin ka," Aliyu yace "gud," a tare suka koma falon, bbu kowa falon sae Tv dake aiki, momy ta fito dan Haisam ne yyi sallamar, tace "A'a har ka dawo Haisam," Haisam yace "wllh momy, ya jikin inteesar din," momy tace "da sauki," Haisam yace "wae fa dubata Aliyu ya shigo yi shine ya kasa cewa komai," bbu yabo bbu fallasa momy tace "ayyo ae tana ciki," Haisam yace "to shi dae na gani ya shigo ya xauna kmr," da sauri Aliyu ya take kafar Haisam, Haisam ya rama snn ya ci gaba, "maimakon yace ga abinda ya shigo yi, ynxu bacci take momy?" momy bata kallesu ba tace "eh" snn ta fice daga falon, Aliyu ya mike da sauri yyi hanyar bedroom din Haisam na cewa "kai wa yace ka shiga," ko kallonsa bae yi ba, kwance ya tarda ta cikin bargo ta lullube gaba daya har kanta, ya cire bargon, jikinta yyi mugun xafi, ya dagota yana kallonta da tausayi, a hankali ta bude ido tana kallonsa, ya rungumeta murya kasa yace "srry my Fateema," turasa ta shiga yi yaki sakinta, ta fashe da kuka tace "ni ka rabu dani," ya rufe bakinta yace "kiyi hkuri don Allah," lamo tayi jikinsa a hankali yace "kin ci abinci?" ta girgixa masa kai yace "sbda me," da kyar tace "amai," yace "ki gaya min inda ke maki ciwo fateema," tayi shiru bata ce komai ba, ya kwantar da ita ya mike ya bude kwanon da ya gani kusa da gadon, shinkafa ce da miya, ya shiga xuba mata snn ya dawo kan gadon rike da abincin xae bata, da sauri ta kauda kanta ta fada kan gado cikin kuka tace "amai xanyi ka ajiyesa," ya mayar ya ajiye da sauri snn ya dago ta yace "to me xaki ci," ta girgixa masa kai, ya rungumeta yana shafa gashinta, mikewa yyi ya shiga bathroom ya dibo ruwa a roba, snn ya fito yana tambayrta ko xae samu dan tawul, tayi shiru bata ce komai ba sae da ya dawo gabanta a hankali ya kara mata tambayar snn ta nuna masa, ya mike ya dauko ya saka cikin ruwan, ya cire mata rigar jikinta da xani snn ya shiga matse tawul din yana goge mata jiki da shi, karfe goma yace xae tafi bayan ya lallabata ta sha tea kadan, har lkcn tana rungume jikinsa, ta gyada masa kai kawae, snn yace "gobe da safe xan xo da magunguna da injectns dinki kinji kanwata," kai kawae ta gyada masa, ya daura mata kiss a bakinta, ta lumshe ido da sauri, yyi mata sae da safe, ta bi shi da kallo har ya fita, ya fita da minti biyar momy ta shigo, xani ne kawae jikinta, kunya ya kamata ta rufe ido da sauri kmr me bacci. Kullum sae Aliyu ya xo sashinsu da safe da dare, ya kan siya masu fruit ko nama, duk da ko kadan momy bata sake masa, sae dae yyi ta xamansa a falo idan ta fita sae ya shiga dakin, laulayin inteesar ya dawo sabo kullum cikin wahala da amai take yana mugun tausayinta har mmki abun yake bata, duk da tasan duk sbda cikinsa ne, wani lkcin idan ya shigo gidan sae karfe sha daya yake wucewa duk da bbu wanda yasan yana xuwa har inna, idan kuwa tayi bacci me ddi to a jikinsa ne, don yana xuwa ya rungumeta bacci yake xuwa mata, wani lkcn ma sae dae ya kwantar da ita kawae yyi ma momy sallama ya wuce, duk dare Abba ma na shigowa dubata hka Haisam, inna kam bata san ashe jarababbun yara na makale jikin inteesar ba, su kansu Hajiya basu sani ba. Yau ta cika sati biyu gun mamanta, momy na kula da ita ssae kuma tana tausayinta ganin yanda cikin ke bata wahala, karfe hudu na yamma Aliyu ya shigo gidan ranar yaci sa'a bbu kowa tsakar gida ya nufi sashinsu inteesar, xaune ya tarda ta da momy a falo ta sata gaba sae ta shanye kunun da ta dama mata don bata cin komai, ya gaida momy tayi kmr bata ji sa ba ta fice daga falon, ya dawo gefen inteesar ya shiga lallabata yana bata kunun har ta sha rabi, snn ya ajiye ya rungumota jikinsa yana buga mata baya kar tayi amai, tayi lamo tana sauke ajiyar xuciya, a hankali yace "fateema," ta dago tana kallonsa ya mayar da kanta kirjinsa yace "gida nake son tafiya dake fateema, nasan sae da amincewarki Abba xae yarda na daukeki, ki tausayamin plss my wife" . Inteesar ta kwace kanta daga rungumar da yyi mata tana masa mugun kallo tace "waye wife din taka? Sae yau da kaga ciki a jikina kasan ni wife dinka ce, to ni ba matarka bace wllh, bari ma kaji abinda baka sani ba ya Aliyu, wllh bana sonka bana sonka, tun ynxu nake son mu ajiye yarjejeniya da kai a kan cikin nn," yyi shiru yana kallonta xuciyarsa na tafarfasa, tunanin me yake hka har ya kai sa ga kiranta da wife dinsa, ya rike temper dinsa yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "yarjejeniyar me," tana masa wani irin kallo tace "na farko ina haifa abinda ke cikina xaka bani takardata, na biyu kuma ni baxan shayar da danka ba tun ynxu ka sani, idan ka yrda da deal din nn, to na yrda xan bar cikin nn, idan kuma akasin hka, to wllh wlh xan sake komawa a cire min cikin kuma baxa ku sake gani na ba," ya sauke ajiyar xuciya yana kallonta, ransa yyi mugun baci, amma da yake yaransa kawae yake so, sae yace "ok na yrda xan baki takardarki kuma baxa ki shayar da su ba," tace "ka rantse da mahaliccinka," yyi shiru yana kallonta snn yyi wani irin murmushi yace "na rantse," tace "kuma ni daga ynxu ka daina xuwa gurina na yafe maka," yace "ok ngdd," snn ya mike ya fice ba tare da yyi mata sallama ba ma, ta mike ta koma daki da kyar ta kwanta kan gado ta lumshe idonta dake cike da hawaye, yes hkn kadae ne mafita a gareta, Aliyu bae cancanci ta xauna da shi ba ko kadan, idan yana shisshige mata hka xata iya canxa ra'ayinta. Tun daga ranar Aliyu bae sake xuwa sashinsu ba duk da tasan yana xuwa gidan, yau kusan sati knn tayi forcin din kanta xuciyarta taji hkn da yyi yafi burgeta yafi mata ddi amma ta kasa, baccin kirki gagaranta yake duk da ynxu laulayin nata da sauki cikinta ma ya dan fara fitowa, in kaga yanda inna ke ji da ita da cikin sae ka rantse kace ba ita ke jinjina mata xubar da cikin da tayi kwanaki ba, tunda ta gane ciki na nn maimakon a ga inna ta bata rae ko makamancin hka sae aka ga ta buge da murna har da rawanta, kullum ita ke ma inteesar girki safe da yamma wae don yaran suyi karfi, su Hajiya ma ba karamin girgixa suka yi ba da kursum ta gaya masu ae ciki na nn kuma har ya fara fitowa, umma tace "tab, wllh ki san abun yi tun wuri Hajiya," Hajiya da abun duniya ya isheta tace "to umma ya xanyi ni wllh duk jikina ma ya mutu, taya xa'ayi Aliyu ya hada xuriya da marasu asali kuma mugaye, umma ta tabe baki tace "ki shigo anjima da daddare ina da shawara da xan baki," Hajiya taji ddi ssae tace "to umma naji ddi amma, xan shigo anjiman" Yau lahadi inteesar na xaune tsakar gida da inna da yamma wajajen karfe biyar suna ta hira tana cin gyada kursum na kwance kan tabarma a gefensu tana danna wayarta, ynxu kam bbu laulayi sae shegen kwadayi kmr xata ci bbu, sae nauyi da jikinta yyi mata don cikinta ya fito ssae watan shi na biyar knn, duk da tana tattare da damuwar da bata san dalilinsa ba sae kyau take karawa abunta kmr ba ita ba ga wani haske da ta kara a kan nata, cikin ya amsheta ssae yyi mata das das a jiki gwanin sha'awa, ta mike knn xata dauko ma inna tsintsiya ta tattare bawon gyadan da suka ci don kursum tace baxata tashi ba tunda bata ci gyada ba, suka ji an bude gate, gaba daya suka maida hankalinsu ga gate din, Aliyu ne ya shigo gidan safeena na biye da shi a baya, kallo daya tayi masa ta dauke kanta tayi gun inna rike da tsintsiyar a hannunta, ya kasa dauke idonsa daga kanta sae binta da kallo yake, ya sauke idonsa kan cikinta ya sauke ajiyar xuciya, muryar inna ne ya dawo dashi cikin tsawa tace "su waye wa innan xasu fado mana gida kmr tsofaffin arna ba sallama," safeena da ta kasa daina kallon Inteesar ita ma xuciyarta na harbawa ta maida kallonta gun inna tana mata wani shegen kallon rainin wayo, Aliyu ya harari inna yace "ke dae kin banu wllh, ae randa xaki mutu a gidan nn sae na xuba ruwa a kasa nasha," a fusace inna tace "karyanka yaro kuma sae ka riga ni mutuwa," inteesar ta juya da sauri tana kallon inna tace "kai inna," inna ta mike tana gyara daurin xani tana huci tace "ku fita ku ban waje, kar na walakanta ku ynxun nn," Aliyu yyi dariya yace "to mai gidan," safeena ta tabe baki tayi bangaren Hajiya inna ta sha gabanta tana huci tace "ina kike tunanin xaki mahaukaciya," inteesar ta mike da kyar tayi sashinsu Aliyu ya bi ta da kallo har ta bace masa, snn ya maida dubansa ga inna dake fada safeena na fada, bbu tonan sililin da inna bata yi mata ba, yace "ke safeena," ta juya ranta a bace tana kallon Aliyu tace "ka ja ma tsohuwar nn kunne ta fita harkata don ni nafi karfinta wllh," ya daka mata tsawa yace "tunda tace ki fita ba sae ki fita ba, sa'ar kakarki ce aka ce maki wnn" safeena ta shiga hawaye tana kallonsa, yyi tsaki ya karasa gun inna yace "kiyi hakuri inna, bata cika hankali bane yarinyar," inna tana wage baki tace "ae naga alama maxa ta fitar min daga gidan dana, sannu da xuwa Aliyu ina ta cigiyarka" yyi murmushi yace "ae gani innata," tana dariya ta ja sa suka yi sashinta, shi ko sae murmushi yake don yana da dalilin yin abinda yyi Safeena ta juya tana kukan takaici ta bar gidan, da sauri Hajiya da umma dake leke ta taga suna kallon duk abinda ke faruwa suka fito, Hajiya tabi bayanta tana kiranta cikin lallashi tace "kiyi Hkuri safeena ki kyaleni da shi, wancan kuma me ya kai ki musanyar yawu da ita baki san mayya bace," Safeena tace "ae kam naga alama Hajiya, amma ni dae wllh nafi karfinta" ta karashe maganan tana kuka, Hajiya ta ja suka yi sashinta umma na biye dasu a baya suna lallashinta, kursum ta tabe baki ta mike tace "lallai wnn jaka ce mara xuciya," fura inna ta shiga dama ma Aliyu yana kwance kan dogon kujera suna hira, yace "ae idan yarinyar nn ta haihu ke xaki je mata xaman jego," da sauri inna na wage baki tace "haba," yace "eh mana," tace "wayyo amma naji ddi wllh, Allah yyi maka albarka," ya dan tabe baki yace "Ameen, to ma taya xaki je xaman jegon tana nn," inna tace "yo ba sae ta koma ba," ya danyi murmushi yace "to kiyi mata magana, don tafi jin maganarki kan na kowa a gidan nn" inna tace "to bari na aika a kira min ita na gaya mata ynxun nn ma, yo ae wnn ba wani abu bne," dae dae nn khadija ta shigo, ta gaida yayanta snn tace "inna an aiko ni wajen ki," inna tace "waye," khadija tace "wae mamata tace naxo na amshi dari biyar din da kika ara hannunta kwanaki," inna ta bude baki tace "lah ku ji min mata, ki je kice mata taxo ta danne ni ta kwata, naga dae gun dana take samun kudin kajin min fitsararriyarkawae," khadija ta juya xata fita Aliyu ya kirata ya ciro dubu daya ya mika mata yace "gashi ki kai mata," inna tace "ae da ka kyaleni da ita Aliyu, ita don bata da kunya don na amshi wani shegen dari biyar a hannunta kusan shekara daya knn sae ta aiko a karba, maxa kice kuma ta baki canjin dari biyar ki mayar min," khadija har ta fita inna ta kwalo mata kira ta dawo fuskarta a daure tace "wae meye ne inna," inna tace "kije ki kira min inteesar ynxun nn," ta fice daga falon Aliyu ya daka mata tsawa baki ji me tace maki bne "ta leko tace naji ae," snn ta wuce, bayan kmr minti goma inteesar ta shigo falon tana rike da kugunta daga bakin kofa tana kallon inna tace "gani inna," Aliyu dake xaune yana shan fura ya juya yana kallonta, inna tace "to bakin kofar xan xo in same ki," inteesar ta shigo ta xauna gefenta da kyar, sae bin ta da kallo Aliyu yake, tace "me xan maki inna bacci fa nake, inna tace "kai haba, to shiga ki kwanta in kin tashi ma yi maganan," inteesar ta mike xata shiga daki, inna tace "lah baki ga Aliyu bne, naga baki gaidashi ba," inteesar ta juya tana kallon inda yake, har lkcn kallonta yake, yyi murmushi ya ci gaba da shan furarsa yace "ni na isa ta gaishe ni," inteesar ta dan yi tsaki ta shige daki abinta, inna tace "to Allah shi kyauta," hira Aliyu ya kwanta gefen inna yana mata tana biye masa muryarta har waje, sae ka rantse kace ba Aliyu bne, duk inteesar na kwance a daki tana jinsu, rabon da Aliyu ya tsaya suyi hirar arxiki da inna har an manta, yace "ni fa inna yunwa nake ji kin wani hada ni da fura," tace "lah me xaka ci toh," yace "jollof rice nake so da farfesu," da sauri tace "to bari in je in maka," ta mike tsaye tana gyara dankwalin kanta tace "yo nayi ma wasu bnxa ma bare kai," ta fice tana kwala ma kursum kira taxo ta hura mata gawayi, don bata gane gas acewarta bata lkci ne. Aliyu ya juya yana kallon kofar dakin kmr ya shiga ya fasa, yana ta danne dannen wayarsa amma lkci lkci yakan juya ya kalli kofar dakin, inteesar taji shirin yyi yawa, wata xuciyarta tace ta leka taga ko yana falon, a hankali cikin sanda ta isa bakin kofa ta dan bude labulen a hankali tana lekensa, shima ya juya knn yana kallon kofar dakin xuciyarsa na son ya shiga, suka hada ido, ta sake labulen da sauri yyi murmushi bae dae ce komai ba, ganin xuciyarsa ta kasa hakura da shiga dakin kuma baya so ya shiga yasa ya mike da sauri ya fice daga falon yyi sashinsa. Ko da inna ta shigo falon tana kiran inteesar ta fito ta ci abinci da xafinsa, da sauri ta fito kmr jira take, taga inna kadae ne xaune falon, tace "wae ni kika ma girki," inna tace "aa Aliyu nayi ma," inteesar tace "to ina yake," inna tace "ae ni da kaina na kai masa yana kwance a dakinsa yaron kirki." inteesar bata ce komai ba ta dauki furan da ya rage ya rufe ta shiga sha, inna tace "ke dae kin banu da kwadayi, naki ne," ko kallonta inteesar bata yi ba ta shanye ta ajye kofin, snn ta fara cin abincinta, ta gama cin abinci knn, khadija ta shigo dakin tace "wae ina furan ya Aliyu" inna tace ahaf gata nn ta shanye khadija tayi tsaki ta juya ta fice. Karfe tara inteesar tayi ma inna sae da safe tayi sashinsu, har ta wuce bangarensu Aliyu ta dawo tana lekan ko yana nn ko ya tafi, ita dae bata ga alaman ya tafi ba kuma bata ga alaman yana nn ba, ta karasa bakin kofar a hankali da yake basu kunna bulb din wajen ba ta durkusa tana lalube ko xata ga takalminsa, dae dae nn aka bude kofar Haisam ya fito, daga ita har shi sae da suka tsorata. Ashe Aliyun ma na kallonta daga bayanta ya fito daga bangaren Hajiyarsa knn. . Haisam yace "me kike yi a nn Inteesar," ta ji kmr ta nutse wajen don kunya ta fara kame kame, Haisam yyi dariya yace "to ae baya ciki ya fita sae dae in xaki shiga ki jirasa," kmr xata yi kuka tace "wayyo ni ya Haisam abu na ne ya fadi nke nema," bata jira me xae ce ba ta juya da sauri xuciyarta a dagule xata bar wajen ta kusan cin karo da Aliyu dake tsaye har lkcn yana kallonta, gabanta yyi mugun faduwa, tabi gefensa da sauri xata wuce ya rikota, Haisam dae yyi gaba abinsa yana dariya, ta buge masa hannu ta daure fuska tace "meye hka malam," dariyarsa mai kyau yyi snn yace "me kike bukata daga gare ni da kika biyo ni," ta fashe da kukan takaici tace "waye ya biyo ka, Allah ya isa na, da'alla ka sake ni na wuce don naxo neman abu na shine na biyo ka," dariya ya dinga yi har da buga bango yace "ae nine abun naki, ni kika xo nema 4 sure na sani," ta fixge hannunta xata bar wajen yyi saurin rikota ya bude kofar falon ya ja ta suka shiga, kuka ssae take yi kuma na takaici, ka kyaleni ya Aliyu bana son hka, yyi murmushi ya rufe kofar falon da key ya karaso bayanta ya tsaya a hankali yace "am srry fateema, i also feel...." sae kuma yyi shiru ta juya tace "ka bude min kofa in fita nace maka," bae ce mata komai ba ya dauketa sae bedroom yace "ki bari in gaisa da yarana," kuka ta dinga yi tana jin haushin kanta ita kam har ga Allah ganinta kawae tayi a bakin kofar bata san ya aka yi ba, ya rufe kofar dakin ya xaunar da ita kan gado yana kallonta ya durkusa gabanta yace "its High tym mun fahimci juna fateema," cikin tsawa tace "wace fahimta kuma, ka bude min kofa in fice daga dakin nn" yyi murmushi ya kauda kansa yace "ok," snn ya mike ya bude mata kofar dakin da sauri ta fita, ya bi ta baya ya bude mata na falo ma ta fice, snn ya mayar da kofarsa ya rufe. Ko barin wajen bae yi ba ta fara buga kofar da sauri, ya bude yana kallonta ta shigo falon da sauri tace "momy xata gan ni" yace "a ina," tace "wucewa take," bae ce komai ba ya xauna kan kujera, ita ko tana tsaye bakin kofar sae leke leke take, ta kai minti kusan goma a hka snn yace "to ki xauna mana," ta juya ta galla masa harara tace "ina ruwanka da tsayuwata," yyi murmushi ya dauke kansa bae sake cewa komai ba har ta gama tsayuwarta ta bude kofar ta fice, ya sauke ajiyar xuciya, shi kam baxae iya tsayawa rokan karamar yarinyar nn ta koma gidansa ba ta ci gaba da raina sa ba, duk da abun yana damunsa but ya gwammace yyi ta damunsa din. Kullum sae Aliyu ya xo gida da daddare duk dan sbda inteesar amma baya nunawa, ita kuwa idan bata gansa ba har bata jin ddi, tayi ta sintirin xuwa gun inna knn, ta rasa me ke damunta kan Aliyu, gashi ko sun hadu kallon arxiki bata yi masa bare gaisuwa, shi kam sae dae ya bita da kallo, tun ran da inna tayi mata maganan komawa gidanta ta balbaleta da masifa bata sake yi mata ba. Cikinta ya shiga wata na shidda amma bbu me yi mata maganan komawa gidan mijinta, Yau tana xaune falon inna ya shigo da daddare, inna na bakin famfo tana wanke robobinta, ya xauna yana kallon inteesar dake xaune tana shan watemelon, kallo daya tayi masa ta dauke kanta, ya sauko gabanta ya xauna yana kallonta, tayi kmr bata san da shi ba tana ta shan kankananta, ya shafi cikinta ta buge masa hannu tace "meye hka," bakinsa ya daura an nata yana kallon cikin idonta, gabanta yyi mugun faduwa ta rufe idonta da sauri ya shiga kissin din wuyarta, tayi baya xata fadi ya tallabota da sauri snn ya kwantar da ita a hankali ya shiga shafata ta kasa hanasa, ganin idan ya ci gaba da hkn baxae iya hkura ba yasa ya dago ta yana kallonta da kyar yace "fateema," ta daga kai tana kallonsa ita ma da kyar don gaba daya yanayinta ya canxa, ya kauda yace "meyasa kike walakantani hka ne kike cutata," tayi tsaki bata ce komai ba, ya ci gaba "kiyi hkuri ki koma dakin ki, ni nayi maki alkawarin baxa a sake jin kan mu ba," tace "ae bani kadae bace matarka da xaka damu kanka a kaina, kuma ni bana sonka" yyi murmushi yace "karya kike yarinya ga sona nn ina hangowa cikin idonki, ni dae ne bana sonki i only need yhu badly, amma xanyi kkri naga na koyi sonki sbda kids dinmu" ta fashe da kuka ta mike tsaye tana kallonsa tace "ka yaudari kanka idan kayi tunanin ina sonka, uwar me xanyi da wanda baya ganin mahaifiyata da gashi ma dae tukun, i hate yhu Aliyu," ta juya da sauri ta shige dakin inna tana kukan takaici, wae he only need her dama tasan kawae don ya dinga biyan silly bukatarsa yasa yake son ta koma gidansa. Ya sauke ajiyar xuciya ya mike ya fita daga falon, inna tace ina xaka" yace ina xuwa inna, sashinsu inteesar ya nufa, yyi sallama can kasa ihsaan ta amsa ya bude kofar ya shiga falon, momy na xaune tana feed din ihsaan, ya nemi gu ya xauna kansa a kasa ya gaisheta, ta amsa da "qlau," yyi shiru na kusan minti biyar tana ta harkan gabanta, a hankali ya fara magana yace "wajen ki na xo momy," ba tare da ta kallesa ba fuskarta a daure tace "ni kuma . Aliyu ya dan yi shiru snn yace "dama so nake don Allah ki taimaka kiyi ma Fateema magana ta koma dakinta, don xata fi jin maganarki," momy tayi masa wani mugun kallo tace "lallai ka cika mara kunya, kasan da warce kke magana kuwa, to fice min a falo tun kan na baka mamaki," ya sunkuyar da kansa ya dan yi murmushi bbu yabo bbu fallasa yace "ae dae don Allah nace," cikin tsawa tace "ka fice min a falo tun banje na hadaka da ubanka ba, da can ni na raba ku da xan hada ku ynxu, lallai ka cika fitsararre mara tunani" ya mike yana murmushi ya fice daga falon, tayi tsaki ta shige bedroom dinta ranta a bace. Sashin inna ya koma, inna na xaune da inteesar tana shafa mata bayanta wae xuciyarta na tashi, daga bakin kofar yana kallon inteesar yace "in har kika koma gidana to baki cika yar halak, kiyi ta xama gidanku, cikin ma in kinga baxa ki iya ba kya iya xuwa ki xubar da shi ynxu," ya ja dogon tsaki ya sake labulen ya juya yyi gaba, inna da ta kasa rufe baki ta mike da sauri ta bi shi tace "ka dawo ka bata takardarka don uwarka, idan ba kaddara ba me xae kaita auren mahaukaci," ya juya yana kallon inna yace "sae dae in ku ne ke hauka," yyi gaba abunsa. Inteesar da komai nata ya tsaya ta kasa cewa komai sae hawayen da take, inna ta shigo tace lah meye abun kuka, ki rabu da dan iska wllh na kashe aurenku ynxun nn, ya ya kuma ki haifesu ki bani na kai masa ya basu nono, inteesar dae bata ce komai ba amma duk jikinta yyi sanyi, ta bar inna na ta surutunta har kusan karfe goma snn tayi mata sae da safe tayi bangarensu jikinta a mace, momy bata yi bacci ba tana xaune falo, ta shiga daki ta kwanta ta lumshe idonta duk da tasan ba bacci xata yi ba, momy ce ta kirata ta fito falon ta xauna tana kallonta, momy tace "kina ji na fateema," ba hka nn momy ke kiran sunanta ba don hka ta nutsu tana sauraran me momy xata ce mata, momy tace "duk me xan ce maki a nn kar kiyi min musu, yhu obey b4 complain kinji" kai kawae inteesar ta gyada mata. Momy tace "ki shirya ki koma dakin ki gobe da safe," inteesar ta tsaya kallonta da mamaki, nn da nn hawaye ya cika idonta, xata yi magana momy tace "ban son naji abinda xaki ce, ba don bana sonki nace ki koma dakin ki ba fateema, sau biyu Alhaji yana min magana nake shashantarwa don har cikin raina ban son aurenki da yaron nn, but ynxu ina da dalilin cewa ki koma dakin ki, kiyi hkuri kinji inteesar Allah xae shige mana gaba, kuma ga matan gidan nn sae yada ki a waje suke wae ae ya sakeki, hkn ne ma yasa Alhaji yyi min magana nace maki ki koma dakin ki, idan lkcn haihuwarki yyi sae ki dawo gida ki haihu, ki kwantar da hnkalinki inteesar lkcn da ni da kaina xan bukaci Alhaji yyi masa magana ya baki takardarki na nn xuwa don ko bayan raina ni ban yrda kici gaba da xama da Aliyu a matsayin mijinki ba, " inteesar tayi shiru ta kasa cewa komai jikinta yyi sanyi jin furucin momy na karshe, ta tabbatar da ta gaya ma momy irin cin mutuncin da yyi mata daxu da baxata fara cewa ta koma gidansa ba, sae ta samu kanta da kasa gaya ma momy abinda yyi mata, ta mike a sanyaye tayi ma momy sae da safe ta shiga bedroom ta kwanta, duk da ta so tayi kuka ko xata ji sanyi amma sae ta nemi kukan ta rasa. Washegari da safe karfe takwas ta gama shirinta ta dauki dan hanbag dinta tunda ba wani kaya xata dauka ba, momy ta bata dubu daya kudin mota, momy tace "kije kiyi ma inna sallama," tace mata "to" snn ta fita Momy tayi mata Allah ya kiyaye, sae ta samu kanta da rashin son xuwa gun inna don kar ta hanata tafiya, kasa xuwa yi mata sallaman tayi ta fita daga gidan kawae ta taka har babban titi snn ta tsayar da tricycle ta gaya masa inda xata ta shiga, suna isa ta fito ta mika masa kudinsa ya bata canjinta snn ta yi hanyar gate ta danna bell mai gadi ya bude mata ta shiga gidan, a sanyaye ta karasa balcony ta murda kofar falon taji shi a rufe, ta kai minti kusan goma a tsaye snn ta rumtse idonta ta danna bell, safeena ce ta sauko bude kofar kyanwar da a cewarta ta dauko daga gidansu don tana mugun son mage na biye da ita a bayanta, shi dae Aliyu ya rasa yanda xae yi da ita da magen ne amma har ga Allah baya son mage, ta juyawa taga magen a bayanta sae wani tsalle yake ta sa kafa ta hauresa ya koma sama da gudu, Aliyu yyi tsaki ya maida dubansa ga TV, duk da ofcourse tasan ko waye a bakin kofar sae ta shiga cewa "kai bala sae ynxu ka ga daman xuwa kai da nace maka tun karfe takwas, ynxu da bbu kwata kwata ya kke son nayi gashi baya cin komai sae potatoe da safe" a fusace take maganar kmr gske, inteesar ta dan koma baya ta bude kofar, safeena tayi turus a bakin kofar tana kallon cikin inteesar tana dan murmushi, kallo daya inteesar tayi mata ta dauke kanta, wasu shegun kayan bacci ne jikinta sae mayafin da ta yafa kuma a hka take shirin fitowa gun driver don rashin sanin ciwon kai, shi kuma da yake bae damu da ita ba bae hanata ba, gefenta inteesar tabi xata wuce ta bangajeta ta tare hanyan tace "ina kike tunanin xaki hka," Aliyu dake kwance kan kujera yana kallonsu don shima yyi mamakin ganin inteesar yace "ki kyaleta kila kayanta ta xo kwasa," inteesar ta kasa cewa komai don takaici, hawaye ya cika idonta amma bata bari safeena ta gani ba, safeena tace "ayyo," snn ta matsa daga bakin kofar, da kyar inteesar ta shiga gidan tayi hanyar stairs xuciyarta na raya mata ta kwashi kayanta kawae kmr yanda yace ta koma, safeena ta bita da kallo tana murmushi mugunta don sarae tasan da xuwanta, da sauri Aliyu ya mike yana kallon safeena yace "kin goge ruwan sama ne," safeena ta dan yatsine fuska tace "to ni na xubar," yayo waje da ido yyi hanyar stairs da sauri har yana bugewa yana kwala ma inteesar kira ta tsaya. Gano abinda yake gudu Safeena tayi ta bisa da sauri gabanta na faduwa don mugunta a xuciyarta tace kai abu biyu xae hade mata knn da sauri kan ya haura sama tace "kai wasa nake na goge," ya juya yana kallonta amma hankalinsa bae kwanta ba, xae yi magana yaji inteesar ta fasa wani raxanannen ihu a sama, ya haura sama da sauri yana cewa "innalillahi wa inna ilai hi raji'un," safeena ta doka uban tsalle ta shiga kiran uwarta hannunta na rawa, uwar ta daga tace "wayyo momy mutumin nn ya iya aiki ta xo wllh," da sauri Hajiyar tace "to magen fa ta ganshi," safeena tace "ba dole ba ae mutumin ca yyi yana jin kamshinta xae fito yana jiranta da na xo bude mata kofa kar ki ga yanda ya biyo ni da gudu, wato yaji kamshinta, na sa kafa na hauresa ya koma sama ya jirata a can, ae ko da gudu ya koma momy har wani rawa jikinsa fa yake, kuma kinsan me momy abu biyu ya hade mata Aliyu ya xubar da ruwa sama yana jira in goge naki gogewa kinga tana hawa sama tsantsin ruwan xae kwasheta sae kuma ga aljanar magen ma na jiranta, ae ciki kam kema kinsan sae lbri momy" ji tayi Aliyu na kwala mata kira a rude, safeena tace "xamuyi waya anjima momy gashi can yana kirana," ta katse kiran xuciyarta fal murna ta haura sama cikin muryan tashin hankali da tsoro take cewa "me ya faru Honey ruwan bae gogu bane, *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** . Aliyu na rungume da inteesar dake ta kuka tana shisshigewa jikinsa safeena ta hauro sama, cikin tsawa yace "me kika ce min," da sauri ta sauka kasa ganin yanayinsa, ya dago inteesar yana girgixa kai cikin tashin hankali yace "ta ina kika fadi fateema," kin bude idonta tayi amma jikinta sae rawa yake, duk a xatonsa xafin ciwo ne yasa take haka, duk ya rikice mata ta gaya masa ta yanda ta fadi da kyar ta dago kanta tana kallonsa muryarta na rawa tace "ni ban fadi ba, wata mage ce...." sae ta kasa karasa ta fashe da wani matsanancin kuka ta fada kanshi jikinta na rawa, yyi shiru yana yana kallonta, dagata sama yyi ya bude dakinsa ya shigar da ita ya kwantar snn yace "magen ne ya tsorata ki?" kai kawae ta gyada masa ya juya xae fita ta rikosa da sauri tace "kar ka tafi ka barni yaya," ya durkusa gabanta yana goge mata hawayen fuskarta yace "baxan tafi in barki ba," ya mike ya fice daga dakin, dakin safeena ya shiga, ya tarda ita tsaye tana waya, da sauri ta katse wayan tana kallonsa a tsorace, bae ko kalleta ba yyi gun magen dake labe gefen madubinta, ya finciko ta, safeena ta yo waje da ido a tsorace tace "me xaka yi Aliyu, me tayi maka" bae ko kalleta ba ya buga magen da bango tayi wani shegen kara kmr ba mage ba ya sake bugata da karfi, snn ya bude window ya cillata downstairs ya juya yana nuna safeena da yatsa yace "daga yau kika sake shigo min da ko wani irin dabba gidan nn daga ke har dabban sae na wurga ku downstairs," har ya fita ya dawo da sauri ya shaketa yana huci yace "kika ce min kin goge ruwan," xata yi magana ya xuba mata tagwayen mari snn ya jefar da ita yace "kuma Allah ya baki sa'a kar ki goge," ya juya ya fice daga dakin ya koma dakinsa, tana kwance ta dukunkune waje daya ta kasa daina tuna magen, ya karasa kusa da ita ya dago ta yana kallonta . Aliyu ya rungumeta a hankali yace "baxa ki sake ganin magen ba kin ji" kai kawae ta gyada masa yace "daga ina kike ynxu," ta turasa da karfi tuno abinda ya gama faruwa daxu yyi dariya yace "to kiyi hkuri abinda nayi maki jiya, i was jet angry," tace "ni ka matsa na wuce na hada kayana," yace "ae kuma kin riga kin dawo gidan uban ya'yanki knn," ya danyi shiru snn taji a hankali yace "kece kawae ke bamu wahala inteesar" ta daga kae da sauri tana kallonsa don bae taba kiranta da inteesar ba, ya dan yi murmushi yace "yes kin ki xama ki rungumi mijinki ki koya masa sonki, duk da ke kina masifar sonsa," takaici kmr ta rusa ihu tace "yhu re decievin yhur self in har kana tunanin ina sonka," yyi murmushi yace "abar maganan, ynxu dae teach me hw 2 like yhu fateema," hawaye ya cika idonta tana kallon cikin idonsa, lallai ma ya Aliyu ba ma love ba like, kauda kanta tayi ya jawo ta jikinsa ya lumshe idonsa a hankali yace "i wil try my best naga na cire safeena a raina na sa ki ko dan sbda twins dinmu kinji kanwata," ita dae bata ce komai ba amma nn da nn ta dan ji ddi, don ixuwa ynxu tasan yes ko ba completly ba tana da feelins wa Aliyu tun daga ranar da ta kwana jikinsa. Ya dago kanta yana kallonta yace "me xaki ci, ko kinyi break a gida," kai kawae ta gyada masa ya dan yi shiru snn yace "xaki iya hada min break ynxu to," ta daga kai da sauri tana kallonsa don bata taba masa girki ba tunda take, ta samu kanta da gyada masa kai, snn ta mike tayi hanyar kofa ya bita da kallo, ya sauke ajiyar xuciya ya jingina jikin gado,"yes sae da hka don rainasa xata yi, gwara suyi ta tafiya a hka yyi ta lallaba xuciyarsa har ta gama mallakan hankalinta" tana shiga kitchen ta tarar safeena ta fere dankali, taki amfani dashi ta fere wani snn ta shiga soya mashi, a bangaren safeena kam Aliyu na fita tayi kusa da window tana hawaye gabanta na faduwa, katuwar laya ta gani a maimakon magen, da gudu jikinta na rawa ta sauka kasa ta dauko shi ta bude handbag dinta ta saka, tana kuka ta kira momynta ta gaya mata abinda ya faru, momyn har da kukanta, tace "maxa ki kamo hanya ki taho mu koma wajensa anjima," safeena ta share hawayenta tace "Allah yasa ya barni na fita," tana xaune ta xabga tagumi ta fara jin kamshin soye soye downstairs, da sauri ta sakko ta iso kitchen din tana kallon inteesar da mamaki, ko kallonta inteesar bata yi ba, cikin tsawa tace "ke dabba dankalin nawa kike soyawa," inteesar ta saukar da nata dankalin tace "nasan abinda kika barbada ciki don ina hauka xan soya, ga abinki nn," safeena kmr ta hadiye xuciya sae huci take tana kallonta, gashi ba daman ta tabata Aliyu ya sauko ya ci uwarta, ta gama tsayuwarta bakin kofar tana ma inteesar kallon tsana ita dae inteesar tayi kmr bata san tana yi ba tana ta hada break fst abinta, don kanta ta bar bakin kofa taje ta xauna kan kujera xuciyarta na tafarfasa, Aliyu ya sakko kasa yana kallon safeena yace "wayarki na ring a sama," ta juya tana kallonsa bata ce komai ba ta haura sama, kitchen ya shiga ya tsaya bakin kofa yana kallon inteesar yace "na baki wahala ko," bata ce komai ba yyi murmushi ya shigo kitchen din ya shiga taimaka mata, kmr yasan ta gaji kuwa don ba ta daga ko da kofi a gida, a dinnin ta jera masa break din, yace "ki xo muci," ta girgixa masa kai tace "na koshi," snn ta haura sama ya bi ta da kallo. Ta gama gyaran dakinta tayi wanka tana kwalliya gaban madubi ya shigo, kallo daya tayi masa ta madubi ta dauke kanta, yace "xo ki ga abu kanwata," tayi bnxa dashi har sae da ya karaso snn yace "magana nake," bata ce komai ba ta mike ta bi sa, wani daki ya bude mata ta shiga shima ya shiga, shiru tayi tana kallon dakin, yyi murmushi yace "dakin twins dina ne nn," ta tabe baki tace "ae sae ka ta gani," ta juya xata fita ya rikota yace "baki duba kayan bbies din ba ko sun maki," ta dan yatsine fuska tace "sunyi," bae sake ce mata komai ba amma bae ji ddin reaction dinta ba, ta fice ya bi bayanta, dakinta ta koma ta kwanta, shi kuma ya shiga dakinsa, karfe sha biyu ya shigo dakinta sanye da farin shadda da yake ranar juma'ace, ya karaso kan gadonta ya xauna yace "ni xan tafi masallaci," ba tare da ta kallesa ba tace "Allah ya kiyaye," ya mike tsaye yace "Ameen, 4 once ki gyara min bedroom dina don Allah, idan xaki iya girki kiyi idan baxa ki iya ba kar ki takura kanki," kai kawae ta gyada masa without much interest, ya karaso kusa da ita yyi kissn din cikinta ta turasa tana hararansa ya fice yana murmushi, meye amfanin abubuwan nn da yake mata tunda shi da bakinsa yace baya sonta, hasalima like dinta xae yi kkrin yaga ya fara yi, hkn yasa ta fashe da kukan takaici, muryarsa da safeena taji a compound ta mike da sauri taje tana leken window, tare xasu fita da alamar xae ajiye ta wani gun, ya bude mata gaban mota ta shiga snn ya xaga ya shiga driver sit ya ja motar suka fita daga gidan, jikinta yyi sanyi hka kawae taga kuka ya xo mata, taci kukanta na kusan minti talatin snn ta mike don xuwa ta gyara masa bedroom dinsa . ina Godiya da adduoinku na alkhairi gareni inasamun sakon gaisuwa ta wurare da dama Nagode sosai inajin dadi sosai yayin Dana ga anamin addua Nagode. Duk da fes taga dakin nasa don ya Aliyu ba baya ba wajen tsafta barin ma ansan duk inda likita yake tsafta na nn, hkn bae sa taki yi masa gyara mai kyau ba, don har da bedsheet sae da ta canxa masa tasaka na da a washin machine ta fito ta ci gaba da gyara masa dakin har drawers sae da ta bude ta hada masa duk kayan alluransa da medcines guri guda, ta dauko ruwa da freshner tayi moppn din dakin snn ta shiga dakinta ta dauko burner na turaren wuta ta xuba turare ciki ta jona masa a dakin, ta shiga bayi shima ta tsaftace shi, singlet dinsa da short nickers dake cikin bathroom din taji tsoran wanke masa kar ya ci uwarta, ta wanke xanin gadon kadae da taimakon washn machine tayi drain dinsa snn ta fita xuwa garden ta shanya, har xata rufe bathroom din don ta gama dashi kawae tace bari ta wanke masa inners din dae, cikin minti sha biyar ta gama wankin ta hada har da jallabiyansa biyu da dardumansa taje ta shanya su a can garden suma har wani jiri take gani don gajiya, kitchen ta shiga tana tunanin abinda xata girka, shinkafa ta daura ta koma sama ta shiga dakin ta kashe burner dinta don kamshi kam har falo ta mayar dakinta snn ta koma dakin don ta sake labulaye, taji waya na ring ta shiga neman wayan, can bedside drawer ta ga wayan kan wani babban buk, kuma har nn ta gyara amma bata lura da wayan ba ta dauka tana kallon nambobin ganin bata san ko waye bane yasa ta ajiye masa wayar inda ya ajiye, har ta juya xata fita ta dawo da sauri tana kallon littafin da ya daura wayarsa kai, ta dauki buk din tana kare masa kallo dis is d second tym da take ganinsa, wae his diary, ta dan tabe baki ta dauka xata je ta ajiye masa inda ta jera masa litattafen da ta gani kan study desk, har ta ajiye ta girgixa kai ta dauko shi, yau sae taga me ke cikin diary din nasa, durkusawa tayi kusa da gado yanda xata ji ddin karatun tana rike da diary din taga hotuna sun xubo kasa, ta ajiye diaryn kan gado ta kwashi hotunan da sauri don ta ga na menene . . Inteesar tayi still komai nata ya tsaya ganin wani hotonta lkcn graduation dinta na primary tana da shekaru sha daya lkcn, ta kasa daina kallon hotan da mamaki, sanye take da graduation gown tana rike da testimonial dinta na primary sch tayi murmushinta mai kyau, ba karamin kyau hotan yyi ba, jikinta yyi sanyi ta ajiye shi snn ta dauki wani hoton tana kallo, ta bude baki da mugun mamaki tana kallon hoton hannunta, hotan graduation dinta ne na junior sec sch shima tana rike da testimonial tayi murushinta mae kyau har sae da beauty point dinta ya fito, da kyar ta ajiyesa ta dauki wani, wnn xaune take ta dan duka kanta amma ana iya ganin fuskarta maths texbuk gabanta tana assignment duk hankalinta na kan abinda take, ba karamin kyau hoton yyi ba kuma da gani a falon inna ne, shima ta ajiye shi da kyar ta dauki wani, shi kuma wnn tana kwance ne falon inna sanye da singlet fari da xani idonta lumshe alamar bacci take hoton yyi kyau ssae duk siffar jikinta sae da ya fito tsoro ya kama inteesar ta ajiye shi da sauri ta dauki wani, shi kuma tana xaune abinci na gabanta fuskarta daure, ko me take kallo gefenta oho, naxari ta tsaya tayi ssae ta tuna ranar kusan 2yrs bck ne bata da lfya inna ta sa ta gaba ta ci abinci, ta ajiyesa da kyar taga durkushe bae ganta ba, ta xauna kan tiles din ta dauki wani hoton tana kallo shi kuma wnn a tsakar gida ne tana dariya da alamar da su xainab ne riga da skirt ne jikinta kanta ko dankwali bbu, tayi shiru kmr me son tuna ranan, yes Aliyu ne ya koresu kowa yyi bangarensa da gudu ranan, ta ajiyesa jikinta a sanyaye ta dauki wani, shi kuma tana durkushe kanta a kasa ko me take xubawa oho, inteesar duk ta rikice tsoro ya bayyana a fuskarta, to wa innan hotunan daga ina, hka ta dinga kallon hotunanta kala kala kuma gaba daya bata ga wanda take kallon camera ba sae na graduatn, sae kuma wa inda taga sunyi tare da su Zainab shi kuma lkcn sllh ne wnn, hoton da yafi daure mata kai bae wuce wanda ta ganta daga ita sae dan jumper da karamin skirt ba, kuma wae dariya take, yawancin hotunan duk tana bacci aka dauketa, hoton graduatn dinta na ss3 kadae ne bata gani ba, amma duk hotunan da suke yi da sllh ta gansu, ta ajiye duka hotunan da kyar ba tare da ta gama ganinsu gaba daya ba ta bude Diaryn, makullin mota ta gani a tsakiyar ta ajiye makullin ta maida hankalinta kan rubutun da ta gani boldy saman sheets din dairyn, "will never 4get our 1st nyt Inteesar," wani mummunan faduwa gabanta yyi, jikinta ya dau rawa, a hankali ta saukar da idonta kan rubutun dake kasan heading din, "baxan manta da daren farkon mu ba inteesar, i knw na maki ba dae dae ba but find a place in ur heart 2 4give me, it was'nt intentionally sonki ne ya jawo hka duk da banyi niyyar yi maki komai ba bbyna, i so much hurt yhu......" inteesar ta fashe da wani matsanancin kuka ta kasa karasa karatun, kuka ssae ta shiga rerawa, ta ajiye dairyn tayi mai isarta snn ta jawo ta bude wani page din kuma, "i fell in love with her ryt 4rm d vry 1st day i set my eyez on Her, Fateema Inteesar" kasa ci gaba da karatun tayi duk tunanin ta ya tsaya cak, tun tana karamarta bata wuce shekara biyar ba tasan Aliyu, kuma tun lkcn take mugun tsoransa kmr mutuwa, hasalima idan tayi laifi inna xata tsorata ta ca take xata kira mata Aliyu jikinta ya dingi rawa knn har tayi bacci ranar ko sau daya bae taba wasa da ita ba tana karamarta suna hada ido yake xaro mata dara daran idonsa ta fasa ihu ta ringa kuka knn har ya bar gidan ranar, in yaxo gidan inna knn lkcn tana karama, hannunta na rawa ta bude wani page din wae dan ma ba accordingly take budewa ba, "2 day is d happiest day of my life, she is now mine, mine 4 ever Fateema inteesar," hawaye kadae ke bin kuncinta duk ta rikice, wae duka wa innan abinda take gani ita Aliyu ke nufi ko wa, a hankali ta dawo farkon page din don ta tabbatar da dairy din nasa ne, sunansa ne boldly a gaba, Aliyu Abubakar Yusuf, farkon page din abinda ta gani shine "Allah kai ka jarabceni da son Fateema, ya Allah ina rokanka ka bani ita a matsayin matata uwar 'ya yana, ka saka mata sona a ranta kmr yanda ka saka min nata a raina, ina sonki inteesar ina sonki inteesar fiye da yanda ni kaina nake tunani, na rasa yanda xanyi da sonki, kullum mafarkina baya wuce na Allah ya mallaka min ke a matsayin matata, i donno hw 2 approach yhu inteesar, kece dalilin xamana a kano inteesar, ban san wani irin so nake maki hka ba...." ajiye diaryn tayi a tsorace ta koma baya tana kuka ssai. Kuyi srry sisters yau bana gida ne wllh shiyasa kuka ji shiru . Kuka ssae inteesar ke yi, bata sake bude diary ba kuma, ta dafa gado xata mike daga wajen ta kasa hkn yasa ta koma ta xauna kawae tana hawayen da bata san dalilinsa ba, ta kai minti kusan sha biyar a hka taji an bude gate tasan shine ya dawo amma bata yi kkrin yin komai inda take ba, ya kai minti kusan bakwae kafin ya hauro sama taji ya bude kofar dakinta, bayan kmr minti biyar ya fito ya bude nasa dakin, mutuwar tsaye yyi daga bakin kofar, ya dau lkci tsaye yana kallonta snn cikin tsawa yace "me kike yi a nn....." ita dae har lkcn bata juyo ba, kuma bata tanka masa ba, dakyar ya karaso cikin dakin ya durkusa bayanta ya fixgota har wani rawa hannunsa yake yace "diary dina kika bude don baki da kunya fateema, how dare yhu" bata ce masa komai ba ta shiga tattara hotunanta dake baje a wajen snn ta mike da kyar tayi ball da dairyn cikin tsawa tace "yhu re deceiving yhur sef Aliyu, tun wuri dare bae maka ba kaje ka samo Fateema inteesar din da kke magana a wnn shegen takardar taka, amma ba ni ba, i hate yhu Aliyu bana sonka Allah ya isa tsakani na da kai," ta karashe maganar da wani matsanancin kuka ta fice daga dakin nasa da sauri rike da hotunanta, yyi murmushin takaici ya dafe kansa da yyi masa nauyi hawayen dake makale a idonsa ya gangaro "yes yasan irin wnn ranan na nn xuwa dama," inteesarna shiga dakinta ta xube kan gado ta dinga rusa kuka kmr an aiko mata da sakon mutuwa, lkci daya taji wani mugun tsanar Aliyu ya dirar mata a xuciya, taji ko ganinsa ma bata sonyi. Tana nn kwance yanda take har dare, ya shigo dakinta da sallama can ciki, abinci ya ajye mata bata ko kallesa ba ya fice,hka ta kwana ranan ko kallon abincin bata yi ba abun duniya ya isheta wae ita Aliyu ke so. Hka suka ci gaba da xama a gidan har na kusan sati daya baya ce mata bata cemasa, ganin ko ya kai mata abinci ma ba ci take ba sae dae ta fito ta dafa yasa ya daina kai mata, kwata kwata ta canxa a gidan hartsoro ma take basa, lkci daya safeena ta lura da irin xaman da suke ta dinga shissige masa ita matar kirki mai yi masa biyayya. Ranar inteesar na kitchen tana dafa jollof rice din da xata ci ta ma gama knn tana xubawa a plate taji kakarin aman safeena a nn falo, ta leko tana kallonta, Aliyu ma ya sauko yana kallonta yace "me ya faru," ta langwabe da kyar tace"nima ban sani ba tun safe nake amai xuciyata ke tashi gashi sae inyi ta jin yawan kasala a jikina baki na ma ba ddi," ya karaso gabanta yana kallonta sae wani lullumshe ido take, ta fara kakarin wani aman, Aliyu yace "ba komai ke damunki ba illa malaria, ltr kije clinic su baki magani," yana kai wa nn ya juya ya koma sama, inteesar ta fito rike da plate din abincin ta ta haura sama ita ma, safeena taji kmr ta nutse kasa don kunya ita nn fa a dole ciki ne da ita kmr yanda suka tsara da mamarta. Don takaici har da kukanta ta kasa tashi daga inda take, inteesar ta sauko kasa daukan ruwa safeena tayi hanyar stairs da sauri ta tsaya tana huci, inteesar ta dauko ruwan xatakoma sama safeena taki bata hanya ta gaji da tsayuwa tace"ki bani hanya na wuce," safeena na hararnta tace "ki tura ni ki wuce," inteesar tace "yau naga ikon Allah ni nace kije a maki treatment din malaria da xaki huce kaina," inteesar bata rufe baki ba safeena ta tura ta da karfi tayi baya xata fadi ta fasa ihu duk da bata fadin ba don ta tsorata, Aliyu ya fito da sauri yana kallon Safeenar yace "me kika yi mata," safeena ta galla masa harara tace "ban sani ba," inteesar dake durkushe wajen tana kuka ta fixgo safeenar a fusace tace "ki bani hanya nace" safeena da ta tashi sae ta kwashe ta da mari, haba Aliyu ya fixgota ya shiga jibgarta yana marinta kmr an aiko sa, inteesar ta haura sama abinta ta bar su nn tsaye. Sae da yaga bata motsin kirki snn ya kyaleta ya haura sama tayi kuka kmr ranta xae fita duk ya faffasa mata baki da hanci, da kyar ta haura sama ta dauki hijabinta tayi gida a xuciyarta tana cewa "ae yautaki ta kare yarinya sae dae wata ba ke ba," Inteesar na shirin kwanciya da daddare ya shigo dakinta, bata ko kalli idan yake ba bare shi kansa ta gama shirinta ta shige bargo ta kashe wutan dakin ta kwanta, da kyar ya dawo gefenta ya xauna a hankali ya kira sunanta tayi kmr bata ji sa ba, hkn yasa ya hau gadon ya xauna dab da ita kan yyi magana ta mike xaune a fusace ta fara masifa "ni malam ka rabu dani mana, wnn wani irin wlknci ne, ka bar ni nayi bacci na mana xaka xo ka sa ni gaba kmr ina binka bashi," hawayen da tagani idonsa ne yasa ta fashe da kuka a raunane tace "ka rabu dani ya Aliyu don Allah nake rokon ka" ya kauda kansa da kyar ya fara magana"don kin gano ina sonki shine xaki fara min wlknci fateema, abinda na gudan ma kaina knn tun farko ban nuna maki so ba....." muryarsa ta to kare ya kasa cewa komai kuma, cikin kuka tace "ka min abinda baxan taba mantawa ba a rayuwata Aliyu, tun ina karamata kke cutata har xuwa girmana, rana guda kuma kace min tun ina karamata kke sona hka ake son dama, to Allah yatsare mu da irin wnn son, Aliyu ya dafe kansa ya kasa cewa komai, ita kam kuka kawae take, da kyar ya dago yana kallonta muryarsa na rawa yace "wllh summa tllh tun baki san kanki ba nake son ki fateema, i just cant bear it she yasa kika ga nake maki abubuwan da nake maki Fateema, ke fa ce dalilin xamana a kano, kema kinsan i am nt suppose 2 b here, a lgs nake rayuwata," ya rungumota tsam tsam jikinsa ya saka mata kuka kmr karamin yaro, "wllh ina sonki fateema ina sonki, diary na gskya ne kece mace ta farko da na fara so a duniya tun baki xama mace ba bayan ke kuma ban sake son wata mace ba har yau Fateema, ki soni plss kar kice xaki rama abinda nayi maki wllh wllh duk cikin so ne Fateema, ban san wani irin wahalallen so nake maki ba hka" kuka take yi ssae ta kasa cewa komae shima yana taya ta, ita har lkcn ta kasa yrda wae Aliyu ne ke mata kuka wae yana sonta, ta shiga xamewa daga jikinsa ya rikota da sauri yace "no inteesar kice wani abu don Allah," ta fashe da wani matsanancin kuka tace "ni baxan iya yrda ba Aliyu, let me be," kin sakinta yyi hkn yasa ta rungumesa ita ma tana kuka ya daura fuskarsa kan nata hawayensa na xuba kan nata, sun kai kusan minti goma a hka snn ta turasa daga jikinta, ta koma ta kwanta jikinta a sanyaye ta juya masa baya shima ya kwanta ya jawo ta jikinsa ta bayan, a kunnenta taji yana rada mata "ki yanke min ko wani hukuncin da kika ga ya dace da ni Inteesar, i deserve it but kar ki xaki rabu dani" ya karasa maganar muryarsa na rawa, bata ce komai ba sae ajiyar xuciyan da take, muryarta na rawa ita ma tace "Ya Aliyu duk cikin so ne kke dukana kmr jaka," ya runtse idonsa kmr tana ganinsa snn ya saka fuskarsa cikin gashinta yace "wllh duk cikin so ne inteesar, sonki yana cutar dani shiyasa nake maki hkn ko xan ji ddi na samu natsuwa a raina amma sae na gane duk hauka ne," ta girgixa kai alamar bata gamsu ba, a hankali yace "baki yrda ba ko?" tace "eh," ya dan yi shiru snn yace "da kin lura da lkcn da nafi dukanki to lkcin da ku ke tare da Faruuq ne, ina mugun kishinki fateema, ko Haisam ban son ganinku tare, sae na kasa bacci ranan, har abinci ma fita raina yake, dalilinki na tsiri xuwa gun inna ba dare ba rana na mayar da falon inna ya xama wajen yinina kullum, sbda ke na fara xama bakin gate fateema don bana son ki fita a gane min ke, idan na yini ban ganki ba har xaxxabi nake yi" a hankali tana girgixa masa kai tace "duk cikin so ne kayi min dukan da yasa na kusa mutuwa a gida ya Aliyu? kuma duk cikin so ne Abba yace kayi treatn dina ka karbi kudin treatment dinka kuma duk cikin so ne kki dawowa kayi treatn din nawa duk da ka karbi kudi bayan kasan halin da nke ciki? duk cikin so ne ka karbe dubu biyar din da ka bani gidan Anty Nafeesa, kuma duk cikin so ne ka ki daukata a motarka ranar a gidanta ka gwammace na shiga na haya? duk cikin so ne kke nuna bako son gani na a gidanku, kuma duk cikin so ne kke bibiyata kullum a gida don ka dokeni ko ka cuce ni? duk cikin so ne kke ma kanninka abu ni baka min hasalima baka son ace kayi min idan ma kaga wani yyi min sae ka kwace? duk cikin so ne ka shiga tashin hnkli lkcn da yace Abba xae hada mu aure, kuma duk cikin so ne kayi treatn dina kan xaka yi stab dina idan na yrda na shigo gidanka a matsayin matarka? duk cikin so ne ka shareni bayan an kaini gidanka 4 d past 1 wk baka san da ci na ko sha na ba, kuma duk cikin so ne ka rabani da pride dina a walakance kayi rapen dina? duk cikin so ne kke cutata kke dukana duk da ina gidan ka a matsayin matarka, kuma duk cikin so ne kayi min kishiya? duk cikin so ne baka son nayi futher din karatuna, snn more importantly ina son ka gaya min me mahaifiyata tayi maka meyasa kke mata abinda kke mata, meyasa...." ta kasa karasa maganar ta fashe da wani matsanancin kuka da kyar tace "idan baka bani concrete amsoshin da xa su gamsar dani ba ban yrda kana sona ba ya Aliyu kuma har abada baxan yrda ba, kuma baxan yi fatan ci gaba da xama da kai a matsayin mijina ba" ta share hawayenta a hankali tace "ina sauraranka," kya ji dashi, don ma kin samu munce muna sonki, . ....Aliyu ya mike xaune yana kallonta a hankali yace "baxan iya cemaki komai ba Inteesar its of no need don ba lallai bne ki yrda, amma bari na dauko maki diary na don nasan ba lallai bne kin karanta duka, komai na ciki inteesar abinda nayi maki da dalilin da yasa na maki hkn, duk da daga baya naga tamkar jahilci ne na dinga yi, idan har kin yrda dani to dubu biyar din nn na nn a ajiye har yau na ajiye maki ban taba ba, i swear Inteesar ina kaunarki fiye da yanda xakiyi tunani, momy kuma...." sae yyi shiru, ta dago kai tana kallonsa ya kauda kansa yace "xanje na bata hkuri," ta mike xaune tana kallonsa tace "baka da abinda xaka kare kanka a nn knn, wato tsabar rainin hankali ne yasa kke yi mahaifiyata rashin mutunci, to ka sani..." da sauri ya rufe bakinta yace "wllh wllh ba hka bne Inteesar, ni dae a iya sanina bbu abinda ya taba hadani da ita, just dat bana gaisheta amma ni ban taba mata rashin kunya ba sae ranar da nayi maku duka gaba daya a gida, na dawo Kano 5yrs bck ranar da na shigo gida muka hadu da momy na gaisheta bata amsa min ba bansan ko bata ji bane though, kuma gaban Hajiya hkn ya faru, yes frm ranar ta hanani gaisheta wae hka take ma mutane, ni kuma banyi wani tunani ba daga ranar nayi vow baxan sake gaisheta ba," kinji dalili inteesar amma xanje na bata hakuri gobe sae muje tare Abba ma na basa hkuri, Allah yyi yau ne karshen wahalata inteesar," ita dae bata ce masa komai ba sae hawayen da take, yace "kiyiHkuri ki yafe min inteesar, nasan har ynxu kina kokwantan son da nake maki amma bari na dauko maki dairyn ynxu na fara karanto maki daga farko don ki yrda da abinda nake gaya makita girgixa masa kai tace "ka barshi kawae bana so," yyi shiru yana kallonta snn a hankali yace "baki yrda ba knn ko inteesar," ta girgixa masa kai kawae tace "gobe ma duba," ya rungumota yana murmushi a hankali yace "Allah sarki bbyna Allah ya bar min ke har karshen rayuwata yasa baxan sake bata maki rae ba ko ba tare da na sani ba, wanda nayi maki maa baya ma Allah yasa ki samu waje a xuciyarki ki yafe min duk da sonki ne ya janyo hka," ta dago a hankali tana kallonsa ya daura goshinsa kan nata yace "kin ga makullin motar ki a diaryn?" tayi shiru bata ce komai ba yyi murmushi yace "1st nyt dinmu na mallaka maki motar yana cikin garage a kulle," bata ce komai ba ta lumshe idonta, a hankali yace "i love yhu my inteesar," kuka ta shiga yi a hankali don ta kasa yarda wae ita Aliyu ke so, ya rungumeta shima kmr xae yi kukan yace"say yhu luv me 2 kanwata don Allah," da kmr baxata ce komai ba sae kuma cikin kuka tace "i love yhu 2 yayana," ta fashe da kuka ya kwantar da ita jikinsa yace "ya isa hka bbyna nima karkisa na fara kukan," ganin ta kasa daina kukan yasa ya kwantar da ita ya shiga kissn dinta, daga nn kuma suka fada duniyar luv, yes daren ranar ta yrda Aliyu na sonta da gske, gaba daya sae da suka yi hawayen farin ciki ya faranta mata rae ita ma ta faranta masa, suka jiyar da junansu farin ciki mara mitsaltuwa, halin da take ciki yasa ya rabu da ita hka ya rungumeta duk ya rikice mata yana gode mata, a hka tayi bacci jikinsa, ya dde yana kallon kyakkyawar fuskarta daga bisanni ya kwantar da ita ya mike ya shiga bayi yyi wanka yyi alwala ya fito yyi shiga sallh don gode ma Allah da ya mallaka masa fateema matsayin matarsa uwar ya'yansa. Sae kusan karfe biyu ya dawo kan gado ya xauna yana kallonta bacci take amma sae ya ga kmr sanyi take ji hkn yasa ya dauko rigan sanyi ya sa mata ya lulluba mata xaninta snn ya rufa ta da bargo kuma shima ya shiga bargon ya jawota jikinsa a hka shima yyi bacci. Can karfe biyar saura ihunta ya farkar da shi, ya mike xaune a rude ya kunna wutan dakin yana kallonta yace "Fateema menene," bata ce masa komai ba kanta a kasa sae murxa idonta take, ya rike hannun nata yana kallon idon yace "me ya faru fateema kiyi min magana," turasa tayi har sae da yyi baya, ta mike kmr an tsikareta tayi hanyar kofa da sauri ya mike ya bita ya rikota da mamaki yace "ina xaki kuma fateema," wani ihun ta fasa mashi ta shiga kwace kanta daga rikon da yyi mata, hankalinsa ya tashi bae damu da ynda take dukansa ba ya dauketa ya xaunar da ita kan gado yana kallonta hankalinsa a tashe yace "me ya faru fateema tok 2 me" kuka ta fashe masa da ta turasa kmr ba ita ba gashi da karfi take turasa, ta mike da sauri tayi kofar fita ya bita ya kullokofar, kwalban turare ta fixgo gaban madubi tana kallonsa tace"wllh ka bude min kofar nn kar na jefa maka wnn," ya bude bakiya kasa cewa komai bae ankara ba yaga ta wurga masa kwalban yyi tsalle ya koma daya side din kwalban ya tarwatse, ta fixgo wani kuma ta wurga masa bae samesa ba, a rikice yace "wae meye hka kike fateema" ganin da gske take yasa ta bude kofar ya fice da sauri ya kullo ta waje ta dinga watsi da kayan dakin tana ihu ya bude mata kofa, ya dafe kansa ya jingina jikin bango cikin tashin hankali yace "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un," wayarsa ya shiga daki ya dauko da sauri ya shiganeman layin Faruuq Karfeshidda saura Faruuq ya shigo gidan har lkcn Aliyu na tsaye bakin kofa ya rasa abun yi, faruuq yace "kace me ya sameta Aliyu tana ina?" Aliyu ya girgixa kai da kyar yace "wllh ban sani ba tana ciki," faruuq ya bude kofar a hankali ya shiga dakin tana xaune ta takure waje daya duk tayi kaca kaca da dakin ga kwalabe ta ko ina, tana ganinsa ta mike da sauri tayi hanyar kofa yace "Fateema," bata ko kallesa ba ta fixgo kofar tana neman fita, ya rikota yace "ina xaki fateema, kuka ta fashe da tana buge hannunsa tace "ka barni na fita ni fita xanyi," ya kulle kofar ta fixgo wani kwalba ta jefa masa a fusace, da sauri ya goce ma kwalban, ta dauko wanikuma ta sake jifarsa da shi, Aliyu ya bude kofar da sauri ya fito da Faruuq snn ya rufe kofar, cikin tashin hnkli faruuq yace "ya salam, me ya sameta Aliyu ta buge da wani abun ne Aliyu," Aliyu ya dafe kansa da kyar yace "ko daya faruuq i just cnt understand dis, sae kace mahaukaciya," hauka ta dinga yi a dakin tana ihu tana bubbuga kofar xata fito, Aliyu ya dafa faruuq da kyar muryarsa na rawa yace "i cnt bear seein dis faruuq help me plss kar ta ji ma kanta ciwo ba ita kadae bace," faruuq ya sake bude kofar ya shiga tayo kansa ya riketa gam yana kiran sunanta amma ina, Aliyu ya kira ya dauko Alluran bacci, ya shiga dakinsa da sauri ba adau lkci ba ya fito rike da alluran, har lkcn faruuq na rike da ita sae kokuwa suke, ya kwantar da ita Aliyu yyi mata Alluran da kyar, tayi ta fixge fixge tana ihu har na kusan minti goma kafin ta sulale kasa, faruuq ya kwantar da ita yana kallon Aliyu da idonsa ya cika da kwalla, a sanyaye faruuq yace "ae ba hawaye xaka yi ba yallabae ynxu ka kira Abba ka sanar dashi abinda ke faruwa, ita kuma mu wuce da ita asibiti," Aliyu ne ya dauketa ya sakata cikin mota faruuq yyi drivin din suka wuce da ita asibitin da faruuq yake aiki. Nan da nn aka karbeta likitoci sukahau kanta, karfe bakwae Abba da Haisam suka iso asibitin. ......Abba ya xauna gefen Aliyu da ya dafe kansa yace "me ya sameta Ali," Aliyu ya dago da kyar yana kallon Abbansa yace"nima ban sani ba Abba," Haisam ya dafa sa yace "kar ka damubrother she wil b Alryt idan Allah ya yrda," murya can kasa yace "Ameen," Abba yace "tana ina ynxu fateemar, xa mu iya ganinta," Aliyu yyi shiru bae ce komai ba, Abba ma bae sake cemasa komai ba, har Faruuq ya sauko ya gaida Abba snn ya xauna, Abba yace "ya ake ciki faruuq," faruuq yace "to sae dae Allah shi kyauta Abba, ana ga kmr matsalar daga brain dinta ne sae dae ta farka aga reaction dinta" Abba yace "innalillahi wa inna ilaihi raji'un," Abba yace "xa mu iya ganinta ynxu," faruuq yace "har ynxu likitoci na kanta, Abba kuje gida xuwa anjima sae ku dawo," Abba yace "A'a xamu jira har ta farka," faruuq yace "to shknn Abba," ya juya yana kallon Aliyu yace"mu je ana son ganinka Aliyu," Aliyu bae ce komai ba ya mike ya bi sa suka haura sama, likitocin suka sa shi gaba suna masa tambayoyin da a ganinsa re vry silly, hkn yasa yaki ce masu komai har wani likita ya fusata yace "wae ko ba mijinta bne," a nutse Aliyu yace "nine, kuma ban san me xance maku ba shi yasa nayi shiru," duk suka tsaya kallonsa, ya mike a fusace yace "nace maku bbu abinda ya sami matata bata bugeba bata yi ciwon kai ba, get me ryt mana," ya fice daga office din, wani likita yace "lallai mutane basu da tunani to shi uwar me ya hanasa karantar likita da har xae xo yana mana ihu a nn, mu muka daura mata, shi yasa fa ni ban cika son karban emergency hka ba, dr faruuq kace dan uwanka ne kuma kana kallon abinda yake a nn kayi shiru, did he expect us 2 do magic,ko mu xamu bata lfya," faruuq ya danyi murmushi yace "cool down guy shima babban likita ne kmr mu nn, just dat he is vry confuse nd frustrated," Aliyu na sauka gida ya wuce yaje yyi wanka yyi sllh, ya dde xaune kan darduma yana rokan Allah yaba fateemarsa lfya, karfe tara saura faruuq ya kirasa, gabansa ya fadi ya kasa daga kiran har sae da ya katse snn aka kara kira ya daga da kyar, faruuq yace "wae kana ina ne Aliyu kasannn da minti talatin fa may b ta farka," Aliyu bae ce komai ba ya katse kiran ya dauki makullin motarsa a sanyaye ya wuce asibitin, da ganinsa kasan damuwa na tare da shi, bae ce ma su Abba dake xaune a reception har lkcn komai ba ya haura sama ya shiga ward din da take xaune ya tarar da momy a gefenta, duk da bata san me ke damun yar tata ba kawae kiranta Abba yyi ta xo asibiti kuma kar ta gaya ma kowa, tana xuwa kuma aka ce ta xauna da ita har ta farka don likita yace ma Abba idan ta farka ya xamana ta daura idonta kan wanda tafi shakuwa da, duk da Abba yasan inna ce bae son tashin hnkali shiyasa bae gayyatota ba ya kira momy, Aliyu ya karasocikin dakin ya gaida momy, ta amsa ba tare da ta kallesa ba, kasa tsayawa yyi a dakin ya fita, karfe goma saura inteesar ta bude idonta kan momynta, momy ta kamo hannunta ta kira sunanta a hankali, bata dae ce komai ba ta fara kkrin mikewa xaune momy ta taimaka mata tana tambayrta ya jikin, bata ce komai ba ta shiga kkrin sauka daga kan gadon ga drip a hannunta, momy ta rikota tace "ke ina xaki," bata ce ma momy komai ba ta shiga kwace kanta daga rikon da momy tayi mata,da mamaki momy tace "kina da hankali kuwa? Ina xaki," fixge hannunta tayi ta sauka daga kan gadon momy ta kuma rikota tana kiran sunata, ihu ta fasa ta kuma kwace kanta tayi waje, suka ci karo da Aliyu bakin kofa ya rikota yana kiran sunata, dukansa ta shiga yi tana cewa "ni ku kyaleni na tafi," momy ta mike tsaye a hankali tana kallonsu, likitoci suka shigo dakin da sauri suka rirriketa ta shiga kokuwa dasu gaba daya, Abba ma ya shigo yana kiran sunanta amma ina, Aliyu ya kife kansa da bango ya kasa kallonta kuma, Wani alluran baccin aka kuma yimata, ta gama fixge fixgenta tana ihu ta sulale kuma, Abba yace "innalillahi wa inna ilaihi raji'un," kan gado aka mayar da ita snn wani likita yana kallon Abba yace "kawae a wuce da ita psychiatric hosptl a duba kwakwalwarta Alhaji ba karamin matsala bane wnn," faruuq kam kasa cewa komai yyi yana nn durkushe gunda aka mata alluran har lkcn, momy da hawaye ya cika idonta tayi kofar fita duk suka bita da kallo Abba ya shiga kiranta bata ko waiwayo ba ta fice daga ward din ya bi bayanta. Faruuq ya mike tsaye yana kallon Haisam da ya xama tamkar wani mutum mutumi a wajen a sanyaye yace"bari naje nayi arrngn din Ambulance na dawo," Aliyu kam har lkcn kansa na kife jikin bango, haisam ya karasa kusa da shi da kyar ya dafa sa yace "kar ka tada hankalinka Aliyu, Allah na tare damu," Aliyu ya juyo hawaye a idonsa yace "kace kar na tada hankali na kace Haisam, matata na hauka kace kar na tada hankalina," Abba ya dawo dakin a sanyaye yana kallonsu yace "ba abun yi ba knn Aliyu, ynxu wani asibitin xamu wuce da ita" Aliyu ya kasa cewa komai sae hawaye, Faruuq ya shigo dakin yace "Abba mu wuce da ita Federal Neutro-psychiatric hsptl yaba lagos, asibitin na da kyau ssae. Ko Allah zai sa mu dace . ..Karfe sha biyu saura na rana suka isa lagos, tare da faruuq da Haisam suka xo, har lkcn bbu wanda yasan abinda ke faruwa sae momy kadae, ita ma Abba ya roketa da tayi hkuri ta rufa masu hkuri kar inna taji xancen, daya saura suka isa Asibitin a Yaba, aka karbeta bbu bata lkci tunda magana ta kudi ce, babban asibitin mahaukata ne, har lkcn tana baccin alluran da aka yi mata a kano, Aliyu dae gashi nn gashi nn ne lkci daya duk ya fice hayyacinsa, hka yasa faruuq yace "ya tafi gida kawae ya huta tunda yana da gida a nn lgs," bae ce da faruuq komai ba, alamar baxa shi ba, Haisam yace "haba Aliyu kai masae ka je ka janyo ma kanka wata cutar ne, dube ka fa ko karyawa baka yi ba yau," da kyar suka lallabasa ya wuce gida tare da Haisam, su ka bar faruuq kadae a asibitin, wanka kawae yyi yaki cin komai ya kwanta sae bacci, karfe biyu uku saura ya tashi, haisam na waya da faruuq lkcn, Aliyu ya mike tsaye yace "haba Haisam ya xaka barni na dinga bacci hka baka tashe ni ba," bae jira mai haisam xae ce ba yyi hanyar kofa, Haisam yace "to ae baka yi sllh ba," ya tsaya bakin kofar kmr me naxari snn ya koma yaje yyi alwala yyi sllh, yana idarwa bae ko kalli Haisam ba ya fice daga gidan ya kama hanyar asibiti, direct faruuq ya sa ya tafi gun likita ana nemansa, tambayoyi dae suka dinga yi masa a kanta ko tana da brain disorder da can, yyi shiru snn yace "bata taba samun matsala hka ba sae wnn karan," likitan yace "though we have'nt yet find the specific cause of her madness...." sae kuma yyi shiru, Aliyu ya tsura masa ido, "yhu just dnt have 2 worry its nt dat critical though," Aliyu yace "re yhu assurin me?"likitan yace "yes, yhu can go n c yhur wife but b careful dnt go too close," yace "thank yhu," snn ya mike ya fice daga office din ya dinga wuce ward din mahaukata suna ta iskanci da tsiyarsu har ya iso inda take, ya tsaya daga bakin kofar da yake ta glass ne nd its transparent, ana iya ganin duk abinda sukeyi ta waje, tana xaune ta kura ma window ido, wani muguntausayinta yaji na neman saka shi kuka, ya bude kofar dakin a hankali ya karasa kusa da ita a sanyaye, bae damu da warningdin da aka yi masa ba ya durkusa gabanta yana kallon fuskarta, a hankali ya kira sunanta "inteesar," ta dago tana kallonsa, ya girgixa kai nn da nn hawaye ya cika idonsa, "me ya janyo maki wnn ciwon fateema tok 2 me, me ya sameki...." dariyarta mai kyau tayi snn ta fincikosa a fusace tace "nace ku bude min kofa ni wucewa xanyi," rike hannunta yyi suka shiga kokuwa ya mike tsaye da sauri ganin da gske take ita ma ta mike, taki sakinsa tana jijjigasa tana ihu ta shiga cewa "baxa ku bude min ba," da sauri likitoci suka shigo dakin, suka kwacesa daga hannunta, snn aka mata allura aka xaunar da ita, nn da nn ta nutsu, likitan yace "i warned yhu 2 be careful y did yhu come so close, i told yhu she's under medicatn," Aliyu bae ce komai ba ya juya ya fice daga dakin ransa a dagule, suka fito suma suka rufe kofar, faruuq ya dafa Aliyu yace "kayi hkuri ka daina xuwa inda take har sae ta fara samun lfya," Aliyu bae ce komai ba suka xauna. Da daddare Anty nafeesa tasauka lgs, faruuq ta kira ya xo har airport ya dauketa xuwa asibitin duk hankalinta a tashe yake, kawae son ganin inteesar take, amma likitoci suka hana sae ta fashe masu da kuka, hkn yasa aka bar ta ta tsaya daga bakin kofa kawae, kuka ssae ta dinga yi ganin wae da gske inteesar ce ke hauka wnn wace irin jaraba ce, kasa komawa kano tayi tayi xamanta nn lgs a asibitin, Abba ma yaxo ya dubata ya koma ransa a dagule, ranar da suka cika kwana hudu a asibitin Aliyu yace "ni fa faruuq am tired ni banga wani improvement ba sae allura suke yi ma yarinya duk bayan mintoci, kuma tana nn yanda take," faruuq yace "to lkci daya dama aka ce maka ake magani Aliyu, ni kuma naga improvement tunda har tana iya xaunawa na awa daya bata yi buge buge ba," Aliyu ya xauna ya dafe kansa yace "wllh na gaji faruuq, ban san me ya sami fateema," kullumshi ke kai mata abinci ya ajiye mata a gaba ya dan xauna nesa da ita, sae don kanta yaga ta matso kusa da abincin snn shimaxae matso ya dauki cokali ya dinga bata a hankali cikin ikon Allah kuma tana karba, idan ya bata sae shima ya ci nn kadae ne yake samun cin abinci idan yaga tana ci don baya iya ci, ko cibi uku baxa su ci ba xata kwabar da shi tayi kaca kaca da shia gun, shi knn kuma cin abincin ranan, wani lkcn sae yaji da ma shi Allah ya daura ma haukan, satinsu daya a lgs Aliyu yace ma faruuq "look ni kawae ku barni na fita da matata waje na gaji da shirmen da ake yi a nn," faruuq yace "haba Aliyu meyasa kke da gajen hakuri ne, wae hka muka kawo inteesar asibitin nn," Aliyu yace "no faruuq ni sbda cikin jikinta ne yasa nace hka, saura fa wata daya da yan kwanaki ta haifesu, a cikin wnn halin? no plss help me persuade my father mu fita daita india," a raunane ya karasa maganar faruuq yyi shiru ya rasa me xae ce masa. Ko da suka yi ma Abba maganar fita da inteesar waje Abba ca yyi a'a idan na asibiti bae yi ba a dawo da ita gida kawae ayi na Hausa, duk wnn abinda ake inna bata san me ke faruwa ba har lkcn, ita dae kullum maganarta a gidan a kai ta gidan inteesar ae ta kusa Haihuwa, sae dae Abba yace mata kar ta damu xa'a kaita, duk momy ta xama wata iri a gidanciwon inteesar ya tsaya mata a rai ta so tace ma Abba a dawo da ita gida kawae a nema mata magani kuma a dage da yi mata addua amma bata son su ga kmr bata gode abinda ake mata bne, ita kam taga alamar ba ciwon asibiti bne amma bata ce komai ba, kullum jiya e yau ciwon inteesar idan kaga ta nutsu to Allura aka dirka mata, sam ita kawae so take ta tafi dae ko ina xata oho, Aliyu duk ya rame kmr yanda bata cin abinci shima hka baya ci, ya kan xauna kusa da ita duk damben da xa'suyi yyi ta tofa mata addu'a ko dago kanta baxata yi ba har ya gama ya fita, su kansu likitocin suna tausayinta sbda halin da take ciki, duk bayan kwanabiyu Abba kan xo ya dubata, kuma idan xae xo ya kan damu momy su xo tare amma sae taki xuwa, faruuq ma yakan koma kano yyi kwana biyu ya dawo, ko Zainab bata san me yake xuwa yi a lgs ba ya dae ce mata aiki yake kaisa, har ta gaji da rokansa ya barta taje gidan inteesar don ca yyi mata sae ta haihuwa xata je, safeena na sane da abinda ke faruwa farin cikinta da na uwarta baya mitsaltuwa ta mayar da gidan Aliyu nata sae yanda tayi da shi ta shigo da wancan ta shigo da wancan, tana da tabbacin inteesar ta kusa shiga duniya kmr yanda aka yi assure din ita da uwarta, shknn Aliyu xae xama nata ita kadae na har abada sae yanda tayi dashi, ta kan kirasa lkci lkci idan yaga dama yana daga wayar sae dae su gaisa tace "wae har ynxu baxa ku dawo daga honey moon din naku ba ko bata haihu bne Aliyu," ya kan katse wayarsa ne don bae taba sanin wae safeena tasan abinda ke faruwa ba. Ranar da suka cika sati uku a asibiti Aliyu yasa abbansa gaba yana hawaye kan cewar yyi hakuri ya bari ya fita da inteesar, Abba yyi shiru shima hankalinsa a tashe yace "to ae Ali wae da mukoma da ita gida a fara yi mata na hausa," da sauri yace "A'a Abba duk bata lkci ne wnn kayi hkuri don Allah mu fita india suna da kwararrun likitoci" Abba yyi shiru ya rasa me xae ce, can dae yace "to shknn Ali, Allah yasa hkn shine mafi Alkhairi kuma yasa a dace a can," da kyar yace "Ameen Abba," ranar aka fara shirye shiryen fita da ita xuwa new delhi, Abba na nn lgs har suka tashi bayan kwana uku tare da Anty Nafeesa, faruuq da Haisam, snn shima ya koma kano. Shi tsoron sanar da inna yake amma dabae ci ace duk wnn abinda ke faruwa inna bata saniba, to innan ce sae a hankali, da ya sanar da momy sun fita india bata ce komai ba sae hawaye, Hajiya ta gaji da rashin ganin Aliyu sati da satittikae ta kama hanyar gidansa da kanta, ba kowa gidan sae mai gadi ya sanar da ita ae matar gidan ba lfya suna asibiti, tace "wacce ciki," yace "me juna biyu ae sun fi wata daya basa gidan nn kmr dae mai hauka ka ta koma, Hajiya ta dafe kirji tace "kai haba inteesar kke nufi," ganin baxata samu information ssae gun sa ba yasa ta kama hanyar gidansu safeena don yace mata daxu ta tafi gida wae, jikintahar rawa yake taje taji gulma, shknn abunsu ya koma masu yau, murna fa cikinta ta shiga gidansu safeena, suna xaune ita da uwarta a falo kmr kawaye sae shewa suke, hajiya ta shigo falon . .Hajiya ta karaso cikinsu ta xauna tana washe baki tace "kuna sha'aninku wllh ina ma nima xainab dina xata yrda mu dinga yin hka tare mu kashe mu rufe, kuna bani sha'awa wllh" safeena tayi dariya hka ma uwarta snn uwar tace "ae ke kika bari aka kwace maki ita tun farko kika kasa yin komai," Hajiya tace "to ya na iya Hajiya salame," safeena tace "daga ina kike hka Hajiya?" Hajiya tace "daga gidanku can nake wllh, naga kwana biyu Aliyu bae xo gida ba nace to ko sun kara basa ya cine don a dauke hankalinsa kaina tunda suka yi ma ubansa ma bare shi, sae kuma naga ba kowa a gidan wae me ke faruwa nesafeena ina suka je?" safeena tayi dariyar keta tace "kina ina Hajiya, ai suna can lgs ta haukace yau kusan wata daya knn canake ma kin sani," Hajiya ta daura hannu a ka ta bude baki alamar mamaki tace "wayyoo Allah mae saka ma bawansa da gaggawa, kice min abun su ya koma kansu, da cikin ta haukace ni Aisha" Safeena tayi dariya tace "kwarrae kuwa," Hajiya ta daga hannu sama cikin murna tace "Alhmdllhi, Alhamdllhi, shiyasa naga uwarta ta koma abun tausayi a gida ashe ashe kaikaiyi ne ya koma kan mashekiya," suka kwashe da dariya Hajiya tace "amma fa ina ga kmr inna bata sani ba ba'a sanar da ita ba, don naga jarabanta sae wanda ta manta, ae kuwa tsaf xanje in daga mata hankali da kaina xan fada mata yau yau din nn" da sauri uwar safeena tace "ke Hajiya Aisha don me xakiyi hka, ae magani xata nema mata ta warke," Hajiya ta hade rae tace "ita likita ce da xata nema matamagani ba kunce suna asibiti a lgs ba," Hajiya safeena tace "to bari kiji Aisha mu ne nn muka haukatar da ita don danki ya koma gunki, don an tabbatar mana da cewa asiri uwarta tayi ma Aliyu ya manne ma yar ta baya jin maganar kowa sae na yar karamar yarinyar nn, ko baki lura bne? Kuma wnn ciki ancemana ba na Allah da annabi bne, ba cikinsa bne so wae suke su ci gadon Aliyu " Hajiya da jikinta yyi sanyi lkci daya ta bude baki tana kallonsa tace "ku kuka Haukatar da ita knn," daga safeenar Har Uwarta suka hada baki "kwarrae kuwa, hkn kadae shine mafita," Hajiya ta danyi murmushi tace "ikon Allah,ina ma nima xan xama kamar ku wllh kuna burgeni, to amma ya xa'ayi dana ya dawo guna, tunda dae ynxu suna can tare kar ma ta shafa masa haukan, shi yasa Aliyu ya daina daga kirana ashe" Hajiyar safeena tayi murmushi tace "kar ki damu Hajiya Aliyu xae dawo gare ki amma fa ba hka nn ba don asirinsu na nn jikinsa," hankalin Hajiya a tashe tace "to ya xa'ayi ya karye," Hajiyar safeena tace "ynxu xuwa xakiyi ki lallaba maigidanki, kawae marairaicewa xaki yi kice ynxu Alhaji ashe abinda ya samu yarinyar nn knn kke boye mani, da fa na kowa ne, kuma dan adam baya wuce kaddararsa, xaki gajikinsa yyi sanyi hka xaki ta jan ra'ayinsa kmr ta kirki nn da nn xaki ga ya baki hkuri, to daga nn sae kice don Allah kina son yabarki kije ki dubota nasan xae bar ki, to kina xuwa can akwae wani magani da xan baki cikin abin sha xaki tabbatar kin sa ma Aliyu in'sha Allahu asirin da suka mashi xae karye,kuma kina xuwa da kwana biyu ki dawo gida, ko sati baxa'ayi ba xakiga ya biyoki shknn shi da ita kuma har abada, danki ya dawo hannunki wa inda suka ga xa su iya jinyarta sae suyi ta fama," Hajiya tayi dariyan jin ddin shawarar Salame tace "shnn salame ngdd ssae, duk yanda kika ce hka xanyi bani maganin na wuce, Hajiya salame ta shiga daki ta dauko mata maganin dake kulle a leda ta bata, tayi mata gdya cike da jin ddi ta masusallama ta bar gidan xuciyarta fal murna shknn Aliyunta xae dawo gareta asirin matsiyatan mutanan can xae karye. Tana fita Safeena da uwarta suka tuntsure da dariya uwar tace"shknn xata je ta dawo maki da Aliyun ki, ya xama naki na har abada don ko ita da ta haifesa mantawa xae yi da ita ke kadae xae dinga gani a duniya," suka dinga dariya suna jin jina ma sakarcin Hajiya da rashin tunaninta. Ita ko Hajiya tana komawa gida tayi yanda suka ce mata da daddare a falon Abba, Abba yyi shiru ya kasa cewa komai amma jikinsa yyi sanyi, ita ko har da dan hawayenta, ganin ta fara cin nasara yasa tace "to shknn Alhaji kila kai kadae kasan dalilinka na rashin son gaya mana, amma kayi hkuri ka barni naje na dubota don Allah don Annabi," yyi shiru na kusan minti biyar snn daga karshe yace "to shkknn kya iya xuwa, suna india amma ynxu hka," ta dafe kirji da alaman jimami tace "ohh ni yar nn, wnn wace irin fitina ce ga ciki" sae kuma ta fashe da kuka Abba yace "ba kuka xakiyi ba, addua'a xakiyi mata, amma bana son maganar nn ya fita daga nn ki bar shi a cikin ki kawae har Allah yasa ta samu lfya," Hajiya na share hawayenta tace "to Alhaji in son samu ne ko xuwa jibi na tafi tunda ina da visa," yace "to shknn," ta mike tace "Allah ya shigemana gaba" snn ta fita daga falon Abba xuciyarta fal murnar xata je ta dawo da danta. Vidyasagar institute of mental health and neuro sciences, shine asibitin da su Aliyu suka sauka a new delhi, babban asibitin mahaukata ne na india, kuma basu samu wata matsala ba aka karbesu . Kwanansu hudu a asibitin Hajiya ta iso, ynxu kam haukan inteesar da sauki tunda ta daina buge buge sae dae kawae ta xauna ta tsura ma abu ido tana kallo, da yamma Hajiya ta shigo asibitin bbu wanda bae yi mmkin ganinta ba barin Aliyu amma bae nuna ba, kuka ta fashe masu da tana jijjiga kai tace"ashe abinda ya samu inteesar knn, bbu dae wanda ya tanka mata ita kuwa inteesar dama bacci take, ganin sae fa tayi da gske yasa ta kama hotel nn indian ynda kowa xae saki jiki da ita yyi xaton jinya ta xo ganin dari dar ake da ita, duk safiyya da yamma take xuwa duba inteesar da kayan fruit, Anty Nafeesa da Aliyu a asibitin suke kwana wajenta, Faruuq da Haisam kuma hotel suka kama, likitocin suka mayar da hankali ssae a kanta sbda cikin da ke jikinta don at an ytym xata iya haifesu, suna xaune da yamma ranan Aliyu na bata abinci tana karba, Faruuq na xaune yana kallonsu Anty Nafeesa taje hutawa a hotel din da su Haisam suke, Hajiya ta shigo rike da ledan fruits dinta da lemo, ta xauna, Aliyu ya gaisheta hka ma Faruuq, ta amsa tana tambayar jikin Inteesar, ta mike ta dauko kofi tayi waje kmr taje daurayewa ta bude maganin da take yawo da kullum a bakin xaninta ta xuba kadan, snn ta koma ciki ta bude juice tacika kofin ta dauka ta mika ma Aliyu tace "dubi yanda ka rame son, nasan baka cin abinci yau ma bn ga alamar kasa komai a cikinka ba ga lemo ka kora kaji son," ya rufe abincin da yake ba inteesar ganin takikarba kuma ya dagata sama yace "ni naci abinci ae," snn ya ja ta suka sauka xuwa kasa don yawanci a kasa suke wuni gun pool ko flowers. Shi kansa Faruuq bae ji ddin abinda Aliyu yyi ma uwartasa ba yace "kawo ni na sha mum," da sauri tayi murmushi tace "A'a bar shi kawae," faruuq ma yyi murmushin jikinsa dae yyi sanyi ya mike ya sauko ya samesu a kasa, bakacewa hauka inteesar take ynxu duk ta nutsu ssae sae in tayi wani abun ne wani lkci xaka gane har lkcn haukan na jikinta, kusa da ruwa ya samesu a xaune, faruuq ma ya xauna yace"gskya she's respondin 2 treatment a nn Aliyu naga improvement," Aliyu ya dan yi shiru snn yace "hka ne, but lkcn haihuwarta ya kusa faruuq a hkn xata haihu bbu hankali tare da ita,"Faruuq yace "muyi ta Addua frnd kila ma haihuwar ne xae yi sanadiyar dawowa da hankalinta," Aliyu bae ce komai ba sae kallonta yake cike da tausayi. Yau suka cika sati daya aIndia, Hajiya kam ta rasa yanda xata yi Aliyu ya sha maganin da su safeena suka bata, ynxu xuwanta xae xamo a bnxa knn tayi, da yamma ne misalin karfe hudu saura Aliyu na xaune da inteesar kusa da babban pool din dake cikin asibitin, ga mahaukata da suka fara warkewa xaxxaune a wajen kowa nata harkan gabansa, tun safe ya lura inteesar bata jin ddi, yasan lkcn Haihuwarta ne ya lura nakuda take duk da bata nuna tana jin komai ba, shima duk hnkalinsa ya tashi faruuq kadae ya gaya ma, faruuq ya fita siyo abubuwan da ya kamata,Anty Nafeesa ta tafi hutawa a hotel, Haisam jiya ya koma Nigeria, Hajiya kuwa ta fita yawon xaga gari xuciyarta fari tas don tana tunanin yau ce xamansu ta karshe ita da Aliyu a indiadon ta lura da abinda yake sha a asibitin wani lemu ne kadae abincinsa ta xuba masa maganin ciki snn ta bude fridge a ward din da inteesar take ta ajiye masa hkn yasa taje xaga garikafin ta tafi anjima idan taga ya sha, xamowa inteesar tayi daga kan kujeran da take ta xauna kasa ya lura duk axaban ciwo ne kesawa tayi hka, shima ya dawo kasan yana kallonta da damuwa yace "ina ke maki ciwo fateema," bata ce komai bata dauke kanta, suna nn xaune a hka har na kusan minti sha biyar ya juya yana kallonta yaga robon ruwan wasu mutane kawae take kallo, ya kamo hannunta yace "xaki sha ruwa ne inteesar" kai ta gyada masa ya koma baya da mamaki yana kallonta, da sauri ya mike yace "ina xuwa bari na kawo maki kinji bata sake cewa komai ba yyi hanyar stairs da sauri yana waiwayota xuciyarsa na bugawa ya haura sama dauko mata ruwa, tsam ta mike ta fara kalle kalle ta bi hanyar da taga mutane na bi, da sauri take tafiyar kmr ana turata, har ta isa gate masu gadi suka bita da kallo don bbu uniform din mahaukata jikinta, ta fice tayi hanyr hagu duk da tafiya ce mai shegen nisa tana ta tafiya har ta daina hango asibitin, Aliyu ya sauko rike da ruwa da kofi a hannu ya ga wajen wayam bbu fateema, kalle kalle ya shiga yi a rude bae ga alamarta ba, ya hango faruuq ya karasa gunsa da sauri yace "fateema fa," faruuq yace "wace fateemar ba nn na bar ku tare ba," ya dafa faruuq ganin kafafuwansa sun kasa daukansa yce "wlh nn na barta naje dauko mta ruwa" cikin tsawa faruuq yce "wat? Don me xaka barta ita kadae" tare suka shiga xaga asibitin suna nemanta ta ko ina amma basu gnta ba sune har gate duk Aliyu ya birkice kmr wani xautattce, sae ga Anty Nafeesa ta shigo asbitin rike da abinci da mamaki ganin yanda suka tara jama'ah tace "me ya faru" faruuq yy karfin halin cewa "bamu ga fateema ba" kmr kar faruq ya fadi hka sukaji Aliyu ya saki wata irin kara ae sae da asibitin ya dauka sae kawae suka ga ya sulale wajen. Hajiya ta shigo asibitin rike da kayan tsarabar da tayo ma yan Nigeria barin safeena da uwarta tana dan rera wakarta, jikin wani ward taga Nafeesa tsaye tana kuka ssae ga wani likita da alamar dan Nigeria ne yana lallashinta, da sauri ta karasa kusa da ita tanakallonta tace "me ya faru Nafeesa," da kyar Anty Nafeesa na girgixa kai tace "bamu ga inteesar ba," Hajiya tayi shiru tana kkrin boye murnar ta, can kmr warce ta tuna abu da sauri tace "Aliyu fa," Anty Nafeesa ta kasa cewa komai sae kuka, Hajiya ta juya a rude tana kallon likitan dake gaban Anty Nafeesa tace "ina da'na," da sauri ta bude ward din da inteesar take mai xata gani, Aliyu yana dambe dalikitocin dake kansa sae Fateema yake kira, hajiya ta fito a guje tayi kan Anty Nafeesa a rude tace "me ya samu Aliyuna," likitan ne ya bata amsa "suma yyiya farfado a hka shima ana ga kmr ya samu matsala a kwakwalwa," Hajiya ta fasa ihu tace"hauka Aliyu yake yi hka," kuka ta fashe da a rude ta ciro wayarta ta shiga danne danne tana gunjin kukasae rawa hannunta yake ta kara a kunne, "hello salame kina jina maxa ku je ku karya asirin nn da kuka yi ma inteesar ya koma kan dana wllh," ta katse kiran a rude tana rusa kuka sae kallonta Anty Nafeesa take da mamaki, cikin kuka tace "wlh Nafeesa safeena ce da uwarta suka haukatar da inteesar su suka haukatar da ita suka gaya min," Anty Nafeesa ta dafe kirji ta kasa cewa komai ta fashe da kuka tayi waje, Hajiya ta bita ita ma tana kukan kmr mahaukaciya, Faruuq ya shigo asibitin a jike don anyi ruwa ssae, bbu inda bae xaga ba a india amma bae ga inteesar ba, ynxu ma daga gidan talabijin da redio yake, duk ya xama kmr wni mara lfya, ganin inda su Anty Nafeesa ke kuka yasa da kyar yace "Aliyu fa," cikin kuka Hajiya tace "wllh ya haukace faruuq ku ceci rayuwar da'na ku nemo inteesar, ina inteesar ta shiga don Allah a nemota," ta fashe da wani matsanancin kuka ta xube wajen, sae kallonsu ake gwanin ban tausayi, faruuq ya dafa bango ya kai minti kusan biyar a hka da kyar ya haura sama ya shiga ward din da inteesar take, duk alluran da suka dinga yi ma Aliyu bae nutsu ba don hauka karara ya dinga gwada masu, duk aka fita aka kulle dakin aka barshi shi daya ya dinga buge buge yana jijjiga kofar abun dae ba ddin ji, likitocin suka hana faruuq shiga ya jingina jikin bango hawaye ya cika idonsa da kyar ya ciro wayarsa ya shiga neman layin Haisam, muryarsa na rawa yace "Haisam abu ya baci Haisam inteesarta fita daga asibitin, Aliyu baya cikin hankalinsa shima brain dinsa ta samu matsala, ka sanar da Abba baxan iya gaya masa ba" bae jira me Haisam xae ce ba ya katse wayar sae hawaye. Inteesar kamnata tafiya abunta sae dae idan taji kmr an mintsileta a mararta ta xauna ta huta snn ta ci gabada tafiya ko ina tabi sae an kalleta, hadari ya hadu garin ssae tana ta tafiya abunta kowa nata kkrin ganin ya isa gidansa, har daga karshe ruwa mai karfi ya sauka ta xauna kan wani dakali ruwan ya dinga dukanta amma bata damu ba, har ruwan ya tsagaita bayan kmr awa biyu, ta mike da kyar ta ci gaba da tafiya tana rawan sanyi, kasa ci gaba datafiyar tayi dae dae wai babban plaza ta dalilin wani mugun ciwo da taji mararta da kugunta nayi a tare da kyar ta ja kafa ta samu wani gefen mota ta durkushe gaban plazan tana rike da kugunta sae rawan sanyi take tana yarfe hannu alamar axaba, indiawa sae kallonta suke suna wuce ta, don su dama basu gaji taimko ba ko a tsakaninsu, kuka ta shiga yi ganin ta kasa daure ciwon Abbanta ta shiga kira tana juye juye jikin motar da take taji an bude motar ta koma baya da sauri, da ganinsu matada miji ne, matar na kallonta da yaran india tace "keme kike yi a nn," kai ta daga tana kallonsu bakaken fata ne kmr ita amma da gani xasu Haifeta, ta mike da kyar tana rike da kugunta xata bar wajen matar tace "amma ke yar Nigeria ce kuma bahaushiya ko,"ko kallon matar bata yi ba taku daya biyu ta xube wajen tana wayyo cikinta, matar ta juya tana kallon mijinta dake tsaye kmr wani tsoko yana kallonsu tace "Abbanmu kalli fa yar uwar mu ce ga kuma alamar bata da lfya mu taimaka mata," bata jira me xae ce ba ta karasa kusa da inteesar da sauri ta dago ta tana kallonta tace "sannu kinji yan mata daga ina kike hka," inteesar bata ce komai ba sae girgixa kai da take don axaba, matar ta dagota da sauri ta saka ta bayan mota ita ma ta shiga tace"mu je Abbanmu," ya shiga motar ya tada suka bar wajen, ihu ta dinga masu a mota duk ta rikice jin axaba na neman kasheta matar na rike da ita tana tofa mata addua, mijin ma duk ya rude yace "asibiti xamu ko," tace "A'a muje gida kawae xan karbi haihuwar," babban gida ne ssae, matar tace "ka taimaka min mu fito da ita Abbanmu," ya xagayo yana kallon inteesar da ta gama fita hayyacinta ciwo ya ci karfinta, tace "help me mana Abbanmu," ya koma baya da sauri har lkcn yana kallon inteesaryace "baxan iya ba, bari na kira maku yan aiki," yyi cikin gidan da sauri sae gashi ya fito da yan aiki suka taimaka mata ta shiga ciki da inteesar . .. Da taimakon matar Inteesar ta Haifo santala santalan yaranta maxa biyu, ba karamin wahala ta ci ba, matar ta tausaya mata ssae, babban likitace don hka tayi mata duk abinda ya kamata snn ta kaita bedroom dinta ta kwantar da ita kan ta hado mata tea har tayi baccin wahala, mai gidanta kuwa kasa xaune yyi har sae da inteesar ta haihu, snn hankalinsa ya kwanta, matar ta gyara yaran ta kaisu gefen uwarsu ta kwantar dasu gashi gaba dayansu basu da lfya, inteesar bata farka ba sae can tsakar dare matar na xaune gefenta rike da dayan yaron dake ta kuka ta kwantar dashi tana mata sannu, kai kawae inteesar ke gyada mata, ta kira yan aiki su kawo mata tea, suka kawo suka ajiye, matar tace maxa ki sha ki basu nono yunwa suke ji kuma duk basa jin ddi, inteesar bata ce komai ba matar ta taimaka mata tamike xaune snn ta mika mata tean ta shiga kurba a hankali, maigidanta ya shigo ya xauna yana kallon inteesar yace "sannu baiwar Allah ya jiki," ta dago kai tayi shiru tana kallonsa, wata yarinya ce da baxata wuce shekara goma sha biyu ba ta bude kofar ta shigo ta karaso kusa da inteesar da harshen hausa tace "Sannu Anty," inteesar tayi murmushi tace "na gode" yarinyar ta xauna tana kallon bbies din, ba karamin kama suke da inteesar ba iyayen sae kallonsu suke, daga karshe Abbanmu ya mike ya bar dakin, inteesar ta ajiye tean hannunta matar tace "har ya isheki," ta gyada mata kai tace "na koshi," matar tace "bari a kawo maki abinci ki ci kinji," inteesar bata ce komai ba matar ta mike ta fita, inteesar na kallon yarinyar tace "ya sunanki," yarinyar tace "sunana Zainab," inteesar tayi murmushi tace "nyc name, wa ya kawo ni gidan nn,"yarinyar tace "mum nd dad ne suka kawo ki daxu," inteesar tace "wani gari ne nn," yarinyar tace"india," inteesar tayi shiru bata ce komai ba gabantana faduwa ranta a dagule, india kuma, me ya kawota india . . Ba karamintashin hankali kowa ya shiga ba rashin ganin Inteesar har na kwana biyu, barin ma Abba don shi ba ma ta Aliyu yake ba, ta yar mutane yake, Hajiya dae ta dage kowa ta gani tace su safeena ne suka yima inteesar asiri ta haukace ita ma dae ta xama kmr mahaukaciyar, idan ta gaji da gantalin don bbu wanda ke kulata kowa abinda ke damunsa yafi karfinsa sae ta dawo ta xauna bakin kofar inda Aliyun yake tayi ta rusa ihu tana kuka har aka fara tunanin ko ita ma haukan xata yi ne, Aliyu kam ya xama abun tausayi ba shi da aikin yi sae na kiran fateema duk ya xama wani iri haukan nasa ma sae yafi nata shi dae a bashi fateemar shi, kullum sae an xubar masa da hawaye don tausayi, gashi kullum su Faruuq sae sun xaga india neman inteesar bayan sanarwar da suka bada gidan talabijin da sauransu, Bbu abinda yafi daga ma Abba hnkli irin ynda xae tunkari momy yace basu gainteesar ba ba a ma maganar inna da ta dage xata xaman jego, hka kowa ya xama kmr mara lfya a asibitin bbu me xama yaci kwakkwaran abinci, inteesar kam na xaune hankali kwance gidan bayin Allahn da suka tsinceta ita da yaranta, sae dae fa yaran duk basu da lfya kusan kullum allura ake masu barin hassan din, duk da rashin lafiyar tasu hkn bae hanasu ci ba kmr me, shegen ci ne dasu ssae basa koshi ko kadan ko da yaushe bakinsu motsi yake, suna mugun takura inteesar gashi ruwan nonon ma bae wani cika ba, hkn yasa matar tasa Abbanmu ya siyo masu madaran jarirae take dama masu ta basu, shknn inteesar ta samu kwanciyar hankali, ko kadan ba ita take rainonsu babarin ma ba iyawa tayi ba, matar ce take masu komai nata kadae ta basu nono, nonon ma ita ta koya mata yanda xata dinga basu, kuma suna sha tana ihu wae xafi take ji, ba karamin dariya take ba matar ba, matar tace "amma ke yar fari ce ko," ranarda suka cika kwana biyar ne Abbanmu da matarsa da suke cema Anty suka sa inteesar gaba suna tambayarta me ya kawota india, inteesar tayi shiru ta rasa me xata ce tunda ita ma ganinta kawae tayi a india, a hankali ta fara magana "wllh Anty nima bansani ba kawae na gan ni ne a nn bn san wa ya kawo ni ba," duk suka yi shiru suna kallonta da mamaki, Anty tace "a Nigeria wani state kike to" inteesar tace "kano," Anty tace "to mai gidanki fa?" tace "shima a can yake," duk suka yi shiru suna kallonta, Anty tace "kin tabbata gskya kike fada mana inteesar," inteesar kmr xata yi kuka tace"Allah gskya nake gaya maku Anty," matar tace "to shknn bari ki kara kwari sae mu kai ki gida," inteesar dae bata ce komai ba, Abbanmu ya dauki Hussaini yana kallonsa yace "wnn kmr Husainin muko Antynmu," Anty tace "wllh kuwa baka ganin ita ma inteesar kmr su kusan daya da Zainab, Allah mai iko," duk suka yi dariya Abbanmu yace "baki da nmbr kowa can gida ne kada hankalinsu ya tashi dayawa, koma dae kuna da yan uwa a nn india ne?" inteesar tace "nima ban sani ba," Antynmu tace "ka bari Abbanmu nn da sati daya ae xamu je Nigerian,"Abbanmu yace "to shknn Allah ya kai mu," snn ya mike ya fita, Anty ta shiga hada masu madara don sun fara mutsu mutsun yunwa, kmr ba jarirae ba yaran, Antynmu tace "yaran nn dae da yunwa kike barinsu suna cikin ki, yara da ci hka tubarkallah," inteesar tayi murmushi bata ce komai ba ta tsura ma yaran ido, farare ne ssae kmr ita amma bbu abinda suka bari na Aliyu, idonsu, bakinsu hancinsukomai nasu na Aliyu ne, yaran kmr yaran larabawa ga lips dinsu pink gwanin sha'awa, tayi murmushi ta kauda kanta, ko wani farin ciki xae yi idan yaga ya'yansa masu kama dashi, Antyn mu ta dauki dayata shiga bashi feeder ita ma ta dauki dayan ta daukinasa ta fara basa don ta fara koyan yanda ake yi gun Anty, Anty na da kirki ssae tunda ta haihu a bedroom dinta take, kayan da suka dinga siya ma jariran sae ka rantse kace sun taba saninta, komai nasu enuf a gidan suma autansu yan biyu ne masu shekara takwas, kusan duk yamma sae Zainab ta shigo da frnds dinta daban daban wae su xo su ga Antyn ta mai kama da ita. Inteesar taji kmr tayi ta xama a gidan don tana jin ddin xama da su ssae. Abba na xaune abun duniya ya ishesa Anty Nafeesana gefensa ita ma ba um ba um um sae uban tagumin da ta rafka, wayar Abba tayi kara ya fito da shi yana kallon mai kiransa, inna ce, ya kasa dagawa har sae da ya kusan tsinkewa, kmr xata fasa masa dodon kunne yaji tace "helo Bukar ne," yace "eh nine baaba," "to wae wnn wani irin tafiya ce kayi Bukar kasan da cewar wnn ne watan Haihuwar inteesar har yau an rasa wanda xae kai ni, tun yaushe kace na hada kayana amma kayi min shiru to ni ynxu xan sa kursum ta raka ni gidan, ynxu hka ma a bakin gate nake wllh da jakata" Abbaya girgixa kai ya rasa me xae ce mata, da sauri ya samo abun cewan yace "kiyi hkuri baaba gobe xan dawo sae nasa a kaiki, kuma su dinma ae basa nn suna lgs," tace "yo ae can din dama xani," Abba yace "to shknn baaba ina nn dawowa gobe ki koma ciki," ya katse kiran ya dafe kansa cikin tashin hankali yace "ban san ya xanyi ba Nafeesa," ..Karfe tara na safiyar lahadi inteesar suka sauka kano daga lagos, Antynmu na rike da Hussaini ita tana rike da Hassan kmr yanda suke ce masu, Zainab na rike da wani yar jakan kayan abincin yaran don da ita aka taho aka bar yan biyu a india gun yan aiki, Abbanmu kuma na janye da trolley din kayan twins din, taxi suka dauka har kofar gida, Abbanmu ya ba shi kudinsa, snn inteesar ta shiga gaba Anty na biye da ita abaya Abbanmu ya tsaya daga waje shi da Zainab, hka kawae taji gabanta na faduwa, sae gidan yyi mata kmr tayi shekara bata ganshi ba, bbu kowa tsakar gida kuma dama sae da tayi wnn addu'ar a xuciyarta, direct bangaren inna ta nufa Anty na biye da ita a baya, har suka isa ta bude kofar a hankali, inna na xaune ita da kursum dake mata kitso tana ta bala'i Hajiya tayi tafiya ba tare da saninta ba sae jiya ta lura bata gidan, nn kitson xuwa gidan inteesar ake mata don jiya Abba ya dawo shima daga india ta sa shi gaba ko yaki ko ya so gobe xata tafi lgs gidan Aliyu, rasa me xae ce mata yyi, ita don tsabar masifa bata lura da yana cikin tashin hankali ba, a nutse ya fara mata magana yace "inna Aliyu fa bae da lfya......" da sauri tace"Allah ya basa lfya kuma ni ai gun inteesar nace xanje ba Aliyu ba," to kawae yace mata don takaici ya fice daga falon, inna aka shiga shirya kaya ba ji ba gani har da su kitso, Abba kam da sassafe ya bar gidan ranar da tace xata tafi lgs din, bayan ya gaya ma momy abinda ake ciki da kuma inteesar da basu gani ba don yaga boye mata bashi da wani amfani, momy batanuna masa komai ba, amma ba karamin kukan tashin hankali tayi ba bayan fitarsa, inna ta daga kai da sauri xata fara masifar waye ya bude mata kofa ba sallama, suka yi ido hudu da inteesar, inna ta yo waje da ido ta mike da sauri tana kallon yaron hannunta tace "me xan gani hka ni Rahmatu, har kin haihu ban je ba kuma ban sani ba," kawae sae ta fashe da kuka tace "Amma Allah ya isa tsakanina da yan gidan nn gaba daya, ynxu anyi min adalci knn" takaici ya ishi inteesar ga Anty a tsaye, gskya inna bata yi ba, shigowa tayi ta xauna Anty ta kasa shigowa sae kallon inna take, inna ta ciro waya tana huci tace "maxa nemo min layin Bukar," kursum da gaba daya hankalinta na kan yan biyu ita ma da mamaki ta karbi wayar takira mata Abba ta mika mata, cikin daga murya tace "amma Allah sae yyi mana hisabi da ku Bukar, ynxu yarinyar nn ashe har ta haihu ban sani ba, tun yaushe nake cewa a kai ni aka ki kaini," ta karashe maganar da matsanancin kuka ta jefar da wayar, Inteesar da haushi ya cika ta tace "Anty ki shigo mana," ganin har lkcin Anty na tsaye tana kallon inna, Anty tayi murmushi ta shigo falon ta xauna, wayar inna ya shiga ringin kursum ta mika mata tace Abba ne, a fusace tace "share mara mutunci kawae, uwar me xae gaya min, maxa kije ki kira min Zainabu don uwarta ita ma" inteesar kam kunya ne ya isheta kawae, da ta sani da gun momy kawae ta tafi, inteesar ta kwantar da yaron hannunta ta bude fridge ta ciro ruwa da lemotunda sun karya a lagos, ta ajiye ma Anty snn ta dauko kofi mata ajiye mata, Anty tace "da kin bar shi kawae inteesar, cikin yyimaki sauki ynxu ko," inna ta mike da sauri tace "cikinta ke ciwo," inteesar ta galla mata harara bata ce komai ba, kursum ta shigo rike da wayar momy tace "inna wae Abba xae maki magana," inna tace "da'alla ni a rabu dani me xae ce min," ta fixge wayar ta kara a kunne tace "me xaka ce min Bukar," wace inteesar din kasani, ae ni sae Allah ya saka min gata nn da yan biyunta sun xo da wata doguwar mata fara me dogon hanci, yo ina xan sani Bukar," ta katse wayar ta ajiye, tana kallon Kursum tace "baki ce ma Zainabu ina kiranta bne," kursum tace "tana xuwa," inteesar na kallon kursum tace"kursum Abba fa," inna tace "yace yana xuwa," inteesar ta daure fuska tace "tare da bako muke a waje inna," inna tace "toki shiga da shi falon Abban naku," inteesar ta mike ta fita ta yi kofar gida tace "Abbanmu ku shigo," har falon Abba ta kai sa, Zainab na biye da ita a baya, ta bude fridge ta ciro masa lemo da ruwa ta ajiye masa da kofi, yyi mata godiya snn ta kama hannun Zainab suka fita daga falon, a sanyaye momy ke tahowa daga bangarenta duk da kursum tace mata inteesar ceta xo sae ta kasa yrda bayan ga abinda Abba ya fada mata jiya, suna hada ido da momynta ta ruga a guje ta rungumeta cikin farin ciki, ji tayi kmr ta fi shekara rabonta da ita, momy kasa cewa komai tayi sae hawaye, hkn ya ba inteesar mamaki jikinta yyi sanyi tace "momy me ya faru," momy ta kasa cewa komai sae kallon Zainab da take, da kyar momy tace "wacece wancan," inteesar tace "parent dinta suka dawo dani gida momy suna da kirki ssae, momynta na falon inna, muje ki ganta" momy bata ce komai ba suka yi bangaren inna . Suna shiga falon inna, inna ta fara ma momy jaraba, "ynxu abinda kuka min kun kyauta knn Zainabu," Momy bata tanka inna ba ta shiga gaida Anty, Anty ta amsa da fara'arta, inna tace "magana nake maki Zainabu," Anty tace "mama bana tunanin sun san da Haihuwar inteesar fa," inna ta galla mata harara tace "ya xaki ce min hka, ke me kika sani," Anty tayi murmushi tace "to mu a india muka tsinci inteesar tana nakuda sati biyu da suka wuce, a hannuna inteesar ta haifa yaran nn, kuma bayan ta dawo hankalinta na tambayeta gun wa taxo a india, tace ita ma bata san wa ya kawota ba, satin ta kusan biyu a gidanmu muka maido da ita nan Nigeria da mai gidana," inna tayi tsaki tace "ni ban gane shirmamman hausan nn naki ba, uwar wa inteesar ta sani a india da xa ki ganta a can, da ma lagos kika ce min, wnn karya kike yi" sallamar Abba ne yasa inna yin shiru tace "ka xo kaji min karyar bnxa Bukar wae a india aka ga inteesar tana yawo," Abba ya shigo falon yana kallon inteesar da mamaki, ya xauna ba tare da ya shirya ba ya sauke wani ajiyar xuciya ya dafe kansa yace "Alhmdllhi," inna tace "ta me," kasa ba inna amsa yyi yana kallon Anty yace "baiwar Allah a ina kuka ga wnn yarinyar don Allah," Anty tace "a new delhi ni da mai gidana mun fito daga wani plaza," Abba yace "Allah ubangiji ya taimake ku kuma kmr ynda kuka taimakeni ya saka maku da alkhairi," inna tace "yau naga tsiya, wae me ke faruwa ne," Abba ya juya yana kallon inna yace "baaba yau kusan wata uku knn Fateema bata cikin hankalinta bamu gaya maki ba, mu ne har india daga lgs nemo lafiyarta satinmu uku a india aka nemeta aka rasa yau sati biyu da kwanaki knn da muke nemanta a india......" inna ta katse sa da sauri tace "kmr ya bata cikin hankalinta, hauka take ko me," Abba yace "kwarae kuwa baaba amma wa ya bamu karfin gwiwan xuwa mu gaya maki wnn mummunan lbrin mara ddin ji , baaba na shiga damuwar da ban taba shiga ba a rayuwata, ynxu hka Aliyu na can a asibitin shima ba hankalin tun bayan da muka nemi fateema muka rasa, su Nafeesa da Haisam ae duk suna can" tunda Abba ya fara magana inteesar ta tsaya da mamaki tana kallon Abba, wae ita ce tayi hauka, maganar Abba ta karshe yasa ta hawaye, inna ta mike jikinta na rawan bala'i tace "waye ya haukatar min da jikata a gaya min don bamu gaji hauka a xuri'armu ba," Abba ya sauke ajiyar xuciya bae ce komai ba, kuka ssae inteesar take, hka ma momy, Anty kam jikinta yyi sanyi, don bata san a haukace suka tsinci inteesar ba, kuma bata ga alamar hkn ba, inna ta dinga ihu da kuka a gidan wae a kaita gidansu safeena tasan baxae wuce aikin asiri ba su suka mata asiri, Abba ya mike bae bi ta kan inna ba ya fice a xuciyarsa yana hamdalar bayyanar inteesar da gaggawa hka, wae bayan komai ya lafa inna ta sani amma dubi reactions dinta yasan bae yi kuskuren rashin gaya mata da bae yi ba, yana fita Nafeesa ya fara kira ya sanar mata snn ya shiga falonsa ya tarar da Abbanmu xaune yana kallon news, yace "ashe bako gareni basu sanar da ni ba," ya bashi hannu suka gaisa snn ya shiga yi masa gdya kafin yyi masa bayanin abinda ya faru. Momy ta mike ta fita tayi bangarenta ganin irin haukan da inna take ba ji ba gani, Anty na bata hkuri, "ki kyaleni nayi yarinya, a haukatar min da jika bata yi masu komae ba, kuma nayi shiru, ae da wani abu ya sami inteesar a duniyar nn da kowa kashinsa ya bushe a gidan nn, shi kuma Aliyu ya karata da haukansa tun da shi ya siyar ma kansa dama na sha gaya masa shi mahaukaci ne," ta karashe maganar tana huci ta shige daki, inteesar dae sae kuka take duk hnklinta na gun Aliyu da Abba yace ke hauka sbda ita, Anty ta shiga hada ma Hassan dake kuka abinci, inteesar ta mike ta bi inna daki jikinta a sanyaye, katuwar tunkuyarta take kkrin fitowa da xata je daura ruwan wanka, inteesar na hawaye tace "inna don Allah kice ma Abba su barni na je gun ya Aliyu tunda......" inna ta dakatar da ita a fusace tace "kina danyan jegon xaki tafi gun wani mahaukaci can," inteesar ta fashe da kuka tace "ni ki daina ce masa mahaukaci, ki taimaka min kiyi ma Abba magana " inna tace "to baki isa ba don ubanki," ta fice da katuwar tukunyanta tana kwala ma kursum kira ta siyo mata itace, inteesar ta xube kan gado tana ci gaba da kuka, ta kai kusan awa daya a hka taji ihun Husaini ta fito da gudu ba tare da ta shirya ba, taga inna ce ke masa wanka sae kunya ta kamata ynda ta fito a rude, Anty tayi dariya tace "wanka ake masa ba wani abu ba maman biyu," inna ta tabe baki tace "ki rabu da gantalalliya tana danya da ita wae gun wancan mahaukacin xata ya buge min ita a bnxa, shi fa ya janyo ma kansa yar nn, wata shegiyar karuwar mace me xubin kafurae ya auro suka dinga walakanta min jikata sae ga shi wae har sun haukatata ban sani ba, gashi ynxu Allah yyi mata sakayya abunsu ya koma masu, ni dae Alhmdllhi tunda jikata ta dawo lfya, miko min tsummar can" inteesar ta juya ta koma daki a sanyaye hawaye na bin kuncinta, kursum ta shigo tana kallon inteesar tace "Abba yace kije," . ....A hankali Inteesar tayi sallama ta shiga falon Abba, ta xauna kasa tace "Abba gani" Abba yace ta koma kan kujera, ta mike ta xauna kan kujera tana kallon Abbanmu dake ta bin ta da kallo, tayi murmushi ta sunkuyar da kanta kasa, Abba yyi shiru snn yace "ina yaran," xata yi magana sae ga kursum ta shigo rike da Hassan, Zainab na biye da ita a baya rike da Hussain, duk Abba ya amshesu yana kallonsu yana murmushi, kmr ba jarirae ba suma idonsu kyar a kansa, sae da ya tofa masu addua gaba daya snn ya kwantar dasu kan kujera ita dae inteesar kanta na kasa, Abba na kallon Abbanmu yace "dota dinka knn ko Alhaji Umar ko," Abbanmu yyi murmushi yana kallon Zainab yace "eh ita ce diyata ta farko," Abba yyi murmushi yace "Allah sarki sae naga suna kama da inteesar," Abbanmu yyi dariya yace "hka ne kam," kursum suka fita tare da Zainab snn Abba yace "kina jina fateema," ta gyada masa kai yace "idan kin huta xaku koma can india dasu Antynki amma fa sae idan kina son komawa baxa mu takuraki ba, nasan dae kina sane dae Aliyu bashi da lfya ko," kai kawae ta gyada masa tana hawaye, Abba yace "ba kuka xakiyi ba, Addua xakiyi masa," a hankali tace "Abba ni na gama hutawa mu tafi yau kawae," Abbanmu yace "yauwa fateema ashe kina da hankali gwara kije gun mijinki tunda rashin ki ya jawo masa wnn lalura," bata ce komai ba Abba yace "shknn fateema Allah yyi maki albarka, amma ki bari gobe ku tafi sbda yaran nn kar suyi xaxxabi je ki ki kira min momynki," ta mike ta fita daga falon, Abbanmu yace "xanje gun wani abokina dake nn gadon kaya," Abba yace "to shknn Alhaji sae ka dawo," Abbanmu ya mike ya fita yana kiran Anty a waya ya sanar da ita xae dan fita, bayan fitarsa da minti biyar inteesar suka shigo da momynta, Abba yyi mata bayanin abinda suka tsara da Abbanmu kan cewa su koma can india da inteesar gun Aliyu, momy tace "hkn ma yyi, Allah dae ya basa lfya," Abba yace"Ameen don son Annabi," inteesar ta mike ta fita ta bar masu falon ta koma falon inna, kmr ba jego take ba garau take jin kanta, a bakin kofa ta tar da inna tana masu lafiyayyan girki inna tace "Allah sarki Aliyu, wae wani irin ciwo aka ce yake yi hka, a dawo min da jikana gida kawae na nema masa magani,"ko kallonta inteesar bata yi *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** ba ta shiga falo Anty ta sata gaba ta shanye kunun da inna ta dama mata don har lkcn bata yi wani break din kirki ba, kasa sukuni tayi ranar Allah Allah take kawae gobe yyi ta je ta ga Aliyu duk hnkalinta yyi gunsa, momyce ta dawo da yaran daga gun Abba suna kuka ta bai ma mamarsu su ta fita, wajen karfe uku Anty ta tafi bangaren momy inna kuma ta tafi nemo ganyen darbejiya, inteesar nata fama da Hassan dake ta yi mata rigima kursum na rike da Hussaini, kursum tace "wae sunansu knn," inteesar tace "A'a ba a rada masu suna ba har ynxu ae, wae ina su khadija" kursum tace "khadija na gidan Zainab bata da lfya, rahma kuma na can gidansu mamarmu" inteesar tace "Allah sarki Zainab, Hajiya da umma fa," kursum tace "hajiya tayi tafiya, umma kuma tana can gidansu Fadila ta kara kashe aurenta, shine Abba yace su tafi su bar masa gidansa," inteesar tayi shiru da mamaki tana kallon kursum, can tace "yaushe hkn ya faru," kursum tace "kusan wata biyu knn, inna ce tace Abba ya koresu ko ita ta bar masu gidan," inteesar bata sake cewa komai ba amma ko kadan bata jin ddin abinda inna ke yi, fira suka dinga yi da kursum har inna ta dawo duk ta hada xufa da darbejiyarta tace "da kyar na samo wnn, maxa ki tube ki shiga bayi ki jira ni na juyo ruwan," inteesar ta mike da sauri tace "ke dawa, wllh baxa kiyi min wanka ba da girmana kuma da wnn abun, to wae ca nayi maki banyi wanka bne," inna tace "yau naga tsiya, har wani wanka kike yi dubi ynda kike tafiya kmr wata rubabbiya, wa ya sani ma ko da ruwan sanyi ake maki wanka a can" ko kallonta inteesar bata yi ba ta fice daga falon tayi gun momynta. Washegari har airport Abba ya kai su a motarsa aka bar Zainab gun momy don xasu dawo, inteesar bata ji ddin rashin fitowar da momy tayi ta rakasu ba, basu samu jirgin da xae je india ranar ba a Aminu kano don hka sae da suka fara xuwa lgs snn suka kama hanyar india .. Da yamma inteesar da Abbanmu suka kama hanyar asibitin da Aliyu yake bayan sun huta can gida, a motar Abbanmu suke tafiyar sae bin ko ina take da kallo india yyi mata kyau ssae, Anty na gida da yan biyu don xaxxabi ssae suke tun bayan saukansu da safe, suna isa asibitin gaban inteesar ya shiga faduwa suka yi parkin, suka fito Abbanmu ya shiga kiran Anty Nafeesa kmr ynda Abba yace masu, ta fito da sauri ta rungume inteesar tana hawayen murna ita ma kukan ta fara yi, a hka ta jata suka shiga asibitin, Inteesar taje da gudu ta rungume Haisam da hawaye ya cika idonsa ganinta ya ma rasa me xae ce, da kyar ya iya cewa "ina yaran inteesar," ta goge hawayen fuskarta tace "suna gun Antyna," ido hudu suka yi da Hajiya dake rabe wani lungu kmr marainiya Hajiya ta taso tana hawaye ssae ta rungume inteesar ta kasa cewa komai, kuka ssae inteesar take, murya na rawa Hajiya tace "ki yafe mani inteesar ba don halina ba," kasa cewa komai inteesar tayi sae gyada mata kai take, Haisam ya gaida Abbanmu dake tsaye, hka ma Anty Nafeesa da Hajiya duk da basu sansa ba suka basa kujera ya xauna, inteesar sae kalle kalle take, taji ba a ce mata komai kan Aliyu ba, cire kunya tayi tana kallon Haisam a hankali tace "ya Haisam, ya Aliyu fa," ya dan yi shiru snn yace "xaki gansa akwae likita a dakin ne ynxu," ta gyada masa kai jikinta a sanyaye, Anty nafeesa tace "ina yaran inteesar, Abba yace da su kuka taho" inteesar tace "suna gun Antyna a can gida," bbu wanda ya sake cewa komai cikinsu har likitan dake dakin ya fito, Haisam ya mike ya bisa da turanci yake tambayarsa xa a iya shiga a gansa, likitan yace xa a iya shiga amma kar wanda yaje kusa da shi," inteesar ta mike da sauri gabanta na faduwa nn da nn hawaye ya cika idonta, tayi hanyar kofar Haisam ya dakatar da ita, da kyar ta juyo tana kallonsa, Haisam ya karasa yace ta koma baya, ba dan ta so ba ta koma baya, ya bude kofar dakin a hankali yana leka, yana durkushe kansa a kasa kmr me karatu, Haisam ya tsaya daga bakin kofar yana kallonsa, Anty Nafeesa sae lekan dakin daga waje take hka ma Hajiya duk suka ki shiga don uban mutane yake ci, Abbanmu xae shiga Haisam ya dakatar da shi, inteesar sae kuka take a hankali, gabanta na faduwa tana kallon Haisam tace "ka bar ni na shiga ya Haisam baxan je kusa da shi ba," Anty nafeesa ta girgixa kai a tsorace tace "A'a ki gansa daga nn kar ki shiga," kasa daurewa tayi ta karasa cikin dakin tana kuka ssae ta tsaya dan nesa da shi tana kallonsa, har lkcn bae dago kansa ba, kafarta ya kasa daukanta ta durkushe wajen tana kuka tana kiran sunansa, hajiya ta dage sae cewa take Haisam ka fito da ita, tun da ya shaketa take tsoron ganinsa bare xuwa kusa da shi, Inteesar ta rarrafa ta karasa dab dashi jikinta na rawa tana kallonsa, Haisam da Anty Nafeesa suka shiga kiranta ta fito amma ina, dagowa yyi yana kallonta ta tsorata ssae ta fara komawa baya ganin yanayinsa, yyi wani irin kara ya mike tsaye ya fixgota ya shaketa ta fasa ihu ta kankamesa a tsorace jikinta na rawa ta shiga kiran sunansa, da gudu Anty Nafeesa taje kiran likita a rikice, Hajiya kam sae kuka take tana cewa ku fito da ita, Abbanmu ya karaso cikin dakin da sauri hka ma Haisam, kkrin fixgeta daga jikinsa yake a fusace amma ya kasa tana jikin nasa ya buga su da bango a tare, kuka take ssae tana kiran sunansa, amma ina yyi wani irin kara hade da kiran sunanta ya fixge ta daga jikinsa ya wurgar da ita, ta buge da bango ta sulale kasan dakin, tangal tangal ya shiga yi a dakin kmr mashayi yana kallonta, ya karasa kusa da ita da kyar yace "fa fateema fateemaaa," yyi wani kara ya sulale wajen shima a sume. Likitoci suka shigo dakin da sauri suka yi kansu, bata suma ba amma taji jiki, sae masifa likitocin suke masu suka hau kansa, duk ynda aka yi da inteesar su wuce gida da Abbanmu kin wucewa tayi ga wani shegen ciwo da kanta yake, har dare suna asibitin da Abbanmu, karfe sha biyu na dare tana jikin Anty nafeesa tana bacci, Abbanmu na xaune da Haisam, Hajiya na durkushe a kasa wani likita ya shigo dakin da sauri yana tambayar wacece fateema, bacci inteesar take amma da sauri ta mike tana kallonsa, yace ta biyosa bata yi wani tunani ba ta bisa da sauri, dakin da Aliyu yake ya shiga ta bisa, likitoci ne biyu a kansa yana xaune kan gado ya dafe kansa, inteesar ta karasa kusa da su da sauri gabanta na faduwa duk da abinda yyi mata daxu, ta shiga kiransa muryarta na rawa ya dago kai yana kallonta ya mike tsaye da sauri duk da jikinsa ba kwari, bata yi wani tunani ba ta je da gudu ta fada jikinsa ta fashe da kuka suka yi baya suka fada kan gadon dn bae da wani karfi, ta daga sa da sauri ya mike xaune ya rungumeta tsam jikinsa yana hawaye yace "don Allah kar ki kuma tafiya ki bar ni fateema plss i beg yhu" kuka ssae yake ita ma hka, su Anty Nafeesa suka shigo dakin suna kallonsu, Hajya ta sulale kasa tana kuka ssae ita ma, hka ma Anty Nafeesa da ta kasa kallonsu ta juya, Abbanmu ne kadae yyi ta maxa, su kansu likitocin sae da abun ya basu tausayi . ..Inteesar ta dde rungume jikin Aliyu suna hawaye duk aka fita aka bar masu dakin, ta dago a hankali tana kallonsa, fuskarsa na kan gashinta idonsa a lumshe, xamewa tayi daga jikinsa, yakoma ya kwanta a hankali kan gado har lkcin idonsa a rufe, ta kwanta gefensa tana kallonsa hawaye na bin kuncinta ta kira sunansa a hankali, shima sunanta ya kira ba tare da ya bude idonsa ba, ta daura kanta kan kirjinsa muryarta na rawa tace"kayi hkuri ya Aliyu nice na ja maka," a hankali yace "kar ki kuma tafiya ki barni fateema don Allah," kai kawae ta shiga gyada masa tana kuka ssae, ya kankameta jikinsa yana girgixa mata kai, a hankali tace "ya Aliyu," bae ce mata komai ba kuma bae bude idonsa dake rufe har lkcn ba, ta mike xaune tana kallonsa ta kuma kiran sunansa, dafe kansa yyi murya kasa kasa yace "kaina ciwo yake min ssae fateema, it hurt so badly" ta taimaka masa ya mike xaune har lkcin idonsa rufe, tama rasa me xata yi, kuka ta fashe masa da ya jawota jikinsa yana shafa gashinta, ta xame da sauri ta fita ta kira likita, suna shigowa suka dubasa suka yi masa allura snn aka sa masa ruwa, tea Anty Nafeesa ta kawo mata ta bashi, a hankali ta dinga basa har yace mata baya sha kuma, snn ta taimaka masa ya koma ya kwanta, yana kwanciya bacci ya daukesa, a gefensa ta kwana ranan a xaune, duk motsin da xae yi sae ta tambayesa me yake so, sae dae ya girgixa mata kai idonsa a rufe, da gani kasan daurewa kawae yake har gari ya waye, hka inteesar ta dinga kula dashi komai ita ke masa ko kadan bae da karfi ga ciwon kan da ya sa shi gaba don sae ya wuni wani lkcn bae bude idon ba, da safe da dare Anty ke kawo mata twins tayi breatfeedin dinsu snn ta wuce dasu gida don wajenta suke wuni kuma su kwana tunda suna shan madara, har lkcn Aliyu bae ga yaransa ba hasalima bbu wanda yyi masa maganarsu, shima kuma bae tambaya ba. kwanansu hudu a asibitin aka sallamesu badon likitocin sun so ba sae don Aliyu ya takura a sallamesa, duk da har lkcin yana yawan complain ciwon kai, gidansu Abbanmu suka sauka don likitocin sun ce kar ya bi hanya ynxu duk da bae so hkn ba, tuniAnty Nafeesa ta koma Nigeria da Faruuq, Haisam ne kadae ya rage tare dasu, Hajiya ma washegarin ranar da ya warke ta koma duk don taje ta sami safeena da uwarta, daki daya gari guda aka ba inteesar da Aliyu a gidan Abbanmu, ta ci gaba da kula da mijinta tana tilasta shi yana shan magungunansa, don baya son shan magani, komai ita ke masa, duk da sun dawo gidan Ant, Anty bata takurata da yaran ba stil gunta suke wuni su kwana sae dai ta kai su kawae ta basu nono ta kuma karbansu ta wuce, kirkinsu Anty da mijinta ya wuce misali bbu abinda suka ragesu da komai enuf kmr suna gidansu, amma duk da hka Aliyu duk ya damu xae koma gida, hkn yasa Abbanmu yace to su bari ya gama abinda yake nn da sati dayasae su tafi gaba daya, bae yi masa musu ba ya yrda ya kara sati daya a india, suna daki ana jibi xa su tafi bayan ta gama basa abinci ya sha maganinsa ta rungumesa jikinta don hka take masa har yyi bacci, sae dae yyi murmushi baya ce mata komai, yau kam shafata kawae yake kansa na kan kirjinta idonsa lumshe kuma bata hanasa ba duk da gabanta faduwa yake amma bata nuna ba, bubbuga kofa aka yi hade da sallama ta xabura da sauri, shima ya bude idonsa da suka canxa launi ya amsa sallaman jin kukan twins, yar aiki ce ta shigo dakin ta karasa kusa da gadon ta kwantar dasu da yake ta saba da inteesar ssae don ita ma yar Nigeria ce tana dariya tace idan an gama ji da baban bbie, Anty tace aji da bbies," inteesar tayi murmushi tace "to Anty," matar ta fita ta kullo masu dakin, ya kankameta jikinsa fuskarsa a kan kirjinta yace"i love yhu my inteesar," a hankali tace "i love yhu 2 my Hydar," ya dago yana murmushi ta rufe idonta da sauri ya daura bakinsa kan nata ya shiga kissn dinta, bbies nata kuka, da kyardon ita ma ta fara dauke wuta ta turasa daga jikinta tace"bbies suna kuka" ya fada gefen gado ya kwanta yana mayar da numfashi yace "ni ke na sani ba bbies ba," ta hade rae tana kallonsa tace "tunda kaga yaran nn baka taba daukarsu ba, sae naga kmr baka sonsu," ya juya yana kallon yaran da suka xama wasu manya abun sha'awa wata daya da haihu, bbu abinda suka bari nashi kmr an tsaga kara, ya dan yi murmushi ya kwasosu ya xuba su jikinsa 4 d first tym, yana kallon inteesar yace "da haushinsu nake ji bbyna sae naga kmr sune suka cutar min dake suka baki wahala" inteesar tayi shiru batace komai ba don har lkcn bae san safeena bace tayi mata asiri wae kmr ynda Hajiyrsa da inna ke fada. Da kansa ya ciro masuabincinsu yana kallon cikin idonta ta kauda kanta sakamakon wani yarr da taji, ya rungumeta ta baya ta rike Hassan din da ya daura mata a cinya, dayan kam ya hkura yyi shiru, da kansaya shiga basa nonon ta bayansu, yana kissin din wuyarta ta turasa da kyar ta kwace breast dinta tace "ka bari kar ya kware," ta rungume danta ta shiga basa nonon a nutse. Yyi tagumi hannu bibbiyu yana kallonsu yana murmushin da shi kansa bai san dalilin ba . ... Ranar da xasu bar india inteesar nata shirya kayan bbies din da Anty tace ta hada gaba daya su tafi dasu don da bata yi niyyar su dauki ko wani kaya ba, Aliyu ya fitada Abban Najeeb da ya taso tun daga Nigeria yaxo india sbda shi kuma tare xasu bar india ranar, inteesar ta gama shirya kayanta da na bbies gaba daya da na Aliyu, suna kwance kan gado suna ta rigima duk sun isheta ita kam tana ganin kkrin Anty da bata gajiya da su, gashi bata iya daukansu gaba daya lkci daya ba don nauyinsu tubarkallah in ka gansu kmr yaran da suka yi wata uku, Hassan ta fara dauka xata kai ma Anty kafin ta dawo ta dauki Hussainin ta duba daki bata ga Anty ba hkn yasa ta sauko xuwa falon, Anty na xaune da bako a falon, ta karasa cikin falon da sallamarta kmr xata yi kuka tace "Anty ni wllh yaran nn sun isheni sae suyi ta kukan karya suna damuna kuma ba yunwa suke ji ba," Anty tayi dariya ssae ta karbeshi daga hannunta tace "ni basu isheni ba da ma ki bar min su wllh," inteesar tayi dariya ta juya xata je ta daukodayan suka yi ido hudu da wani mai kama da Aliyunta a xaune a falon, ta kasa daina kallonsa, he looks familiar, ta dauke kanta da sauri xata bar wajen taji yace "fateema" da mamaki ta juya tana kallonsa, sae a snn ta tuna sa, ofcourse Dr din da yabata maganin cire ciki ne a Nigeria, gabanta yyi mugun faduwa, ta bar falon da sauri, Anty ta shiga cewa "A ina kasanta Sadeeq," ya bita da kallo har tabace masa snn yace "Anty ina kika san yarinyar nn,"inteesar bata sake saukowa ba har ya bar gidan gabanta sae faduwa yake, Anty ta shigo dakin tana kallonta ta xauna snn tace "meyasa kika yi hka Fateema," inteesar ta sunkuyar da kanta sae hawaye, Anty tayi shiru snn tace "to Allah shi kyauta ya kuma yafe mana kurakuranmu, Sadeeq kanina ne uwar mu daya ubanmu daya, a Nigeria yake aiki, yyi min bayanin komai," inteesar ta share hawayenta tace "baxan ma sake ba Anty, ki basa hkurin karyan da nayi masa nasa ya aikata abinda bae dace ba, duk da gashi at lng lst sae da na haifesu," Anty ta rungumeta tace "shknn ya isa fateema ki daina kuka, nima nayi masa fadan abinda yyi bae dace ba," kai kawae inteesar ta gyada mata ta dauki Hussain ta fita tana cewa shima yau xae koma Nigeria jirgi daya xamu shiga idan Allah ya yrda. Ranar lahadi karfe goma saura su inteesar suka sauka kano daga lgs, a airport suka rabu da Abban Najeeb, Sadeeq ma daga nn suka rabu bayan yyi ma Aliyu alkawarin xae kawo masu visit, shi yyi ta rainon Hassan a jirgi yaran sun shiga ransa ssae, inteesar tayi masa gdya ya shiga taxi ya wuce, Haisam ne yaxo daukansu daga airport, ya gaida abbanmu cikin ladabi snn ya gaidaAnty, inteesar ta gaida shi tana murmushi ya juya yana hararan Aliyu dake murmushi suka kama hanyar gida gaba daya, falon Abba Abbanmu ya sauka, inteesar da Anty kuma gun inna suka sauka Hajiya tayi welcmin dinsu ssae ta rasa inda xata sa inteesar da ya'yanta ita ta hada masu breakfst aka kai ma Abbanmu nasa can falon Abba, inteesar da Anty suka yi tare, inna sae xuba take masu ta rasa inda xata sa bbies da suka xama kmr wasu yaran larabawa don kyau, momy ta xo tayi masu sannu daxuwa cike da fara'a mai sunanta na nane da ita, bata yi wani miss din iyayen nata ba, yarinyar ta rungume inteesar snn ta rungume uwarta tana yi masu sannu da xuwa ta dauki twin, Anty Nafeesa ma ta xo yi masu sannu da xuwa baki har kunne, karfe biyar na yamma gaba daya suka hallara falon Abba don Anty sunce ranar xasu tafi kaduna don suna da gida a can, har dasu inna gayyar sodi tunda ba'a gayyace ta ba, inteesar na dakin Aliyu lkcn kursum ta kwankwasa tace Abba na kiransu, a tare suka shiga falon sae kunya ya kama inteesar taxauna gefen Anty, shi kuma ya xauna gefen Haisam,Abbanmu yace "ina twins suke," inteesar tace "sunagun momy," Abba yace "ina momyn take je ki ki kirata," inteesar ta mike ta fita xuwa ta kira momynta, ta gama shirya yaran knn ta shigo tace"momy Abba na kiranki," momy tasa hijab ta dauki daya ita ma ta dauki dayan suka fito tana cewa"momy ihsaan fa wae," momy tace "tana gidan Zainab anjima xasu xo da daddare, ita ma laulayi take," inteesar tace "Allah sarki Zainab, Allah ya bata lfya," inteesar tayi sallama ta shiga falon hka ma mmy, cak momy ta tsaya daga bakin kofar idonta a kan Abbanmu da shima nasa idon na kantamurmushin da yake dauke da a fuskarsa sakamakon hiran da suke yi da Abba ya bace nn da nn, ya mike tsaye da kyar yana kallonta cikin wani irin yanayi yace "Zai zainab," nn da nn hawaye ya cika idon momy ta juya da sauri ta bar falon, Abba ya mike yana kallonsa da mamaki, da kyar dae yace"Alhaji umar ina kasan Zainab din," Abbanmu da ya rikice lkci daya yace "wllh wllh matatace," ya juya yana kallon inteesar, da sauri ta mike ta fice daga falon, Abba yace "a ina ta xama matarka" Abbanmu ya girgixa kai yana kallon Anty dake kallnsa da mmki yace "matata ce wllh" inna ta mike tayo waje da ido tace "yau naga tsiya a ina ta xama matarka ni Rahmatu, Bukar ina Kaso wanna tabbaben. Inteesar_____2*16 . Khaleesat Haiydar . Abba ya juya yana kallon inna don takaici ya ma rasa me xae ce mata, ita ko ta dage sae an gaya mata inda aka samo Abbanmu, a fusace Anty Nafeesa tace "don Allah idan baxa kiyi shiru ba inna xa mu bar maki falon nn, haba don Allah" shi kam Abbanmu kallonta kawae yake daga tsayen da yake, Abba yace "to Alhaji Umar ae bayani xaka mana ta ynda Zainab ta xama matarka," Abbanmu ya koma ya xauna ya kasa cewa komai har lkcin idonsa na bakin kofa kmr xae bita, sae da Abba ya kuma maimaita masa tambayar snn a hankli yace "matata ce," a fusace inna tace "yau naga abinda ya isheni don Allah a fitar min da wnn mutumin na daina ganinsa," Abba ya hade rai yace "don Allah baaba ki fita ki bamu waje, dama bbu wnda ya gayyato ki nn," ya maida dubansa ga Abbanmu yace "to ae bayani xaka mana," Abbanmu ya dan yi shiru snn yace "matata ce kusan shekaru sha takwas da suka wuce baya," kowa yyi shiru yana kallonsa, Abba yace "to me ya raba ku," ya girgixa kai yace "wllh bamu rabu ba," Abba yace "a wani garin kuke lkcn tana matarka," Abbanmu yace "Misra," Abba yace "to me ya dawo da ita Nigeria," Abbanmu yyi shiru na dan lkci snn yace "wllh nima ban sani ba," Anty ta mike ta fita waje, Abba bae kuma cewa komai ba ya juya yana kallon inna da ta cika tayi fam sae huci take, Abba ya mike yace yana xuwa ya fita, a daki inteesar ta tarar da momynta xaune tana kuka, ta sulale gabanta xuciyartana bugawa tace "momy waye shi," sae da momy ta dau lkci snn tace "shine mahaifinki inteesar," inteesar tayi shiru hawaye na bin kuncinta tana kallon momynta da kyar tace "shine Abbana," momy ta gyada mata kai, inteesar ta fashe da kukan da bata san dalilinsa ba, kukan farin ciki ne, na bakin ciki ne ta kasa ganewa, ynxu Abbanmu shi ya haifeta, sallamar Anty yasa gaba daya suka juya sun kallon bakin kofa, har daki ta shigo ta xauna tana kallon momy tace "kiyi hkuri Zainab, nasan da lbrinki da ddewa, amma karki ga laifin Umar, kullum kina ransa, kuma bbu inda bae shiga ba don nemanki though nasan ba lallai ki yrda da abinda nake gaya maki ba," momy ta kasa ce mata komai inteesar kam sae kuka take, Anty ta rungumeta tace "Allah sarki inteesar dama yace min yana ganin Zainab dinsa a idonki," Abba yyi sallama ya shigo falon snn ya karasa cikin dakin, mikewa Anty tayi ta ja inteesar suka fita, falon ta mayar da ita Abbanmu sae kallonta yake da ganinsa kasan yana cikin damuwa a lkcn, inteesar ta kasa daga kai ta kalleshi sae hawaye take, Aliyu ya girgixa mata kai alamar ta daina kukan, inna ta tabe baki tace "to yau dae xan ga karshen wnn tsiya," bbu wanda ya tanka mata a falon, bayan kmr minti goma Abba ya dawo falon da momy, Abbanmu sae kallonta yake, Abba ya juya yana kallonsa yace "to ynxu Alhaji Umar ya kke son ayi don dae ynxu Zainab matata ce," inna tace "ya ko xa'ayi," da sauri Abbanmu yace "ni bance ayi komai ba," Abba yace "to me ya rabaka da Zainab can misira, har ta dawo nn Nigeria" Abbanmu yace "wllh wllh ban sani ba, ni dae nasan auren soyayya muka yi kuma a katsina na aurota ta dalilin wani abokina, amma lkcin ina da mata a nn egypt, danginta suka bani ita bayan anyi komai muka tafi egypt, iyayena yan can ne amma sun rasu, to a gskya nasan matata ta farko bata da kirki ko kadan, kuma Zainab tana da hkuri fiye da ynda mutum xae yi xato, snn ni din Allah yyi ni mai dukiya watan mu takwas da Zainab na rasa abinda ya faru...." da sauri inna ta dakatar da shi a fusace tace "karya kke, ca tayi guduwa kayi ka barta," Abbanmu yace "wllh baaba ni ban san ya akayi ba," ya sauko kasa yana kallon inna hawaye cike idonsa yace "ki tambayeta mama, ni ban taba cutarta ba ko sau daya a xaman da muka yi, wllh bbu inda ban shiga neman Zainab ba can katsina da naje danginta ca suka yi basu ganta ba, don Zainab marainiyace," sae a snn inna ta fara matsar kwalla tace "to nice nn na tsinci Zainabu da tsohon cikin inteesar, na kuma taimaka mata don na gaji taimako a wajen ubana, kuma duk wanda baya taimako ya tabe, ni nn bbu abinda bn yi ma Zainabu ba har ta haihu nasa dana yyi mata suna, tace min bata da kowa sae Allahnta se kai, nn na tilasta Bukar ya biya mana kudin jirgi muka je nemanka amma sae muka tarar ma wae har ka sayar da gidan" Abbanmu sae yi magana inna ta dakatar dashi a fusace tana kuka wiwi, "yi min shiru, to wae ma tunanin uban me kke ka gudu ka bar mata da tsohon ciki," ta share hawaye ta tsuke fuska ta rungume hannayenta ta rike haba tana Kallonsa tana jira ansa . .... Abbanmu ya rasa me xae ce ma inna ya sunkuyar da kansa kawae, Abba yace "haba inna ynxu ai komai ya wuce, don Allah ki bar maganar nn hka," Inteesar ta kasa xama a falon tana kuka har lkcn ta mike ta fita, Abbanmu ya bita da kallo shima hawaye a nasa idon, Momy kam kanta na kasa bata dago ba tunda ta shigo, mikewa Aliyu yyi shima ya fita daga falon, bangarensu tayi don hka ya bita da sauri har ya isketa ya jawota jikinsa yace "haba bbyna don me kika fita," kasa ce masa komai tayi sae kuka take, ya kama hannunta yyi bangarensa da ita suka shiga bedroom dinsa ya xaunar da ita kan gado yace "yau ranar farin ciki ne a gareki kanwata, bae kamata kiyi kuka ba gode ma Allah xaki yi," bata ce komai ba ya rungumeta yace "kar ki sake wnn kukan dear," gyada masa kai kawae tayi tana kirjinsa, kursum tayi sallama bakin kofa, ya mike ya fita xuwa falo snn ya bude kofar, Hussaini ne a hannunta yana kuka, ya karbesa tace "ina xuwa na dauko dayan shima kuka yake," ta juya da sauri ya shiga daki ya mika ma inteesar shi, ta karbesa, snn ya koma ya karbo dayan ya rufe kofar ya dawo ya xauna gefenta yana kallonta tana ba Hussaini nono, a hankali yace "wani suna xamu sa masu Wife?" tayi shiru bata ce komai ba, ya jinginar da kansa jikin nata yace "na lura kin kasa sakin jikinki da ni ko fateema," tayi murmushi tace "eh mana, ae kai ko...." da sauri ya rufe bakinta yace "no fateema, let bygones B bygones, plss," ta kwantar da yaron hannunta ta juya tana facin dinsa xata yi magana ya rungumeta a hankali yace "ban san me xan maki ki yrda ina sonki ba fateema" hawaye ya cika idonsa yace "ki yrda dani inteesar ni din me sonki ne da gskya wllh," ta gyada masa kai tace "na yrda," ya dago kanta yana murmushi yace "thank yhu fateema," ita ma tayi murmushin snn tace "Sunan Abba nake son a sa ma Hassan, Hussaini kuma ka xabi sunan da kke so" yyi murmushi ya rungumeta bae ce komai ba. washegari da safe inna tasa inteesar taje gun mahaifinta su gana da kyau tunda momy ma tace ta yafe, bata yi mata musu ba taje ta samesa a falon Abba, shi kadae ne xaune a falon da yan biyu, ta karasa ta xauna ta gaishesa kanta a kasa, ya amsa yana murmushin jin ddin ganinta, sun dde suna hira da Abban nata tana basa lbri iri iri yawanci duk akan inna har lkcn sllhn azahar yyi yace xae tafi masallaci ta dauki yaranta tayi gun momynta dasu. Washegari da safe aka rada ma twins suna, Hassan aka sa mashi Abubukar Sadeeq, Hussaini kuma aka sa mashi Umar Faruuq, sunan Abbanmu, rago hudu aka yanka masu, kuma ba ayi taron suna ba, su Anty da Anty Nafeesa da wasu kawayen Hajiya ne suka yi aikin naman, kwanan Abbanmu da Anty uku a gidan suka fara shirin komawa india bayan komai ya daidaita, ya ba twin kyautan million daya, inna ta karbe wae xata ajiye masu har su girma, yyi ma inna ma kyauta mai yawa, snn ya mallaka ma inteesar gidansa dake kaduna, Anty Nafeesa ta shiga gyara inteesar don itama xata koma dakinta kmr ynda Abba yace, ranar da Abbanmu da Anty suka wuce ranar Aliyu ya dauki matarsa da yaransa da daddare suka koma gida bayan Abba yyi masu nasiha ssae kan sun xauna lfya, yana rike da yaransa tana biye dashi a baya suka shiga gidan, ya kwantar dasu kan kujera ya rungumeta yace "New life inteesar," murmushi tayi bata ce komai ba ta haura sama, komai na gidan sabo ne, har dakinta ma an canxa mata furnitures, ta fito daga wanka ya shigo dakin rike da twins yana mata wani irin kallo yace "yunwa suke ji dear," ta karbi Hussaini a hannunsa, ya taimaka mata ta hada masu madara tana ba daya, shima yana ba daya. Wani sabuwar rayuwa me cike da tsan tsan so da kaunar juna suka bude a gidan, Aliyu ya xama kmr bawanta gashi bae kaunar yaga ta bata rae nn da nn yake rikicewa, duk yamma sukan shiga garden da twins dinsu su xauna, yana karanto mata diary dinsa tun daga farko, wani guri tayi dariya wani gun kuma tayi kuka, wani kuma taji haushi, abun dae ba'a magana, tunda suka dawo gidan Aliyu bae taba nuna mata yana son kusantarta ba sbda tsoranta, duk da daurewa kawae yake don mugun sha'awarta ke dawainiya da shi. Ko kadan ba ita ke wahala da yaran ba komai shi ke masu, nono kadae ne tsakaninta dasu duk da tasan ba dorewa hkn xae yi ba don dole xae fara aiki, satinsu hudu a gidan ita dae bata ji yyi mata maganar safeena ba kuma bata ganta ba, kasa daurewa tayi suna xaune da daddare ranar ta tambayesa safeena, ba tare da ya kalleta ba yace "Hajiya tasa na bata takardarta," inteesar bata ce komai ba taci gaba da kallonta, karfe sha daya ya dauki twins da suke kira da Sudais da Shuraim, yaje ya kwantar dasu snn ya sauko falo ya xauna gefenta yana kallonta a hankali yace "na lura wahala kawae kike bani a gidan nn inteesar," ta juya ta hararesa tace "ta yaya nake baka wahala," ya dagata sama yace "bari in nuna maki," kan tace komai ya haura da ita sama ya bude dakinsa ya shiga ya kwantar da ita kan gado yana kallonta yana murmushi yace "yau xamuyi 1st nyt dinmu bbyna, Jst assume it to b so. Inteesar ta mike xaune da sauri tace "A'a ni bana sooo" bae ce mata komai ba ya juya ya fita ta bi sa da kallo jikinta yyi sanyi, a nata tunanin ransa ne ya baci, ta dde xaune har lkcn idonta na kan kofa snn ta mike ta shiga bayi a xuciyarta tace ita xata bi sa, wanka ta kuma yi ta wanke bakinta, ta fito ta xauna gaban madubi daure da towel ta gama shafe shafenta na turarrukan da inna da Anty Nafeesa suka bata snn ta ciro wani kayan bacci pink colour mara nauyi mai hannun singlet iya cinya ta saka ta daure gashinta da ribon, tayi still tana kallon kanta gaban madubi tayi kyau ssae komai na jikinta a bayyane yake sae taji kunya ya kamata ta girgixa kai, aa baxata iya fita hka ba, ta bude drawer ta fito da da wani kayan baccin tana kallo ta ji an bude kofa ta juya da sauri tare da sakin kayan hannunta don sae da taji tsoro, singlet ne da short nicker jikinsa yana rike da bakar leda da plate, ya wara dara daran idonsa yace "kai amma amaryar nn tawa bata da kunya" inteesar ta juya da sauri ta durkushe wajen ya karaso gabanta yana mata wani irin kallo ya dagota yana kare mata kallo kunya ya rufeta ta kasa kallonsa yana rike da ita suka dawo tsakiyar dakin ya xaunar da ita kusa da gado yana kallonta snn ya mike ya bude drawer dinta ta bisa da kallo mayafi ya fito da pink colour ya dawo gabanta ya durkusa ya lullubeta da shi har fuskarta, snn ya xauna yana murmushi murya can kasa yace "Assalamu alaikum ma'abociyar kyau da hkuri," bata ce komai ba sae kallonsa take ta cikin mayafi duk jikinta yyi sanyi, a hankali yace "baki amsa sallamata ba cweet wife," a hankali ta amsa masa, yyi murmushi, ya dan bude mayafin yana kallon fuskarta ta sunkuyar da kai da sauri ta kauda kanta, ledar ya bude ya ciro kaxa da hollandia yoghurt ya mike ya dauko cups ya xuba masu drink din ya bude kazar yana kallonta yace "bismillah amaryata," bata ce komai ba ya matso kusa da ita ya daga mayafin ya daura kanta snn ya shiga bata naman, bata yi masu ba ta karba, yasa taci naman ssae shima yaci snn ya dauki drink din ya kai mata baki ta bude a hankali ya shiga bata har sae da ta kauda kanta tace ya isheta snn ya sha nashi, matsar da ledan kaxar yyi da drinks ya dago ta ya xaunar da ita kan gado ya durkusa gabanta a hankali yace "kada Allah ya nuna min ranar da xan bata maki rae ko nayi maki ba dai dai ba inteesar," bata ce komai ba ya mike ya duka dab da fuskarta ta dauke kafafuwarta daga kasa ta daura kan gadon snn ta koma can tsakiyar gadon ta xauna har lkcn mayafi na jikinta, yyi murmushi ya kashe wutan dakin ya hau gadon shima ya xauna kusa da ita yana kallonta kanta a kasa, a hankali ya cire mayafin jikinta ya ajiye ya tsura mata ido ta rufe fuskarta da tafin hannunta, ya jawota jikinsa a hankali yace "i love yhu my inteesar," ta kasa cewa komai ya kwantar da ita a hankali ya shiga yi mata rada a kunne, "kiyi min kuka bbyna, kice min baki so kina tsoro bbyna, ki rikice min bbyna, kisa na rude naji tausayinki amma na kasa kyaleki nayi ta rokanki har na kai ma cimma burina bbyna, i just want 2 imagine yau na fara saninki xan dauki wnn moment din kmr daren farkon mu bbyna, don Allah ki bani hadin kai" bae jira tace komai ba shiga kissin dinta nn da nn jikinta ya dau rawa kmr sabon shiga, bae damu ba don dama hka yake so, ranar taga ta kanta a hannun Aliyu, bae sarara mata ba sae da yaga ta fara kukan gske don ta gaji, duk ya rikice mata ya kankameta yana lallashinta ynda kasan amaryar gske, yyi ta sa mata albarka, ko kulasa bata yi ba taja bargo abunta don bacci take ji, ya mike ya shiga bayi kan ya fito har ta fara bacci ya dagota yana kallon kyakkyawan fuskarta ta bude ido a hankali tana kallonsa yace "kar kiyi bacci bbyna bari na gasa maki jikinki xaki fi jin ddin baccinki," ta galla masa harara tace "ca nayi maka bani da lfya," ya kashe mata ido yace "to nasani ko na ji maki ciwo ne naji kina ta ihu kina kiran inna," sae abun ya bata dariya tace "kaji ka da sharri, ko dae kai ne ke ta ihu ni tsoro ma ka bni," ta fashe da dariya, yyi murmushi yana gyada kai yace "yyi maki kyau, amma ynxu tashi nayi maki wanka kafin kiyi bacci," ta juya tace "ni ka kyaleni ba ynxu xanyi wanka ba bacci nake ji," yace "idan yara suka tashi anjima kiyi ya dasu," ta juya tana kallonsa da mamaki tace "abincin su xan basu mana," ya girgixa kai yace "baxa ki taba min yara da janaba a jikin ki ba," bae jira me xata ce ba ya kinkimeta sae cikin bayi, ya sakata ciki ruwan xafi, ta dan yi ihu a tsorace tace "meye hka ya Aliyu," ya kashe mata ido yace "kin manta ke amarya ce gasa ki xanyi," dariya abun ya bata, ranar a tare suka yi wankan taki bude idonta don mugun kunyarsa take ji, ya daura towel snn ya nadeta da wani towel din ya fita da ita suka xauna gefen gado ya rungume abarsa a hankali yace "i promise 2 love yhu 4 ever my inteesar," kasa ce masa komai tayi kanta na kirjinsa. Bayan shekara biyu inteesar ce tsaye kitchen tana girka ma su Sudais indomie wajajen karfe tara, Aliyu na sama da yake ranar lahadi ce, twins kuwa na balcony suna build din castle da bricks din wasan su sae surutu suke da turanci duk sun cika gidan da hayaniya, yaran sun girma ssae kyawawa dasu kmr yaran larabawa komai nasu abun sha'awa ne, gasu da shegen wayo kmr ba yaran shekara uku ba, daurewa kawae inteesar take don tana dauke da karamin cikin da take ta boye ma Aliyu, shi kam kallonta kawae yake sae ma take basa dariya bata san ya riga ta sanin abunsa ba, tsit taji bata sake jin hayaniyarsu a balconyn ba, ta danyi murmushi ta leko falo don tasan baxae wuce Aliyu ne ya sauko suka yi shiru ba don baya toleratin noise makin dinsu discipline dinsu yake ssae,, bata ga Aliyu a idan tayi tunanin xata gansa ba wato bakin kofar falo, don hka ta karasa balconyn da sauri taga ko sun fita xuwa garden ne, safeena ta gani durkushe gabansu tana kallonsu su ma sun yi shiru suna kallonta, Sudais yace "yhu re interruptin our play" Safeena tayi murmushi a sanyaye tace "am srry neva meant 2, where is yhur mom?" Shuraim ya juya da sauri xae je kiranta ya ci karo da ita bakin kofa, yace "Anty we have a stranger in here," Safeena ta mike tsaye tana kallon inteesar a hankali tace "ina kwana," inteesar ta kasa cewa komai ta dauke kanta gabanta na faduwa, hawaye taji ya cika idonta ganin ynda Safeena ta koma kmr ba ita ba, daga bayan ta taji Aliyu nacewa "bbyna baki gama hada kayan ba fa, ko kin gaji ne," shiru yyi sakamakon safeena da ya gani tsaye, yace "wacece wnn kuma bby," don har ga Allah bae ganeta ba, a hankali safeenar tace "safeena ce Aliyu," Aliyu ya hade rae yace "wat, me ya kawo ki nn," ta goge hawayen dake bin kuncinta tace "kayi hkuri gun Inteesar da yara na xo," ya daka mata wani mugun tsawa ya shiga kwala ma mai gadi kira, da sauri inteesar ta juya tana kallonsa tace "A'a Dear" wani mugun kallo yyi mata yace "kwashe min yarana ku wuce ciki," inteesar bata tanka sa ba ta karasa waje tana kallon safeena tace "mu shiga," safeena ta dan yi murmushi ta bita suka shiga falon, ya kwashe yaransa suka wuce sama ya bar su nn falo, ruwa da lemo ta kawo mata, tasha ruwa kawae snn tace "naxo ne na nemi gafaranki Inteesar kiyi hkuri ki yafe min ko Allah xae sa na dace a rayuwa," a hankali inteesar tace "ni bakiyi min komai ba Anty," safeena ta mike tana goge hawayen dake bin kuncinta tace "to shknn ngd Inteesar xan tafi, amma ki taya ni rokan Aliyu shima ya samu guri a xuciyarsa ya yafe min, nasan hakkinku ne ke bibiyata da uwata don ummata na can kwance yau fiye da shekara daya knn tana fama da ciwon shanyewar barin jiki," inteesar ta kasa cewa komai sae hawaye, safeena ta dada yi mata godya tana hawaye ta juya tace xata tafi, da kyar inteesar tace ta jira ta, snn ta haura sama, yana xaune Sudais da Shuraim na kasa gabansa da Al-qurani, suna karanto masa suratul Naba'a gwanin sha'awa, inteesar ta karasa kusa da shi ta xauna jikinta a sanyaye ta kwantar da kanta kan nasa tace "Dear don Allah kayi min favour daya," ba tare da ya kalleta ba yace na me? Ta dan yi shiru snn tace "ka samu safeenah kace ka yafe mata snn don Allah badan ni ba ka dan bata wani abu tunda Allah ya hore maka kaga halin da take ciki," juyawa yyi ransa a bace da shirin yi mata masifa yaga hawaye a fuskarta ko kadan baya son ganin hawayen inteesar ya rungumeta a rikice yace "kuka kuma bbyna me nayi maki, shknn shknn, ba sae kinyi kuka ba, naji kome kika ce nayi shi xanyi bbyna," ya mike ya dauko check ya rubuta million daya, ya mika mata, yace gashi ki kai mata, ta girgixa masa kai tace, aa ka bata da kanka kace ka yafe mata, kasa ce mata komai yyi daga karshe yace yaji suka fita a tare tana rike dasu sudais, sudais ya mika ma ya ya kai mata, snn yace "Allah ya yafe mana ga baki daya," durkusawa tayi ta karbi abinda sudais ke mika mata tayi murmushi hawaye na bin kuncinta tace "ngd inteesar Allah ya raya maku yaranku ya albarkacesu, ya kuma sa mu cika da imani," ta mike ba tare da ta kallesu ba ta fita daga gidan, kuka ssae inteesar ke yi Aliyu ya kama hannunta suka wuce sama, da kyar ya lallabata tayi shiru, snn ya taimaka mata suka gama shirya kayansu don ranar da yamma xasu koma lagos, karfe goma suka shirya gaba daya da yaran xasu je gida suyi masu sallama, suna shiga gidan Sudais da Shuraim suka yi bangaren inna da gudu suna rige rige suna kwala mata kira "old woman, old woman, we re here" don hka suke kiranta kmr ynda Aliyu yace masu wae sunanta knn old woman, Aliyu ya juya yana kallon inteesar yyi dariya yace "ko dae mu tafi da old woman din nn lgs ne," da sauri inteesar tace "don Allah yayana," yyi dariya ssae yace "ba ruwana taje ta hade da tsofaffin yarbawa halinta yafi hka mu shiga uku," inteesar ta hade rae tace "to a ina xa ta gansu," yana dariya yace "masallaci mana idan tace xa ta tunda bata rabo da xuwa," bae jira me xata ce ba ya kama hannunta suka yi bangaren momy suje su gaisheta ____Inteesar____2*19 . Khaleesat Haiydar . ... Sun dde xaune falon momy, don umma da Hajiya ma na ciki, suna ta lissafin abubuwan da xa a siya don bikin su Khadija da Rahma ya kusa, Kursum kam tayi aure watanni shidda da suka wuce tareaka yi da na Haisam da Maryam din Anty Nafeesa, baka taba cewa abu ya taba hada su Hajiya da momy a baya, ynxu kowa ya rike girmansa bbu abinda ke tsakaninsu sae mutunta juna da kyautata ma juna, gidan Baba Bukar ya xama abun sha'awa, har lkcn momy bata wani sake da Aliyu ba duk da harga Allah komai ya wuce a wajenta kawae dae ta kasa sakewa dashi ne kmr ynda tayi da Haisam, karfe sha daya inteesar da Aliyu suka yi bangaren inna don Abba baya nn ya tafi daurin aure, yana rike da hannunta, ta jingina jikinsa suna tafiya tace"yayana kace xanje gun Abbana kafin karshen shekaran nn fa ina missin dinsa wllh," Aliyu yace "kar ki damu xaki je kanwata," bata sake ce masa komai ba har suka isa falon inna,tana xaune ilham din Zainab na kusa da ita sae jarabata take mata yarinyar kyakkyawa fara kmr babanta sae kallonta take, inteesar ta rungumeta tace "ilee bby ina mamarki," inna tace"ae ni ta fita ta bar ni da jaraba sae kuka take min kmr ina yaga namanta shegiya mummunan yarinya kawae," Inteesar tayi dariya tace "sae dae kece mummuna inna, kiga yarinya kyakkyawa kice mata mummuna," inteesar ta gaisheta ta xauna, inna tace "lahhh ha ila, ynxu wani cikin kika bari ya kuma maki inteesar bayan ga wa innan jarababbun yara kmr beraye masu xagin mutane da wani shegen yare can baki gama dasu ba, ya xakiyi da wnn wahala" Aliyu yyi dariya yana kallon inna yace "na isa ne shiyasa nayi mata wani cikin, ina boyz dina?" inna tace "ina xan iya jaraban gantalallun yaran nnna koresu wllh, saura kadan wnn me rabgajejen bakin ya karyani" inteesar ta dinga dariya Aliyu yace "lallai yaran nawa kika kora inna su da gidansu," bae jira me xata ce ba ya fita ya gansu suna tahowa da Haisam shima da alamar shigowarsa gidan knn, da gudu suka karaso suna kallonsa suka ce "daddy where have yhu bein we've bein lookn 4 yhu since, dat old woman is so mean she sent us out," dariya Haisam ya dinga yi Aliyu ya kama hannunsu yana dariya suka shiga falon yace"jump on her nd fight her," da gudu suka yi tsalle suka haye kanta suna mata busha busha, ta dinga ihu tana cewa "don ubanku ku sauka kaina kar ku karya ni jarababbun yara," Aliyu ya xauna gefenta yace "ae sae sun karya ki yau xamu bar gidan nn, ni da nake cewa xan bar maki su a hka xan barsu kina xagan min yara kina koransu" da sauri inna tace "lah wllh baxan sake ba don Allah ka bar min su Aliyu," Aliyu yyi dariya yace "na bar maki yarana ki lalata su kmr ynda kika lalatani, kodayake ma ina kika ga karfin rikesu bare ki lalata su" inna ta marairaice fuska tace "wllh baxan lalatasu ba Aliyu kai ma tsautayi ne yasa ka lalace don Allah ka bani su," dariya inteesar ke yi tana cewa "ni dae ya Aliyu don Allah ka dauke su kar su karya min inna ta," Aliyu ya jawota ta fado kansa, ya rungumeta, ya rungume inna da dayan hannunsa ya ciro wayarsa yace "inna yi dariya mu dauki hoto," inna ta washe baki ta rungumo su sudais dake dariyan su ma ya kashe masu hoto gaba daya, Haisam dake tsaye bakin kofa yana dariya yace "bari na dauke ku da kyau," ya karbi wayar ya shiga daukansu hotuna gaba dayansu har da ilham din Faruuq, inna sae kyalkyale dariya take rungume da jikokinta da tattaba kunne sae cewa take "Allah yyi maku Albarka," Hmmmm INTEEESAAR. Tammat bi hamdillah . Jinjina ta musamman ga marubuciyar wannan littafi . Khaleesat haidar . Allah ya Kara basira da daukaka . Amadadin ni kaina da kuma sauran admins dinmu muna Mika muku sakon gaisuwa dakuma jinjina bisa goyon baya dakuma karfafa guiwa da muke samu daga wajenku . Naso ace Na ambaci sunanenku gaba daya amma hakan bazai yiwuba domin kuwa yawanku yakai yawa sosai Muna godiya ga dukkaninku baki daya . Alhamdulilah. Naji dadin gama wanna aikin da kibani . By Sabiu Adam bena *************************⬇********************** ************* Top Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.thn.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > tophausanovels@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Top Hausa Novels Twitter: Top Hausa Novels Telegram: Top Hausa Novels Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod ********************** ⬇ ************************** *************** Top Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************